*BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F* *Bismillahi Rahamanir Raheem* *Page 1* Wai saurin me kake yi ne haka"? Wayar sa ya Kara duba wa tare da Kara sauri Yana "Jirana ake fa karki damu yanzu zan dawo bazan dade ba yace tare da yin waje da sauri. Da ido na bishi har ya fice daga gidan naji karar tashin lifan dinsa. Tagumi nayi tare da bin kulolin da na ajiye a tsakiyar kafet din palon da ido,abincin daren dana dau tsawon lokaci ina yinsa duk sabida na faranta Masa duk da cikin dake jikina ina jin yunwa haka na hakura da cin abincin sabida idan ya dawo muci tare kamar yanda Muka Saba sai gashi daga dawowar sa ya sake wanka ya fice daga gidan da Sunan kawunsa na neman sa. Kwana biyu kenan Yana min haka. Haka na zauna raina a b'ace Ina tsaki kasa kasa ganin idan na cigaba da zama a haka batare da naci abincin ba zan cutar da kaina da abinda ke cikina yasa na zuba abincin na fara ci. Ban wani ci da yawa ba na rufe sauran na jawo wayata na fara chatting abinda kawai zai rage min kadaici da takaicin fitar da mahfuz yayi ya barni ni kadai a gida kamar Mayya. Mahfuz bai dawo ba sai wajen goma na dare zuwa wanan lokacin Raina ya Kai kololuwa wajen b'aci kafa kawai nake girgiza wa Koda ya shigo da sallama ciki ciki na amsa mishi,ya saki murmushi Yana "Afuwan tawan wlh wani waje na raka kawu bansan zamu dade haka ba kiyi hakuri kinji matata" Bansan Mai yasa bana iya dogon fushi da mahfuz ba Yana min murmushi da yar murya zanji na sauko. Ledar daya shigo da ita ya bud'e Yana "Kinga kayan kwadayin dana taho Miki dashi A binka da mai ciki da sauri na wafci ledar ganin alewar Madara da gulisuwa yasa na washe baki dan duk wani Abu Mai Madara da siga Ina so. Sai da na fara Shan alewar Madarar na kalli mahfuz da ya zauna a kasan kafet Yana Danna wayarsa "Baza ka ci abincin bane?" "Wlh kawu ya tilasta min cin abinci a gidansa sai dai gobe ki dumama min kafin na fita" "Yanzu ko cokali daya bazaka yi ba sabida Kai na girka fa" "Ai nace Miki gobe sai kimin dumame wlh yanzu a koshe nake" Badan raina naso ba na cigaba da Shan alewar Madarata shi kuma ya mike kafarsa da hannu bibiyu Yana latsa wayarsa har da dan murmushinsa. Ido na zuba Masa Ina tunanin canjawar da yayi a kwanakin nan,Mahfuz mutum ne da bai wani damu da chatting ba dan sau tari ni nake tilasta Masa yin chatting sabida Ina tura Masa sakwanin ta watsapp,ada idan ya dawo gida ko waiwayar wayarsa baya Kara yi sai dai yayi ta jana da hira Yana bani labarai idan yaga na dauko wayata sai ya kwace yace a hakura da danna wayar nan azo a ji da ni amma a kwanakin nan har da asuba Zan ga Yana latsa wayarsa ban taba zarginsa ba bana Jin Zan Kuma zarge idan na tuna San da muke yiwa juna,ba Kuma mu dade da yin auren ba tunda yanzu shekara biyu da auren mu a yanzu Allah ya azurtani da samun ciki "Wai Mai kake yi a wayar kake ta murmushi haka"? Dagowa yayi da sauri Yana "Da Abdul muke hira fa sai dariya yake bani kinsan halinsa da barkwanci" Murmushi nayi nima Ina "Gwauro ba har yanzu sai ruwan ido yake ya kasa tsayar da budurwar balle mu sha biki" Yana chatting muna hira har zuwa sha daya da rabi na dare kafin mu tafi daki mu kwanta. Fitsarin da nake ji ne ya farkar dani sai da na wartsake na mike zaune ga mamakina mahfuz baya d'akin har Kara shafawa nayi Naga ko dai lumewa yayi a bargon da muka lulluba sai dai bargone kawai baya d'akin. Kasa kunnena nayi naji ko dai Yana bandakin a daidai lokacin da na daga kaina Ina kallon agogo d'akin karfe biyu da minti goma Sha biyar na dare. Mik'ewa nayi a hankali Ina mamakin Inda Mahmud yayi dan nasan baya bandaki tunda banji motsi ba. Sai dana kunna fitilar d'akin na nufi wajen k'ofar dakin da aka dan bud'e idan har zan tab'a k'ofar ba abinda zai hana yayi Kara daga d'akin Ina Jin maganarsa hakane yasa nake so naji mai yake cewa zuciyata fal da mamaki da wa Mahfuz yake magana a tsakar daren nan ya baroni a daki ni kadai. A hankali na samu na fito daga d'akin batare da na bari kofar tayi Kara ba, cikin sand'a na fito na nufi palon da yake akwai siririn corridor kafin a iso palon. Hasken wayarsa kawai nake hango wa yayi rub da ciki fitilar palon a kashe. "Nifa bana ganinki sosai wai me hakane"? Abinda ya sauka a kunnena kenan daya bala'in fadar min da gaba har sai dana dafe cikin jikina sabida motsawar da yayi. Ban motsa ba na tsaya Ina cigaba da Jin hirarsa da macen da nake Jin saukar muryarta a kunnena. "Bana so na kunna haske na tashi Ameera fa Wai yanzu baka ganina" "Rowa kawai zaki min Kisani mafarki a banza" Dariya macen ta kyalkyale dashi Yana shirin magana bansan rike numfashina nayi ba Ina sakin numfashin yayi jifa da wayar da sauri Yana "Lubna" Duk da jikina balain rawa yake Ina hada gumi bansan ya akayi nayi jarumtaka wajen daidaita kaina Ina "Farkawa nayi zanyi fitsari da ban ganka a d'aki ba shine na fito" "Ooo e'e'e motsi naji a waje shine na fito naga waye har waje na fita ma" Yace Yana in'ina ya sunkuya dan ya dauki wayarsa na juya jikina na cigaba da rawa nabi bango na koma d'akin Yana daga bayana Yana fadin Yana tunanin barayi sun adabi unguwar bance Masa komai ba na kwanta tare da Jan bargo dan har wani zazzabi naji Yana neman rufeni. Yana kwanciya a gefena ya fara k'ok'arin jawoni idan har na hana shi rungumeni zai zargi naji maganar da yake yi da mace. Halin da nake ciki yasa ban iya jure rungumar da yamin ba dan gani nake kamar ya manna min garwashin wuta na janye jikina banaso nayi magana sabida Zan iya fallasa halin da nake ciki bana so nayi abinda zanzo Ina nadama inaso na samu nutsuwa nayi tunani Mai kyau. Koda na janye jikina bai Kara jawo ni ba yace tom yau bbyn bayaso a tabaki kenan ya juyamin baya tare da Jan bargo saman kansa. Ido na zubawa bayansa Ina Jin tashin maganarsa a kunnena nifa bana ganinki sosai wai me hakane Rowa kawai zakimin kisani mafarki a banza. Da wa Mahfuz ke video call da tsakar daren nan har ya barni a daki ya tafi palo wacce ce ita,har yaushe Muka yi Aure da mahfuz zai fara kula Yan Mata,Anya ma mahfuz dina ne wanan ko dai mafarki nake yi na mitsini kaina wai dan na tabbatar da ba mafarki nake ba. Zuciyata wani irin zafi yake min na tsananin kishi mahfuz dama Yana da budurwa duk soyayyar Nan da yake min dama zai iya kula wata, mahfuz makota ma sun shaida irin kaunar da yake min. Soyayya mai tsafta muka yi a shekara uku da muka hadu dashi,naje banki zan bude acct shi kuma anan yake aiki,tun ban dauki soyayyarsa da wani mahimmanci ba har sai da ya samu matsuguni a zuciyata,ba Wanda baisani dashi ba a cikin dangina haka ma danginsa,kawayena Kan roki Allah ya basu irin Mahfuz sabida yanda baya iya b'oye san da yake min a gaban kowa, nida kawayena mun Sha hada Kai mu siyi layi dan mu gwada shi,Yana Jin muryar mace zai kashe dan kafin muyi aure Ina balain saka kaina a matan da suka yi sa'a da dace samun nagartace kamar mahfuz ban fuskanci wani matsala ba har mukayi aure zan Kuma iya shaidarsa dan ba abinda yake boye min,a gurin mahaifiyarsa Hajiya Ammi kawai nake ganin ban wani samu karbuwa ba duk da da yawa ance haka take bata fiye sakarwa sirikanta fuska ba,da na auri Mahfuz sai na fuskanci idan kina so ta sakar Miki fuska ki bata abin duniya a ranar zata sakar Miki fuska na Kuma ji halayenta a wajen matar yayyen mahfuz Inda Suka ce Kar na sake duk wani abu da zai hadani da Mahfuz nace Zan Kai kararsa wajen mahaifiyarsa tsana zan janyowa kaina dan bata san laifin yayanta ko kad'an. Daga aurena da mahfuz zuwa yanzu ban wani fuskanci matsala ba duk da kyautata min da yake Yi a waje da bambanci a yanzu da muka yi aure, dama can ba soyayar kudi muka yi ba shiyasa Koda muka yi aure ba wani kudi yake bani ba nima ban damu ba bansani ba ko dan ban Dade bane Zan bukaci kudi a gaba kayan abinci dan abinda bazaa rasa ba ban Kuma damu ba. Zuciyata suya kawai take bacci ya kauracewa idona zuciyata nata sak'a min na tashe shi na tambaye shi da wa yake waya,wata zuciya.kuma na hanani akan nabi komai a hankali. Kiran sallah asuba a kunnena dama Ina rigashi tashi sallah ni nake tashinsa.Haushinsa da nakeji yasa ban tashe shi ba naje.na daura alwala inaga motsin rufe k'ofar bandakin ne ya tashe shi.Koda ya mike Yana Hamma yace "Da ban tashi ba,bazaki tasheni ba kenan"?Ban ma iya bashi amsa ba bama naso nayi magana dan wani abu ne ya tokareni a mak'oshi. Banida burin daya wuce ya tafi massallaci na dan bincike wayarsa dan na tabbatar da zargina.Sai dai yana fitowa daga bandaki ya zura wayarsa a jallabiyarsa yayi ficewarsa.Zuwa yanzu zargin mahfuz nada budurwa ya tabbata dan a kwanakin nan yafara haka,amma baya fita da wayarsa har password dinsa nasani dan sunana ne.Ina zaune ne kawai akan sallaya zuciyata fal da tunanin da mamakin mahfuz dana d'auko so da yarda na dora masa. Mahfuz ba mutum bane da idan yaje massallaci Yake dadewa sai gashi har gari ya fara haske bai dawo gidan ba.Tuni wani irin kishi ya turnike ni jikina har rawa Yake.Har zan fita waje na koma dakina na dauki wayata tare da bin umarnin zuciya ta akan na gwada Kiran wayarsa naji ko dai wayar yake.Ina kuwa kira ya nuna call waiting Wanda hakan ya kara saka kirjina nauyi sabida kishi ban hakura ba na cigaba da kira dan idan har ya daukeni da mahimmaci ya Kamata ace ya dauki wayata tunda nasan dole zai ga kirana sai dai bai dauka ba nima ban fasa Kira ba nasan bazai wuce layin unguwar ba dan gida uku ne tsakanin mu da massallaci da hijabin jikina na fita waje wayata Kare a kunne na a dakalin gidan makociyata na hangoshi a zaune.Yana ganina ya katse wayar tare da mik'ewa tsananin bacin rai yasa tun kafin ya iso nace "Mahfuz da wa kake waya"?Murmushi ya sakar min Yana da Abdul nake waya ManaKatse shi nayi a dan tsawace Ina "Wlh karyane Mahfuz da mace kake waya bada Abdul kake waya ba""Ni nake miki karyar"?Yace Yana nuna kirjinsa fuskarsa ta sauya daga murmushi zuwa bacin rai"Ai nasan karyar ne mahfuz dan idan da Abdul zaka yi waya bazaka fito waje kayi wayar ba, jiya ai naji duk hirar da kake yi da budurwar ko zaka rantse ba da budurwa kake wayar ba,Mahfuz wacece ita?dudu yaushe muka yi aure da har wata zata fara d'auke maka hankali jiya har ka barni a daki ka fito Palo Kuna video call har kana ce wa zata saka kayi mafarki a banza"?Dogon tsaki yaja ya ratsa ta gefena ya Shige ciki na juya da sauri raina na balain suya daki ya nufa nabi bayansa Ina cigaba da tambayar sa da wa yake waya amma ko kallona baiyi.Takaici yasa na fashe da kuka Ina "Mahfuz wacece ita mai na maka da zaka sakamin da cin Amana"?Banza ya bawa ajiya ta abinda bai tab'a min ba ya d'auko wayarsa ya fara lalatsawa kamar ba dashi nake magana ba,tun auren mu bamu taba hayaniya dashi ba,bamu taba dogon fada dashi ba,Mahfuz da nasani Ina d'an b'ata rai zai hau rarrashina Yana bani hakuri sai gashi yanzu kuka nake a gabansa amma ko kulani baiyi baYanda ya watsar dani ya bawa banza ajiyata yasa na fusge wayar daga hannunsa a zuciye ya dago da idonsa da suka dan rine sabida b'acin rai ya mik'omin hannu Yana "Bani wayata Lubna kafin na sassab'a miki""Bazan bayar ba Mahfuz har sai ka Gaya min da wacce Yar iskar kake waya"Mik'ewa yayi Yana k'ok'arin Magana naji wayar sa na vibrating a hannuna da alama ya cire ringing tone din a vibrating yasa.Da sauri na juyo da wayar naga SR ke kira a waya a cikin Sakani na dauki wayar na Kara a kunnena yayo kaina da balain sauri a daidai lokacin dana ji muryar budurwar da bazan tab'a mantawa ba a rayuwata wacce ta watsa min farincikina ta kusa zautar dani."Sugar lafiya kuwa naji ka katse wayar"Maganar daya fito a bakinta kenan "Allah ya tsine Miki shegiya kwartuwa" Ihu na saka sakamakon murd'emin hannu da yayi ya fusge wayar a hannuna Yana "Ke wacce irin wawiya ce mara hankali kinsan wacce kike zaginta"?"Nice wawiya mara hankali sabida na zagi budurwar ka mahfuz"?Nace Ina nuna kaina hawaye mai zafi ya hau zubomin yaja dogon tsaki ya nufi wajen wadrobe din kayansa ya fito da kanan kaya hawaye kawai nake Ina kallonsa har ya gama canza kayan jikinsa ko kallona baiyi ba ya fice daga d'akin.Rawar da jikina keyi yasa na zube akan gwiwa ta na cigaba da kuka Ina tunanin ko dai mahfuz ba'a hayyacinsa yake ba har wani dumm na ringa ji a kunnena dana tuna sunan da Yar iskar ta Kira mahfuz dashi Sugar.... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 2* Bansan tsawon lokacin dana d'auka a durk'ushe a kasa ba,zuciyata Kamar an cinna Mata wuta ban tab'a sanin haka nake da tsananin kishi ba kawai Ina hararo irin so da kaunar da mahfuz yake gwadamin ya fara gwada wa wata,har ta d'auke Masa hankali a kaina akanta ya cemin wawiya Mara hankali waya sani ma ko zance yake zuwa wajen tsininiyar yarinya da ta Kira mahfuz da sugar,har san da yake Mata ya Kai Muna kwance ya baroni a daki ya fito Palo dan kawai yayi waya da ita. Ko dan na samu ciki hallitar jikina ya canza yasa mahfuz ya fara ganin munina Tunanin daya darsu a raina yasa na m'ike a hankali na nufi wajen da mudubi yake na fara karewa kaina kallo tunda ga saman goshina tare da shafa fuskata. Tunda na samu ciki wani irin kananan pimples suka feso a fuska ta suka Sakani Muni,siririn lebbena yayi kauri.Haka hancina da bai fiye tsini ba ya doke nasan cikin nan yasani muni ba kadan ba fari dai na Kara tunda ni fara ce.Baza'a sakani a sahun masu tsayi da kyau sosai ba akan dai mahfuz za'a sakani a sahun masu kyau duk da mace sai ta dan yi kwalliya kyaunta ke Kara fitowa.Kwalliya da nake yi yasa ake ganin kyauna sosai. mutum tara yake bai cika goma ba abinda na rasa shine nono banida cikar kirji Sam idan na ga mace mai kirji sai naji Kamar na sace ko dan mahfuz da sai da muka yi aure na fahimci Yana balain san no-no,kafin na samu ciki indai Muna zaune hannunsa na saman kirjina Yana shafawa wai idan ana yawan shafa shi Yana fitowa.Bansan Yana san nono ba sai da naga ya fara siyomin duk wani cream ko supplement akan na ringa Sha zai taimaka wajen fitomin da nono.Ba abinda banyi amfani dashi dan nono ya girma ko dan na farantawa mahfuz rai amma abin ya gagara daya ga na fara matsawa kaina ya ce min na daina takura kaina duk da haka burina na samu nono na ya girma idan na d'auke nonon ba wani abu a jikina da baya burge mahfuz.Idan ya dawo bashida wajen kwanciya sai a jikina ya gwadamin kaunar daya narkar dani a kogin Sansa burina bai wuce nayi abinda zan faranta Masa ba Koda bana so har na samu ciki banga canji a wajensa ba duk da mitar da nake akan cikin ya sani muni hakan na iya sawa mahfuz ya rage ji dani.Idan na ce masa nayi muni dariya yakemin yace shi bai gani ba ai cikin nan yasa kirjina ya ciciko,bamu tab'a fushi da juna ba,bamu taba sa'insa ba,bai tab'a gaya min bak'ar magana ba sai gashi wata Yar iska tana neman juyar min da kwakwalwar miji bansan adadin tsinuwar da nayiwa macen da ta Kira shi ba.Gajiya nayi da tsayuwa agaban mudubin na koma Kan gado na kwanta Ina sak'e sak'en yanda zan biyowa mahfuz ni nasan idan ya dawo dole ya bani hakuri dan baya iya dogon fushi dani dole na nuna Masa bacin raina na Kuma jawo shi jikina na binciki wayarsa nayi blocking din Yar iskar yarinya da take kiransa,da Wanan tunanin na samu nayi wanka abincin ma da kyar naci sabida b'acin rai,sai duba wayata nake naga ko zai kirani ko zaimin text,har watsapp na hau naga ko ya ajiyemin sako duk shiru,hakan kuwa ya Kara saka min Jin haushinsa na tanadi masifar da zan Masa idan ya dawo.Kamar bazan yi girkin dare ba na daure na dafa jollof din shinkafa na hada Masa zobo.Nayi kwalliya kamar yanda na Saba na zauna zaman jiransa raina a had'e.Mahfuz bai dawo gidan ba sai goma da rabi na dare Ina Jin sa ya shigo da machine dinsa.Ciki ciki yayi sallamar ya hade rai da leda a hannunsa bai Kuma Kalli inda nake ba.Baki sake nabi shi da kallo har ya shige daki mamaki da bakin cikin halin ko inkular da ya nuna min ya rufeni,Mai mahfuz yake nufi dani yamin laifi ya nade tabarma da kunya a zuciye na tashi zan bishi har d'akin. Kafin na isa d'akin na tsaya Ina bin umarnin zuciyata dana watsar dashi zai nemeni da kansa. Da wanan tunanin na nufi daya d'akin da idan ba baki muka yi ba ba Mai kwana a ciki.Nan na shige zuciyata na balain tafasa Duk abinda nayi dan na samu zuciyata tayi sanyi duk a banza kofa kawai nake kallo ko zanga shigowarsa yazo bani hakuri ga yunwa da nakeji amma bana jin cin abincin. Watsapp na hau sabida na samu nayi hira da Yan uwana da muke grp daya ko zan samu na rage bakin ciki dake Raina sai dai Ina hawa na duba mahfuz naga Yana online,wato ba abinda ya dame shi ni nasan da Yar iskar yarinya yake hira.Ban iya hakuri ba na rubuta "Mahfuz yanzu nice abar wulakantawa a wajenka ko,"? Bai bud'e sakon da wuri ba na fara k'ok'arin Kara rubutu naga ya bude ya turo "hmmmmm" Bakin cikin bazai iya bani hakuri ko ya biyoni daki ba yasa na kashe data na wurgar da wayar,Idona akan agogo har karfe daya na dare sai juyi nake ba alamar bacci zai daukeni sai tunani daya cike min zuciya tunda mukayi Aure bamu taba raba shimfida da mahfuz ba sai gashi a sanadin haduwa da wata nayi fushi dashi bai ma kalleni ba. Hawaye kawai ke zubomin Ina tsinewa macen da ke san Shiga tsakanina da mahfuz har ta samu matsayi haka a wajen mahfuz da zai k'i nemana a kanta sai da cikina ya tsufa mahfuz ya fara daga min kafa amma ko yayane sai ya nemeni ko period nake sai na Masa dabaru har hirar na tab'a yi da wata aminiyata take cemin namijin da baya iya daga ma kafa ba karamin gamsar dashi ake ba.Amma mahfuz yamin laifi akan Ina kishinsa bai iya bani hakuri ba,nifa yayi wa laifin nan amma shine ya kasa bani hakuri.Har tunani na Kara yi a tsanake dan naga ko dai zaginsa nayi cikin fushi batare da nasani ba sai dai banda karya tashi da nayi na zagi tsinaniyar da ta kira ban Masa komai ba.Zuciyata raya min kawai yake akan naje d'akin na sameshi wani b'ari na zuciyata na hanani akan shi yamin laifi shi ya Kamata ya nemeni.Haka na kwanta zuciyata kamar tayi bindiga dan bakin ciki sai biyu da wajen rabi na dare bacci yayi awon gaba dani. Ban tashi bude Idona ba sai wajen bakwai da minti goma Sha biyar.Na Mik'e da sauri Ina sallati na tsani naga sallah asuba ta kubcemin.Da balain sauri na fada bandakin na daura alwala na fito.Sai dai banida hijabi a dakin bana san zuwa dakina naga mahfuz sai dai ya zama dole tunda ba hijabi a d'akin.Fuskata a had'e na nufi dakina a hankali na tura k'ofar na shiga.Bangan shi a dakin ba na dai jiyo motsinsa a bandakin da alama wanka yake. A madadin na d'auko hijabi na wajen da na hango wayar sa a saman bedside drawer na nufa da sauri na dauki wayarsa na fita daga dakin na koma daya d'akin na saka key na zauna a saman gado hannuna sai rawa yake.Ko da na bud'e wayar ajiyar zuciya na sauke da naga ba password.Message dinsa na fara shiga SR da na gani ta turo message da bai bud'e ba yasa na bud'e message din jikina na balain rawa Message ta turo.masa wajen biyar na asuba da alama reply ta Masa "Kayi hakuri sugar banga kiranka ba sai yanzu kasan jiya ban kwanta da wuri ba how was your night my love zaka biyo d'in I missed you"Hannuna rawa kawai yake kirjina Kamar ya fado ji nake ma dakin na juya min"Lubna ki bud'e min k'ofar nan sabida Mai zaki zo ki dauki wayata?Wai me yake damunki ne"Najiyo mahfuz a bakin k'ofa Yana jijjiga k'ofar.Rawar da jikina keyi yasa ban ma iya mik'ewa ba na nemo lambar SR na fara kiranta a wayarsa bugu daya ta d'auka murya can kasa tace "Sugar ka iso ne"?"Kutumar bura ubanki tsinanniya ya iso wajen ubanki shegiya laananiya"Kit naji ta kashe wayar na Kara kiranta bata d'auka ba,ban hakura ba na cigaba da kiranta Mahfuz kuwa sai jijjiga kofa yake Yana kwalla min Kira akan nazo na bud'e k'ofar na bashi wayarsaGanin tak'i d'aukar wayata yasa na m'ike jikina na rawa naje na bud'e k'ofar mahfuz ya fado dakin da sauri ya fusge wayarsa daga hannuna idonsa ya Kada yayi jajjur cikin k'ak'ausar murya yace "Daga yau karki Kara tab'a min waya lubna wlh Kika Kara sai ranki ya b'aci kinji na fada miki"Ya fara k'ok'arin juyawa ya bar dakin na Sha gabansa da sauri hawaye na zubomin "mahfuz mai na maka da na cancanci haka daga wajen ?Mahfuz jiya baka san a ya na kwana ba amma ka kira wacce ba matarka ba dan kaji lafiyarta Kuma har zaka biya ka ganta kafin kaje wajen aiki, Mahfuz Kaine kamin laifi Ina gefenka ka fita Palo dan kayi waya da mace dan na tambayeka da wa kake waya ka rufeni da fada ka kirani wawiya mara hankali laifine dan nayi kishin ka har yaushe muka yi auren da zaka min haka?Ina duk alkawarikan da kayi min a baya Koda zaka kula mace mahfuz bazaka kwantar min da hankali ko dan cikin jikina ba? kayimin adalci kenan"? Na karashe hawaye na zubomin "Lubna kina da matsala shikenan dan kinji.ina waya da mace sai ta zama budurwa ta,kinsan ya muke da ita da zaki zageta ne?wajen aikinmu daya da ita kuma ba komai a tsakanina da ita sai Yar tsokana amma sabida balai kin dorawa kanki kishi,har kina Neman zagina,wane bayani kikeso na miki? Mamakin maganar sa ya sa na kasa motsawa na zuba Masa Ido har ni zai cewa ba budurwarsa bace shi kuwa ganin ban magana ba yace "ba wani abu a tsakanina da ita ke kikesan ki dorawa kanki abinda ba haka ba,abinda yasa jiya ban waiwayeki ba naji Haushin karyatani da kikayi bai dace na miki magana ki karyatani ba har kina neman zagina kina nufin baki yarda dani ba kenan,nidai zanje wajen aikii dan na makara daga haka ya ratsa ta gefena nabishi da ido har ya shige ko minti biyar baiyi ba ya fito daga d'akin ganin Ina hawaye Ina Kuma tsaye ban motsa ba ya iso wajen da nake tsaye yana "Kina nan a matsayin da Kika sanki a zuciyata ba Wanda ya Isa ya kwaceni a wajenki gwara ki kwantar da hankalinki daga haka ya sunkuyo yamin kiss a kumatu ya juya Yana "Sai na dawo" Lumshe idona nayi Dana shaki kamshin turarensa kukan da nake dannewa ya kwacemin har ga Allah ni nasan Mahfuz soyayya yake yi da wata amma yake San raina min hankali Ina balain San mijina dama yarinya nan ta barni da mijina ta nemo wani nayi nadama da ban dauki lambarta a wayarsa ba. Ban tab'a tunanin mahfuz zaimin haka ba A daddafe nayi Sallah na dumama abincin da mahfuz baici ba naci dan yunwa nakeji. Sai da na gyara ko'ina nayi wanka na zauna Ina tunanin hanyar da zan bi na raba mijina da SR dinan da take neman d'auke min hankalin Miji. Kiran aminiyata farinciki rayuwata abokiyar sirrina ce ta katse min tunanin da nake mahaifiyata banida wacce tafita duk duniyar nan ba abinda nake boye mata a haka na taso sabida yanda take jana a jikinta ba Kuma Ni kadai ba haka duk kannena,koda na tashi aure ajiye kunya tayi a gefe ta karantar dani rayuwar aure da yanda zan kula da mijina. Mahaifiyata a waye take dan nurse ce bama na iya boye mata komai. Ina sallama na hau gaisheta bata amsa ba tace "Mai yake damunki Lubna"? Kamar Mai jiran kiris na fashe mata da kuka. Sai da naci kuka na na koshi bata hanani ba ba ta kashe wayar ta ba Jin na tsagaita tace "Ina jinki lubna mai yake faruwa" Tiryan tiryan na kwashe komai na gaya mata ba abinda na cire har yanda mukayi da Sr din da bansan sunanta ba sai da na gama tsaf ta sauke ajiyar zuciya tana "Wlh bansan bakida wayo da tunani ba sai yau,Lubna waye ya gaya miki ana yiwa namiji haka,waye ya gaya miki ana fada da budurwa Miji a waje,salon ki jawowa kanki raini,daga lokacin da Kika d'auko wanan hanyar kin kashe kanki da kanki ai komai dan wayo ne da dabara wlh na raina wa wayon ki Lubna,ai kiyi fushi da mijinki ko kiyi gaba dashi dan kin gano Yana da budurwa ba shine mafita ba dan kin nisanta kanki daga wajensa ne kin kusanta shi da budurwar tasa dan su maza haka suke Abu kad'an ka d'auke musu hankali,daga lokacin da Kika fara wanan haukar fita zaki nayi a zuciyarsa ya fara ganin aibunki,waccen kuwa dama burinta ta samu ta kwace shi, karki sake wanan gangancin yanzu damara zaki daura ki jawo mijinki jikinki cikin kirsa ki rabashi da wancan yarinya cikin ruwan sanyi,ki rubanya kyautatawarki a gare shi. Ai ke mijinki ma Yana shakarki tunda a boye yake Mata waya kinsan akwai mazan da agaban matansu zasu yi wayar sai dai ta hadiyi zuciya ta mutu. Ki nesanta kanki da tab'a wayarsa ko da Kinga an turo masa text an Kira karki sake ki nuna Masa kingani cikin salo zaki rabashi da ita, kiringa kai zuciyarki nesa kishi hauka yake sawa da tarin nadama, kifita a zuciyarsa yaji ma gwara yayi auren kawai tunda kin k'i ki kwantar masa da hankali,ba dai text take tura masa ba kema sai ki dage wajen tura masa,Yana fita ki kirasa kiji lafiyarsa sau uku kafin ya dawo anan zaki ga hankalinsa ya fara rabuwa gida biyu har kiyi nasarar dauke masa hankali akan wacce yarinya ki fito da salo salo na soyayya da bai sanki dashi ba kiga ikon Allah" Sai da muka shafe awa daya mahaifiyata na bani shawara na Kuma ji dadin shawarawarin da ta bani duk da ba k'aramin dauriya zanyi ba dan Ina da tsananin kishi bana iya controlling kaina idan ya motsa min. Koda muka gama waya wacce take min lalle na Kira akan tazo tamin na Sha damara dawo da hankalin mahfuz kaina insha Allahu sai na raba shi da SR dinan MAHFUZ Allah Allah yake ya isa gidansu Hadeeza dan ya bata hakuri tunda ya fito daga gida yake kiranta a waya taki d'aukar wayarsa. Koda ya iso k'ofar gidansu ya cigaba da kiranta a waya bata dauka ba sai da ya mata text akan ya iso Yana waje ta fito Yana jiranta. Sai da aka kwashi mintuna wajen goma Kafin ya fara shako kamshin turarenta daya saka shi lumshe Ido ya bud'e Idonsa a hankali ya zuba Mata tana daga bakin k'ofa a tsaye ta harde hannayenta a kirjinta ta had'e Rai...... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166. *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 3* Sauk'owa yayi daga Kan machine d'in fuskarsa d'auke da murmushi dan yasan fushin zagin da lubna ta mata take yi. D'auke kanta tayi ta maida gefe Mahfuz ya sake sakin murmushi Yana "Kiyi hakuri wlh wanka na Shiga ta d'auki wayar bansani ba""Jiya ma haka kace wanka ka Shiga ta d'auki wayar ta zageni kaga ma d'aukar wayarka bashida amfani tunda ko na d'auka itace ta bugo dan ta zageni na rasa mai na tare mata inaga baka tab'a bata labarina ba in ba dan kaddara ba tasan bata Isa ta rigani samunka ba"Tace tana Jan siririn tsaki"Kiyi Hakuri hakan bazata sake faruwa ba ki dan saki fuskarki mana sweet dina"Sai a lokacin ta dan saki murmushi tana "Hmm Mahfuz ya zancen namu saura wata biyu naje gida fa"?"Karki damu insha Allahu madam na haihuwa zan yunkuro ki kwantar da hankalinki Sai a lokacin Hadeeza ta saki murmushi tayi wal da Ido ta juya ta koma cikiBata fi minti biyar da Shiga ba ta fito da wani leda mai dan kyau ta mik'awa mahfuz daya washe baki Yana "Bakya gajiya sweetyna" Ya bude ledar ya dauko dan karamin flasks din potato balls ne a ciki ai sauce din albasa sai kamshi ke tashi har dasu chocolate dasu biscuit. Yana Jin dadin yanda Hadeeza ke hada Masa break fast sabo da girkunanta yasa baya damuwa yaci na gida duk da yasan lubna itama ba a baya bace wajen iya girkin.Bai tab'a tunanin zai dawo da Hadeeza rayuwarsa har ta samu gurbi a zuciyarsa ba.Dan ta wulakanta shi a baya kafin ya had'u da Lubna yaso ya auri Hadeeza sai ta nuna Masa tafi karfinsa,dan zai iya cewa shine mai karamin karfi a manemanta. Yana ji yana gani ya hakura da ita,Allah cikin ikonsa ya hadu da lubna da ta saka shi manta wata Hadeeza har yaji a yanzu yasan ya had'u da wacce take Sansa sabida Allah Tuni ya shafe babin Hadeeza ya manta da ita har Allah yayi aurensa da lubna wata hud'u da aurensa sai ga Kiran Hadeeza a wayarsa koda ya daga a gigice ta jefa mishi tambayar "Mahfuz dagaske ne kayi aure"?Duk da yasan itace cewa yayi "Da wa nake magana"? Kamar zatayi kuka tace "Haba Mahfuz Kamar ya da wa kake magana Hadeeza ce" "Wacce Hadiza wai kimin bayani nagane"? yace Yana hararar wayar dan karfin hali yake gani a wajenta""Mahfuz dan Allah ka bari nasan kasan wacce take magana so kake kawai ka wulakantani"Tsaki yayi ya kashe wayarsa ya danna lambarta a block dan kallon mai kwadayin abin duniya yake mata ko uban Mai yasa ta kirashi yanzu ko kunya bata ji ba.Kwana biyu a tsakani ta sake kiransa da wani lambar Yana Jin itace ya Kara kashe wayarsa Yana mamakin mai take nema a wajensa. Bata hakura ba ta hau tura Masa message ta watsapp da message ko karantawa baya yi sai ya goge.Bata tab'a fashin kiransa ba Kiran da take masa har da tsakar dare akan dole ya koma kashe wayarsa daddare ranar da abin ya ishe shi Yana d'aukar wayar yace "Wai Mai kikeso a wajena ne Hadeeza naga mun rabu nayi Aurena mai Kuma kike nema a wajen wanda ba ajinki ba"?Cikin muryar kuka tace "Mahfuz yanzu dagaske kayi aure kana nufin ka hakura dani ya kake so nayi da san da nake maka wlh ko a baya Ina kaunarka wlh gwadaka nake daga naje gida na dawo kawai naji labarin aurenka a wajen Abdul (A gidan kanin mahaifinta take a zaune tana karatu Iyayenta suna garin gombe) Tsaki mahfuz yayi yace "Hadeeza ba gwadani kike ba a samarinki da kikeso ki aura aka yaudareki shine yanzu Kika nemoni nidai a yanzu nayi Aurena na auri matar da nake balain so da kauna muna zaune lafiya Dan Allah ki rabu dani ki daina kirana a waya"Daga haka ya kashe wayarsa ko minti biyar ba'ayi ba sai ga message kaca kaca daga wajenta na ban hakuri da irin san da take mishi ya bata dama ta gwada mishi irin san da take masa,ta yarda zata je ata biyu za Kuma tayiwa matarsa biyayya.Ko ta kanta bai bi ba ya danna Mata blocking dan ko mai zata yi bayajin zai saurareta shi da Allah ya bashi finta ma Lubna Mai so da kaunarsa ba abinda ta rage shi dashi.Ga mamakinsa Hadeeza haka ta cigaba da canza lambobi tana kiransa ko da zai gaya mata bak'ar magana hakan bazai saka ta fasa kiransa ba har ta kai message din safe daban na rana daban na dare daban.Bai tab'a bari lubna tagani ba take yake gogewa dadin dayaji lubna bata mai bincike bata damu da taba masa wayarsa ba. A haka ya samu shekara da Aurensu da Lubna watarana yaje wajen aiki awa biyu a tsakani sai ga Hadeeza a office dinsa.Rabonsa da ita shekara biyar kenan taci kwaliyya ta Kuma yi kyau kamar ba ita ba ta canza akan sanin daya mata a baya ta Kara gogewa sai kamshin turare take. Ledar da ta shigo dashi ta ajiye masa agabansa ta langabar da kai ta hau matsawar kwalla. Mahfuz kuwa kau da kansa yayi yana "Hadeeza dan Allah mai kike nema a wajena""Ba abinda nake nema a wajenka so nake kawai komai ya wuce mu cigaba da soyayyar mu""Shekara daya da Aurena Hadeeza idan ba yaudararki kikeso nayi ba banida ra'ayin yin soyayya ko na Kara aure matata ta isheni rayuwa Dan Allah kije ki nemi wani"Bai idda magana ba ta fara hawaye har da sheshek'a mahfuz ya shareta ya cigaba da danne danne a laptop din gabansa sunansa data Kira yasa ya dago ya kalleta"Allah ya jarrabceni da kaunarka mahfuz bansan ya akayi na wayi gari cikin tsananin sanka ba amma tunda kace haka dan Allah Ina neman alfarma mu cigaba da zumunci ka zama abokina""Ana abota tsakanin namiji da mace ne Hadeeza cigaba da muamalla dake kamar dai muna soyayyar kenan Mai amfanin haka""Dan Allah Mahfuz iya alfarmar da zaka min kenan ko ba kullum ba muringa waya ko chatt har Allah ya yaye min"Burinsa kawai ta tafi daga mata Kai kawai yayi yace jeki naji"Washe baki tayi ta mike tana "Nagode mahfuz ga wanan ba yawa sai na kiraka anjima" "Hadeeza karki kirani kinsan inada mata kidaina kirana anyhow""Bakada matsala" tace tare da sakar.masa murmushi ta juya tana wani irin takun daya sa Mahfuz kasa d'auke idonsa akanta har ta fice.Sai da ya gama abinda yake ya bude ledar da ta kawo turare ne.masu kamshi sai snacks da akayi wrapping a foil paper har zai mayar da snacks din ya gutsiri meatpie din yaji ya masa dadi a haka ya gyara Zama yaci iya Wanda zai iya ci dan ta hutashe shi siyan abincin Rana, lubna taso ta ringa aika Masa da abincin rana ya hanata dan baya san ya wahalar da ita.Tunda ga lokacin Hadeeza da zage wajen zuwa office d'insa tun bai wani bata fuska ba har ya fara bata fuska duk zuwan da zatayi da kalar abinda zata kawo Masa, text kuwa haka take tura masa.Bai tab'a d'aukar wayarsa ya kirata ba sai dai ita ta Kira shi. Yau da gobe a hankali ya fara damuwa da lamuranta har idan bata zo wajen aikinsa ba bayajin dadi, yayi balain sabo da snacks masu Dadi da take kawo Masa. A irin wanan yanayin ta daina aiko Masa da text din da ta sabar.masa dashi,ta bar zuwa office d'insa haka.kawai.yaji ya damu tun Yana ganin zai iya daurewa har yaga bazai iya ba aranar da aka samu sati daya baiji daga wajenta ba ya kirata a waya sai daya mata.miscall ya kusa goma Kafin ta daga murya can kasa da Sunan bata da lafiya shiyasa yaji shiru Nan kuwa karya takeyi so take ta gwada shi taga ko ya damu da ita. Ana tashi daga wajen aikin ya kirata ta mishi kwatancen gidan da suka koma bai Sha wahala ba dan ba wani nisa tsakanin gidan nasu da wajen aikinsa. Sai gashi har da kayan dubiya. Har dan karamin palon gidan aka masa iso da alama ba kowa a gidan sai kannenta da suka kasance yaran kanin mahaifinta. A kwance ya sameta a doguwar kujera ta Sha kitson attach da tayi parking,sai riga yar kanti armless da taje mata har kasa duk da batayi kwalliya ba bata yafa komai ba tayi wa mahfuz kyau. Nanarkewa kawai take tana shagwaba Kamar bazai tafi ba lubna dake ta kiransa a waya yasa ya Mik'e ya Mata sallama ya ajiye Mata kayan dubiya ya fito. Wani ikon Allah Koda ya dawo gida suna Hira da lubna Yana tuno Hadeeza da yanda ta ringa Masa shagwaba tunda ga wanan lokacin ya dawo da Hadeeza rayuwarsa ta samu matsayi a zuciyarsa dan ta Kai yanzu har breakfast take Masa idan zai wuce ya karba da Rana ma abincin take aika Masa. Dak'yar yake yakice cin abincin dare a wajenta gudun kar Lubna ta zarge shi. Zuwa yanzu baya iya kwana biyu bai ga Hadeeza ba duk da ba abinda Lubnarsa ta rage shi dashi wanan kenan. LUBNA Jan kunshi mai kunshina ta rangada min a hannu da kafa. Tana ciremin na sallameta ta tafi na hada Abubuwan da nake dan gyaran jiki dashi na hada na mulka a jikina dashi sabida fatata ta Kara laushi. Iya kokarina zanyi dan na dawo da hankalin Mahfuz kaina bazai yu wata Yar iska can ta kwace min shi ba,nima sai a yanzu naga wautata da na hau fushi da shi,waya sani ma ko kwana ma yayi jiya yana waya da yar iskar SR. Sai da na goge ko'ina na jikina na Shiga wanka har wani iska naji Yana Kara Shigana. Mahfuz na san shinkafa da wake da salad hakane yasa na dafa shinkafa da wake na hada masa zobo sai da na gama na koma d'akina Ina duba kayan da Zan saka yau nayi Masa kwalliya yasan har yanzu da saurana ciki ne kawai yasa bana kwalliya duk kayana sun min kad'an dak'yar na samu wani kamfala da nayi wa dinkin bubu mai kalar dorawa da bak'i ya shigeni ya kuwa min kyau dan na cika kayan bansa breziya ba dan mahfuz bai fiye San na saka breziya ba, Hoda da Jan baki na shafa Nima kaina nasan nayi kyau na mulka jikina da turare na fito daga d'akin na koma Palo na zauna. Wayata na dauko na kira shi a waya Yana fara ringing ya dauka na sauke ajiyar zuciya da naji muryarsa "Matata ta kaina kin sauko kenan"? "Hmm dama ni ba fushi nayi ba kishin mijina kawai nake aka nuna nayi laifi" "Mijinki nakine ke kadai bai Kamata ki dagawa kanki hankali ba" "Tom mijina ya Kamata ka dawo yanzu matarka nasan ganinka" "Mai Kika ajiyemin"? "Kaima kasani" nace Ina sakin murmushi kamar Ina gabansa Murmushi yayi yace gashi nan ya kashe wayarsa yana kashe wayar Kiran Hadeeza na shigowa wayarsa. Bayaso ya d'auka tace Masa yazo tunda har ya samu lubna ta sauko da kanta Kamata yayi shima ya faranta Mata. Kashe wayarsa yayi gabad'aya dan yasan Kira zatayi tayi Ana kiraye kirayen sallah magriba naji tsayuwar machine d'in mahfuz ido na zubawa kofar har ya shigo idonsa kyam a kaina Nima idon na zuba Masa ina dan sakin murmushi dan har dan sakin baki yayi nasan mai hakan ke nufi IIyye wai duk wanan kwalliyar ni akayiwa Kinga yanda kikayi kyau kuwa aikuwa ya Kamata na biya kudin kwalliyar nan daga haka ya nufo wajen da nake baiyi wata wata ba ya daukeni dak'yar Yana nishin nayi nauyi Nasan Mai yake nufi ce Masa nake ya bari muyi sallah fir yak'i har sai da muka samu nutsuwa da juna na gamsu da mahfuz nawane ni kadai ba wata Yar iska da ta Isa ta rabani dashi sannu a hankali zan rabashi da wata SR. Tare muka yi wanka muka yi sallah mu kaci abinci tamkar lokacin da nake amarya. A kan cinyarsa bacci ya d'aukeni Yana ta shafa min kaina Ina jinsa ya d'aukeni dak'yar ya je ya kwantar dani a d'aki bacci mai dadi da nutsuwa yayi awon gaba dani. MAHFUZ Daga sakin munsharin da lubna keyi yasan bacci yayi awon gaba da ita,baisan Mai yasa hankalinsa ya rabu gida biyu ba so yake kawai ya Kira Hadeeza ya riga ya Saba sai sunyi waya ko video call yaji muryarta ta masa shagwaba a hankali ya zare jikinsa daga jikin lubna cikin sand'a ya fito daga d'akin ya fito daga palon ya fita can waje gudun ma Kar lubna ta Kara kamashi. Akan dakalin gidan ya zauna ya fara Kiran Hadeeza da tak'i daga wayarsa hankalinsa yayi balain tashi hakane yasa ya dage da kiranta. LUBNA karar bud'e k'ofar palona yasa na bud'e idona dan banida nauyin bacci ko kad'an Mikewa nayi a hankali na zauna da naga mahfuz baya d'akin. Haka kawai gabana ya Yanke ya fadi Allah yasa ba Kara Kama mahfuz zanyi Yana waya ba. Daga idona nayi na kalli agogon d'akin 12:20am. Saukowa nayi daga Kan gadon haka kawai naji zuciyata na rayamin Mahfuz na palo Yana waya da Yar iskar yarinya Nan da bansan adadin tsinuwar da na mata ba. Kishin daya rufe min ido yasa na fito daga d'akin da sauri sai dai Koda na fito baya palon hakane yasa nayi wajen tsakar gidan dan k'ofar palon a bud'e yake haka ma k'ofar gidan dagani sai sleeping dress na nufi wajen k'ofar a hankali kirjina na bugawa,zuciyata Raya min kawai take na koma Kar naji abinda zai daga min hankali daya zuciyar tawa da bakin kishi na ingizani da gwara na ganewa idona mai mahfuz keyi waje. "Dan Allah kiyi hakuri haba mana na fada miki bada gangan na kashe wayar ba abinda ya sauka a kunne na kenan.... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 4* Runtse idona kawai nayi jikina na rawa badan nayi da gaske ba ba abinda zai hanani faduwa. Tamkar a handsfree ya saka haka nake jiyo maganar ta Cikin shagwaba da kuka "Dan kaga Ina sanka da kaunarka kake wulakantani mahfuz mai yasa kake min haka"? "Wlh ba haka bane haba sweetyna ya za'ayi na wulakantaki ban isa ba cajina ne ya d'auke Kuma wani uzuri ya tasomin naje gidanmu ban baro can bama sai goma na dare wlh " "Wlh ban yarda ba kace matarka dai ta kwace wayarka ta kashe ta hana ka zuwa wajena na dade da sanin tsoranta kakeji ka sa na sha wahalar dafa maka abinci har konewa nayi a hannu" "Ya salam dan Allah kiyi hakuri wlh ba da gangan naki zuwa ba ki hakura Mana karki sa na kasa bacci" "Um um bazan hakura ba sai ka goyani Kuma wlh sai ka biyo gobe kacinye abincin Nan shine kawai zan hakura" Dariya mahfuz ya kyalkyake dashi Yana "Angama sarauniyar mata idan na fara goyaki sai kin gaji gobe weekend bana fitowa da wuri wajen 10 zanzo a dumama min abincina,kinyi kitso da kunshin"? "Emana har kwalliya nayi fa da sabon Kaya kak'i zuwa" "Haha karki damu gobe idan nazo zan ma biya kudin kunshi da kitso amaryata kifita wajen haske na kiraki video call" Iya abinda na iya jure ji kenan zuciyata kamar ta fado sabida tsananin bakin ciki mutumin daya gama tumurmusheni san ransa da tsohon cikina shine yanzu ya baroni a daki yake zuba soyayya da wata. Wutar kishi kawai ke ruruwa a raina Ina Jin kamar na rufe kofar na kulle ya kwana a waje ko yaje wajenta ya kwana da bakin ciki da takaici ace kina iya k'ok'arinki akan ki kyautatawa namiji amma shi ba take yake ba zuciyarsa na wani wajen. So nake na bar gurin amma.kafafuna sunki bani hadin kai,haka na zubawa mijina Ido,dake ta murmushi kamar an Masa bushara da gidan Aljanna har Mai nayi Masa haka,dame na rage shi da zai min irin wannan sakayyar bana ma iya gani sosai sabida hawayen daya cikemin idona. Nasihar mahaifiyata kawai ke dawo min kaina da kyar na iya danne abinda nake ji da shaidan daya ke ingizani akan na kulle k'ofar ya kwana a waje ko naje na cakumu wuyan rigarsa na dadana Masa ashar. Dak'yar na koma ciki Ina Shiga daki na kwanta naja bargo har saman kaina hawaye na cigaba da zubarmin zuciyata na suya,daga yanda Mahfuz ke magana da yarinya nan ba karamin so yake Mata ba har baya iya bacci idan baiji muryarta ba, wato shiyasa yanzu bai damu da yaci abincina ba? wacece yarinya nan,da take San kwace min miji,.har tana Masa shagwaba da sai ya goyata,tunani na tafi mai zurfi naga ko dai akwai ta inda na gaza har wnan yarinya ta dauke masa hankali Ina matarsa ta sunna ya baroni a daki ya fita waje dan kawai yayi waya da ita,tsafta, girki mai dadi, uwa uba iya gado,daga samun cikina na zama raguwa,Ina da kunya amma sabida kawai na faranta masa, duk da ni ba jarababiya bace har nemamsa nake da kaina,dan naji matan da suke neman miji da kansu daban suke a wajen mazajensu. Ganin ya dade bai shigo ba yasa na daga kaina na kalli agogo karfe biyu saura minti goma,wasu matan na can rungume a kirjin mazajensu ni gani a kwance nikadai mijina na waje Yana Shan soyayya. Motsin rufe k'ofar Palo yasa na d'ad'a Jan bargon kaina. Ina jinsa ya shigo cikin sand'a har da lekani kafin ya kwanta a gefena a hankali ko minti goma baiyi da kwanciya ba naji Yana sakin munshari. Haka na kwanta zuciyata kamar tayi bindiga har aka Kira sallah na Mik'e naje na daura alwala na tada Sallah. Har na iddar bai tashi daga bacci ba ta Ina zai tashi ya kwana Yana waya. Ko ganinsa bana so nayi hakane yasa na koma Palo, so nake na taushi zuciyata na daure Kar na nuna Masa komai a fuska nabi shawarar mahaifiyata dan tunda na taso duk shawarar da ta bani idan har nabi Ina ganin haske. Yanda nakejin jikina nasan ko tsinke bazan iya dagawa ba nama wahalar da kaina dafa Masa abinci shi da zaije wajen budurwarsa yaci dumame. Haka nayi kwanciya ta a dogon kujera wajen tara sai gashi ya fito Palo Yana "Uwar biyu shine yau baki tasheni nayi Sallah ba ko wlh bansan ya akayi na makara haka ba,A'a lubna lafiya kuwa ya Naga idonki a kumbure ko bakida lafiya"? Duk maganar da yake ban daga kaina na kalleshi ba,ban tabbatar idan na Budi baki dan na masa magana ba magana zan gaya Masa ba hakane yasa ban magana ba na ja bakina na tsuke Kai kawai na gyada masa da Sunan banida lafiyar" Kamar gaske ya nufoni da sauri ya zauna tare da jawoni jikinsa Yana tattab'a jikina. Na janye na koma na kwanta sam bana San ganinsa duk abinan da yake na munafircine Yana da wacce yake so da kauna. "Jiya Kuma kalau kika kwanta fa,Allah dai ya saukemin ke lafiya sannu kinji" Yace tare da manna min kiss a goshi,nidai lumshe idona nayi, ba'a zagin miji amma na danna masa Ashar a zuciyata. "Bari na dan gyara gidan mai zakici na dafa miki"? Ganin ban bashi amsa ba yasa ya kara yimin sannu ya fita waje nabishi da mugun harara inajin Kamar na jawo shi na rufe shi da duka,sabida me zai nuna min kulawa alhalin Yana da wacce yake so da idan baiji muryarta ba baya iya bacci,a yanzu Kuma banida burin daya wuce na san wacce yarinya ce wanan da har ta d'auke masa hankali. Bai dade ba ya dawo da leda a hannunsa daga kamshin nasan kosai ya siyo Ina balain san kosai da kunu,Yana cikin abincin dana fiso na karya dashi da safe kitchen ya wuce dama muna da garin kunu,da alama shi yake damawa. Yanda yake nuna damuwarsa a kaina yasa wani bakin cikin Kara turnikeni duk abinan da yake min da wata a zuciyarsa. Motsinsa da naji yasa nayi saurin maida idona na rufe Ina jinsa ya ajiye kofin daya damo kunun a ciki ya ajiye Yana "Lubna tashi ki karya kinji ga magungunan ki nan sai ki sha. Ya jawo kafafuna kasa. "Bana Jin cin komai" "Ki daure mana kinsan baaso mace Mai ciki ta ringa wasa da abinci ko dan abin cikinta" yace Yana kawo kosai bakina na d'auke kaina Ina "zanci anjima" Tilasta min ya ringa yi naci nasan nacinsa akan dole nasaka hannu na fara cin kosai na karbe kofin a hannunsa dan bana San munafircin wani bani a baki. Dadin daya min yasa na zage naci kosai baifi biyar ba na bari, na Sha maganguna na, ya dauki flasks din ya Kai kitchen,ya fito da tsintsiya ta share palon har da mopping mahfuz ba dai baya ba wajen aikin gida idan dai Yana nan, wanke wanke ne kawai bayamin. Mai Mahfuz yake nema a wajen wata ya mace dan Allah mai na rage shi dashi daga kaina nayi na kalli agogo tara da rabi karfe goma sukayi da budurwarsa akan zaije wajenta bari naga ko zai hakura da fitar na ayyana a raina a daidai lokacin daya gama goge kayan kallon ya fara k'ok'arin nufar d'akin da a raina nasan wanka yakeso yayi ya fita. "Kai mai zakaci"? Na jefa mishi tambaya tare da zuba Masa Ido "Ai zanje gida yanzu inaje can sai na karya na taho Miki da abincin rana ba sai kin wahalar da kanki wajen girki ba kiyi kwanciyarki ki huta kawai" "Indai har dan abincin zaka fita yau weekends daya Kamata ka zauna a gida na samu kulawarka Zan daure na maka girkin ba sai kaje ko'ina ba" "Ba iya dan na karya zan fita ba,Hajiya tace tana san ganina Yau bansan neman da take min ba" Ko kunyar yanko karya baiyi ba na gyada kaina kawai ina Jin wani irin zafi a zuciyata bai kara cemin komai ba ya shige daki na fara tunanin.hanyar da zan bi na hana shi fita. Tunanin daya darsu a raina yasa ni mikewa na nufi d'akin nawa Ina k'ok'arin.murda.kofar naji muryarsa Yana "Nan da minti goma Zaki gani wlh na shirya" Murda k'ofar nayi na Shiga yaya saurin sauke wayar daga kunnesa ya cigaba da goge jikinsa murmushin da bai Kai har zuci ba na sakar Masa Ina "bari na saka Kaya nabika dama na kwana biyu banje gidan ba" "Keda bakida lafiya Lubna Kika je can ma hayaniya kawai ta isheki kiyi kwanciyarki ki huta kawai bazan dade ba Zan dawo" "Aaa nima inaso na dan fita na Sha iska bana san na zauna Ni kadai a gida kamar mayya" Take naga fuskarsa ta sauya ya Kuma kasa min magana na wuce shi na nufi wajen wadrobe na bud'e dan yau zanga iya gudun ruwansa. Bakar doguwar Riga na jawo na fara k'ok'arin sakawa a daidai lokacin da wayarsa ta hau vibrating na juya na kalleshi Ina "Kila hajiyar ce ke kiranka ka fada Mata tare zamu Zo" "Lubna ba dadewa zanyi ba wlh yanzu zan dawo bai dace ma ki hau machine da tsohon ciki ba" Ban ce masa komai ba na saka hijabina na fita Palo dan wlh yau kafata kafarsa inyasan wata bai San wata ba. Mahfuz kuwa rasa yanda zaiyi da lubna yayi,ga Hadeeza sai kiransa take,bazai so yau ma yayi wa Hadeeza laifi ba, dabarar da ta fado masa hakane yasa ya shirya tsaf ya fito Kamar waya yake Yana "Wai da da Lubna ma zamu zo ok to shikenan sai kun dawo" Ya sauke wayar daga kunnesa ya nufi wajen lubna Yana "Kinga ma hajiyar ce ta kira Wai sunje gaisuwar mutuwa sai anjima zasu dawo idan sun dawo sai muje,tunda kin hanani fita bari na fita waje na siyo abu na dawo yace da sauri Yana k'ok'arin yin waje ga wayarsa na vibrating. Yana faramin bayani nima na shirya karyar da zanyi Yana zuwa bakin k'ofa na kwalla ihu tare da dafe cikina Ina wayyo Allah cikina Zan mutu" A guje yayo wajena ni kuwa na cigaba da zunduma ihu. Mahfuz ba karamin rikicewa yayi ba hakane yasa ya ajiye wayarsa akan kujera duk ya dauka da gaske ne banida lafiya Yayi waje da gudu wai zai nemo.mana machine Mai kafa uku Yana fita tsinaniyar na kiransa a waya Aikuwa da sauri na dauki wayar Ina dauka tace cikin shagwaba "Nagaji da jiranka fa haba Mana Nima fa ban karya ba yunwa nakeji Kai nake jira ka karaso muci tare" "Tunda nake ban taba ganin jaka balagaza irinki ba,tom jiya mahfuz ya bani labarin irin nacin da kike Masa yace kuma.ba kaunarki yake ba dan haka kije ki nemi wani, shegiya asarariya ko kunya bakiji ba mutum da matarsa kina wahalar da rayuwarki wajen.masa girki har da sai ya goyaki yazo yaci abinci da Kika girki kamar mijinki" Kit naji ta kashe wayar nayi saurin ajiye wayar na cigaba da zunduma ihu danaji Mahfuz ya shigo. HADEEZA Hawaye ne ya hau wanke Mata fuska ta zubawa wayarta ido...... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 5* HADIZA Kukanta taci ta koshi,duk zagin da Lubna ta mata ya hau tafasa mata zuciya,ashe dai hasashen da takeyi akan Mahfuz tsoron matarsa yake ji da gaske ne,Karo na uku kenan da Lubna ke zaginta, ta rasa ya ake yi wayar ke zuwa hannunta,duk uban wahalar nan da take sha duk dan ta samu Mahfuz ya aureta,bata San tana San shi ba sai da yayi Aure, duk da sai da Wanda ta kwalafa rai da auren wani saurayinta mustapha ya yaudareta,hakane yasa ta komawa Mahfuz,dak'yar dak'yar ta samu ya fara kulata, shine matarsa take neman hanata rawan gaban hansti, taga alamar idan har batayi da gaske ba,bazata bari Mahfuz ya aureta ba,aikuwa idan ta san wata bata san wata ba ba boka ba Mallam sai ta auri mahfuz ta wulakanta Yar iskar matarsa da sam bata ma san sunanta ba balle tasan kamaninta ta matukar tsanar matar mahfuz Kamar ta kasheta haka takeji,shi Kuma mahfuz bari taga karyar da zai Kara shara mata tun jiya yake raina Mata hankali har ace ya kasa tsawatar wa shegiyar matarsa da take zaginta idan ta kirashi. Bakin ciki ne yasa ta kashe wayar gabad'aya dan tasan ta kafu a zuciyar mahfuz gwara ta Masa barazana akan zata hakura dashi idan yaga da gaske ne dole ya tura manya gidansu ta gaji so take kawai ta samu ta Shiga daga ciki ta fitar da lubna ma daga gidan ta bar mata mahfuz dinta. Mahfuz Gigicewar da yayi yasa Sam bai bi takan wayarsa ba har suka isa asibiti da lubna dake ta zunduma ihun wayo cikinta sai kuka take. Koda suka isa ihun da lubna ke zubawa taki bari ma likita ya dubata dak'yar dak'yar aka samu tayi shiru. Likitan ya dudubata,yanda take ihun cikinta yasa likitan yi mata allura. Ba abinda yafi komai faranta min rai sama da zagin da nayiwa Yar iskar yarinya nan, yanda na zuba drama ba mai yarda ba Ciwon marar nake ba,dan har da kukana awar mu daya a asibiti aka sallame mu ya kashe wajen Dubu biyar a siyan magani sai yaje ya biya kudin kunshi da kitso nagani. Koda muka isa gida yanda nake langab'ewa Ina matsar kwalla yasa bai motsa daga kusa dani ba sai aikin yimin sannu da yake. Abincin ma sai shi ya shiga kitchen ya dora da wanan na samu na goge Kiran da tayi dazu so nake nayi ta hadasu fada. Sai da ya bani abinci naci na koshi Ina yamutsa fuska ya bani magunguna na Sha. Sanan naga ya dauki wayarsa yayi hanyar palo Na riga nasan Kiranta zaiyi a waya. Fitarsa da minti biyar sai gashi ya shigo bansani ba wayar yayi ko baiyi waya ba,Ya zauna a gefen gadon Yana matsamin kafa da hannu daya Yana latsa wayarsa da hannu daya,Sam fuskarsa ba walwala ba Kuma abinda ya shafeni addua ma nake Allah yasa ta sosoka masa Ashar wlh da wayar zai shigo hannuna text zan Mata na zazzageta. A ranar ma ban bari ya fita waje waya ba dan kwanciya nayi a kirjinsa,ko da bacci ya fara daukana idan na tuna sai nayi sauri na kankame shi. A ranar dai baiyi waya da ita ba duk da naga alamar idonsa biyu ba bacci yayi ba MAHFUZ Tunda suka dawo gida yake gwada lambar Hadeeza yake jinta a kashe,ya dubata ta WhatsApp nan ma Bata hau ba ya rasa duk Mai ke mai dadi,yasan fushi tayi sam bai so yau baije wajenta ba,dan shima ji yayi Kamar ya dade bai ganta ba,burinsa bacci ya dauki lubna ya fita waje ya kirata a waya idan yaji a kashe ya kira Ameera kanwarta,muryrta da zaiji kawai zai saka ya samu nutsuwa sai dai lubna kankame shi tayi taki barin jikinsa abu kadan sai yaga ta bud'e idonta a haka ya kwanta kamar yayi kuka baccin Kuma yak'i daukarsa. Allah Allah yake gari ya waye idan ya fita massallaci ya kirata a waya. Wajen tara yaje gidan nasu. Kiran sallahr asuba a kunnensa hakane yasa ya mik'e da sauri ya fada bandaki ya daura alwala a daidai lokacin da Lubna ta mik'e zaune itama tana yamutsa fuska "sannu ya jikin naki"? "Wlh har yanzu ciwo yake min ga kaina Kamar ya rabe gida biyu dan Allah ka zauna kaja mu sallah ba sai kaje massallaci ba" "Haba Lubna jiya ma fa banje massallaci ba ai ana iddar wa zan dawo bari naje" Yace da sauri tare da yin waje ya jefa wayarsa a aljihunsa. Na tabe baki dan nasan Kiranta zaiyi a waya,yau ma bazan bari yaje ko'ina ba Sai dai mayyar taci kanta,na tsaya ma Ina neman dorawa kaina hawan jini bayan ga hanyoyi nan da Zan bi wajen rabasu,yanzu wayarsa ta kara zuwa hannuna lambarta zan d'auka Bai dawo gidan ba sai wajen shidda da rabi. Daga yanda naga fuskarsa ba walwala nasan ko bai samu yin waya da ita ba ko Kuma ta zazzage shi Kamar yanda nake fata da Addu'a. Ban koma bacci ba na dafe marata na fara wash wash,ya dafe kansa Yana "Lubna wanan wane irin ciwon Mara ne" Ban bashi amsa ba na hau matsar kwalla. Mahfuz kamar ya sa kuka dan bakin ciki,dan Yana ta Kiran Hadeeza a waya bata d'auka ba,karshe sai text tayi Masa da Allah ya hada kowa da rabonsa bazata iya ba tunda matarsa ke controlling dinsa. Ya Kira dan ya bata hakuri Sam taki dagawa,bashida burin daya wuce tara yayi yaje gidan nasu. Sam bazai iya hakura da Hadeeza ba Yana jinta a ransa ba abinda yake Balain so da ita sama da shagwabarta ko ba'a fada ba yasan idan ya mallaketa zai Sha soyayya sai gashi yau ma Lubna na neman hana shi fita. magungunan ta ya d'auko mata ya siyo kayan shayi ya hada mata. Sai dai Koda ta Sha bata fasa ihun ciwo mara ba,Yana ji Yana gani Lubna ta dabaibaye shi bai samu ya fita ba a ranar. Hadeeza kuwa ta Kara cika tayi fam tana ganin wulakanci mahfuz din ke san yi Mata ta dauka da ta Masa text din zai zo gidansu da sassafe sai dai ko keyarsa bata gani ba. Sam ba walwala a fuskar mahfuz har wani tsawa tsawa yake min idan zaiyi magana hannunsa manne da wayarsa nima bakin cikin duk wanan abun akan wata can a waje ya keyi dan kawai bai samu fita wajenta ba,har mamaki yake bani wlh bantab'a zaton haka daga wajen sa ba, banga ta Zama ba ko Ina so ko bana so dole gobe zai fita Kuma yaje gidan nasu sai dai Allah ya kawomin mafita. Daddaren ma ban bashi space ba haka.na manne Masa banga Kuma alamar zai fita waje waya ba sai tsaki da nakeji yanayi akai akai. Washegari kuwa da sassafe ya fice daga gidan kamar akan Kaya yake mahfuz da ni nake tilasta.masa fita sabida kar ya makara sai gashi yau wata ta d'auke masa hankali koma wacce yarinya nan ban yafe mata ba na share hawayen daya zubomin na dauki wayata dan na Kira Mahaifiyata ita kawai zan Kira na samu kwanciyar hankali dan nasan zata bani shawarwari masu kyau. Mahfuz Dak'yar ya samu Hadeeza ta fito dan sai da yayi ta turawa gidansu Tama k'i d'aukar wayarsa. Koda ta fito shi kadai ya hau maganar sa Yana bata hakurin dalilin dayasa bata ganshi ba Lubna ce bata da lafiya kwanan su biyu a asibiti bada gangan yak'i zuwa ba Sai a lokacin Hadeeza ta kalleshi idonta cike da kwalla tana "Mahfuz Ina kaunarka amma ya zama dole na hakura da Kai dan na riga da nasan b'atamin lokaci kake,wlh bazaka iya Aurena ba,bazaka iya rik'e Mata biyu ba,dan kana balain tsoron matarka mahfuz zagi da cin mutunci haka ta zuba min sau uku kenan tana zagina da iyayena har karuwa tace min idan har bata da lafiya zata zageni ne"? "Wlh da gaske Lubna bata da lafiya ko dai wata ce ta kiraki ta zageki matar da bata da lafiya taya har zata kiraki ta zageki"? "Hmm Mahfuz kenan karya Zan Mata kenan wlh Azeem bamu dade da waya da kai ba na sake kiranka ta d'auka ta hau zazzagina har da cemin Kai ba sona kake ba,na like ma Ina ta dafa maka abinci Kamar wata matarka" "Ikon Allah Mahfuz yace tare da d'auko wayarsa ta Shiga call log na ranar asabar din sai dai Sam bai ga Kiran Hadeeza ba dan suna waya yake goge lambar yanzu ya haddace lambar baiyi saving a wayarsa ba har wane lokaci Lubna ta daga wayar tayi zagin bayan yazo fita ta fara ciwon maran "Wlh Kinga banga Kiran naki ba" "To na mata karya Mahfuz" "Ba haka bane bance kinyi karya ba amma kiyi hakuri dan Allah hakan bazata sake faruwa ba insha Allahu" Dak'yar dak'yar ya samu Hadeeza ta hakura Inda yace Mata ta daina kiransa ta bari ya ringa kiranta da kansa gudun sake faruwan hakan da haka Suka rabu akan zata aika Masa abincin Rana,dan ba karya Yana Jin dadin abincin ta sosai. Yana isa office Kiran lubna na shigo wa wayarsa sai daya zauna ya daga wayar yana tunanin ko wani matsalar ne ya taso,ga mamakinsa Yana dauka lubna tambayar sa tayi ko yaje office lafiya dalilin dayasa ta Kira kenan. Murmushi ya saki Suka dan tab'a hira da ita kafin ta Masa sallama. Yana kashewa ta turo Masa kalamai masu balain Dadi ya hau mamakin Kira da text din da ta masa bata Saba da Masa hakan ba. LUBNA Shawarwarin mahaifiyata na dauka,na zage damara wajen San na dawo da hankalin mijina kaina,hakane yasa muna gama waya da ita na kirashi a waya naji ya Isa office d'insa kalau.na Kara da Masa text dan mahaifiyata tace na dage da haka,da rana ma sai da na kirashi na sake Masa text Inda ya hau tsokana ta Wai ko dai soyayayar ce yau ta motsa min. Murmushi kawai nayi nace Masa ee. Tunda ga lokacin ban Kara ganin tsinaniyar na kiransa ba,har wayarsa na bincika daya shiga bandaki dan naga ko zan samu lambarta,sai dai na gama dube dubena banga lambarta ba. Ba karamin danne zuciyata nake ba dan Yana yawan fita wayar daren Koda kuwa a kirjinsa nake zai kwantar dani ya fita. Na rasa mai yake nema a wajen wata,nasan da kunya yanzu ya ce zai Aure ko shekara biyu ban rufa ba. A cikin wanan yanayin cikina ya Shiga wata na tara dama mun riga da munyi dashi Ina shiga watan haihuwa na zan koma gida har sai na haihu,dan sai na fi samun kulawa a wajen mahaifiyata tunda haihuwa farine,ji nayi Kamar na fasa tafiya gida dan nasan yanzu mahfuz zai baje kolinsa wajen waya da budurwarsa a baya yakan ce jina kawai yake bazan je gida wanka ba,sai gashi shine Kan gaba wajen hada min kayana. Ko da nayiwa mahaifiyata magana fada ta rufeni dashi akan na fiye kishi na watsar da komai na ringa kyautata wa mijina zato. Da haka na tattara na koma gidan mu amma hankalina na wajen mahfuz,haka zuciyata zata tayimin sake sake akan Yana can Yana waya ko ya tafi zance take Zan kirashi a waya tunda bana nan dani.ya Kamata ya ringa hirar. Muna cikin wayar ba dadewa zaice min zai kwanta bacci yake ji. Bayan Yan mintina idan na kirashi zanji alamar Yana waya haka.zan cika fam.idan ya biyo Kiran sai yacemin da Wani yake waya. Mahfuz Tafiyar lubna gida haihuwa ba karamin Dadi yaji ba dan yanzu kullum Yana gidansu Hadeeza anan yake cin na safe rana da dare,haka ya bude Mata bakin Aljihu. Waya kuwa idan suka fara kamar bazasu rabu ba. Duk da yakan ware lokacin da zaiyi waya da lubna gudun zargi. A haka lubna ta samu sati biyu da komawa gida. A yau daya kasance weekend ya Yanke ya dan wanke kayansa,ya gyara gidan inyaso yau yaje wa lubnar da ta dage akan yau a gidansu take so ya wuni ta ajiye Mai abinci yau ma zizilewa Hadeeza yake dan baya so tace masa yazo. Ya gama wanki kenan Yana cikin gyara gidan sai ga Kiran Hadeeza a wayarsa. Abin mopping din ya ajiye ya daga wayar "lek'o waje" Shine kawai abinda tace tare da kashe wayar Wayar yabi da kallo cikin mamaki kafin yayi wajen Yana lekawa waje ya hango ta a machine mai kafa uku taci kwalliya tayi kyau Wajenta ya Karasa Yana "Kai Ina zakije haka wai dama kin san gidana" Murmushi ta sakar Masa tana "idan inasan abu dagaske nakesan abun ka gama wankin ne ga abinci na kawo ma kasan bazan bari ka zauna da yunwa ba" Mahfuz kasa ma magana yayi ta sauko da basket din abincin tana "Wai ko dai bakaji dadin zuwana bane" Mahfuz keya ya sosa ya hau dube dube dan bayaso Yan unguwar suyi Masa wani fassarar, "Kinsan Yan unguwar tamu suna da sa Ido" "Tab Kai kake tsoron Yan unguwa ma muje" Tace a daidai lokacin da ta bawa Mai machine d'in kudinsa Mahfuz Kamar Wawa yayi gaba da sauri ya shige gidan. Yana dan mamakin Hadeeza da tazo masa har gida. Hadeeza kuwa ko a jikinta da biyu tazo gidan so take taga ya gidan ma mahfuz din yake ta dade tana Neman wanan damar daya ce Mata lubnar ta koma gida. Suna Shiga palon ta ajiye basket din ta hau kalle kalle tana "Masha Allah gidan namu yayi kyau sai dai ya Mana kad'an nida Auntyna" Murmushi ya sakar mata Yana "ki zauna na d'auko Miki ruwa ya nufi wajen da fridge ke,Yana d'auko ruwan yaga ta cire mayafi ta d'auko mopstick ta hau mopping.... LUBNA... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 6* Mahfuz duk kasa sakin jikinsa yayi Kamar Mara gaskiya sai yake Jin Kamar Lubna zata iya fadowa gidan. Hadeeza kuwa ko a jikinta ta zage ta gama mopping ta fara goge kayan kallon sai ce mata yake ta barshi amma fir tak'i har sai da ta gama tsaf ta koma ta zauna tana "da akwai wuta har guga zan maka" Murmushi ya sakar mata Yana "haba dai wankin ma bayarwa nake Mai wankin ne baya gari" Tana k'ok'arin Magana wayarsa ta fara ringing gabansa ne ya Yanke ya fadi daya ga Lubna ke kiransa. Mikewa yayi da sauri yayi hanyar d'aki ya kalli Hadeeza data kura Masa Ido Yana "Ina zuwa" Yana shiga d'akin tayi sauri ta mik'e ta leka k'ofar da ta gani,ganin kitchen ne yasa ta tab'e baki ta leka daya d'akin da ke bud'e ta daga labulen nan ma ta tab'e baki tana "ko kayan kirki.ma Babu a gidan da sannu Zan shigo kifita insha Allahu" Tayi sauri ta koma ta zauna ta cigaba da karewa palon kallo,Sam palon lubnar bai wani burgeta ba kayan lubnar ma duk ba masu tsada bane da zasu daga mata hankali. Rigar jikinta ta kara gyarawa na fulaninta ya fito ta saman riga sosai,dan so take ta rikita mahfuz yayi ya fito ya aureta. Da zata samu yanda take so da lubna ma kafin ta dawo daga haihuwa zata zo ta tarar da sunyi aure da mahfuz har ta tare,sai dai ta rasa mai yasa mahfuz ya kasa motsawa duk gani take tsoron lubna yake,so take ma taga hoton lubnar amma babu ko daya data gani a palon,wayar mahfuz Kuma akwai password a wajen hotunan,da alama shegiyar matarsa ce ta kirashi ya wani shige daki,take taji ranta ya fara b'aci ta had'e rai. LUBNA Kwalliya nayi sosai na gyara d'akin kanina dan nayi kewar mijina duk da yana zuwa ganina so nake yau idan yazo mu dan keb'e dashi na faranta masa rai dan nasan halin kayana hakuri kawai yake. Da taimakon kanwata zainab na tuka Masa tuwon semo da miyar wake na jera duk a d'akin kanina. Karfe biyu muka yi dashi akan zaizo idan ya gama wankin da yake. Ganin biyu da rabi tayi baizo ba yasa na fara k'ok'arin kiransa a daidai lokacin da kiran makociyata ya shigo Mmn Iman" Ina dauka tace "Lubna kin dawone"? "Na dawo Ina"? Shine tambayar da na mata cikin mamaki "Ina nufin kin dawo gidanki ne"? "Aaa Ina gidanmu mmn imam Mai zai dawo dani nida na zo gida haihuwa lafiya kuwa" "Eee toh lafiya ba lafiya ba wata naga kamar ta Shiga gidanki sai na dauka ko kin dawone" Kirjina wani irin bugawa yayi nace "wata kika.ga ta Shiga gidana wacce" "Nima bansani ba wlh ko bakuwa kikayi batasan bakya nan ba"? "Mmn Iman da idonki Kika ga mace ta shiga gidana Dan Allah jeki dubamin wacece" Tana k'ok'arin Magana na katse wayar da sauri ko dai budurwa Mahfuz ce taje har gidana dan taga bana nan,? Yanzu mahfuz zai iya cin amanata? Mikewa nayi da sauri hankalina ma na neman barin jikina sosai zuciyata ke sak'a min kila budurwar mijina ce taje har gidana, Wayar Mahfuz na Kira jikina sai bari yake sai dube duben mayafi ko hijabi nake akwai tazara daga gidanmu zuwa gidana amma tabbas zanje gidana na indai har naga mace wlh tallahi sai na raba ta da numfashin ta,Yana daga wayar nace "Mahfuz kana Ina"? "Gani a gida na shirya yanzu zan taho" "mahfuz karya kakeyi wlh mace ka kawo min har cikin gida sabida kaga bana nan, yanzu cin fuska da cin amanar taka har ta Kai ka kawo min mace gidana Mahfuz innalillahi wa Inna ilaihi rajiun" "Kanki daya kuwa wacce mace na kawo gidan kin fara ko" Mahfuz yace cikin dauriya numfashin sa na Neman daukewa "Ai gani nan a waje wlh tallahi idona idonta.mahfuz sai na rabata da numfashinta.mahfuz" Na katse wayar mahfuz yayi waje da sauri a daidai lokacin da ake buga kofar gidan Hankali a tashe ya d'auka da gaske Lubnar ce hakane yasa yayi Kan Hadeeza aguje baiyi wata wata ba ya rike hannunta ta ya fara janta ya kaita daya d'akin ya tura ta bandakin daya d'akin nasu "Mai haka mahfuz lafiya kuwa"? "Shiii kiyi shiru Lubna ce ta dawo" Cire hannunsa tayi daga bakinta tana "Toh sai me dan ta dawo ai ba wani Abu mukayi ba shine hankalinka ya tashi haka Mahfuz" "Dan Allah kiyi shiru Hadeeza Ina zuwa karkiyi magana " Yace tare da jawo kofar yayi waje da sauri Lubna Ina katse wayata Kiran makociyata na Kara shigowa wayata a daidai lokacin da na samu na tare abin hawa Ina dauka tace "gani a k'ofar gidan Ina kwankwasa wa" "Ki taimaka min mmn Iman Ina hanya yanzu dan Allah idan har Kinga mace a gidana ki rikemin ita har sai nazo Dan Allah dan annabi wata kwartuwa yarinya ce take bibiyar mijina" "Nidai Naga shigar mace banga fitowarta ba,ba lallai Kuma budurwar tasa bace kila bakuwa kikayi amma dai Ina kwankwasa k'ofar ba'a bud'e ba" Katse wayar tayi adai dai lokacin da Mahfuz ya bud'e kofar ganin mmn Iman ce dan.ya Santa yasa shi sakin ajiyar zuciya take zuciyarsa ta bashi ita ta gayawa Lubna mace tazo gidan,kila taga shigar Hadeeza gidan. Ko amsa gaisuwar da ta masa baiyi ba yace "Yanzu Mai amfanin abinda kika yi mace da cikinta kin daga mata hankali,daga gidan mu aka aiko min da abinci kanwata ce kuma tsabar munafirci shine Kika Kira lubna kika ce Mata mace tazo gidana dan Allah bakiji kunya ba da kika zo kina kwankwasa wa dan ki tabbatar toh kishigo kigani" Yace mata a dan tsawace Ja da baya mmn Iman tayi sam bataji dadin abinda lubna tayi mata ba "Wlh ba ni nace Mata mace tazo ba ni muciya nazo ara ma wlh" Tsaki Mahfuz yayi ya rufe k'ofar Mmn Iman itama ta juya da sauri ta shige gidanta bakin ciki Kamar ya kasheta banda b'atar basira da rashin hankali irin na lubna name zata kira ma mahfuz da zuwan zatayi ai bai dace ta kira mahfuz ba. Mahfuz kuwa Yana jikin kofa Yana ganin mmn Iman ta shige gida yayi sauri ya koma bandakin da Hadeeza take itama ta cika tayi fam,bata bari yayi magana ba ta fito daga bandakin ta fito palo ta d'auki Jakarta bata saurari mahfuz dake mata magana ba ta fice daga gidan tana zuba sauri mahfuz ya balain Kona Mata rai har mace yake tsoro haka Kamar wata uwarsa,har da kaita wani bandaki ya kulle wlh da ace ma tazo ba abinda zai hana ta fitowa ta ganta sai dai duk abinda zai faru ya faru,taya Mahfuz zai iya Kara aure Yana tsoron matarsa haka,yanzu Yana nufin ma yafi fifita matarsa akanta,duk wahalar nan da take sha akansa shine zai wani kaita bandaki ya b'oyeta sabida Yana tsoron kar matarsa ta ganta,shi daya Kamata ma ya fara gayawa matarsa tun yanzu akan aurenta zaiyi. Da tsanin bakin ciki ta isa gida tana zuwa ta hau watsapp ta fara zanna Masa ta WhatsApp akan ta gaji da wanan kumbiya kumbiya idan har yasan ya isa da gidansa ba tsoron matarsa yake ba ya turo manya gidansu. Mahfuz Wani irin Ajiyar zuciya ya sauke daya ga Hadeeza ta bar gidan,shi baiga abin Jin haushi dan ya b'oyeta ba yanzu da lubna tazo ta ritsa ta mai zai ce Mata har ga Allah bai tab'a tunanin zata zo Masa har gida batare da ko tsoro ba,har mamakin confidence dinta yake,Koda ba wani Abu suke yi ba ai bai dace lubna tazo ta ga ya kawota har gida ba, duk wanan munafikar makociyar tasu ce ta jaza Masa Kuma sai ya rabata da Lubnar baiji dadin fushin da Hadeeza tayi ba ya Kamata ta fahimce shi. Mahaukacin bugun da aka yiwa k'ofar yasa shi mik'ewa yayi waje ya ma riga da yasan lubnar ce sai daya je bakin k'ofa ya tuna bai d'auke basket din abincin ba Yana bud'ewa lubnar ta Fada gidan tana hucci Mahfuz kuwa ya hade rai Yana "Lubna daga yau karki sake ki Kara min wanan haukar ke yanzu ko tararki akayi akace miki na kawo mace gidanan sai ki yarda kina nufin zargina kike"? Ko ta kansa ban bi ba na ratsa gefensa nayi cikin gidan sai da na hau napep naji Kamar na rufe kaina da duka da nasani ban Kira shi a waya ba da tahowa kawai nayi da kila na ritsa Yar iskar yarinya,ai nasan dole ma kafin na dawo yasa ta gudu zuciyata ko gezau batayi ba na yarda dari bisa dari itace ta biyoshi har gida dan taga bana Nan, Basket din abincin dana gani ya tsakiyar palon ya Kara tabbatar min da zargina abinci ta kawowa mahfuz har gidan Aurena,kila ma har iskanci sun yi,dandaga muryar ta da naji da goyata da tace ayi nasan yarinya Yar duniya ce Yar iska Basket din na d'auka a daidai lokacin da Mahfuz ya shigo Yana cigaba da bambamin fadan zargin sa da nakeyi. "Mahfuz yanzu dan bana Nan shine zata kawo maka abinci har gida"? "Lubna Nagaji da wanan halin naki ni nace Miki macece ta kawo min abinci tunda kika tafi kabiru abokina yasa ake kawo min abinci wai wanan wane irin Hali Kika tsiro dashi ne?kishi hauka ne"? Ni kadai nasan halin da nake ciki jikina har rawa yake mahfuz na san sakamin hawan jini, palona na fara karewa kallo Ina ganin kamar Zan iya ganinta ma a cikin gidan, Ban bi ta kan masifar da yake ba na Mik'e da basket din a hannuna na Shiga dakina tamkar zan ganta a ciki Koda na Shiga ciki ma har karkashin gado na tsugunna na duba na kurawa gadona Ido naga ko an kwanta a akai shigowar mahfuz d'akin bai hanani cigaba da dube dubena ba Inda yaja wani dogon tsaki ya nufi wajen kayansa ya fara zurawa Na zauna a gefen gadon na zuba Masa Ido hawaye na zubo min "Mahfuz mai na maka dana cancanci haka daga wajenka, mahfuz ko aure zakayi bai Kamata ka kawo budurwar ka har cikin gidanan tazo ta gane min sirrina ba,mahfuz ni nasan ba rageka da komai ba Ina iya kokarina dan naga na faranta maka rai, a yanzu da nake d'auke da cikinka bai Kamata ka daga min hankali ba,wlh Tallahi budurwar ka tazo gidanan,mahfuz palona kamshin turare yake na daban da nida Kai mun San bamu irin wanan turaren har yanzu bamu yi shekara biyu da Aure ba,mahfuz mai kake nema a wajen wata da bani dashi,wlh tallahi yarinya da ta san Mai takeyi bazata ringa dafa maka abinci ba sabida tasan kana da aure, mahfuz bansan yarinya nan ba amma na mugun tsanarta mahfuz na yarda idan ma auren zaka Kara ka kara ka auri koma wacce Banda tsinanniyar yarinya nan da har dan bana nan zata biyoka har gida duk halin da kake ciki da ita nasani mahfuz magana ce kawai banayi,haka zamu kwanta dakai ka fita ka barni kaje kana waya da ita daddare wane irin kallo kake so tayimin shashasha ko wacce bata da matsayi a wajen mijinta?namiji shi yake fara siyawa matarsa mutunci da daraja a wajen budurwarsa,idan har kana min haka kana tunani ko Allah ya kaddara aurenka da ita bazata balain rainani ta ringa min gori ba,Kai kana tunanin idan ka auro mace irin wanan da bata damu da kana da Mata duk abinda ta ga dama shi zatayi da muyi fada da Kar muyi fada ba abinda ya dameta har kana tunanin zamu zauna lafiya idan ka aurota". "Hmm Ke dai kin d'auko wani banzan halin da bansanki dashi ba ni nace miki Ina neman aure ne,ai ko budurwa ma zan kula kinsan dai ba haramun bane Allah ya hallata Mana mu Kara auren ballantana ni bakiji a bakina nace Miki Zan Kara aure ba,amma tunda kin dorawa kanki balain kishi har dasu zargi ke Kika jiyo kizo muje na maidaki gida" Wani mugun kallo na watsa masa na kwanta akan gadon dan na dawo gida kenan,tunda abinda yakeso kenan na bar gidan Ganin na share shi yasa ya fice daga d'akin a daidai lokacin da mahaifiyata ta kirani Ina dagawa na bata labarin duk abinda ya faru na kara da "tunda har dan.bana gidan take kawo Masa abinci har gida gwara na dawo gidana mummy Nagaji yarinya Nan so take ta zautar dani" "Ke dai ba bazaki bi komai a hankali ba Zaki kuwa dorawa kanki hawan jini yanzu ke da kika je kinganta da idonki,a gaskiya kishin naki ya Miki yawa dole ki daura aure da hawan jini kuwa, nace kiringa bin komai a hankali,idan har namiji ya fara kulle kullen nan, wlh baki Isa ki Hana shi ba ko dafa kanki Zaki ringayi kina bashi Yana ci,wanan haukar kishin da kike sai dai yasa ma kifita a ransa kuyita fada dashi,yaji ya daina ma Jin dadin Zama dake a karshe ma ya fara Shirin auren amma tunda kin k'i bin shawara ta shikenan Anjima zan turo miki zainab ta zauna dake har ki haihun Allah dai ya kyauta" Daga haka ta kashe wayar Mahaifiyata bazata Gane halin da nake ciki ba ni nasan wanan yarinya da ta likewa mahfuz idan har banyi dagaske ba idan ni ban hanata shigowa ba fitar dani zatayi. Badan babu kyau zubar da abinci ba naso na zubar da abincin a karshe na bawa almajirai narasa Ina Iyayenta suke suka barta take aikin dafawa saurayi lafiyayyen abinci haka,waya sani ma ko zaman kanta take Yar iskar. Idan ferfesun mahfuz keso nima ya ringa siyowa yaga idan ban masa ba,duk bakin ciki da takaici ya cikani. Koda na Shiga gidan mmn Iman masifa ta hau yi tana "da nasan Zaki Kira mijinki wlh Tallahi da ban kiraki ba,Haka kawai kin zubar min da mutuncina yanzu zai ringa mun kallon munafika,ke sam baki iya ba da so kike ki tabbatar ko ki kamashi,ai da baki kirashi a waya ba da muka gama waya dake sai kizo ki ritsa shi gajen hakurinki ya Miki yawa" "Hmm mm Iman bazaki gane ba,kisa kaina a matsayin kece na kiraki nace ga budurwa ta shigar Miki gida baban iman na Nan wlh abinda nayi zakiyi" "Hmmm ai shikenan Allah dai ya kyauta" "Dan Allah baki ga fitowarta daga gidana ba Naga dai kayan abinci bansameta ba" "Ya zaayi ma kisameta kiringa da kin kirashi tab a gaisheki ni banga kowa ba dan gida nayi shigowa ta da mijinki ya rufeni da masifa na hada Masa munafirci" "Na Shiga uku mmn Iman ki kawomin agaji wlh yarinya Nan so take ta kwacemin miji ta k'arfi da yaji" Shawarwari mmn Iman ta hau bani akan na ringa daurewa Ina danne kishina zuwan zainab kanwata yasa nayi Mata sallama muka koma gida ta dora Mana abincin dare Ina ta tunanin Inda mahfuz yayi. Mahfuz kuwa Yana barin gidan, gidansu Hadeeza yaje. Da isar sa ta fito fuskarta a hade Mahfuz kuwa Sam bai lura da fuskarta ba shigar da tayi ne ya d'auke masa hankali dan indai lafiyayen namiji yaga a yanda yaga Hadeeza dole yaji ya harba Farar doguwar riga ta sa dayaje mata har kasa kana iya hango duk undies dinta har kalarsu. Yawu ya hadiye ya daure ya d'auke idonsa daga kirjinta Yana k'ok'arin Magana tace "Mahfuz idan har kasan kana Sona ka tura manya gidan mu ka daina b'ata mun lokaci a gaskiya Nagaji dan bazan zauna na ringa wahalar da kaina akanka alhalin ba Aurena zakayi ba,dan a yau na Kara tabbatar wa da cewar tsoron matarka kake ji bazaka ma iya Kara auren ba Ina kuwa dalili wlh indai dagaske kake.kana sona kazo ka samu babanmu idan Kuma kasan matarka tsoron ta kakeji bazata barka ka Kara aure ba tom sai mu hakura da juna dan a yau ka tsoratani"....... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 7* Wlh idan Kika ce Ina tsoron matata mamaki kike bani,haba Hadeeza karki manta fa gidan ta kikaje Taya zan bari tazo ta Sameki ai sai tayi mana wani fassarar,kamar ace ke yanzu muyi aure bakya nan kizo ki tarar na kawo mace gidan ya zakiji?ai ba batun tsoro bane,sanan zancen na turo mubi komai a hankali na samu na shirya a tsanake ,tunda kinsan ba yaudararki zanyi ba, idan har gurin manyan naki kikeso naje zanje na same su su san kina da tsayayye Nan da shekara mai zuwa sai a saka mana rana" "Tabdijam Nan da wani shekarar fa kace wane shiri zakayi haka,haba Mahfuz ka duba maganar nan taka,har sai wata shekara zamuyi aure,a gaskiya yayi nisa ni kaga idan har tunanin kashe kudi zakayi wajen yimin lefe ni na yafe lefen kayimin daga baya,wlh mahaifina kullum sai ya bugowa Abba waya akan na fito da mijin Aure,ni banga dalilin da baza muyi auren ba yanzu,dalili daya kawai zaka cemin zai saka kace min bazaka iya Kara aure ba tsoron matarka kakeji mahfuz a gaskiya lokaci yayi da zaka daina mata b'oye boye ka fito ka fada mata matsayina a wajenka,ni ka fara so kafin ka sota,ni ka fara sani kafin ka santa banda dai kaddara wlh da bata Isa ta sameka ba" "Ban da dai san zuciya irin naki Zaki ce koma Mai yafaru ai ke Kika jawo Hadeeza Kinga koma mene bai dace kiringa ganin laifina ba,a lokacin da na so aurenki ai k'i kikayi Kika ringa wulakantani wlh ba dan Ina kaunarki ba kinsan ko saurararki bazanyi ba a lokacin da naso muyi aure k'i kikayi sai yanzu ni Kuma da na riga da nayi auren zaki sakoni a gaba" "Kayi min gori mahfuz kayimin gori dan nace kazo muyi Aure" Hadeeza tace idonta cike da kwalla "Nifa ba gori nayi miki ba Wai inaso ki daina ganin Kamar k'in fitowa nayi na aureki zan aureki idan Allah ya yarda ki dan bani lokacin yanzu dududu shekara daya da wata takwas Aurena Kinga ya Kamata ace na bari na shekara biyu kafin na koma musu da zancen Karin aure" "Hmm" Kawai Hadeeza tace tana share hawayen daya zubo Mata "Haba Sweetyna kiyi hakuri dan Allah nifa bana san haka" "Yanzu dai yaushe zaka zo ka samu Abban mu yasan da maganar taka,zaka iya turowa fa inya so sai a saka shekara guda Kamar yanda ka bukatan" "Ki bari next week zanzo na same shi amma batun turowa ki dan bani lokaci Hadeeza wai ko dai yarinya auren take so hakane" Yace yana kanne mata Ido daya Ta sunkuyar da Kai tana "toh laifi ne dan naso auren masoyina" Murmushi Mahfuz yayi suka cigaba da hira a bai bar gidan ba sai da ya take cikinsa da tuwon shinkafa miyan kuka dayaji nama. Ba laifi kanin mahaifin Hadeeza nada rufin asiri Yan boko ne shiyasa basu damu da yanda Hadeeza ke aikin girki ba akwai komai a gidan enough,shi kansa mahfuz din da kwadayin yanda take zuba girki da namomi kaza kifi da sauransu yake, har ya Kai ma ko Lubnar tayi abinci sai yaji Kamar girkin nata bai Kai na Hadeeza dadi ba,bai sani ba ko dan ba kasafai yake Kai naman ayi girki dashi bane, Lubna ce ma ke dan k'ok'arin dafa abinci da Naman. Wajen karfe goma ya iso gida tun kan ya shiga gidan ya had'e rai dan Yana so ya nuna wa Lubna yaji Haushin zargin da ta masa dazu ya hada Mata da borin kunya,har ga Allah ya kanji Kamar baya kyauta Mata toh ya zaiyi shima zuciyarsa batayi shawara dashi ba ya fara san Hadeeza duka su biyun gani yake bazai iya rayuwa batare dasu ba. A Palo ya tarar da Lubnar da tsinin ciki ta baje a kasan kafet Zainab kanwarta na dadana mata kafa da ya kumbura,take yaji tausayin ta ya Kuma ji dagaske bai kyauta mata ba ko Yaya dai cikinsa take dauke dashi kulawarsa tafi bukata yanzu. Gaisuwar zainab din da ta mik'e da sauri ya amsa,ta nufi d'akin bakin Ya zauna shima a tsakiyar kafet Yana neman kwayar idon lubnar da ta sunkuyar dakai tunda ya shigo bata daga kanta ta kallesa ba. "Uwar biyu fushin kike dani kenan"? Ko kallonsa banyi ba na janye kafata daya fara k'ok'arin d'anna min, ko ganinsa bana san yi dan na riga da nasan wajen dai budurwarsa yaje da ta fini mahimmanci,a yau ma da na dawo gidana sati biyu rabona dashi,ba dokin zuwana yake ba,ba nice a gabansa ba budurwarsa ce a gabansa,wlh a baya ko fita nayi haka zai ta jera min Kira Yana tambayar na dawo,bazai daina kirana ba har sai na dawo gida hankalinsa zai kwanta,ni nake tilasta masa ya fita ma,yayi ta mitar korarsa nake, soyayya muke yiwa juna mai wahalar fassaruwa,mahfuz yaji dani ya soni,sai gashi lokaci guda ya canza min duk wanan soyayyar Yana neman rushewa a gaban idona, tunanin da nayi yasa hawaye zubomin na share hawayen naji saukar hannunsa a kumatuna ya dago fuskata "Lubna dan Allah ki daina sawa kanki damuwa wlh tallahi Ina kaunarki kina nan da matsayin ki a zuciyata,ki cire komai a ranki ni mahfuz nakine ke kadai" "Mahfuz wlh idan har kana kaunata Kamar yanda kace bazaka so bacin raina ba mai na rage ka dashi dan Allah,dududu yaushe mukayi Aure da zaka fara kula wata mahfuz Ina alkawarikan da kayi min,ko shekara biyu mahfuz har yanzu bamu yi da Aure ba har wata ta d'auke maka hankali akaina baka iya bacci idan baka ji muryarta daddare ba,har abincinta yafi maka nawa dadi, haba Mahfuz a haka kace kana kaunata,sati biyu rabona dakai amma na dawo ko a jikinka ka fice sai yanzu zaka dawo?Mai na maka dana cancanci haka daga wajenka dan Allah"? Na karashe tare da fashewa da kuka ya jawoni da sauri ya rungumeni tunda na fara magana Naga ya kyab'e fuska da alama maganganu na sun shige shi sai bubuga bayana yake Yana bani hakuri na janye jikina daga nasa Ina"Mahfuz Dan Allah wacce ita? "Dan Allah kibar zancen nan" "Dan Allah ka fadamin wacce ita yaushe kuka hadu"? "Tsohuwar budurwa ta ce lubna mun dade da haduwa da ita,Allah ne yayi bantab'a baki labarinta ba dan har ga Allah a lokacin da na had'u dake na shafe babinta a rayuwata" "Mai yasa baka aureta ba Mai ya rabaku"? "Wai Dan Allah Mai ya kawo tambayoyin Nan lubna"? "So nake na san matsayinta a wajenka Mahfuz" "Allah baiyi munyi Aure ba lubna sai a yanzu kaddara ta sake hada mu" Shiru nayi ina jin wani irin abu ya tokare min makoshi bana jin ma zan iya maganar so nake na auna maganganun sa "Wlh Lubna ita ta dawo rayuwata ta nace min na rasa yanda Zan yakice ta" "Kana santa Mahfuz ni ba mahaukaciya bace wlh nacewa juna kukayi,ba itace ta nace maka ba,yanzu aurenta zakayi kenan"? Na zuba masa Ido gabana na faduwa "Lubna mu bar zancen nan kema ko yanzu aka ce miki zanyi Aure ai zaki karyata kin isheni rayuwa" "Na isheka rayuwa kake kula wata yaudarar ta kake ko watsewa kuke idan har ba aurenta zakayi ba Mai amfanin kulata ka b'ata mata lokaci mahfuz"? Lubna dan Allah ki bar zancen nan haba kiji da cikin Nan dake jikinki muyi addua Allah ya saukeki lafiya haba Ina ta kwantar Miki da hankali kin kara dagawa kanki hankali" Yace a d'an tsawace tare da mik'ewa tsaye "Ga abincin ka nan ko kaje wajenta kaci"? "Lubna dan Allah kidaina min maganar wata idan har kina san mu daidaita dake wai wane irin dabia Kika samo haka mara kyau ni nace miki naci abinci" 'toh zauna kaci abincin" Tsaki yayi ya zauna duk da a koshe yake ya bude flasks din ganin faten doya ne yasa ya zuba kad'an ya fara ci yanda ya had'e rai yasa ban sake magana ba har ya gama cin abincin ya kwashe komai ya Kai kitchen. Ya dawo ya taimaka min na Mik'e muka Shige d'akin mu. Koda ba kallonsa nake ba idona na kansa Yana fitowa daga wanka ya kashe wayarsa ya jefa a side drawer ya Kwanta. Nima nayi Shirin kwanciya da maganganu a bakina amma akan dole na hakura na kwanta a gefensa. Ya mirgino kusa dani,muka faranta wa juna bana iya kwanciya ba tare da nayi wanka ba a dadafe nayi wanka sabida baccin daya cika idona Ina kwanciya bacci yayi awon gaba dani. A zababben ciwon Mara ne ya tasheni daga baccin daya daukeni Damko mahfuz nayi Ina sallati Dan ciwon maran haihu daban yake kamar yanda ake bamu labari nasan haihuwa zanyi A gigice ya mik'e Yana tambaya ta lafiya Dak'yar na hada Masa kalmar haihuwa zanyi. Wani irin dirowa yyi daga Kan gado ya kunna fitilar d'akin ya kalli agogo karfe uku da minti ashirin "Bari na leka gidan Hamisu ya taimaka min da aron motarsa Ina kayan naki yake" "Mummy ta riga da hade min shi waje daya kayiwa Zainab magana na karashe Ina Kara sallati dan ciwon gadan gadan ba kaukautawa ga wani abu Mai dumi danaji Yana bin kafata. Mahfuz shi ya taimaka min na saka Riga da zani hannunsa sakale a kuguna kamar Mai koyan tafiya mukayi wajen da Hamisu mijin mmn iman ke jiranmu dan cewa yayi shi zai kaimu daga shi har matarsa suna da balain kirki sun san Kuma darajar makota. Bansan sanda ma aka iso asibiti ba ban iya tafiya ba sai gado suka kawo da taimakon mahfuz suka dorani sukayi d'akin haihuwa dani zainab na biye dani Mahfuz sai sannu yake min hankalinsa duk a tashe. Da shigar mu d'akin da haihuwata baifi minti ashirin ba. Duk Wanda bai haihu ba ba lailai yasan darajar mahaifiyarsa ba Allah ya saka wa iyayenmu da Aljannatul firdausi banyi doguwar nakuda ba amma naci ubana bayana Kamar baa jikina yake ba. Sai da suka gyarani Suka gyara yarinya da ta d'auko kamani na ba Inda ta baroni amma bata kaini haske ba da alama hasken babanta ta d'auko ido kawai na zuba Mata Ina Jin kaunarta har a cikin raina. Muryar mahfuz danaji akaina yasa na d'auke idona daga kanta "Sannu Lubna sannu da k'ok'ari wanan diyar tawa ta baki wahala" Yace tare da daukarta yana murmushi. Nima murmushin na sakar masa. Bakinsa ya kafa a kunnenta Ina kallonsa ya gama ya kwantar da ita a gefena Yana "Sunanki na saka mata Allah ya Raya mana ita sai ki zab'a mata sunan da zamu ringa kiranta dashi" Har ga Allah naji dadi a raina ban manta da Addu'a mai nakuda karbabiya ce hakane yasa na zage nayi addua Allah ya raba mahfuz da tsinaniyar budurwar sa dana tsana tamkar mutuwata. Karfe bakwai na safe aka sallamo mu. Da taimakon kanwar mahaifiyata nayi wanka tayi wa mimi wanka sunan da za'a ringa kiranta dashi,baccin gajiya yayi awon gaba dani duk da ana ta tururwa shigowa yimin barka. Kukan da Mimi keyi yasa na bud'e idona babu ma ruwan nono haka Aunty Sa'a tace na bata no-no tana fita sai ga mahfuz ya shigo sai da ya gama tsokanata yake tambayar Koda wani abu da muke bukata, Girgiza masa Kai nayi dan bana Jin akwai abunda muke bukatan dan yayi Mana siyayya daidai karfinsa nama Mai yawa ya siyo aka saka min a fridge. Bakin da ake tayi yasa ya mik'e dan mahaifiyarsa ma tazo "Nidai bari na fita waje idan ana bukatar wani abu ki kirani na manta ma Abdul yace na gaisheki zai shigo Nan da jibi" Murmushi na saki dan muna shiri da abokinsa Abdul sosai Yana da matukar kirki Yana Kuma sona da Mahfuz aikine ya mayar dashi garin inyamurai. Har yaje bakin k'ofa nace "kaci abinci kuwa"? Gyada min kai yayi Yana "Na Sha kunu ama koshe nake ke kuwa na zama uba wa yake ta wani abinci. Murmushi na sakar Masa ya fice daga d'akin budurwar sa da ta fadomin yasa naji farinciki da nake ciki Yana neman gushewa,tun jiya dai banga alamar waya a hannunsa ba Addu'a nake Allah yasa maganganun da mukayi dashi jiya yasa ya canza alhamdulillah na haihu lafiya yanzu zan daura damarar kwato mijina na dawo da hankalinsa kaina da izinin Allah Mahfuz Yana fitowa daga d'akin ya Shiga daya d'akin da yawancin Yan barkan anan Suka zauna wasu Kuma a Palo,ba laifi lubna Yar dangi ce shima haka, Wajen Mahaifiyarsa Hajiya Ammi yayi dan so yake yace Mata fita zaiyi. Sai dai Yana gaya mata ta mik'e tana itama tafiyar zatayi ya sauketa a gida. Tare Suka fito daga gidan Bayan ta Kara yiwa Lubna barka. Har gida yaje ya sauketa baiyi niyyar shiga gidan ba tace ya shigo magana zasuyi. Yasan halin mahaifiyarsa da mita da kin d'auke Ido akan Abu duk kankantarsa duk tunani yake kila wani abun tagani a gidan nasa. Sai dai Yana zama tace "Dazu nan wata yar albarka tazo har gidanan ta gaisheni tace min ita budurwa ka ce yama take da suna yauwa Hadeeza yarinya tana kyau da hankali ga tarbiya wlh kaga ma abin arzikin da ta kawomin da ta tashi tafiya har dasu kyautar kudi da dukan alamu Yar baban gida ce"? Tace tana zaro turmin zani daga ledarsa har da mayafi da turare Tsananin mamaki ya hana mahfuz magana "Ammi Hadeeza ce tazo har gidanan"? "Eee fa wlh har gidanan tazo yarinya ta matukar burgeni a gaskiya Ina kaunarta kaga tsalallen atamfar da ta kawomin har da mayafinsa kaga na samu na sawa ma ranar suna" Tace tana washe baki Mahfuz kasa magana yayi dan har lokacin mamakin yanda Hadeeza tasan gidansu yake.har gidansa ma ta sani,haka kawai yaji baiji dadin zuwanta gidan su har tazo wajen Mahaifiyarsa ba wani zubin Yana ganin rawar kanta ba kad'an ba "Baka ce komai ba ka tsaya kana wani zare Ido ko bakaji dadin kyautar da ta kawomin bane ta girmamani a matsayina na mahaifiyarka yau naga yaro da yiwa uwarsa bakin ciki" "Wlh ba Haka bane Ammi ni mamakin yanda tasan gidanan nake" "Mai wani abun mamaki yarinya Yar arziki a Ina kuka hadu da ita ne"? "Ammi tsohuwar budurwa ta ce fa ita na fara nema kafin lubna Allah baiyi ita zan aura ba na auri lubna sai kuma yanzu ta dawo rayuwata,k'arfi da yaji so take muyi aure Bayan ban dade da auren ba,har ga Allah banida niyyar Kara aure yanzu amma ta dage min" "Aikuwa gwara ka daura damaran auren dan nikam tayi min haka nake san mutum mai mutunci da sanin ya Kamata,matarka tunda ka aureta sau daya ta taba bani turmin zani wanan kuwa bama ka aureta ba ta gwangwaje ni da irin zanin nan har dasu mayafi ga kudi Kuma habawa ai ka shirya Kara Aure insha Allahu" Yasan halin mahaifiyarsa Sarai wajen san abun duniya yasan kila ma ta zubar Masa da mutunci a wajen Hadeeza Sam baiji dadin zuwan da tayi gidansu ba. "Kayi mata godiya idan kaje" "Zan mata insha Allahu bari naje" Yace tare da mik'ewa yayi waje Yana k'ok'arin tayar da machine dinsa kiranta ya shigo wayarsa tun da ya baro gidansu jiya basuyi waya da ita ba dan wayarsa a kashe take bai ma kunna ba sai dazu da text dinta ya shigo bai Kirata ba dan so yake yaje inyaso ya fada mata haihuwar Lubnar daga wayar yayi Yana "Gani Nan zuwa yanzu" Ya katse wayar...... Kunsan yawancin novel dina true life ne na baya na canza na Kara daga wanan shafin zuwa na gama ya faru a gaske KAYAN MATA Assalamualaikum kina mace hadaddiya komi kincika ama kinada nakasu tawurin dadadawa miji? Shin kinkai kin isa kina gogayya d sauran mata Amma tafannin ozaroom mishkila tasamu? Shin sanyi y addabeki tayanda Baki iya gamsarda miji kullum kina makalemai yana kauda Ido? Shin minene matsalar? Kinshiga ko Ina kinnemi magani bawani chanji? Tosaurara yar uwata aminiyar arziki, ubangiji yakawo mikini har inda kike,kizo kiji qawata, Inada maganin sanyi me fatattakar kowani irin sanyi duk fitinarshi d izinin ubangiji seyabarki, Munada magungunan mata masu matuqar kyau,hadaddu gangariya kizama t gaban goshi,komi kikace oga yace don, 🥰 kikerewa sa'o'i, kizama abun riritawa abun tarairaya a kudi qalilan,karki cuci kanki kizauna kina cewa ayni nasan kaina,a inadin? Wallahi ko kanada kyau qara d wanka Kisha kiyi qattt kigigita oga, Munada tsumi nau'i nau'i Gumba ta madara,ridi,gyada,dabino,kwakwa,dasauransu Akway ruwan jaraba Ruwan Dadi Hadin minannas Hadin dafa kaza(manta uwa) Hadin yar gaban goshi, Turarukan mallaka. Duk a farashi mesauqi. Serious buyers call, WhatsApp 07046881166 Senajiku kusiya kuyi godiya Kuma kumin addua❤️nagode Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 8* Koda isarsa a karamin palon gidan da suke zance yayi zamansa Yana jiranta,tun kafin ta iso palon ya fara jiyo kamshin turaren ta, Hadeeza ba baya ba wajen saka turare a ransa Yana so ya nuna mata rashin Jin dadinsa da zuwa gidansu da tayi baya san garajen nan da takeyi yafisan su bi komai a hankali yasan Yana santa amma har ga Allah da san zuciyarsa ne babu bukatar wani Karin Aure,Sam baiji dadin yanda lubna duk ta dago halin da yake ciki da Hadeeza ba tun a jiyan ya daura damarar canzawa wajen iya takunsa sam bayaso ta ringa Jin kamar ya daina santa,yasan tana iya k'ok'arin ta wajen faranta Masa Sallamar da Hadeeza tayi cikin takunta najan hankali ya katse masa tunanin da yake ya dago idonsa Yana kallonta har ta samu waje ta zauna ta sakar Masa murmushi,dayasa ta kashe Masa jiki kwana biyun nan tana shigar dake dan bayyana surarta. "Sai yanzu ka tuna dani,jiya ko bacci banyi ba dan banji muryarka ba" "Lubna ta haihu fa an samu bby girl shiyasa Sam jiya ban bi ta Kan waya ba" Sai da ta dau tsawon lokaci kafin ta daure ta saki murmushi dan Addu'a tayi a ranta dama mutuwa lubnar tayi da tazo haihuwar "Masha Allah Allah ya Raya mana ita kace na samu takwara" "Sunan lubna na saka Mata zaa ringa kiranta Mimi ashe kinje gidanmu dazu"? Kamar ya watsa Mata ruwan zafi dayace sunan lubna ya sawa yarsa dan taji labarin idan har miji yasa wa yarsa sunan matarsa ba karamin kaunarta yake ba,bata so ta nuna Masa rashin Jin dadinta yak'e tayi tana "Eee dazu naje na gaida mama tunda baka tab'a cewa muje na gaisheta ba" "Dama kinsan gidanmu ne"? "Tunda har nasan gidanka sanin gidanku bazai min wahala ba Mama nada kirki wlh tayi min tarb'a Mai kyau da dukan alamu na samu karbuwa a wajenta ba nida wani fargaba" "Hmmm ai da kinn fada min zakije kila akwai shirin da zanyi kafin kije din amma tunda kin riga da kinje shikenan tace na miki godiya" "Ba wani damuwa ai nima mahaifiyata ce" "Hadeeza" "Naam" "Magana nakeso muyi mai mahimmanci Ina fatan Kuma Zaki fahimceni" Gaban Hadeeza yanke wa yayi ya fadi duk tunani take mahfuz cewa zaiyi tayi hakuri bazai iya aurenta ba bata iya cewa komai ba ta zuba Masa Ido "Kinsan dai Ina sanki Ina Kuma kaunarki,fatana Allah ya mallaka min ke Babu yaudara a tsakanina dake,da ace bana kaunarki bana Jin zan tsaya na ringa b'ata Miki lokaci ina b'atawa kaina,saura wata hud'u na samu shekara biyu da aurena,kafin ki dawo rayuwata wlh banida wani plan din auren Mata biyu a nawa tsarin mace daya ta isheni rayuwa sai dai idan Yana cikin kaddara ta sai na Kara Aure,Hadeeza Kamar yanda Kika sani a baya ni ba wani shahararren Mai kudi bane da na tada kai,rufin asiri gareni rayuwa ta a saukake nake yinta,kina kallo ko mota har yanzu bani dashi,dama burina bai wuce idan lubna ta haihu na fara tunanin yanda Zan samu motar ba,banida wani gida daya wuce Wanda Lubna ke ciki sai wani fili da na siya nida wani abokina Abdul komai a rayuwa sai kana tsarawa yanda bazaka yi abinda zai takura ka a yanzu nauyi ya Kara hawa kaina.tunda na fara tara iyali,Hadeeza abinda yasa nake Miki wanan maganar naga kin matsu kina so ko a yayane na turo muyi aure, inaso kisan komai sai da plan bana so muyi gaggawa ko garaje,inaso mubi komai a hankali a yanzu da Allah ya kaddara Zan aureki Zan fara shirye shiryen yanda Zan zauna da Mata biyu,dan haka zanzo na samu Abban naku yasan da maganar auren a bani lokaci na samu mu tsara komai,na biyu ba zancen Ina tsoron matata bane ko wani abu,inaso mu canza taku yanda ba zaa ringa saurin dago mu ba,wayar daren nan da mukeyi inaso mu hakura da wanan wayar, Idan na fito daga gida Zan Kira ki da kaina. kema kinsan Ina samun sarari Ina baki lokaci sosai a wajen chatting wanan shine maganar kawai dafatan Kuma zaki fahimceni" Ba karamin dauriya tayi ba wajen danne zuciyarta cikin yak'e tace "Na fahimceka wlh ba wani damuwa zan daina kiranka idan kana gidan kamar yanda ka bukata amma inaso kasan cewa wlh ba sharri a zuciyata bansani ba ko matarka wani abu tace maka kazo kake min maganganun nan" "Aaa wlh ba abinda tace min kawia naga ya dace yanda nake baki lokaci itama na ringa bata lokacinta Kinga bai dace na ringa shiga hakkinta ba ko" "Eee hakane kuma" Tace cikin yak'e tana "yaushe zanzo barka ne kaga ya Kamata naje naga 'yata" "Kai aaa Zan kawo Miki ita idan ta fara wayo" "Kasan kuwa next week su Abba zasu tafi umara wlh dukansu har da yaran ni Kuma wai na koma gida idan sun dawo sai na dawo" "Allah sarki kice zanyi missing dinki" "Tab ai ba Inda zani bazan iya kwana biyu banganka ba wlh" Dariya mahfuz yasa Yana "toh ya zaayi kenan"? "A jaka zan saka ka mu tafi can" Hira kawai suke mahfuz Sam baima San lokaci ya ja ba sai da aka fara Kiran sallah magriba yaso daga massallaci ya wuce gida Hadeeza ta hana shi har sai daya ci abincin dare a gidan. A lokacin daya isa gida har Lubna tayi bacci. Zainab da Aunty Sa'a kanwar mahaifiyar lubna kuwa Suna daya d'akin Yana jiyo hirarsu. Wanka kawai yayi yazo ya kwanta ganin Lubna na bacci yasa ya kunna data Suka hau chatting da Hadeeza da ta ajiye masa message rututu na irin kaunar da take Masa ta hada da ya turo mata hotunan baby. Sai da ya fara Jin bacci yayi Mata sallama ya kashe wayarsa. LUBNA Ba laifi naga canji daga wajen mahfuz tunda na haihu,ban sake ganin yayi wayar dare ba,idan ya dawo gida baya sake fita har a raina naji dadi Inda na ringa addua Allah yasa ya dore a haka Allah yasa ya rabu da wanan tsinaniyar budurwar tasa,har bincike nayi a wayarsa na shiga message dinsa da watsapp banga alamar lambarta ba a wayanda yake Hira dasu yafi hira da Abdul na Kuma ji dadi sosai. Ba laifi ya min dinki masu dan kyau da tsada daidai karfinsa duk da mummy ta riga da tamin dinkin fitar suna haka ma ta kusa cikowa mimi akwati da kaya. Hankalina kwance muka Sha Suna a ranar sunar ba inda Mahfuz yaje Yana nanike dani,Muna ta hotuna. Ko kunyar mutane bayaji da suka cika gidan,har anko mukayi dashi na wani blue shadda munyi kyau sosai Koda ba'a fada ba. Zuwan mahaifiyarsa Hajiya Ammi da ta had'e rai tana dan harararsa yasa ya bar wajena yayi waje. Koda na gaisheta Mimi kawai ta karba daga hannuna ta amsa gaisuwar ciki ciki nakan yi mamakin yanda take min,Banda matan yayyen mahfuz nace min haka halinta yake da nace sona ne batayi. Yan uwana sai da suka tayani kintsa koina Kamar ba'ayi taro a gidan ba kafin suka tafi Aunty Sa'a Dai sai ta Kara kwana biyu kafin ta tafi. Mahfuz Yaji dadin hadin Kan da Hadeeza ta bashi wajen daina damunsa a waya suna gama chatting yake gogewa gudun kar Lubna ta masa bincike a waya ta gani yafiso ta dauka sun rabu da Hadeeza Sam bayasan ta ringa zarginsa tana dagawa kanta hankali. Ranar suna da Mai kwalliya tazo ta rangada wa Lubnarsa kwalliya ba karamin kyau ta masa ba hakane yasa yayi ta zuba musu hotuna a wayarsa da mimi. Hotunan dayafi kyau ya zab'a ya Dora akan status da rubutun "Allah ya Raya mana Mimi ya baki lafiyar shayarwa Rabin Raina Ko minti biyar baiyi da sawa ba sai ga Kiran Hadeeza a wayarsa. Bai kawo komai ba ya daga wayar Kukanta ne ya karade wayar Sam baisan Mai yasa ta kuka.ba hakane yasa a rude ya hau tambayarta lafiya mai ya faru bata ce masa komai ba ta cigaba da rusa kuka. Katse wayar yayi ya haye machine dinsa yayi gidansu dan bata tab'a kiransa tana rusa uban kuka haka ba. A lokacin daya iso gidansu sai daya dade Yana jiranta kafin ta fito idonta ya kada yayi jajjur. Mik'ewa yayi da sauri dan ya d'auka ko wani ne ya mutu da sallati yace "Lafiya kuwa Hadeeza Mai faru A wajen kafarsa ta zauna ta Kara fashewa da kukan Ya zauna da sauri.yana "Hadeeza wai Mai yake faruwane" Dagowa tayi kafin ya ankara ta jawo hannunsa ta manna a kirjinta "kaji zuciyata Mahfuz kaji yanda yake bugawa,Ina da kishi mahfuz hotunan nan daka dora ya daga min hankali mahfuz anya kana Sona kuwa"? Tunda muke da Kai baka tab'a dora hotona ba" "Wai wane hotone ya daga Miki hankali hoton nida Lubna ko me"? "Gyada Masa Kai tayi har lokacin Tana kankame da hannunsa ba hotunan da sukayi tare da mahfuz ne ya daga Mata hankali ba bata kawo Lubnar ta kai haka kyau da haduwa ba,bata ga abinda zata Gaya wa Lubnar ba,sai taga ma kamar ta girmi Lubnar Sam ta kasa danne kishinta har sai data Kira mahfuz din,gani take mahfuz na iya kubce Mata kowane lokaci,tundaga lokacin daya kafa mata sharadin kiransa a waya,ta tsorata dashi,dan taga dagaske Lubna nada wani irin matsayi a wajensa abu.kadan na iya sawa mahfuz yace ya fasa aurenta. Tsananin mamakin Hadeeza yasa ya saki baki Yana kallonta kallon Anya ma tana da hankali kuwa hoton lubna ne bataso ya dora ko me "Yanzu ke kishin lubna kikeyi har dasu kukan ki yanzu laifi ne dan nayi hoto da matata matata ce fa ba wata ba"? "Mahfuz bazaka gane ba nidai dan Allah kayimin alkawari bazaka rabu dani ba duk runtsi duk wuya" "Wai duk hoton namune ya rudaki haka,lailai kinma fi lubna kishi to bakya so muyi hoton ne ko me" "Ni ba haka nake nufi ba" "Toh Mai kike nufi" "Nidai kayimin alkawari bazaka rabu dani ba" Girgiza Kai mahfuz yayi Ya hau dariya dan dariyar ma ta bashi biye mata yayi yace yayi alkawari kafin ta yarda ta cika Masa hannu tace Masa tana zuwa. Bayan minti goma sai gata ta dawo cikin kwalliya ta Sha shadda pink mai duhu ta kashe dauri, Da ido yake binta har ta zauna a gefensa kafadarta na guga nashi ga kamshin turarenta nan ya bade ko'ina. Bai san mai take nufi ba sai da ta d'auki wayar ta tana "nima hotunan zamuyi naji dadi dama bamu tab'a hoto ba tace tare da daga wayar murmushi kawai yayi ta hau yi musu hotuna har tana dadafa shi kamar irin couples dinan da basu Dade da Aure ba. Shi dai biye mata yayi sukayi tayi har da su videos sai daya gaji ya kwace wayar daga hannunta yana ya isa haka. Jera hotunan ta hau yi status sai duk yaji hankalinsa bai kwanta da dorawa da tayi ba duk da yasan Lubna ba saninta tayi ba yanzu idan ya ce ta cire sai ta masa wani fassarar. Yanda take wani nanarke Masa tana neman daga Masa hankali a banza yasa ya mik'e yace Mata zai tafi. Sai da ta raka shi har waje ta Kara komawa ciki ta d'auko leda mai dan girma ta bashi tana ya kaiwa yarta. Yakan yi.mamakin Inda take yawan samun kudin da take kashewa haka,duk da yasan shima Yana tura Mata kudi Dan Yana da acct number dinta sai dai kudin daya ke tura Mata bai Kai yawan hidimar da take dashi ba har dinkin shadda ta Masa da agogo da turare mai tsada lubna duk ta d'auka shi ya siyo da kudinsa. Godiya yayi Mata bayan ya roketa da daina dorawa kanta wahala haka. Koda ya isa gida a zaune ya tarar da Lubna tana shayar da Mimi yanda ta zubo Masa Ido yasa yaji duk ya tsargu sai yake ganin kamar zata gane wajen Hadeeza yaje. "Ina ta gwada wayarka tundazu Ina ka shiga ne"? Nace Ina Kare Masa kallo nidai duk da ban Kara Kama shi Yana waya ba idan har ya dan Dade a waje sai naji kamar zance yaje. "Ina can gida mun hadu da Yaya Mustapha" Ya mik'o min ledar hannunsa "ga Kaya nan inji wani abokina" Karba nayi na bud'e na fara fito da kayan ciki,kayane masu kyau da tsada wajen kala biyar sun balain yimin kyau "Wane abokin naka ne ya Mana abin arziki haka"? "Baki San shi ba a wajen aikinmu yake" "Aikuwa ya kyauta sosai kayi Mana godiya" Kai kawai ya gyada min ya hau Wasa da mimi. A yanzu dai Zan iya cewa banida wani matsala Ina samun kulawa sosai a wajen mahfuz, tuni hankalina ya fara kwanciya dan da alama yanzu baya tare da yarinya data so saka min hawan jini sau tari na Sha Masa bincike ban ga alamar bakon lambar da bansani ba. A yau da nasamu sati biyu da haihuwa baifi saura kwana shidda ayi babbar sallah ba bayan fitar mahfuz wajen aiki ya kirani a waya akan Abdul Yana hanya zai zo ya shigo garin na tanade shi. Nasan yanda Abdul yake a wajen Mahfuz aminan juna ne Yana da balain kirki Nima Ina matukar ganin mutuncinsa,baya Wasa da duk wani abu daya shafi Mahfuz duk da baya garin na haihu sai da ya hada kayan barka ya aiko Mana dashi. Kitchen na Shiga da kaina na fara k'ok'arin dafa fried rice a cikin awa daya na kamalla komai na gyara gidan zainab bata Nan taje gida ta dawo. Wajen karfe biyu naji sallamarsa tare da bugun k'ofar gidan. Hijabina na saka har kasa,naje na bud'e k'ofar fuskata d'auke da murmushi. Tsokanata ya fara yi Yana "Uwargida sarautar mata" "Dagani ba kari insha Allahu na karashe Ina "toh ashe da amaryarka kake tafe aa lalle marhaban shigo shigo. Nace Ina bawa macen dake biye dashi a baya fuskata washe ita kuwa sai wani sunkuyar da Kai take hannunta janye da dan madaidaicin trolley. Suna Zama na dauko musu ruwa da lemo Ina satar kallon budurwar Abdul din bana iya ganin komai na jikinta dan hijabi tasa har kasa fuskarta ce kawai a waje kyakyawa ce ba laifi. Mimi kuwa na hannun Abdul Yana ta mata Wasa "wato ka gaji da gorin auren da muke ma kenan" Nace ina tsokanar Abdul daya gyarawa Mimi Zama a jikinsa Yana "Tukunna dai wlh har yanzu ban samu wacce ta kwanta min ba wanan ai 'yar babar yayar mu ce da suke zaune a Lagos inaga mahfuz ya tab'a baki labarinta lokacin dayaje can Lagos din ko"? "Kwarai kuwa ya tab'a bani labarin yayarka ta Lagos" "Toh wanan yarta ce ta fari. Ta shigo garin nan ne zatayi wani training na kwana goma,shine nace bari na kawota nan ta zauna idan ba damuwa" "Haba haba ba wani damuwa wlh ai an Zama daya fatana dai ta saki jikinta Nan ma gidane ai" Muka hada ido da ita ta sakar min murmushi tare da sake sunkuyar da Kai,nikam yanayin ta ya burgeni da alama tana da nutsuwa da kamun Kai. Sai da suka ci abinci na Kai mata akwatin ta daya dakin. Muka dan tab'a hira da Abdul kafin yamin sallama.akan goben nan zai koma ya ajiye min kudi Mai yawa na hau yi mishi godiya har bakin k'ofa muka raka shi nida ummi bakuwar da mukayi sabida tsiya irin na Abdul Ashe bai fadawa mahfuz zai kawota ba Wai Idan ya dawo na fada Masa..... Wanan novel din na kudine a page 10 zamu gama free pages biya 500 dan ki samu kicigaba da karatunki cikin sallama tura 500 ta 2029764071 first bank nafisa Nuhu ko ta wanan 0000551222 Taj bank nafisa Nuhu turo da shaidar ta wanan lambar 08033719070 ko katin mtn ta wanan layin 08033719070 karku bari a barku abaya. KAYAN MATA Assalamualaikum kina mace hadaddiya komi kincika ama kinada nakasu tawurin dadadawa miji? Shin kinkai kin isa kina gogayya d sauran mata Amma tafannin ozaroom mishkila tasamu? Shin sanyi y addabeki tayanda Baki iya gamsarda miji kullum kina makalemai yana kauda Ido? Shin minene matsalar? Kinshiga ko Ina kinnemi magani bawani chanji? Tosaurara yar uwata aminiyar arziki, ubangiji yakawo mikini har inda kike,kizo kiji qawata, Inada maganin sanyi me fatattakar kowani irin sanyi duk fitinarshi d izinin ubangiji seyabarki, Munada magungunan mata masu matuqar kyau,hadaddu gangariya kizama t gaban goshi,komi kikace oga yace don, 🥰 kikerewa sa'o'i, kizama abun riritawa abun tarairaya a kudi qalilan,karki cuci kanki kizauna kina cewa ayni nasan kaina,a inadin? Wallahi ko kanada kyau qara d wanka Kisha kiyi qattt kigigita oga, Munada tsumi nau'i nau'i Gumba ta madara,ridi,gyada,dabino,kwakwa,dasauransu Akway ruwan jaraba Ruwan Dadi Hadin minannas Hadin dafa kaza(manta uwa) Hadin yar gaban goshi, Turarukan mallaka. Duk a farashi mesauqi. Serious buyers call, WhatsApp 07046881166 Senajiku kusiya kuyi godiya Kuma kumin addua❤️nagode *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *PAGE 9* Koda muka koma ciki,a kasan kafet ta zauna ta miko min hannu tana na bata mimi. Mik'a mata Mimi nayi Ina "Mai Kika zauna a kasa ki koma ki zauna mana akan kujerar" "Nan ma yyi Aunty ngd" "Kai Kai sunana Lubna ba Aunty ba" Murmushi kawai tayi ta cigaba da Wasa da mimi tana ta zuba mata kiss a fuska ni.kuwa take ta sake burgeni ni nasan Zainab gajiya tayi ta gudu toh tayi a banza tunda na samu Yar tayin hira. Hira na fara janta dashi Ina dan jefa Mata tambayoyi duk dan ta saki jikinta,anan take fadamin ta kamalla degree dinta tana neman aiki, shine kafin su dauketa suka turota nan ta danyi wani programme a shiyarsu ta nan. Ina da saurin sabo da mutum kamar na dade da saninta haka na hau janta da hira bamu tashi ba sai da aka Kira sallahr laasar. Na nuna Mata d'akin bakin akan ta Shiga ciki tayi sallarta. Nima na shige d'akina dan na canzawa Mimi Pampers dan bansamu tsarki ba tukunna Ina cikin sawa Mimi Pampers Kiran Mahfuz ya shigo wayata Ina dagawa yace "Ashe har Abdul ya tafi yanzu nan ya kirani Kuma kinsan dan wulakanci bai biyo ta office dina ba wlh sai na Masa rashin mutunci" Murmushi na saki Ina "kunfi kusa kaima kasan bazai tafi batare da ya ganka ba kila anjima kaga ya dawo,tare yazo da wata bakuwa Wai zata yi wani program Yar yayarsa ta Lagos bansan bai fada ma ba sai daya zo tafiya Wai Idan ka dawo na fada maka" "Wlh Abdul ya Raina ni yanzu nida gidana zai kawo min wata bai nemi izini a wajena ba" "Kai Kam da rigima kake wlh yanzu dan Yar yayarsa zata zo tayi kwana biyu a gidanan shine sai ya nemi izininka"? Tsaki yayi Yana "Zan Masa rashin mutunci ai sai mun hadu dashi tukunna" Murmushi na sake yi nace "ba ruwana Ina daga gefe" "Ina Mimi"? Gata nan yanzu nan na canza Mata Pampers goyata zanyi na Shiga kitchen Hira Muka dan Kara tabawa kad'an kafin ya kashe wayar na goya mimi na fito nayi kitchen banga ummi a palon ba nasan tana cikin d'akin kila hutawa take tunda Lagos ba nan ba duk da banga alamar gajiya a tare da ita ba kila jirgi suka hau dan su Abdul din nada rufin asiri. Ina cikin kitchen din na jiyo muryar Mmn iman tana kwankwasa k'ofa. Ajiye muciyar hannuna nayi naje na bud'e Mata k'ofar ta shigo da ledoji a hannunta ko bata fadamin ba nasan na menene kayan gyara ta kawo min dana bata sautinsa dan so nake na tsantsame kafin na samu tsarki. "Ke Kaya masu zafi ta kawo wlh sai kinyo ciko" Gefenta na zauna na fara duba kayan a daidai lokacin da ummi ta fito daga d'akin motsinta yasa muka dago muna kallonta nace "kinfito kenan da zan shigo nace ban sani ba ko baccin gajiya kike" Murmushi tayi a daidai lokacin da ta karaso wajenmu ta zauna a kasan kafet tana "Aa idona biyu ai ba wani gajiya da nayi tunda jirgi muka biyo Ina wuni" Ta gaida mmn iman ta amsa cikin sakin fuska tana "kice bakuwa kikayi"? "Eee wlh tun daga Lagos tazo" Na bawa mmn Iman amsa na cigaba da duba jarkokin tsumin data shigo dasu da dan bokitin da aka dafa min ciccibi a ciki. Kice Abban Mimi zai Sha Dadi na kashewa mmn Iman Ido data dafe baki tana "lah bakida kunya fa agaban bakuwar kike badala ko dai matar aure ce"? Sunkuyar da kai tayi da muka hada ido da ita dan ni banma San kallona take ba Murmushi nayi Ina "ba matar Aure bace wlh Mai dan nayi wanan hirar a gabanta ai Yan matan suma yanzu sun San komai" Na karashe Ina dariya a daidai lokacin da nake dandana wani zuma Nan ma na sake hada Ido da ita ta sunkuyar da Kai da sauri Mmn Iman tace "nidai mallama ki bani cikon kudin dana ranta Miki" "Har nawa Kika ranta min"? "Dubu bakwai na cika Miki wlh" "Kai dubu ashirin na baki fa" "Kwarai kuwa ai kayanta masu kyau ne da tsada wlh tamkar budurwa Zaki koma duk Inda Kika saka kafarki bbn mimi na biye dake" Washe baki nayi Ina "Zan baki kudinki idan na Kai shi duniyar can kila na baki fiye da Dubu bakwai din" Tafawa muka yi da ita ta mik'e tana "naji ma kamar abincin da kika Dora na kauri bari naje Nima na dora nawa girkin na biye miki ba abinda zan zanyi. Tayi hanyar waje nayi mata godiya tare da kwashe kayan da dan bokitin cicicibin nayi hanyar kitchen dan a kitchen nake ajiyar irin kayan nan sabida wani zubin mahfuz akwai dube dube,Ina zuwa bakin k'ofa naji muryar ummi tana "Aunty ba abinda zan kama miki a kitchen din"? "Lah tuwone kawai zanyi ba abu Mai yawa ba inada Miya dama ngd ki saki jikinki dan Allah Nan ma gidane ki kunna tv kiyi kallo" Ina daga kitchen din nake Mata maganar na fara k'ok'arin tuka tuwon. Muryarta da naji a bakin k'ofa yasa na juya "Bari na Kama miki wani Abu aunty ki kawo na tuka miki" "Kai haba wlh ki barshi" Dak'yar.na samu ta koma Palon na tuke tuwon na kwashe. Na Kara gyara ciccibin da aka kawomin na dumama na juyo a plate na dauki tsumi daya da na zuba a fridge din kitchen na nufi palon. Tana zaune wanan Karin a saman kujera tana latsa wayarta har yanzu da hijabinta a jikinta har kasa. "Wai bakya Jin zafine ki cire hijabin naki ki Sha iska Mana dagani sai ke a gidan fa kin k'i sakin jikinki" Murmushi tayi bata ce komai ba na kwantar da mimi akan kujera na zauna a kasan kafet na mik'ar da kafafuna sabida naji dadin cin cicibin. Ban taba ci ba na dauka dadi ne dashi ai Ina kaiwa bakina naji daci daci na kwabe fuska Muka hada Ido da ita dama tunda zu Ina Jin idonta a kaina Dak'yar na hadiye Ina "Kai kinji daci kuwa da kina da Aure da kinci kinji" Murmushi ta sake yi wani zubin Ina da surutu na hau zuba "Kinsan mace sai da gyara idan baka dage kayi gyaran nan ba sai namiji ya fara k'ok'arin hango ta waje kuma idan mace ta haihu Salam take komawa dole sai ta zuba gyara sosai zata koma yanda take sai kinyi Aure zaki gane haka,Amma dai kin kusa shiga daga ciki ko"? "Eee" Washe baki nayi Ina "Masha Allah ansa Rana.kenan kice Muna da zuwa Lagos Shan biki dama ban taba zuwa ba Kinga ta silarki sai naje" "Insha Allahu" "Saura wata nawa"? "Saura wata uku" Masha Allah Allah ya nuna mana shima acan Lagos din yake"? "Eee acan yake" "Saurayine ko Mai Mata,kiyi hakuri Kinga Ina ta zuba miki tambayoyi" "Lah ba komai wlh Mai Mata ne" "Kash amma banji Miki Dadi ba auren mijin wata ai bashida wani dadi,ki more aure shine ki samu santalellen saurayi ki aura ku Sha soyayyar ku,kai amma na tausayawa wacce zakije ki tarar nasan tana nan zuciyarta kamar tayi bindiga kishiya ba dadi sam Allahu ya tsare mu da ita ya nisanci mazajen mu da tsinannun Yan matan Nan dake makale wa mazajen mutane,kiyi hakuri fa karki ce da ke nake wlh nima Ina da wata shegiya da ta makalewa mijina sai da nayi da gaske suka rabu matar saurayinki Allah ya bata hakuri da juriya kema dan Allah karki cutar da ita" "Aunty ai har yan matan baa san ransu suke auren mai Mata ba sai dan kawai ya tsago a kaddararsu nima saurayi naso aura Allah baiyi ba toh ya zakayi da kaddara" "Hakane Kam mudai Allah ya rabamu da mumunan kaddara" Ji nayi nama kasa cin ciccibin hararowa nake ni zaa kawo yarinya irin ummi,satar kallonta nayi Muka hada Ido,ta sakar min murmushi ta sunkuyar da Kai Ni kuwa ban d'auke idona ba na zuba Mata Ido,doguwa ce mai zagayyen fuskan hancinta nada tsayi gashin girarta yakusa hadewa waje daya,tana da dan.manyan ido,da karamin baki,bata fiye duhu ba bata fiye haske ba,duk da banga kalar jikin nata ba,daga zaunen da take Ina iya hango tudun kirjinta indai ba ciko tayi ba tana da na fulani manya kiris ya rage ta shiga sahun masu kib'a indai kishiyar tata ba mai balain zafi bace lailai wanan zatayi saurin kwace shi,badan tace an sa Mata rana ba da gidanmu Zan kaita wlh bazan bari ma mahfuz ya ganta ba na ayyana a raina. Kiraye kirayen sallah magriba yayi daidai da tsayuwar machine d'in mahfuz a k'ofar gida. "Aikuwa ga maigidan ya dawo" Mik'ewa tayi da sauri nace "A Ina zakije ki koma ki zauna idan ya shigo ku gaisa" Komawa tayi ta zauna a kasan kafet ta sunkuyar da kanta sai Wasa take da zoben hannunta inasan yanda take da dan kunya. Shigowar mahfuz da sallama yasa na m'ike Ina "oyoyo Abban Mimi" Na karbe ledojin daya shigo dasu Ina ta mamakin ko dai kudi ya samu haka da yawa wanan uban leda haka. Wajen da Mimi ke kwance ya nufa bai ko kalli b'arin da ummi take ba ya d'auki mimi a daidai lokacin da ummi ta Masa sannu da zuwa sai a lokacin ya kalleta ya amsa ya d'auke idonsa daga kallonta a daidai lokacin da ta mik'e ta nufi daya d'akin sai dana tabbatar da ta shige ciki nace "itace wacce Abdul ya kawo bakuwar tamu" "Naganta takura Mana kawai yakeso yazo yayi dan rainin hankali" Kasa yayi da murya ya matso kusa dani yana "Wai kina nufin a wancan d'akin zata zauna"? "Emana da a Ina kakeso ta zauna"? "Lallai bakida hankali,ga dakinmu ga d'akin da take ciki kinsan kuwa duk motsin da akayi a daki ana jiyowa" "Kai jamaa toh Ina kakeso na kaita"? "D'akin tsakar gida amma zamanta anan ai da takura gaskiya" "Haba Mahfuz d'akin tsakar gida sai kace namiji taya zan sauketa a tsakar gida sai nake ganin kamar hakan bai dace ba ko Abdul ne yazo gidanan yaga na ajiyeta a tsakar gida zaiji ba dadi wlh" "Wlh ba abinda ya shafeni nida gidana baza'a a zo a takura min ba a d'akin tsakar gida zata zauna na gama magana" Ya fara k'ok'arin mik'ewa yanda ya had'e rai.yasa ban Kara magana ba na fara bude ledojin daya shigo dasu,gwanwanin Madara ne dasu bournvita har dasu cornflakes, siyayya sosai har dasu kifin gwangwani da balangu bredi mai yanka yanka mamaki yasa nace "A ina ka samo kudi haka mahfuz" "Wlh wani kudi yau aka raba Mana shine nayo Mana siyayya" Tunda na aure shi bai tab'a yo Mana irin wanan siyayyan ba, shiyasa mamaki rufeni farinciki Kuma ya gaza b'oyuwa a fuskata,dan dama ni mayyar cornflakes ce dan sacet nake siyowa "Yeee nima na faso gari mun zama yan gayu Kai wanan bakuwar ta zo da goshi" Bai kulani ba ya nufi daki Yana bari yaje yayi alwala Cikin farinciki na kwashi kayan na Kai kitchen na hau jerawa a dan glass din dake kitchen din har dasu bama ya siyo Mana na kuwa ji dadi sosai. Sai da na gama jerawa na dauki balangun na juye a plate na dibar wa ummi na saka mata tuwo mulmule biyu da Miya na dauki karamin exotic na hada a faranti gabad'aya na Kai Mata har daki a kwance na tarar da ita da alama daga wanka ta fito dan jikinta da lema ta saka karamin t shirt da bakin dogon skirt,sai da gabana ya Fadi dana ga surarta take na karbi shawarar mahfuz na in maidata d'akin tsakar gida tab. Tana ganina ta rarumo hijabi tasa ta tareni tare da karbar farantin hannuna tana "Sannu Aunty" "Yauwa nace Mata cikin murmushi Ina ga abincin ki nan idan kin gama ci zanzo na Kai ki d'akin can Kamar sai kinfi sakewa acan" "Toh Aunty ngd da dawainiya" "Lah ba komai na sakar mata murmushi na fito daga d'akin. Na Shiga nawa mimi ce kawai a kwance da alama mahfuz ya fita massallaci. Wanka na Shiga dan tuni na watsar da wankan jego na koma normal wanka. Ina fitowa daga bandaki yayi daidai da shigowar mahfuz bai d'auke idonsa akaina ba ya zuba min Ido Nida kayana nasan hali, ya matsu yaga Ina sallah "Mallama Wai har yanzu shiru nafara gajiya fa" "Tab kwana ashirin kawai da haihuwa sai nayi arbain fa" "Wlh baki isa ba tab so kike na mutu kenan ya zauna a gefen gado,na gama shafe shafena na saka kayan shan iska. Ina sai kayi sallah zamuci abinci ko na zubo yanzu"? Bari ayi sallah Isha Kar nazo na kasa tafiya massallaci. "Tom mu tafi Palo mu zauna" Na dauki Mimi nayi gaba ya biyoni a baya. A Palo muka zauna Muna kallo muna tab'a hira Yana latsa wayarsa hankalinsa dai Yana Kan wayar gabad'aya. Sai ni kedai ke zuba surutuna har aka Kira sallah Isha ya fita massallaci bai dawo gidan ba sai wajen tara daga zuwa massallaci abincin ma da na jera Mana ya hucce tuni na cika nayi fam zuciyata ta fara rayamin kodai zance yaje take naji hankalina ya tashi,Ina tsoron tsinaniyar yarinya nan Mai nacin tsiya ce ta dawo rayuwar mijina wayata na d'auko dan na kirashi sai gashi ya shigo,da carbinsa a hannu da jalabiyar sa. "Daga zuwa massallaci abban Mimi"? Ina k'ofar gida wlh da Hamisu muke ta hira da kin leko zaki ganmu ai Sai a lokacin hankalina ya kwanta Muna cikin cin abincin Muka ji motsin bud'e k'ofar d'akin sai ga ummi ta fito da dogon hijabinta har kasa mahfuz ko kad'an bai dago ba Ina k'ok'arin Magana tace "Aunty dama bacci nakeji shine nace ko Zaki nunamin d'akin"? Mik'ewa nayi Ina sude hannuna nace "eee zomuje nama dauka kinyi baccin ne wlh' Nayi gaba tana bina a baya har muka fice daga palon,dama d'akin duk da baa kwana a ciki Ina yawan gyarawa Ina Kuma turarawa sai dai ba bandaki a ciki, bandakin a tsakar gida yake idan nayi baki da bandakin tsakar gidan suke amfani ,Yan uwa ke Shiga bandakin cikin daki. Muna Shiga d'akin nace "dafatan d'akin ya Miki"? Kai sosai ma wlh yayi aunty ngd Allah yasaka da alheri" "Lah ba komai ai an Zama daya sai dai nace sai dasafe kenan" "Toh aunty sai da safe a shafa min Kan Mimi" Da murmushi na amsa Mata na fito daga d'akin. Sai da muka gama cin abincin na kwashe komai na Kai kitchen na dawo na tarar da mahfuz na latse latse a wayarsa. Nima wayata na d'auko na hau latsawa Ina chatting Ina kallo kafin goma naji bacci ya fara k'ok'arin daukana. Hakane yasa na kashe data na kalli mahfuz daya danke wayar sa da hannu biyu nace "Tom nidai bacci nakeji zanje na kwanta" "Kije kiyi kwanciyar ki dan ni ba bacci nake ji ba ko na biki daki ciwon maran zaki sani a banza nidai na fara gajiya fa tam" "Kazo muje mu kwanta na maka tausa wlh Zan maka dabaru" "Naki fa kibar ni na cigaba da hira da abokina" Ya hasko min fuskar wayarsa Inda naga sunan Abdul din da Abokina "Ai shikenan sai ka shigo" Bai bani amsa ba Ina shiga ciki na canza kayan jikina zuwa na bacci Ina kwanciya bacci yayi awon gaba dani bansan lokacin da ya shigo ba. Washegari da wuri na tashi dan na hada breakfast dan mahfuz da wuri yake fita. Ina cikin soya dankali naji sallamar ummi. Na amsa Mata daga kitchen ina mamakin me ya sa ta tashi da wuri haka. Har kitchen tazo ta sameni muka gaisa da ita Ina satar kallonta Ina San yanda take shigar hijabi har kasa da alama tana da kamun Kai "Aunty Ina tsintsiya nayi shara"? "Ummi dan Allah koma kiyi kwanciyarki dan kawai ki tayani aiki Kika taso" "Dan Allah karki hanani tun jiya nakeso na tayaki kina hanani" karfe Tara zanje wajen da zamuyi program din shiyasa na tashi da wuri" Duk yanda naso hanata ki tayi akan dole na nuna Mata wajen da tsintsiya yake ta d'auko ta fara share palon. Har tsakar gidan naji tana sharewa. Sai da ta gama ta Kara shigowa da bokitin mopping da abin mopping din tana cikin mopping mahfuz ya fito daga d'aki cikin shigar suit sai kamshin turare yake. Adaidai lokacin da Nima na fito da farantin abincin karyawarsa. Gaisuwar ummi ya amsa ba yabo ba fallasa ya tambayeta ya bakunta ta sunkuyar da Kai tana murmushi nidai idona nakanta atoh karta sake ta kallarmin miji ganin na ajiye farantin a gabansa yasa ta ajiye abin mopping din tana "idan ya gama na dawo na karasa" Hankalinta na Kara gani,dan naga tana nesa nesa da mijina haka nakeso shima mijina ya iya tsare gida. "Mai kike murmushi ke kadai"? Tambayar da mahfuz ya jefomun kenan "Wlh yarinya nan nada hankali mahfuz da gani ta samu tarbiyya sosai duk da a Lagos take zaune" Tab'e baki yayi bai ce min komai ba Nima ban Kara magana ba har ya gama cin abincinsa Ya Mike zai tafi na tafi dan na raka shi munje bakin k'ofa ya juyo Yana "Na manta ban fada Miki ba Abdul jiya yace na fada Miki wanan yarinyar ba komai ta iya ci ba ya roki arzikin a ringa tambayarta abinda zata ci ko a barta ta dafa abinda takeso dakanta wlh badan kin dage ba da sai na Masa rashin mutunci nida gidana azo ana min iko" "Allah sarki wlh ba damuwa ai kana ganinta kasan Yar hutu ce ba irinmu da duk abinda muka samu ci zamuyi ba Tom ba damuwa ai tunda ba laifi muna da Abubuwan Yan gayu yanzu a gidan idan ma cornflask take so ta ringa Sha gashi nan" "Ku kuka sani" Yace a daidai lokacin da ya ida fitar da machine dinsa ya tayar ya tafi Ina daga masa hannu. Ina komawa ciki na karasa mopping din na turara koina kafin na koma d'akin Ummi dan na tambayeta mai zata ci. Kwalliya na tarar tanayi a lokacin da na Shiga tana ganina ta saki murmushi tana "so nake na shirya kar nayi latti" "Kina nufin bazaki karya ba Zaki tafi nidai na soya dankali da kwai sai kayan shayi bansani ba kinaci ko bakya ci idan bakya ci sai a sama Miki wani abu dan Abdul yace Wai ba komai kike ci ba" "Eee wlh aunty duk wani abu Mai maiko ban fiye ci ba da safe nafiso nasha corn flask haka ko bakin tea" "Toh shikenan ki gama shiryawan akwai cornflask sai ki hada ki Sha" Godiya tamin na sakar mata murmushi na fito. Ban Dade da fitowa ba sai gata ta shigo da dogon hijabinta har kasa da farin glass. Tana Zama na dauko mata kofi da cokali da tuni na ajiye Mata Madara da cornflask din Cikin nutsuwa ta hada ta Sha sai satar kallona take narasa Mai yasa take San satar kallona. Tana gama Sha ta mik'e da Yar Jakarta tana "Bari naje kar makara sai na dawo" A dawo lafiya" ta fice daga gidan ni Kuma na koma daki. Ina kwanciya mamn Iman ta hau bugun kofa tana kwallamin Kira Ko mai take nema a wajena da sassafe haka oho na mike nayi hanyar waje........ Karku manta a gobe zamu gama free pages insha Allahu ku biya 500 ta 2029764071 first bank nafisa Nuhu ko ta Nan 0000551222 taj bank nafisa Nuhu ko katin mtn a turo da shaidar biya ta layin nan 08033719070 yanzu zamu shiga cikin labarin budurwar mijina karki sake a barki a baya KAYAN MATA Assalamualaikum kina mace hadaddiya komi kincika ama kinada nakasu tawurin dadadawa miji? Shin kinkai kin isa kina gogayya d sauran mata Amma tafannin ozaroom mishkila tasamu? Shin sanyi y addabeki tayanda Baki iya gamsarda miji kullum kina makalemai yana kauda Ido? Shin minene matsalar? Kinshiga ko Ina kinnemi magani bawani chanji? Tosaurara yar uwata aminiyar arziki, ubangiji yakawo mikini har inda kike,kizo kiji qawata, Inada maganin sanyi me fatattakar kowani irin sanyi duk fitinarshi d izinin ubangiji seyabarki, Munada magungunan mata masu matuqar kyau,hadaddu gangariya kizama t gaban goshi,komi kikace oga yace don, 🥰 kikerewa sa'o'i, kizama abun riritawa abun tarairaya a kudi qalilan,karki cuci kanki kizauna kina cewa ayni nasan kaina,a inadin? Wallahi ko kanada kyau qara d wanka Kisha kiyi qattt kigigita oga, Munada tsumi nau'i nau'i Gumba ta madara,ridi,gyada,dabino,kwakwa,dasauransu Akway ruwan jaraba Ruwan Dadi Hadin minannas Hadin dafa kaza(manta uwa) Hadin yar gaban goshi, Turarukan mallaka. Duk a farashi mesauqi. Serious buyers call, WhatsApp 07046881166 Senajiku kusiya kuyi godiya Kuma kumin addua❤️nagode *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* *LAST FREE PAGE* *PAGE 10* Ina bud'e kofa na yamutsa fuska Ina "Shi bawa bazaa barsa ya huta ba" "Eee baza'a barki ki huta ba wuce muje" Dariya nasa dan muna Yar Wasa da mmn Iman sosai muna Shiga ciki ta zauna a dogon kujera tana kalle kalle nima na zauna a kujera mai kallonta Ina "kefa wani zubin kanki ba dadi Mai kike dubawa ne" "Mai nake dubawa kuwa so nake na tabbatar da ba kowa a gidan kafin nayi magana duk da Naga fitar mahfuz da bakuwarki" " Ba kowa dagani sai Mimi kin samo mai zafi kenan"? Nace Ina maida hankalina gabadaya kanta dan Naga alamar da magana tazo Mai mahimmanci "Eee da magana nazo Kam amma nariga da nasan halinki gajen hakuri baki iya bin komai a hankali ba" Mik'ewa nayi da sauri na koma gefenta na zauna Ina "Mai ya faru mmn Iman bani labari" "Wai ya kuke da bakuwar nan da tazo jiya"? Yamutsa fuska nayi Ina "Wai Ummi"? "Eee" "Ba dangi iya babu na baba Ina Abokin Mahfuz Abdul da nake dan baki labarinsa Yana yawan yi Mana aike har kike cewa idan kina da kanwa da kin bashi" "Eee na tuna shi" "Toh yarinyar yayarsa ce suna zaune a Lagos tazo nan wani program ne na sati daya ko kwana goma yace ne jiya dai da kansa ya kawota,lafiya kuwa kike tambayeni"? Ajiyar zuciya ta sauke tana "Ni yarinya Sam ban yarda da ita bane naga tana ta Abu kamar mara gaskiya,kinsan jiya nan Ina zaune wlh satar kallonta kawai nake ni a idona ma sai naga kamar kallon banza take miki kasa kasa" Dariya na kwashe dashi Ina "Kai mmn Iman abin naki har da sharri yarinya da ko kallona bata iya yi ga kunya" "Kefa dadina dake hauka wlh Ina miki maganar serious shi Abdul din duk wayanda ya sani anan ga gidansu mahfuz Mai yasa bazai kaita can ba sai nan, Taya zaa kawo Miki tsalleliyar budurwa irin wanan haba mana" "Wani kusancin ai yafi wani mmn Iman shiyasa ya kawota nan Allah sarki kawata tsoro kike zaa kwace mun miji ko" Na kyalkyale da dariya mmn Iman ta zuba tagumi tana kallona "Kwantar da hankalinki ba Mai kwace min miji mahfuz Zan iya rantse Miki ba lailai yasan kamaninta ba dan ko kallonta bayayi,itama ba lailai tasan kamaninsa ba dan tana ganinsa take sunkuyar da Kai" "Tom ai shikenan amma nidai ban yarda da ita ba wlh masu shiru shiru da saka hijabin nan wlh munafikai ne,a idona jiya ta Miki kallon banza ke Kuma ga saurin sakin jikin balai name kike wani janta da hira" "Kai mmn Iman bakonka annabinka so kike na hade rai,nifa kinsan ban iya wulakanci ba" Mmn Iman shiru tayi dan ba iya maganar da ya shigo da ita kenan ba,jiya taji mahfuz nata waya a k'ofar gidan ta har makalewa tayi a jikin kofa dan taji Mai yake cewa soyayya yake zubawa a waya da wata taso ta fadawa lubna ta saka mishi ido amma tuna haukar data Mata kwanaki yasa ta hakura" Maganar lubna ya katse Mata tunanin da take "Mmn Iman mun zama yan gayu fa jiya Kinga siyayyar da Mahfuz yayo Mana kuwa zomuje kitchen kigani" Na jawo hannunta mukayi kitchen din Ina bata labarin abubuwan da mahfuz ya siyo Mana jiya. A bakin kitchen ta tsaya na hau nuna Mata ta ringa gyada Kai dan ita dama mijinta na siyo mata nice dai bakuwa da aka siyomin a Karon farko. "Aaa lailai kam kun zama Yan gayu kin huta da siyan kanana Yan sachet nidai ko dan bakuwar aka muku siyayya haka sabida Kar ta Raina ku"? "Ko daya fa tazo dai a daidai ne wani kudi suka samu yayi Mana siyayyan,dazun Nan yake cemin ya bada kudin ragon layya,yau saura kwana biyar fa Mai da me ya Kamata muyi? "Mai kuwa zamuyi daya wuce ayi yanka mu soya ban karya ba mallama zubo Mana dankalin muci" Ta koma Palon na juyo dankalin a plate da kwai flask din tea din na Palo da bredi Muka fara ci "Kiringa Jan class dinki lubna ki daina sakar wa wanan bakuwar taki fuska kina zuba a gabanta haba jiya kin bani haushi wlh banda kin dage da a shawarce kin yiwa mahfuz magana ta koma gidansu wlh tunda akwai Yan mata acan itama sai tafi sakewa" Mmn Iman nifa haka nake wlh ba sakin baki ne dani ba,ni ban iya wulakanci ba Sam,idan taga bana Mata magana ko bana Mata hira ai sai taga dan tazo gidana cin arzikine kinsan Kuma haka ba dadi" "Hakane Kuma toh ki ringa ragewa" Insha Allahu Koda muka ci abinci hirar muka cigaba da yi ta tayani yiwa Mimi wanka kafin ta tafi. Tana tafiya Nima nayi wanka Yau kwalliya da soyaya nake ji dan dazu mahfuz yamin kyau. Kwalliya naci da sabuwar atamfa a irin dinkin da mummy tamin dark purple ce da zanen yellow ta balain yimin kyau,ni kaina na kasa d'auke idona daga Kan mudubin. Shayar wa da nake yasa kirjina ya ciciko ya fito har ta saman rigar dinkin yamun das a ciki,banida burin daya wuce mahfuz yaga kwalliyar nan. Mimi itama purple din kayan kanti na saka Mata wayata na dauko na kira mahfuz a waya bugu daya ya d'auka Yana "Madam yanzu nake Shirin kiranki naji lafiyarku" Wal nayi ido kamar yana gabana nace "idan ba abinda kake yi ka kunna data muyi video call" "Angama" Ya katse wayar Ina kunna data kiransa na shigowa Ina dagawa na sakar Masa murmushi tare da bankaro kirjina Ido ya zuba min sai daya dade baiyi magana ba kafin yace "hmm kin kirani ne dan kawai ki tsokane ni ko?, zan kamaki ne ai" Yace Yana tauna lebbe na Masa gwallo "Ina bakace nayi kyau ba"? "Sai na dawo zakisan kinyi kyau ko bakiyi kyau ba ke kadai ce a gidan"? "Eee wlh ni kadai ce ummi bata dawo ba so nake ma yanzu na tashi na dora abincin rana sabida ita amma idan tani ne cornflaskes Zan Sha" Tab'e baki yayi bai ce komai ba nace "Ko na dafa har da Kai na Aiko maka dashi"? "No ba sai kinyi dani ba karki wahalar da kanki abincin ranar ma karki wahalar da kanki wani dafa Mata idan ta dawo kice ta Shiga kitchen din ta dafa abinda take so da kanta ba yanda zaayi wata gardiya tazo ta samin mata wahala" Abu kad'an ke Sakani dariya gardiyar da yace yasa nayi ta dariya har cikina na neman kullewa ganin zai kashe wayar nace "bakuwa ce fa bai dace nasa ta aiki ba" "Kika dafa Mata Abu ban yafe ba kibari ta dawo tayi kayanta ke ai Yar aiki ma aka kawo miki har girkin Daren ma ki bata tayi" "Lalalala Haram wata tayiwa mijina girki ni zan ma girki da kaina" "Dariya yasa Yana to ayi mana mai dadi Zan aiko da kayan ciki anjima a dan yi Mana ferfesu" "Waw abban Mahfuz kudi Wai ka samu haka kasan kuwa inata shaawar ferfesun kayan cikin nan bana so na maka maganar ne bansani ba ko bakada kudi" "Da kin gayamin ai tunda na Sunan soyewa akayi karki damu Zan aiko anjima bari nayi wani aiki ya sakar min kiss ta wayar nima na mayar Masa ya katse wayar. Bai sabar mun da haka ba hakane yasa na kasance cikin tsananin farinciki Ina adduar Allah ya Kara buda Masa inasan irin rayuwar nan dama ne bansamu ba. Naso nayi girkin amma sabida mahfuz ya hana ni na hakura idan ta dawo nace ta girka abinda take so din. Bacci bacci na fara ji na kwanta a doguwar kujera Mimi bata da rigima ko kad'an ba karamin abu ke sata kuka ba. Baccina ya fara nisa naji an kwankwasa k'ofa na Mike na kalli agogo karfe daya da rabi. Ina bud'ewa naga Ummi ce da fuskarta ke d'auke da murmushi nan da nan ya dishe ta daskare waje daya tana kallona ni na dauka ma wani abin ne na juya dama da haguna na dawo da kallona kanta Ina "Ummi lafiya kuwa"? Nidai a idona sai naga kamar murmushin yake tayi idonta har ya canza kala "Sannu da gida Aunty kinyi kyau" "Anya kalau kike kuwa ummi na ganki wani iri ko duk gajiyar ce"? Gyada min kai tayi a daidai lokacin da ta shigo tana "bana dan Jin dadi ne wlh" "Allah sarki sannu inaga gajiya ce ki watsa ruwa ko zakiji dadin jikinki Kinga ma ban yi girki ba dan bansani ba ko Zan girka abinda bakya so nace bari ki dawo ki dafa abinda kikeso da kanki" "Toh Aunty ngd bari na watsa ruwan" Ta bude d'akin tsakar gidan ta shige. Na koma Palo na zauna na kunna tv na kai tashar Bollywood Ina cikin kallon aka Kara buga kofa naje na bud'e almajirin mmn Iman ne da kula a hannunsa. Karbe kular nayi nace ya mata godiya na koma ciki. Ina bud'ewa naga danwake ne ya sha hadi har da dafaffen kwai gashi da manja tuni yawuna ya tsinke na je kitchen na wanko hannuna har Zan fara ci na ga dacewar yiwa ummi tayi kila tana cin Dan wake. Labulen d'akin na daga da sallama tana waya kasa kasa shigowata yasa ta katse wayar da sauri,nidai a idona Kamar akwai abinda ke damunta duk sai naji ba dadi a yanda na ganta. "Ummi dan wake aka aikomin dashi bansani ba ko kinaci nace bari na miki tayi" "Wlh aunty ban fiye san dan wake ba ngd sosai "Ummi kodai na kawo miki Panadol ki Sha ne"? "Aaa wlh aunty gajiya ce kawai da yunwa yanzu zan fito na dafa ko indomie ne" "Toh sai kin fito" Na juya na koma palo na zauna na fara cin danwake Ina korawa da exotic din mahfuz ya siyo mana jiya saura kiris na cinye duka sabida dadin daya min. Da sallama ta shigo palon na amsa Ina kallon doguwar rigar da ta saka Mai balain kyau yellow ta yafa mayafinsa. "Bari na dafa indomie Aunty" "Akwai komai mai kike bukata a kitchen din" Ta amsa da toh ta shige na cigaba da kallona Ina hararo doguwar rigarta a jikina yamin kyau inama Ina da kudi na siyi irinsa Ina Kuma mamakin Inda ta ajiye hijabin nata,ko saka hijabin dama na bakunta ne. Ta dan jima a Kitchen din kafin ta fito da plate a hannunta sai pure water da ta d'auko da daya hannun har zata wuce nace "kiyi zamanki anan Mana kici kya shige daki ke kadai ki zauna" Murmushi tayi ta dawo ta zauna a kasan kafet ta tankwashe kafafunta ta dago tana "Aunty kizo muci" "Kai cikina a cike yake wlh" Na saci kallon indomie da ke ta zuba kamshin sardine lailai da alama ummi Yar hutu ce da mahfuz bai siyo kifin ba da kila sai dai ta siyo kifin da kudinta,a Raina na ayyana kila ta d'auka haka muke da kayan a ajiye. Tana cin abinci lokaci lokaci muna hada Ido sai muyi wa juna murmushi,bakina ma nauyi yamin a San na dau shawarar mmn Iman Kar na ringa zuba kamar yanda tace amma so nake kawai muyi Hirar. Sai data gama cinye indomie ta kai plate din kitchen ta dawo ta zauna. A daidai lokacin da wayata ta fara ringing ganin mahfuz ne yasa na d'auka cikin murmushi Ina "Abban mimina" "Madam na aiko yanzu zaa kawo kayan cikin" "Tom sai an kawo ya aikin" "Alhamdulillah Ina mimina"? "gata idonta biyu kaci abinci"? "Aa banci ba sai na dawo zanci abincin Mai numfashi da Mara numfashi tunda har Kika tsokano ni" "Lalala badani ba ban shirya yiwa Mimi kanwa ba" "Zaki shiryeni ki tanadeni mallama" Ya katse wayar na sauke wayar Ina dariya na kallo wajen da ummi ke zaune naga ta zuba min Ido muna hada Ido ta d'auke da sauri. Bance Mata komai ba na ajiye wayar nima Ina satar kallonta tana ta cizar yatsarta. Tuna ban gama Shan tsumin da mmn Iman ta kawomin ba yasa na m'ike naje kitchen na d'auko na dawo na zauna na bud'e ta dago ta kalleni ta sakar min murmushi Nima na sakar Mata na Kai gorar bakina. Wani daci naji ya gauraye min baki na furzar da tsumin da sauri Ina "Subhanallahi" "Lafiya kuwa Aunty"? Ban iya bata amsa ba na cigaba da goge bakina dan daci sosai. Sai da na gama nace "wlh daci ne da tsumin nan sosai ke kinji dacinsa" Bata ce komai ba tamin murmushi na fara mita Ina bari na gama aikina na Shiga gidan mmn Iman na fada Mata. Ba'a fi minti goma ba sai ga Wanda mahfuz ya aiko ya kawo kayan cikin. Ummi ce ta bud'e masa kofa ta Kuma karbo ta kawomin nace ta Kai kitchen karfe hudu zan shiga kitchen,Koda ta Kai banga ta fito ba sai buruntun ta kawai na ringaji a kitchen banaso nabi bayanta ta d'auka ko yarda ne banyi da ita ba hakane yasa na cigaba da Zama amma hankalina na kanta. Bayan Yan mintina sai gashi ta fito tana "tayaki dorawa nayi Aunty na dauraya kwanun da naci abinci dashi "Allah sarki na kuwa gode ummi" Har a raina naji dadi bata da san jiki Sam. Koda na Mik'e dan na Shiga kitchen din tashi tayi ta bini Ina tayi zamanta ba sai ta tayani ba amma ta dage sai ta tayani a dole na kyalleta muka yi fried rice na hada coslow. Ga ferfesun kayan cikin shima yayi dadi sosai. Sai da muka gyara kitchen din. Muka fito tayi tsakar gidan ni Kuma na fara hada ruwan da zanyi wa mimi wankan yamma. Tun jiya kamar jinin ya d'auke duk da Wasa yake min inaga anjima nayi wankan tsarkin amma ban shirya daukan wani cikin ba banaso mahfuz ya tabani har sai nayi tsarin iyali. Ban Kara Jin motsinta ba har nima nayi wankar yau shigar kananan Kaya nake ji. Hakane yasa nasaka Riga da wando maroun yayi balain min kyau banida wani tsayin gashi sai cika na gyara gashin nayi parking na Kara gyara ko'ina na turara jikina da turare na kame a Palo. Kamar zan leka ummin Kuma na fasa dan bana so na Kuma ringa shige Mata tunda nice matar gidan. Gab da magriba mahfuz ya dawo. Sai daya shigo har palon naje na rungume shi dak'yar na kwace bakina daga nasa nayi baya yayo kaina Yana "Baki Isa bafa Ina zaune Kika tsokano ni" Dariya na ringa yi sabida zagaye kujerun Palon mukayi tayi,dana ga ya kusa kamani na fita waje da gudu a daidai lokacin daya damkoni jikinsa Yana "Wa na Kama" Karar faduwar bokitin da muka ji yasa mukayi firgigit muka kallo wajen da muka ji karar Ummi ce a tsaye ta sunkuyar da Kai jikinta na dan rawa da alama ruwa zata Kai bandakin rigar dazu ce dai a jikinta bata cire ba. Mahfuz cikani yayi da sauri ya koma ciki. Na nufi wajen ummi Ina "garin yaya bokitin ya Fadi" Bata dago ba tace "wlh subuce min yayi" "Gashi rigar taki kuwa ta jike" "Ee dama wanka zanyi Bari na canzo ta dago ta kalleni. Yanda take kallona daga sama har kasa yasa nace "Yadai" "Kinyi kyau sosai Aunty" Cikin murmushi nace "Kina san fasa min Kai ummi jeki yi wankanki bari nayi sallah Nima. Na juya na shige palon na barta a tsaye tana kallona Nima ko bata fadamin ba nasan nayi kyau inaso ace min nayi kyau Dadi nakeji, idan har mace Yar uwata zata ce nayi kyau inaga mijina. Ina shiga d'akin mahfuz ya fito daga bandaki ya canza kayan jikinsa zuwa jallabiya ruwan kasa Mai zip a gaba. Ya dau carbinsa yayi waje. Bai dawo cikin gidan ba sai da aka iddar da Sallah Isha Yana shigowa na jera Mana abinci a tsakiyar kafet na zubawa ummi na dora Mata akan karamin farantin na d'auka na Kai Mata har daki. Koda na Shiga akan katifa na ganta a zaune ta saka wani vest ja Rabin na fulaninta a waje sai dogon wando. Da murmushi na ajiye abincin Ina "gashi nan" "Tace ngd Aunty" Nayi waje Ina fatan ba abinda zai sake fito da ita,dan sam.bangane Mata ba jiya wuni tayi tana saka hijabi yau Kuma ba hijabin dan ma naga.mahfuz ko kallonta bayayi abinda ya kwantar min da hankali kenan" Koda na koma Palo hankali kwance muka ci abincin mu muna tab'a hira Inda nake ce Masa jibi zanje kitson sallah da kunshi sabida bazan iya bin layi ba,yace Allah ya kaimu ya bani kudin. Karfe goma naji na fara Jin bacci nikam bansan Mai yasa yanzu nake da saurin Jin bacci ba. Ina mik'ewa shima ya mik'e ya d'aukar min Mimi muka Shige daki. Ban bari yayi komai ba sai dabaru da na Masa Nima yamin muka samu nutsuwa dan ce Masa nayi ya bari nayi allura tukunna. A tare mukayi wanka na dauka zai kwanta ne yacemin Palo zaije yayi kallon ball baya Jin bacci. Sama sama ma naji shi dan baccin ne a kaina sosai. Bansan lokacin daya shigo ba. Washegari ma ummi ce ta tayani sharan tayi mopping Ni Kuma na hada mana breakfast mahfuz yaci ya tafi. Itama Tara nayi ta fice na shiga gidan mmn Iman muka yi ta hira anan nake fada mata a cikin tsumin da ta kawomin akwai mai balain daci,tace tana ganin ba tsumin na Sha ba dan duk tsumin ba mai daci ko kad'an nayita mamaki tace na gwada sauran ragowar naji ko da daci sai da na koma gida na dauko mata ta dandana tayi ta mamaki tana ta sha irinsa ba daci ko daya,ban bar gidanta ba sai karfe biyu na koma gida a daidai lokacin. Da ummi ta dawo wanan karon ma ita ta Shiga kitchen ta samawa kanta abu taci. Ta tayani wanke wanke,girkin yau ma ta dage min ita zatayi yanda ta dage yasa na kyalleta tayi girkin. Yau dai ita take Jin hirar hakane yasa nima na biyeta dan nikam inaso naga muna Hira. Yau ma bata saka hijabin ba Kamar na tambayeta na Kuma share. Sai cewa take na iya wanka zata Zo wajena d'aukar course idan auren ya kusa muna burgeta nida mahfuz Tuni na washe baki nace insha Allahu duk zan bata sirrin zamantakewa na aure,na bata labarin irin soyayya da muka zuba da mahfuz kafin muyi aure,kamar zan bata.labarin tsinaniyar yarinya nan data makalewa mijina da irin hawan jinin da ta so doramin na Kuma fasa. Itama ta bani labarin yanda saurayinta ke Santa akanta har fada yake da matarsa. Anan na nuna mata rashin Jin dadina akan bai dace saurayinta yayi haka ba dan itama zai iya mata haka idan ya aureta idan giyar so na kwasar sa yanzu ta ringa Dora shi akan hanya. Godiya tamin wajen shidda ta mike ta tafi d'akin nima na dau mimi dan yau bamuyi wanka da wuri ba. Haka kawai sai na fara gaskata mmn Iman akan bata yarda da ummi ba,dan sau biyu Ina Kamata kamar hararata take idan taga na ganta sai ta wayance da sosa Ido,yau bansan inda mahfuz ya tsaya ba,bai dawo kafin magriba kamar yanda ya Saba ba. Koda na iddar da magriba ban fito daga d'aki ba dan so nake idan akayi isha sai na fito gabad'aya kafin dai ayi sallah Isha na tashi Ina dan gyara kayana dana hargitso. Sallamar ummi da shigowarta har tsakiyar dakina yasa nayi saurin juyawa Ina kallonta. "Tun dazu ake ta kiranki aunty ganin baki fito ba yasa nace bari na kawo miki" Sam banji dadin shigo min d'akin da tayi tana kalle kalle ba hakane yasa na karbe wayar a hannunta fuskata a had'e nace Mata na gode ta juya ta fice tana karewa dakina kallo kamar na bita na gaura mata mari wlh na tsani a shigo min dakina Da alama fuska biyu ne da yarinya nan,dole kuwa na taka Mata birki bana san iskanci dan ko a yanzu ma ba hijabi a jikinta riga da skirt tasa taci kwalliya kenan ma a palona ta zauna da Mahfuz ya shigo ya ganta fa Take naji raina ya b'aci na dauki Mimi nayi hanyar palo. A kasan kafet naganta a zaune tana kallo mugun hade rai nayi dan naga alamar na sake Mata da yawa. Sau daya ta dago ta kalleni tana "kinfito ne Aunty" "Um"kawai nace mata Karar machine d'in mahfuz da naji a waje yasa na kalleta naga ko zata tashi amma Ina zamanta tayi ba alamar zata tashi. "Ko zaki koma ciki ga Abban Mimi ya dawo" Nace fuskata a had'e. Mik'ewa tayi bata ce min komai ba ta fita waje naja tsaki ta juyo ta kalleni ta Kara d'auke kanta ta fice a daidai lokacin da Mahfuz ya shigo na mike da sauri dan nasan ma ya ganta shegiya kawai naji na auna Mata zagi Daga labule Ina kallonsa bai kalleta ba har ya shigo Yanda yaga raina a had'e yasa murmushi daya shigo dashi ya kau Yana "Lubna lafiya kuwa"? "Ba komai" Kawai nace Masa na samu waje na zauna Ina Masa sannu da zuwa ya amsa Yana "Lubna ban Saba ganinki a haka ba lafiya kuwa"? "Wlh wanan yarinya ce ta bata min Rai kasan na tsani naga an shigar min daki kwatsam sai gata ta shigo min daki ni naga alamar tana da rawar Kai a gaskiya in zata cigaba da min haka bazamu shirya ba" "Oo keda kanki yau Kuma kika cewa ta bata miki rai, da da Kika kawota wancan d'akin fa" "Gaskiya badan kusancinka da Abdul ba wlh gobe zata barmin gidanan bana San munafirci kaga kwalliyar da tayi sai kace wata matar gidan" Daga hannuwansa sama yayi Yana "Ni ba abinda nagani mallama muje ki hada.min ruwan wanka tunda zu ma nake kiranki baki dauka ba" Mik'ewa nayi na nufi d'akin ya biyoni a baya. Koda na zuba Mata abincin a bakin k'ofa na ajiye Mata "Ina ummi ga abincin ki ban tsaya jiran ta fito ba na koma Palo mukaci abinci da mahfuz . Muka tab'a hira lokacin baccina nayi na mike dan nasan sai yayi kallonsa na masifa daya tsiro dashi. Washegari ban bari ta wani tayani aiki ba kafin ta fito na gama komai yau Kam bata Isa na Mata wani abin karyawar va abinda nayi zata ci. Doya da kwai da tea. Har mahfuz ya fita bata fito ba. Ban Kuma damu na dubata ba bansani ba yau ko ba inda zataje,nidai yau fita zanyi zanje kunshi da kitso. Mmn Iman tun jiya tana unguwarsu. Idan ba inda zataje sai ta zauna tayi gadin gida na kulle palona. Na shirya kenan,na fito Palo sai gata ta shigo palon sanye da hijabinta har kasa a Raina nace munafika Gaisheni tayi.murya na rawa na amsa Mata Ina k'ok'arin goya mimi tace " Aunty ko dai akwai abinda na miki ne bansani ba"? "Mai zakimin kuwa ummi"? "Wlh sai Naga kamar na Bata Miki Rai bansani ba Dan Allah kiyi hakuri" Tuni naji ta bani tausayi nace "ba komai wlh ummi jiyan ne raina a bace,ga abincin ki nan fita zanyi kinsan saura kwana biyu sallah zanje kitso da kunshi" "A koshe nake Aunty bana Jin yunwa yau nima ba inda zanje Dan Allah ko zan iya binki kunshi bana so na zauna ni.kadai" "Ba damuwa ki zo mu tafi. Mik'ewa tayi da sauri ta fita waje ba dadewa sai gata ta fito da hijabinta har kasa. Na kulle ko'ina muka nufi gidan kunshin..... *BUDURWAR MIJINA* *NA SADNAF* *E.W.F.* *PAID BOOK* Last free page Anan na kawo karshen free pages tighten your belt dan labari rikita rikita karamin yak'i a cigaban budurwar mijina biya 500 ta 2029764071 first bank nafisa Nuhu ko 0000551222 Taj bank nafisa Nuhu idan katine turo Mtn ko Airtel ta layin nan 08033719070 ku turo da shaidar biya ta nan layin 08033719070 mutanen Niger Kuma katin Airtel zaku turo na dari biyar ta layin mtn din,daa baki labari gwara ki bayar da ki tsaya a sato Wanda ya hucce gwara ki kasance cikin grp ki karanta da duminsa,Yan albarka shekarar Nan hajji nakeso naje maza a harhado na samu na calle😀😀😀 Last free page Ba mu dade sosai a gidan kunshin ba dan dama Mai kunshin tasan da zuwana na Kuma dade da Kama layi. Ni aka fara yiwa hannu da kafa ja da baki. Ita Kuma ummi tace ayi Mata a iya hannu Sai amsa waya take kamar wata Yar kasuwa waya biyune da ita babba da Karama,anfi kiranta a karamar wayar. Na riga ta cire kunshin hannuna,zaman da nayi bana komai yasa nace "Ummi dan bani wayarki na kalli hotuna" zaro Ido tayi tana "Kai Aunty sai dai na baki karamar dan akwa sirrikana a wayar nan kiyi hakuri" Dariya ma ta bani na Kai hannu zan d'auka dan Yana cinyarta tayi saurin daukewa wayarta ya kawo haske. Kamar dai hotonta ne da wani. Girgiza kai nayi Ina "Ai shikenan" A Raina na fara gasgata zargin da nake Mata da kila Yar duniya ce daga yanda maza rututu ke kiranta Anya ma ba karya tamin akan an sa mata Rana ba kuwa". A haka na zauna itama ta cire nata. Hannu na saka ajaka dan na dauko kudin kunshin tunda iya hannu aka Mata Dubu daya dai zan iya biya Mata Dan Dubu biyar mahfuz ya bani sababin dari bibbiyu. Kafin na ciro kudin itama ta ciro sababin dari biyun ta kalli hannuna na kalli nata,ta saki murmushi tana "kema ashe dari bibiyun ne dake,jiya na tsaya a banki na cira" Ta kirga Dubu uku ta bawa Mai kunshin dan nawa Dubu biyune. Na maida kudina jaka Ina ngd. Daga nan Muka wuce saloon,Ashe ba karamin gashine dani akanta ba. Kitso aka fara Mata na kari shuku,ni Kuma aka fara yarfa min kananan kitso da iya gashina dan idan akwai abinda na tsana bai wuce Karin gashi ba banayi Sam duk da kitson Karin na balain saka mace kyau ni iya gashina ake kitsemin Kuma Ina kyau a haka. Ummi kuwa ta balain yin kyau dan kitson nata har gadon baya aka Mata. Bamu koma gida ba sai wajen shidda Da sauri sauri nayi wanka na fito na Dora Mana jollof din taliya da kifin gwangwani ummi Kuma tunda muka dawo data shige daki bata sake fitowa ba. Mahfuz Bayan magriba ya dawo gida. Kamar yanda muka Saba bayan sallah Isha na zuba mana abinci na zuba wa ummi nata daban. Na Kai Mata har daki,sakin baki nayi Ina kallonta dan sleeping dress ta saka fara iya cinya shara shara Ina iya hango komai na jikinta ta saki gashin dokinta har baya, konida nake matar Aure bana fesa uban turaren da ta fesa yanda nake kallonta tasa ta jawo hijabi ta saka tana "Aunty wlh yau zafi nakeji" Gyada Mata Kai kawai nayi na ajiye Mata farantin na fito kaina na Kara daurewa da lamuranta. "Kisa Ido sosai akan yarinya Nan lubna wlh ban yarda da ita ba bansan Mai yasa nakejin kamar ba alherine ya kawota gidanki ba" Na tuna chatt din da nayi da mmn iman dazu Duk sai naji jikina yayi sanyi har muka gama cin abincin abin na damuna a Raina sai matsawa kaina nake da tunani ko dai akwai abinda mmn Iman ta Sani akanta Wanda ni bansani ba,Ni mahfuz ba wani kallonta yake ba ballantana ince zata kwace min miji. Haka dai na zauna mahfuz na latse latse a wayarsa. Lokacin baccinmu nayi nace ya tashi muje mu kwanta sai yace min bayajin bacci Ido na zuba Masa dan a da ba haka yakemin ba ko lokacin da yake ganiyar soyayya da wanan tsinaniyar Yana kwanciya sai dai ya saci jiki ya sake fitowa,Sam bana so Kuma na zarge shi muna zaman lafiya a yanzu. D'akin nawa na shige na bar shi a palon Ina kwanciya bacci ba dadewa bacci yayi awon gaba dani. Mugun kishirwar da nakeji ne yasani tashi daga baccin daya d'aukeni. Idona ya sauka akan agogon daki karfe biyu na dare,ba abinda ke tashi a palon sai karar Tv. Mik'ewa nayi dan naje kitchen na d'auko ruwa kila ma bacci ya d'auke mahfuz akan kujera. Ina zuwa palon na ga ba kowa bansan Mai yasa kirjina bugawa da balain k'arfi ba nayi sauri na Shiga kitchen nan ma mahfuz baya ciki. Na fito da sauri,kwakwalta ta kasa bani wani tunani abinda kawai na iya ayyanawa a zuciyata shine Kar nayi kwakwaran motsin da zaa jini. Hanyar wajen na nufa Ina tafiya cikin sand'a kirjina Kamar ya fado, Hoton ummi kawai nake hangowa a idona data Sha sleeping dress da mijina a d'akin. Tunanin nan ya Sakani tsayawa Dan ji nayi Kamar an caka min wuka a kahon zuciya na Dade a tsaye dan kasa motsa kafata nayi Ido kawai na zubawa d'akin da ummi take dan Ina tsaye a tsakiyar tsakar gidan ba abinda nakeji sai karar fankar dakinta sai gani da adduar Allah yasa mahfuz na waje Yana Hira a waya da budurwarsa ba a d'akin Ummi zan gan shi ba na kara taku biyu zuwa k'ofar dakinta na manne a jikin k'ofar da aka turo ban Bari k'ofar tayi Kara ba. "Dan Allah har ki bar gidanan karki yi abinda zata gane mu pls" Shine abinda ya sauka a kunnena muryar mijina uban yata. Wani Duhu ya giftamin ta Ido naji dum akaina. Nidai bansani ba ko Nike da iko da jikina barin bakin k'ofar nayi na zagaya ta bayan d'akin da window yake burina na leka mijina na tabbatar da shi naji muryarsa A tangal tangal din da hawan jinin a wacce ta samu karamin tabin hankali na leka ta window. A kwance take a kirjin mijina ya cusa fuskarsa a tsakiyar kirjinta ta kankame shi tana shashafa shi sai sauke ajiyar zuciya take. Wani duhu ya kara giftamin sai da na dau tsawon lokaci na fara ganin haske "Jeki kitchen ki d'auko ashana ga jarkar fetur can ki cilla musu ki Konasu Lubna" "D'auko wuka ki Shiga har d'akin ki cakawa Ummi shima ki caka Masa" "Jeki kwanta ki dauki mataki Mai kyau" Duk zuciyata ke sakamin har na koma Palo cikin sand'a. Tamkar wacce aka bawa umarni na shige d'akina na kwanta nayi rub da ciki,abubuwa da yawa na dawo min kaina,fuskar Abdul abokin mijina kawai nake gani,Ummi Mahfuz,waye ya Kamata nafi Jin zafinsa. Ina Jin labaran cin Amana Amma nawa yayi Muni budurwar miji har gidana har dakina" Na kasa furta innalillahi wa Inna ilaihi rajiun idona dai kawai a rufe yake. Anya a duniyar cin Amana akwai irin nawa kuwa"? Dole akwai abinda mmn Iman ta Sani bata gayamin ba ta munafirceni,na Zama shashasha Ina bautawa budurwa mijina a gidan Aurena. Ba digon hawaye a idona zuciyata kawai nasan ke zubar jini. Ina kwance a rub da cikin naji shigowarsa a lokacin da ya kashe tv ya shigo d'akin. Ya kwanta a gefena bayan ya Kara gudun fanka. Tamkar huramin wuta ake a jikina haka naji na kasa tunanin mai ya dace nayi, Ki tashi ki d'auko wuka kizo ki caka Masa Lubna Allah sarki Mata da yawa da suke kashe mazajen su waya sani ko cin amanar da aka musu kenan" Tsawon awa uku akwance rabi mutum rabi Mai tabin hankali zuciya da gangan jiki azabar k'una aka Kira sallah asuba alarm ya tashe shi ya mike ya bar gefena kafin naji Ina shakar iska Mai kyau. Idona rufe sai da yayi wanka ya fito ya zura jallabiya ya girgiza kafata Yana tashi kiyi sallah karki makara yayi waje. Karar rufe k'ofar gidan da yayi yasani na mike tsaye. Na nufi kitchen na d'auko katon muciyata Ina fita tsakar gida na kulle k'ofar da mukulli na Kara komawa na dauko wuka Mai kaifi. Wandone dama a jikina. Tura k'ofar dakin nayi tana kwance da santala santalan cinyarta a waje. Sai zuba minshari take. Take yanda na ganta da mahfuz ya fadomin. Jikina rawa yake hannuna damke da muciya. Wani mugun bugu na Mata da muciyar akanta ta kwalla Kara a gigice ta mik'e zaune Kallonta kawai nake Ina wani iirn hucci dama kece BUDURWAR MIJINA,? girgiza min kai ta fara yi da sauri ta gwallo idonta tana kallona Tunda na gansu sai a yanzu hawaye ya zubomin "DAMA KECE BUDURWAR MIJINA KIKA ZO MIN HAR CIKIN GIDA DAN KI GANE MIN SIRRINA ?UMMI DAMA KECE BUDURWAR MIJINA KIKA BIYO MIJINA HAR GIDA,KARUWANCI HAR GIDAN AURENA UMMI"? "AUNTY DAN ALLAH KI RUFAMIN ASIRI KI TSAYA NA MIKI BAYANI" Wani irin ihu nasa kamar sabon kamu nayi kanta na hau hada kanta da bango na damke gashin dokinta da k'arfi Ina ja Ni nasan daga farko layi har zuwa kasan layi ana jiyo muryarta ban damu da jinin dake zuba a kanta ba Kamar wata doki sabida karfin da nake ji a jikina na cigaba hada kanta da bango Ina bugu. "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun lubna karki kashe yar mutane ki budemin k'ofar Nan naji muryar mahfuz da karfi"...... Dandandan akwai show a gaba akwai Abubuwan daya Kamata a warware Taya Hadeeza ta samu ta rinjayi Mahfuz ya kaita har gidansa?Taya akayi Abdul shima ya yarda ya Kai Hadeeza gidan Lubna? Kallon da Mahfuz yake yawan cewa lubna zaiyi dama d'akin Hadeeza yake tafiya"? Ya kuke ganin zata Kaya tana bude k'ofar?ko ta karfi ake shiga gidan? Mahfuz na auren Hadeeza kuwa? Hmmm kubiyo sadnaf ta Baku labari da dari biyar dinku kacal, Ga wayanda zasu biya yau zuwa gobe karfe dayan rana akwai discount din dari biyu dari uku zaku turo kacal inya wuce gobe dari biyar hanzarta Kar ayi bake🤚🤚🤚🤚🤚 KAYAN MATA Assalamualaikum kina mace hadaddiya komi kincika ama kinada nakasu tawurin dadadawa miji? Shin kinkai kin isa kina gogayya d sauran mata Amma tafannin ozaroom mishkila tasamu? Shin sanyi y addabeki tayanda Baki iya gamsarda miji kullum kina makalemai yana kauda Ido? Shin minene matsalar? Kinshiga ko Ina kinnemi magani bawani chanji? Tosaurara yar uwata aminiyar arziki, ubangiji yakawo mikini har inda kike,kizo kiji qawata, Inada maganin sanyi me fatattakar kowani irin sanyi duk fitinarshi d izinin ubangiji seyabarki, Munada magungunan mata masu matuqar kyau,hadaddu gangariya kizama t gaban goshi,komi kikace oga yace don, 🥰 kikerewa sa'o'i, kizama abun riritawa abun tarairaya a kudi qalilan,karki cuci kanki kizauna kina cewa ayni nasan kaina,a inadin? Wallahi ko kanada kyau qara d wanka Kisha kiyi qattt kigigita oga, Munada tsumi nau'i nau'i Gumba ta madara,ridi,gyada,dabino,kwakwa,dasauransu Akway ruwan jaraba Ruwan Dadi Hadin minannas Hadin dafa kaza(manta uwa) Hadin yar gaban goshi, Turarukan mallaka. Duk a farashi mesauqi. Serious buyers call, WhatsApp 07046881166 Senajiku kusiya kuyi godiya Kuma kumin addua❤️nagode Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare *Wanan littafin na kudine biya 500 zuwa 2029764071 first bank ko katin mtn ko Airtel a tura shaidar biya ta 08033719070* *BM* *Page 13* Mummy da mmn Iman ne Suka bini aguje suka rikeni ta baya. Na saka ihu Ina "ku cikani na kashe shi dan Allah ku cikani" Mummy ta sakeni ta dawo ta gabana ta kwasheni da mari tana hucci "Dama haka kike Lubna Ashe bakida hankali kishi hauka ne"? "Aikuwa ga kishi nan ya sakata hauka ta zama Yar dabba kila har shaye shaye tanayi dan idan ba shaye shaye tayi ba,ba yanda zata zo ta samu Yar mutane ta kulle ta ringa dirmar ta Kai dalla shashasha lusari zoka wuce ka d'auko Yar mutane mu kaita asibiti Kuma wlh a yanzu zaka saketa ka gama aurenta" Ammi tacewa mahfuz daya tsaya a bakin k'ofa Yana zare Ido,shi kawai na zubawa Ido Ina kallonsa,kallonsa da nake ya Kara tunamin Abubuwan da yamin, kirjina Kamar an dora bullo sabida nauyin daya min da azabar tsanarsa rad'ad'in da hannuna yake yasa na d'auke kaina daga kallonsa na kalli tsakiyar hannuna dana Sha Jan kunshi da baki duk a san na burge namijin daya kawomin budurwarsa har gida ya daidaita ni da ita ko nace ya fifita ni akanta,tunda Abubuwan da ya mata ko rabinsa bai min ba, itama har kunshi ta masa ta Sha kitso,na tuna yanda ta fito da Yan dari bibiyu sak irin Wanda mahfuz yabani nata ma yafi nawa yawa tamin karyar a banki ta ciro take na sake tuna wasu Abubuwan da ya Kamata na nasan gaskiya lamarin,hakane yasa na m'ike Sam bajin ma Mai mummy da Ammi ke cewa ba "Ina zakije"? Naji muryar mahaifiyata a bayana duk sun dauka kila dakina zanyi naga alamar tsorona ma mmn Iman da mijinta suke ji,akwai mutane a tsakar gida,Ammi har lokacin bata fasa masifa ba tana "Bari na duba Yar mutane naga ko ta jawo Mana balai tunda wancan shashashan ya kasa zuwa"? Ta shige bandakin ta rafka uban sallati kafin su ankara nima na shige dakin da gudu na fada bandakin a bakin k'ofa take hakane yasa na bangajeta dan da balain gudu na Shiga dan nasan mummy zata iya rikeni. Flat tayi a kasa ta saki ihu na danna k'ofar na saka mukulli najiyo takunsu da ihu dan Ammi itama ihu ta saka tana "Shikenan ta hadamu waje daya zata kashemu Mahfuz" Ta hau kwallawa mahfuz kira ko kallonta banyi ba na tsugunna a gaban Hadeeza dake kwance da alama ta fara fita a hayyacinta jini sai fita yake akanta "tashi zaune" "Bazan iya tashi ba Aunty kimin rai wlh jiri nakeji kaina kamar baa jikina ba Aunty kin karya min hannu Hajiya ki taimaka min ku kaini asibiti Zan mutu tace wa Ammi, Ammi kuwa mahfuz kawai take ihun Kira tana yazo ya cecesu a haukace nake. Ban kalleta ba nacewa Hadeeza "Kin dauka Wasa nake Miki ko"? "Aaa Aunty" Ta fara k'ok'arin mik'ewa zaune tana cije baki Ammi kuwa ihu kawai take tana Mahfuz yazo ya bude kofar zan kashe su sai k'ok'arin balla k'ofar suke, mahfuz na sallati mummy kuwa kuka ta fashe dashi,mmn Iman ma Ina Jin kukanta" "Damka na kaiwa hannunta da yafi kumbura ta saka ihu" Nace "Kudin kunshi da kitson nan mahfuz ne ya baki ko"? "Ee Aunty shi yabani wlh shi yabani dubu Ashirin" Na cije lebbena A ranar daya baki kin bashi kanki kenan"? "Eee Aunty shekaran jiya ne a ranar ya fara sanina" Murmushin takaici nayi dan Ammi sakin baki tayi tana kallonta na watsa Mata harara Na Kara kallon Hadeeza dake sallati tana juya Kai dan jinin sosai yake fita a jikinta nasan dole ma a kwantar da ita a asibiti A gaban ta na ringa hada kayan da nake so nayi amfani dasu dan na farantawa mahfuz kila tama sha wasu bansani ba tunda tana shiga kitchen din Kai tsaye Kuma a Fridge yake take na tuna tsumin dana Sha Mai daci "Ke Kika zuba min abu Mai daci a tsumina ko"? Na Kara matse hannun ta saka ihu tana "eee Aunty shanyewa nayi na musanya Miki da abu Mai daci,na Sha zumar ma dayawa dan Allah Aunty ki cika min hannu zan mutu" Zanso ta mutun a lokacin data ce ita ta shanye min tsumin dana kashewa kudi,nida siya ita da amfani dashi dan ta jiyar da mahfuz dadi anya na tab'a ganin Mai karfin halin Hadeeza kuwa,sai a yanzu na tuno yanda take hararata a fakaice,har da shigowa dakina duk dan taga ya dakina yake. Yanzu da ace ta zubamin guba a abinci naci fa dan duk Wanda zai iya abinda ta yi zata iya kisan Kai har da fasa min bokiti dan tagani da mahfuz. Idan har shekaranjiya ya fara kwanciya da ita hakan na nufin jiya ma wankan tsarki yayi ya nemeta,yaji dadinta kenan ya koma mata na saki murmushi takaici hawaye masu zafi suka hau kwaranyo min Banida nauyin bacci banida Jin bacci da wuri tunda tazo gidanan na fara bacci da wuri mai nauyin gaske har ta Kai idan mimi ta farka sai nayi dagaske nake iya bud'e idona "Mai kuke min keda mahfuz nake bacci da wuri"? Na matse hannunta da k'arfi Wlh magani yake samiki dan kiyi bacci da wuri har yazo dakina ya tafi hannuna zai fita na Shiga uku Maganarta ta dakeni,Ashe Mahfuz ne yake samin magani a exotic din da yake min tayinsa idan muna cin abinci Na runtse idona jikina da kirjina wani irin rawa yake Na sakar Mata hannu a daidai lokacin da sukayi nassarar balla k'ofar, Mummy ta shigo da sauri tana shigowa ta rufeni da duka Tana "Lubna ko dai dagaske shaye shaye kike kanki daya kuwa wanan wane irin azababben kishi ne daga mijinki ya kawo kanwar abokinsa gida sai ki nemi kasheta. Ban bar zubar hawaye ba ina kallon mahaifiyata nace "Abinda yace miki kenan,Hadeeza ke kanwar abokin Mahfuz ce"? Na jefawa Hadeeza tambaya da k'arfi ta bani amsa da sauri "Aaa Aunty wlh ni budurwarsa ce" Mahaifiyata wani irin dafe kirjinta tayi ta maimaita kalmar budurwa ban kalleta ba na fito daga bandakin mahfuz yayi sauri yayi baya,bana kaunar ganinsa a rayuwata na fito daga d'akin inajin mijin mmn Iman na "A gaskiya baka kyauta ba idan har hakane Mahfuz ya za'ayi ka kawo budurwar ka har gida kaci mutuncin matarka wlh baka kyauta ba har gidan Aurenka fa mahfuz" "Kanwar abokina ce Hamisu ba budurwata bace tsorata ta tayi shiyasa ta Fadi haka,zarginmu take na rasa Mai ya hau Kan lubna daga na fita massallaci na dawo ta kulle k'ofar zata kasheta ya fada cikin rawar murya Naso na juya inda akwai tabarya a hannuna ko muciya na jefa masa sanin ba komai a hannuna mahaifiyata na biye dani yasa ban juya ba,Koda na fita palon jiki a sanyaye mahaifiyata ta biyo bayana mmn Iman kuwa sai jijjiga Mimi take tana kallona. "Ammi ta fito tana dafe kwankwaso tana na karyata,har lokacin mahfuz bayani yakewa mijin mmn Iman dake ta Masa fada ce Masa yake yazo ya taimaka Masa ya Kai Hadeeza asibiti kar ta karasa mutuwa,mijin mmn Iman yace haram baa motarsa ba ya dauka mahfuz mutum ne mai hankali da sanin darajar Aure Ashe haka yake ya fito daga d'akin a fusace yacewa mmn Iman tazo su wuce su tafi ya kalleni cikin tausayawa Yana "Kiyi hakuri Lubna wlh bai kyauta ba bai kyauta ba koma waye dole ya dauki mataki yaci mutuncin Aure ya fita a fusace. Sai a lokacin kukan da nake dannewa ya kufcemin na rufe fuskata na fara kuka mahaifiyata ta tsugunna a gabana itama idonta cike da kwalla mmn Iman itama ta tsugunna a gefena ta fara k'ok'arin rike hannuna dake ta zubar jini naga tsumma a hannunta kila so take ta dauremin itama sai hawaye take tana rike hannuna na fusge a fusace cikin kuka ina "kinsan komai mmn Iman,kinsan budurwar sa ya kawo min cikin gida Baki taba fadamin ba Kika sa na Zama shashasha na ringa hidima da ita,Mmn Iman idan nice bazan miki haka ba" Ban bari tayi magana ba na cigaba da rusa kuka itama kukan yaci karfinta dan har ga Allah taso ta fada mata a ranar da taga mahfuz ya tsaya nesa da gidan Hadeeza taje ta same shi ya dauketa suka tafi a ranar tsananin mamaki yasa ta kasa tabuka komai,anan ta Kara tabbatar da zargin da take akan Hadeeza ba dan Allah take zaune da lubna ba taso fada mata amma batasan ta hadata fada da mahfuz hakane yasa ta bata shawarar ta sakawa hadeezar ido ta daina sakar mata fuska. Kasan makoshi mahaifiyata tace "Lubna bansan abinda ya faru ba kenan" Na dago cikin ihun kuka na hau dukan kirjina Ina "Mummy har cikin gida ya kawo min budurwar sa yace min kanwar abokinsa ce wani abu tazo yi mummy na yarda dashi,ya kawo min budurwarsa har cikin gida nake bauta mata har daki nake Kai Mata abinci mummy abinci ma sai ta zabi Wanda take so zan girka mata mummy da zuciya daya,bai tab'a yimin shopping ba amma sabida zuwan budurwar sa gidanan yayo siyayya Mai yawa Ina murna nice har da Masa addua,sau tari inasan abu haka nake hakura duk a tunanina bashida kudi,bana ma iya tambayar sa komai mummy,iya k'ok'arina haka nake yi dan na kyautata Masa,wani zubin na samu canji da kudina nake siyan Naman Miya duk dan Miya tayi zaki yaji Dadi,ko yanka daya bana ci har sai ya dawo yaci san ransa kafin naci sauran mummy amma tunda ya kawo budurwa sa ya tsiri siyo nama balangu duk a tunanina budi ya samu,ya bani dubu biyar kudin kunshi da kitso ya bawa budurwarsa Dubu ashirin,mummy ya kawo budurwar sa gidana tazo ta gane min sirrina su ka maidani shashasha tunda tazo gidanan ya daina kwanciya da wuri,sai yacemin kallon ball zaiyi ya ringa sakamin magani a lemo duk dan nayi bacci da wuri ya tafi d'akin ta yaje ya kwanta da ita,duk hotel din garin nan bai gani ba,ya kawota gidana yasa na ringa hidima dasu mai na Masa dana cancanci haka daga wajensa mummy Mai na Masa" Na Kara fashewa da kuka. Naji muryar Ammi daga d'akin dan komawa d'akin tayi mahfuz ya kasa fitowa "kaje ka dauki yarinya nan ka kaita asibiti karta mutu fa kanta na ta zubar da jini dan ubanka na biku naga likita dan yarinya nan ta karyamin kwankwaso. Ammi bari na Nemo abin hawa Kamar ta suma Duk Ina jinsu idona ma na kan k'ofar ya daga labule kad'an ya lek'o ya koma da sauri Ammi ta hankado shi waje tana "dalla wuce muje ka Nemo abin hawa" Bango ya fara bi Yana kallona cikin wani irin speed na daka tsalle na sha gabansa na cakumo kwalar jallabiyarsa cakuma bana wasa ba nace "Bani takardar sakina dan kutumar ubanka kafin ka Kai karuwarka asibiti tsinanne laanane Allah ya tsine maka albarka" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Wai dama haka yarinya nan take dama Yar dabba ka aura wai"? Ammi tace cikin masifa Mummy tace "Yanzu abinda Zaki ce kenan Aseeya danki yayi wa yata irin wanan cin amanar bazaki Masa fada ba shine kike Kiran Lubna da Yar dabba"? "Ina ganin ikon Allah fadan uban me zan Masa bayan urban dukan daya sha a hannunta har ni bata kyalle ba,ni ban yarda budurwarsa bace azaba ta sha shiyasa ta amsa laifin da ba nata ba dan Sam bata gane Hadeeza ba sabida kamaninta daya canja. Hannuna a shake da wuyar mahfuz da hannu biyu Jin abinda Ammi tace yasa na kalleta cikin tsananin takaici Ina "Taya Zaki yarda budurwar sa ce bayan ta baki abin duniya kin Sha atamfa da mayafi da kudi,ta Ina Zaki yarda kin haifo asarare dan iska dan wuta,taya zaki taba yarda" Lubna mahaifiyata kikewa magana haka"? "Gutsun uwarka da ita nake ka sakeni" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Mahfuz agaban idonka take zagina tana gayamin magana dama Kai dan iskane yanzu kyautar da yarinyar nan tazo tamin zuwa kayi ka fada Mata" "Wlh aa Ammi bansan yanda akayi tasani ba" "Allah ya Isa tsakanina da Kai mahfuz Allah ya tsine maka albarka "Wlh ka gama da Yar iskar yarinya nan a yau zaka saketa na rantse da Allah" Sake shi Lubna kinji" Mummy tace na girgiza kaina na Kara rik'e rigarsa Ina "wlh tallahi sai ya bani takarda ta" "Mahfuz bata takardarta yanzu Nan kafin na tsine maka" "Ammi bazan iya sakinta ba wlh inasan ta sharrin shaidan ne bansan Mai ya hau kaina ba nayi Mata ba daidai ba ki tayani bata hakuri Ammi ta cikani Kar Hadeeza ta mutu" A wanan gabar na hau Kai masa duka a kirjinsa da karfi Yana k'ok'arin rike hannuna Ina "wlh sai ka sakeni na gama Zama dakai mahfuz ko a lahira bana fatan na ga Mai iirn fuskarka" Lubna dan Allah kiyi hakuri Mummy ta janyeni dak'yar daga gabansa Ina rsntsuwa sai ya tsinemin "Wlh indai ni na tsugunna na haifeka sai ka saketa a yau dinan ba iya duka abin nata ya tsaya ba har da cin mutuncina da zagi tace Ina da kwadayi ni da nake mahaifiyarka ka saketa kafin na maka Baki" "Wlh bazan iya sakinta ba Ammi ni na Mata laifi wa kikeso ya kular min da mimi ko wata daya batayi ba taya Zan rabu da ita"? Hakan dayace ne yasa nace "idan mu hadu a kotu ka bani takarda ta" Nayi daki a fusace banida lokacin d'aukar komai iya hijabina kawai na sako mahfuz a gigice ya hau bani hakuri Ammi na dura Masa zagi mummy kuwa ta karbe Mimi daga hannun mmn Iman dake sharar kwalla hakan da nagani ne yasa nace "mummy bashi yarsa bazan shayar da ita ba ya kaiwa budurwsa ta shayar da ita Mimi jinin mahfuz ce banasan naga wani abu daya danganci mahfuz" Gwallo ido Mummy tayi tana mimin Zan ajiye Masa yarki ce fa" "Yarsa mummy kaddara tasa ta tsago jikina ta fito ki basa yarsa mu tafi" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun lubna ki rufamin asiri karki min haka" Mahfuz yace hankalinsa a balain tashe "Mama ki tayani bata hakuri mmn Iman ku tayani bata hakuri" Tsaki nayi na fice duk da zuciyata kuka nake na rabuwa da yata da nake satar kallonta zuciyata a bushe take bana jin komai. Ina jinsa Yana bina ban kallesa ba Ammi kuwa sai masifa take tana a bata mimi ai tana da nonon zata nemi mai bawa Mimi nono....... Duk wacce tamin sharing Allah Yana kallonta Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare *WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 ZUWA 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaida biya zuwa ga lambar 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min sharing idan bansanki ba bana ganinki Allah Yana kallonki na barki dashi* *Bm* *Na Sadnaf* *Page 15* Bugu daya ya d'auka Yana "Kasan kuwa yanzu nake Shirin kiranka inata Kiran Lubna dan na hadata da Aisha su gaisa bata d'auka ba halan bata kusane"? "Hmmm Abdul Ina cikin matsala" "Subhanallahi wani abune ya faru"? "Abdul idan na fada ma nasan zaka ji haushina amma.kasa kanka a matsayina ko kaina zaka iya kwafsawa" Mahfuz kasa ma bashi labarin yayi ya cigaba da kame kame sai daya ga Abdul zai kashe wayar ya bashi labarin abinda ya faru ya Kara da "Bansan Mai ya hau kaina ba banyi tunani ba Sam,wlh Hadeeza kanainayeni tayi,na kasa yakice mata gashi yanzu lubna tayi fushi tunda nake da ita wlh ban taba ganin ta yi irin Wanan fushin ba" "Allah ya Isa tsakanina da Kai Mahfuz baka kyauta min ba yanzu dama yarinya nan budurwa ka ce Taya zaka aikata irin wanan danyen aikin,daka tashi abinka hada dani, wlh Azeem da nasan budurwarka ce ko kallonka bazanyi ba yanzu wane kallo kake San lubna ta ringa min kasa kanka.a matsayin ta yanzu ta kawo maka Saurayi gida ka ringa.kuma hidima da saurayin zaka ji Dadi,ka cutar da ita,wlh ka zalinceta" "Wai dan Allah Abdul ka barni naji da daya Mana yanzu na kiraka dan.na samu kwanciya hankali da mafita Kai Kuma sai Kara maganganu kake" "Toh Mai kakeso nace maka a lokacin da zaka yi abinka kayi shawara dani, wlh Ina Jin labarai naka ya banbanta idan ma holewar zakayi da ita ka kaita hotel mana why zaka kaita gidanka tsakani da Allah kace bazan maka.magana ba yanzu ka jawomin bakin jini a gurinta kenan,yanzu zata dauka da hadin bakina aka kaita gidanka a gaskiya banji dadin abinda kamin ba Yace cikin tsananin b'acin rai kafin mahfuz yayi magana ya kashe wayarsa Mahfuz yabi wayar da kallo,shi kansa Abdul din bai tab'a jinsa cikin bacin rai kamar haka ba,sake kiransa yayi,bai d'auka ba. Haka yayi ta Kira a karshe yaji ya kashe wayar. Mahfuz haka ya rike wayarsa Yana tunanin mafita Abdul kadai yake tunanin zai iya rokon lubna ta sauko sai gashi yak'i sauraransa. Ammi Kuma yasan ko zai mutu ya dawo bazata saurare shi ba,karshe dai sai yayyensa sun Shiga maganar nan dole su zasu shige Masa gaba wajen shawo Kan lubna. Zurfin da yayi a tunani yasa Sam bai san dare yayi ba sai muryar Ammi yaji a kansa tana "Wai uban me kake a daki tundazu baka koma asibitin ba"? "Bana Jin dadi Ammi nima ban wuce a kwantar dani ba bazan iya komawa asibiti ba" "Sabida ka rabu da Yar dabba Yar gwal ko"? shine zaka kwanta rashin lafiya,Kaine ka dauki yarinya Nan ka Kai gidanka matarka ta kusa kasheta badan Allah yasa tana da tsawon rayuwa ba,shine dan wulakanci zaka barta da shemau kawai a asibiti,idan ma dan ita lubna kake duk abinan toh kayi a banza dan ka gama Zama da ita dan yarinya nan Sam ba matuniyar arziki bace,Sam bansan tana da boyayyen Hali ba sai da abinan ya faru,har ni ta kalla ta zaga a gaban idonka ta ringa yiwa mutane hauka a gida,taya zaka dawo da ita ma Haram lubna ba matar da zaa zauna da ita bane" "Ammi dan Allah dan annabi ya kike haka nifa na cutar da ita tsakani da Allah kema kinsani tunda Hadeeza ta dawo rayuwata ta kanainayeni ta hanani sukuni,bansan da manufa a ranta ba ashe so take ta tarwatsa min gida,Ammi Kamata yayi ki shige min gaba muje har gidansu mu basu hakuri bawai ki ringa ganin laifinta ba" "Bakada hankali bazan tab'a taka kafata naje gidansu wata lubna ba Kai da kaga zaka iya da ita sai kaje tunda ka nace amma ka sa a ranka wlh tallahi sai ka Kara aure kurkusa ma kuwa bari yarinya nan ta warke" "Wacce yarinya Ammi"? "Wacce ka Kai gidanka Mana ko ka dauka ka samu abinda kakeso bazaka aureta ba,ai ka gama aurenta ka gama tunda har ka iya Kai ta gidan ka ta zauna kaga kuwa aurenta dole badani zaa cuci Yar mutane ba,wanan zalincin da lubna ta Mata ba abinda zaa saka Mata dashi sama da aurenta,dalla tashi kaje asibiti ka dubata." "Bakin ciki ne ma ya hana shi ce Mata komai yaso ya kwana a gidan nasu,dan ji yayi Sam bazai iya kwanan gidansa ba lubna ba. Amma da takurar Ammi gwara yaje gidan nasa ya kwana. Koda ya bar gidansu gidansa ya nufa da isarsa d'akin lubna ya wuce,da wayarta ya fara cin Karo a side bed kafin ya bi koina da kallo Yana Jin inama mafarki yake ace duk abinda ya faru ba gaske bane yaso da wayarta ta tafi da yau bazai bacci ba text zai kwana Yana tura mata na ban hakuri,sai a yanzu ma yake dana sanin biyewa Hadeeza dan tunda ga lokacin daya Santa yaji kamar ba budurwa bace yaji zuciyarsa na Masa rawa akanta,ta Masa Abubuwan da dama daya sa yake zarginta dan ko a ranar ma dayaje d'akin nata bada zumar wani abu ya Shiga tsakanin su ba yaje,yaje ne suyi hira su dan yi romance Kamar yanda ta fara sabar mai,sai dai Yana shiga yaga taci mahaukacin sleeping dress da babu marabarsa da tsirara a matsayinsa na namiji lafiyayye tuni yaji zuciyarsa ta harba ga wani irin fitinannen kamshin da take, gashi ya kwana biyu rabonsa da lubna hakane yasa Koda suka fara romance ya zarce Romance din ta Kuma bashi hadin kai dan kafin ma yayi wani abu da ita sai da ta kusa haukata shi dan da kanta ta zame wandonsa ta hau tandarsa Kamar ta samu alewa,Yana balain so ita Kuma lubna nada kyankyami ko zata Masa sai yaga tunda ranta bayaso shima ba wani Dadi zaiji ba,da hannu biyu ya damke bakinsa sabida Kar yayi ihu kasan zuciyarsa Kuma balain mamakinta yake taya.akayi ta iya ita da ba Aure ta tabayi ba ko aure kayi indai ba koya ma akayi ba taya ta kware haka,tuna wayayya ce kila bf ta kalla da wanan tunanin ya cire zargin ta a ransa har sai daya kusanceta Kuma yaji Kamar ba budurwa.bace dan lubna ya fara sani a rayuwarsa daga shi har ita ba karamar wahala Suka Sha ba,sai da lubna ta tafi wata uku ma kafin ta fara sabo dashi,Amma Hadeeza Kam Kamar kwararriya dan ta bashi hadin kai kwarai,dan gamsuwa Kuma ya gamsu dan kawai bayaso lubna ta tashi tazo ta Kama su. Ya koma d'akin kamar bai komai ba. Sai jiya da ya Kara komawa kafin su wayi gari yau da wanan tashin hankalin,Sam Hadeeza batazo masa da alheri ba,ba abinda yasa Hadeeza ta Kara fice Masa a rai sama da asirinsu duk da ta tona musu,har da alherin da tayiwa Ammi,yanzu lubna zatayi tunanin shi ya dauketa ya kaita gidansu Hadeeza ta Kara dagula Masa komai. Juyi kawai ya ringayi ya rasa mai ke Masa dadi addua kawai yake Allah yasa Lubna ta sako da wuri. Kowane gida ana shirye shiryen sallah gobe Banda shi da yake cikin tashin hankali da yanzu. Bacci rabi da rabi yayi washegari Koda ya fita.massallaci Suka hadu da Hamisu mijin mmn Iman bai wani sakar Masa fuska ba suna gaisawa ya wuce Kamar ba mutumin dake jansa da hira ba kila haka mutuncinsa ya zube a idon duk Wanda yasan ya kawo budurwar sa har gidansa. Koda ya koma gida daga massallaci Kaya ya canza ya dauki wayar lubna yasa a aljihunsa Yana so anjima kad'an yaje gidan yaga ko zai dace da ganinta. Gidansu ya wuce acan ya hadu da yayyensa dan haka suke haduwa a gida su tafi sallah idi,daga nan su dawo suci tuwon sallah su Kuma bawa Ammi barka da Sallah dan idan har ka hanata haka zatayi ta mita tana bawa mutane labari wane bai bata barka da Sallah ba. Yana k'ok'arin gaishe da Ya Ali da ya kasance shine baba sai Usman mai binsa sai Kuma Mahfuz. Dukansu sunyi aure da matansu kannensu Mata uku suma sunyi Aure,Yar autarsu shemau kadai ce ta rage batayi Aure ba. "Mahfuz ashe abinda ka aikata kenan kanka daya kuwa taya zaka dauki budurwarka ka kaita har gidanka"? Mahfuz najin haka yasan Ammi ce ta fada musu,fada Suka rufe shi dashi Kamar zasu dake shi sai Ammi ce ta tsawatar musu tana "kuka san dalilin dayasa ya kaita gidansa ni abinda yasa na fada muku sabida kuji irin dibar albarkar da yarinya nan tayi mana idan haka ta kasance sau tari mace tagari rufawa mijinta asiri take,amma.yarinya nan haka ta Tara Mana jamaa a yanzu nasan kowa yasan mai ya faru yarinya nan Sam ba matar rufin asiri bace sai kunga yanda ta canzawa yarinyar kamani" "Haba Ammi ya zakice haka wlh duk Wanda akayi wa haka dole ya dau matakin da ta d'auka har gida fa ya Kai budurwarsa dan bashida mutunci ,a madadin ki Masa fada shine kike k'ok'arin fito da laifinta bansan Mai yasa bakya san laifin yayanki ba yanzu da shemau ko Amina akayi wa haka wlh nasan kece gaba wajen cewa Baki yarda ba" "Fito kawai fili ka dura min ashar Aliyu Kai dama ai bakada mutunci tunda kayi aure kunnuwaka Suka Kara fadi kamar na matarka,nama manta Kai waye na tsaya Ina fada muku na manta bazaku bi bayan dan uwanku ba ai bance muku yayi daidai ba abinda yayi Amma abinda ita lubnar tayi yayi yawa yanzu da auren sukayi da yarinya nan halan haka kishi zai saka ta zuba Mana hauka"? Duk sun Riga da sun San halin Ammi dan yanzu nan ma sai laifiin Kuma ya koma Kan matansu da suka San hakuri suke da ita hakane yasa Suka ja bakinsu suka tsuke har ta gama ta fice kafin suma suyi waje gabad'aya dan su tafi massallaci mahfuz na dab da fita Ammi ta tsayar dashi tana "Ka tabbata daga massallaci ka jeka ka gano yar mutane idan an sallameta a yau ta dawo nan din ta zauna kafin Iyayenta su dawo" "Aaa Ammi dan Allah idan an sallameta na bata kudin mota ta tafi wajen danginta ba dai a gidan nan ba yanzu dan Allah idan lubna taji labarin tana gidanmu wlh bazata ji dadi ba zan Kara jawowa kaina matsala ne a wajenta. Mahfuz Anya haka.yarinyar nan ta barka kuwa"? "Mun tafi massallaci Kar mu makara yafice daga gidan da sauri yabi bayan yayyensa. Suna fitowa daga massallaci,Mahfuz cikin kwantar da murya da biyyaya ya hau neman taimakon su ya Alin akan su shige Masa gaba wajen zuwa bawa lubna hakuri,Ya Ali tsaki yaja yayi tafiyarsa Yana ba inda zaije. Sai Ya Usman ne yayi ta Masa fadan abinda yayi a karshe yace "yarinya nan daka Kai gidanka Sam Bata da tarbiyya karka soma aurenta domin ka aureta wlh sai kayi matukar nadama Taya mace zata biyo namiji har gidan aurensa wanan yarinya sam bata da kamun kai, idan ma so kake ka aureta ka gaggauta fasawa Ina laifin matarka yarinya Mai hankali dududu yaushe ma kayi auren dan masifa. Sharrin shaidan ne Yaya tsaki Ya Usman din yayi Yana "Ka fara zuwa asibitin ka dubota karfe uku kazo ka sameni a gida sai mu tafi Allah ya kyauta" Mahfuz machine dinsa ya hau ya nufi asibitin Ya Usman Kuma yaje ya hau motar ya Aliyu suka tafi. Hadeeza. Bakin ciki kamar ya kasheta data ga mahfuz baizo ba,Koda ta ce shemau ta Kira mahfuz taji Yana Ina ce mata tayi ta kirasa bai d'auka ba. Ko baccin bata koma ba har gari ya waye tunani kawai take Yana can kila ma Yana rarrashin Lubnar da ta kusa kasheta ko'ina na jikinta kuwa ciwo yake mata, idan kanin mahaifinta ya dawo sai dai tace Masa hatsari tayi,lubna bata daki banza ba insha Allahu sai ta rama dukan da ta Mata idan ta auri mahfuz sai ta fitar da ita daga gidan,cikin kirsa zata saka Mahfuz ya saketa,dan ta gano logon Mahfuz. Wajen sha daya taga mahfuz ya shigo fuskarsa a daure. Shemau na gaishe shi ta mik'e tana "Wlh dama na gaji Yaya ko sallah idi yau bansamu zuwa ba bari naje gida" Yana Jin idon Hadeeza daya balain kankancewa sabida kumburin da yayi a kansa,ko kallonta baiyi ba dan haushinta Yake ji bashida burin daya wuce ya yakice ta ta barshi ya sarara "Nima ai ba dadewa zanyi ba ai inaga ba wani matsala sallamarta kawai za'ayi yanzu dan na biya ta wajen likita yace ba wani matsala" "Toh nidai na tafi Yaya sai kun fito" Tayi waje da sauri sai a lokacin ya kalli ya Hadeeza da take zubar hawaye fuska a had'e yace "Ya jikin naki"? "Mahfuz sai a yanzu zaka zo wajena"?tun jiya da kuka kawoni mahfuz baka Kara waiwayata ba, kaga yanda matarka ta min lahani kaga fuskata mahfuz duk halin nan da nake ciki matarka ce jefani a ciki amma shine baka zauna dani a asibiti ba sai a yanzu kazo" "Kinsan halin da Kika jefani a ciki ko Hadeeza kin zubar min da mutunci Hadeeza wanan wane irin rashin hankaline taya zaki saki baki ki fadawa lubna komai har dasu Ina zuba mata magani a lemo dan nazo dakinki Kika ce mata kin bawa Ammi atamfa wane irin rashin hankaline wanan"? "Mahfuz mutuwa na gani Kai yanzu damuwarka abinda na fada ba lafiya ta ba haba mahfuz matarka kiris ya rage ta kasheni da ban fada mata ba ba abinda zai hana ta kasheni fada ya Kamata kazo kana min Ina cikin wanan halin tsakani da Allah Mahfuz" "Komai zata miki bai Kamata ki fada mata komai ba kinzo kinsani nayi Abu mutuncina ya zube lubna tayi fushi ta koma gidansu,kin jefani cikin tashin hankali Hadeeza nifa Ina kaunar matata bance Miki bana Santa ba,badan kin dawo rayuwata ba ni ta isheni rayuwa bana bukatar wani Karin Aure Kuma na fada Miki" "A yanzu Kuma fa"? Tace tana zubar da hawaye Mahfuz ya d'auke kansa Yana Hadeeza bari na karbo takardar sallamarki idan an sallameki sai na raka ki tasha na biya Miki kudin mota zan nemeki idan komai ya daidaita" "Taya zanje gida a haka bayan na fada maka ba kowa,can gombe ma ba kowa sai dai naje gidanku" "Hadeeza baza kije gidanmu ba wanan wane irin masifa ne Taya zakije gidanmu da wane Ido kikeso dangina su kalleki a kin gama zuwa gidan aurena kin zauna kin zauna Kuma a gidanmu Zan aureki,sai kace a kudu,a kudu nasan ake haka,mace zata je ta zauna a gidansu saurayi,wannan ba al'adar bahaushe bane Sam,dan haka bazaki zauna a gidanmu ba gidanku Zaki tafi" Yayi waje a fusace Hadeeza tabi shi da kallo baki a sake,sam bata tab'a tunanin zai Mata haka ba,lailai idan batayi dagaske ba Mahfuz bazai aureta ba,da alama duk Haushin tona musu asiri da tayi yake ji anya Haka lubna ta barsa ba asirice shi tayi ba. Mintuna da fitarsa sai gashi ya dawo da likita. Likitan ya duduba ta ya tambayeta inda ke Mata ciwo ta fada Masa kanta ne har yanzu yake balain ciwo. Yayi rubuce rubuce a takarda ya bawa mahfuz akan a siya Mata magunguna Yana karba yace tazo su wuce su tafi A wajen tashin haka tayi ta cicije lebbe tana faduwa da gangan taga ko zai taimaka Mata amma ko kallonta baiyi ba har ta saka takalminta ta fara tafiya a hankali tana binsa a baya. Ta d'auka gidansa zai kaita ta kwaso kayanta tana so taje taga ko Lubnar na nan, sai dai suna zuwa ya tsayar da abin hawa akan ya kaita gidansu zai aiko Mata da kayanta yaki bari ma ya kalleta ganin Yana k'ok'arin tafiya yasa ta ruko hannunsa tana "Ya zancen Aurenmu mahfuz"? "Allah ya Mana zabin daya fi alheri" Yace tare da fusge hannunsa daga nata...... Kuringa hakuri dani wajen posting din Daren da nake a lokacin nake da time Don't share my novels plc Are you guys looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗 Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉 Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product✅ Mg's will gv you the best out of all With mg's product ur skin is 💯 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day💃 We have herbal whitening black soap now nd beauty set available Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it🤗 Just gv it a try now nd see wonders✅ Chat:08062991549 07046881166 Call:08064532391 Soap price:3k set:11k Follow us on Instagram@glow_with_mgs Facebook:mg's skincare what are you guys waiting for hurry nd grab urs💃 now is the time to glow🧖‍♀️ Pamper ur skin🦵 Shine like a bride 👰 be part of the glow team karkubari abaku lbr Just chat 08062991549 to plc ur orders😘 Do not forget to follow us👆 Like nd comment pls dearies😘 Patronize us🙏 mg's always serve you the best✅❤️ *WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min sharing idan bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi* *Bm* *Na Sadnaf* *Page 16* Hadeeza ji tayi wani zazzabi na Neman rufeta dama da zazzabin ma, matsawar mahfuz bai aureta ba taga ta kanta dan shi kadai ne option dinta yanzu bata da wani na aure dukan samarinta Yan bariki ne, lubna kuwa Dole ne ma ta rama abinda ta mata ko yan dabba sai ta haya sun rama mata. Sai da taje gidansu ta tuna mukullin na cikin akwatinta wayarta ma na gidan,sai makota ta Shiga dan ta Kira mahfuz ta gaya masa ya kawo Mata akwatinta da mukullinta a ciki da ace tasan Lubna zata mata irin wanan dukan da bata soma zuwa gidan ba,bata san Mai ya hana ta rama dukan da ta mata ba har ta bari ta Mata irin wanan dukan,Koda ta Shiga gidan makotan mamn khairat sallati tayi ta sanar da ubangiji tana tambayarta hatsari tayi, gyada Mata Kai kawai tayi akan hatsarin tayi dan shine karyar kawai da zatayi,dan ba mai yarda dukan ta Sha haka a wajen siririya da bata kai.ta kauri ba,wayar mmn khairat ta karba ta saka lambar mahfuz sai da ta Masa miscal uku kafin ya d'auka Yana Jin muryarta ya kashe wayar,take ta sake kiransa amma haka yayi ta ringing bai dauka ba sai text ta masa akan kayanta da mukuli. Bata san Mai yasa mahfuz yake neman wulakanta ta ba,bayan uban dukan da ta sha awajen lubna a yanzu ya Kamata yafi kula da ita ya turo kudin aurenta gidansu,sai gashi a madadin kulawar nema yake ya juya Mata baya,haka ta rike wayar tana tunanin zai Kira,bayan minti goma sai ga sallamar almajiri da akwatin ta tayi sauri ta mik'e ta leka waje ko zata ganshi dan tasan dole shine ya kawo Mata kayanta. Sai dai babu shi babu dalilinsa jiki a sanyaye ta ja akwatin ta bayan ta bawa mmn khairat wayarta ta bude gidansu ta shige dole ta zauna a gidan ita kadai har sai sun dawo daga aikin Hajjin. Mahfuz Ji yayi Kamar ya rabu da K'aya a lokacin da Hadeeza ta ta tafi,a lokacin da ta kirashi dama Yana gida sabida ya kwashe kayanta ya Kai Mata sai gashi ta kirashi duk abinan da ya faru gani yake ita ta jawo Masa,balain haushinta Yake ji,duk kayanta ya tattara mata nesa da gidan ya tsaya ya samu almajiri ya bashi akan ya Kai gidan dake jikin gidansu dan yasan Dole tana can, bashida burin daya wuce ya samu ya shawo Kan lubna,indai Lubnar daya sani ne yasan wuyanta su keb'e ya marairaice Mata,da kwarin gwiwarsa ya Kara wanka ya saka sabon kayan daya dinka na sallah,ya nufi gidan ya Usman ya riga da yasan Mai ya kawo shi hakane yasa basu wani b'ata lokaci ba suka nufi gidansu Lubna,a k'ofar gida Suka tarar da zainab na zance kanwar lubna,bata ko kalli mahfuz ba iya ya Usman din ta gaisar yace mata ta musu iso wajen mahaifiyar su Suka zo dan mahaifinsu ya dade da rasuwa,kuma bata sake aure ba. Mahfuz kuwa ganinsa a k'ofar gidansu lubna Kuma sai duk yaji hankalinsa ya tashi dan baisan Mai zai tarar ba. Gabansa ne ya hau faduwa a lokacin da suka shiga gidan har palon mahaifiyar lubna da aka fi Kira da Aunty nurse ita kadai suka samu a palon da alama da baki a gidan sabida ranar take sallah suna Kuma jiyo hirar mutane a dakunan palon. Mahfuz sai wurga Ido yake yaga ko zai ga lubna daga yanda Aunty nurse ta amsa gaisuwar shi sai yaji jikinsa ya Kara sanyi ya sunkuyar da kansa Yana Jan ya Usman na mata bayanin basu dadin abinda ya faru ba,ya hau bada hakuri yana a dubi zuriar dake tsakani. Aunty nurse bata katse shi ba har ya gama kafin itama tayi gyaran murya tana "Abinda Mahfuz yayi ya munana,ba uwar da zaa yiwa yarta haka bata ji zafin abinda aka mata ba,kafin ya Kai budurwarsa gidan ta sha dan min korafin wayar da yake yi da budurwa a cikin gidanta,har barota yake yi a daki ya fita dan kawai yaji muryar budurwarsa wlh idan ta fadamin hakuri nake bata, tana ta Kai zuciyarta nesa,a iya sanina basu wani Dade da Aure ba da har ta cancanci haka daga wajensa iya nan bai ishe shi ba sai gashi ya dauko budurwar ya kawota har cikin gidansa ya zuba karyar Yar uwar abokinsa ce tsakani da Allah yayiwa yarinya nan adalci duk macen da mijinta zai iya Mata haka wlh ba kaunarta yake ba,dan haka a ganina kuyi hakuri yaje ya auri wancan din dan yafi kaunarta,ita Kuma Lubna Allah ya mata zabin daya fi alheri" Mahfuz nasan baiyi daidai ba,abinda yayi ba abinda zaa yi saurin mantawa bane ko a yafe,amma idan kuka tuna Allah ma muna mishi laifi ya yafe Mana Ina ga mu Yan Adam,dan Allah dan annabi kuyi hakuri" Mahfuz baki ya sa ya hau bada hakuri shima Aunty nurse ajiyar zuciya ta sauke tana "ba fa nice lubna ba idan lubna taga zata koma bazan hanata ba dan haka bari na turo muku ita" Ta mik'e ta bar palon ta shige daya daga dakunan dake cikin palon. Lubna Nayi kukan fili nayi na zuciya har na gaji,nasan daga jiya zuwa yau sai da jinina ya hau, duk abinda ya faru dawo min yake kawai a kaina daga lokacin da Hadeeza ta taka kafarta zuwa gidana har jiya da ya kasance min bak'ar Rana, mahfuz yaci mutuncina ya wulakanta ni da yanzu asirinsu bai tonu ba har ta samu ta tafi,da ahaka Zan saki baki ya aurota bayan ta gama sanin komai nawa sai a yanzu na tsani halina na saurin sabo da mutum Koda a ranar na fara haduwa da mutum,Banda mmn Iman ta kwabeni da komai nawa Zan kwasa na fadawa Hadeeza,Ina Jin Haushin mamn Iman har a cikin zuciyata da ace ta fadamin tun wuri da Hadeeza bata Dade a gidanan haka ba,tsabar munafirci mahfuz ko kallonta baya yi Ina murna ba ruwansa ashe yaudarata suke har abin ya Kai ya sakamin magani a lemo,a yanda nakejin zuciyata bana Jin akwai Wanda na tsana kamar mahfuz domin ya ci amanata,Ina matarsa ya hadani da dubu biyar ya bawa budurwarsa Dubu ashirin,wlh ko zaa na rantse min mahfuz zai iya kusanta kansa ga zina karyatawa zanyi,sai gashi a cikin gidana yaje ya kwanta da Hadeeza Ina can dakina ya bugar dani Ina bacci. Mummy gajiya tayi da rarrashina ta hau ni da fada akan Kar naja wa kaina wani matsalar akan abinda ya riga da ya faru ya Kuma wuce dan kuka da saka damuwa a zuciya bashi zai canza komai ba. Hakane yasa na koma kukan zuci,da ciwo Wanda ka aminta dashi ka bashi Amana ya maka irin Wanan cin amanar. Shigowar Mummy data zauna a gefena da Sam bansan da shigowar ta ba sai da ta zauna a gefena na dawo daga tunanin dana tafi. Ido ta zubamin har sai da na sunkuyar da kaina "Haba Lubna wai bazaki sasautawa kanki bane Kinga yanda Kika rame daga jiya zuwa yau haba dan Allah dan annabi so kike ki mutu da bakin ciki ko abinda ya faru ya Riga da ya faru ba abinda zai iya canza hakan nasan da ciwo amma haka zakiyi hakuri ki fuskanci kuma gaba Aure gabad'ayansa dan hakuri ne,duk wata macen da Zaki gani a gidan mijinta da nata kalar jarrabawa da take fuskanta ke naki jarrabawar kenan,dan haka kiyi addua Allah ya baki ikon cinye wanan jarrabawa" Jinta kawai nake dan gani nake ba Wanda ya Kai nawa zafi "Kije Palo yayan mahfuz na kiranki" "Mummy wlh bazan koma wa mahfuz ba na gama Zama dashi idan ma hakuri yazo bani gwara kar ya wahalar da kansa dan na Gama auren mahfuz yaje can ya karata da Hadeeza data fiye Masa ni ya Aiko min da takadar da ta cikin ruwan sanyi idan ba haka ba wlh hisba Zan Kai shi Kuma na Kai shi Kara kowa sai yasan mai ya aikata" "Ki tashi ki saka hijabinki duk sai ki fada masa nidai bazan miki dole ba amma inaso kisan indan Zama bai Kare a tsakanin ku ba haka Zaki hakura ki koma ana abinda yafi wanan ma a koma a cigaba da Zama" Zuciyata tafasa take har nasa ka hijabina bana san ganin Wanda ya danganci mahfuz amma gwara naje idan Yana tunanin dan ya turo yayansa zan hakura toh yayi a banza ba abinda zai taba mayar dani gidansa. Sai dai ga mamakina Ina fita naga ashe har da mahfuz yazo,hada idon da mukayi dashi yasa na watsa mishi wani mugun kallo Ina Munafiki kawai ni nasan yajini haka ma yayansa da isana wajensu na samu waje na zauna banso ma gaida yayansa ba amma sam sai naji bazan iya k'in gaishe shi ba, Ciki ciki na gaida shi ya amsa da murmushi a fuskar sa Mahfuz kuwa yayi rau rau da fuska Kamar zaiyi kuka "Lubna kiyi hakuri Mahfuz bai kyauta ba duk Wanda aka bashi hakuri ansan an cutar dashi,ki dubi girman Allah kiyi hakuri ki yafe Masa wlh yayi nadama ya Kuma gane kuransa ko dan yarinyar dake tsakanin ku kiyi hakuri ba Wanda baya kuskure tunda baki tab'a kamashi da irin wanan laifin ba insha Allahu wanan shine Karo na farko Kuma shine na karshe da Zaki Kama shi da laifi irin wanan" A dake na dago na fara magana ba tare da naji wani nauyinsa ba "Ya Usman wlh ko mahfuz shine autan maza na gama aurensa bazan tab'a komawa gidansa ba inaga karyar da ya Saba yi mutane ya ma shiyasa baka san ainihin abinda ya faru ba bari na baka labarin abinda ya aikata kasa kanka a matsayin yayana idan kanwarka ce ni wane mataki zaka ce na d'auka. Tiryan tiryan na kwashe komai na fada masa game da duk abinda Hadeeza ta fada min har yanda ta shawo kansa kafin ya kawota gidan da duk abinda sukayi na zayyane masa "Idan har Mahfuz zai min haka ya zuba min magani a lemo na Sha dan yaje d'akin budurwarsa karshen cin mutunci yamin wlh Mai kaunarka bazai tab'a maka haka ba tsananin Santa da yake yasa ya kawota gidansa dan ya ringa ganinta bama zai iya Hakuri har sai an daura musu aure ba taya zan komawa Mahfuz da idona nagansa kwance a jikin ta da wane idon zai kalleni na kalleshi har ya samu matsayi a zuciyata da Sunan mijina wane irin Zama zanyi dashi, mutuncinsa ya Riga da ya zube a idona,bazan tab'a girmama shi har na iya Masa biyayyan Aure ba har yaji dadin Zama dani dan haka yaje ya auri hadeezar sa ya kawomin takarda sakina idan na yaye mimi yazo ya d'auketa" Daga yanda Ya Usman ya kasa motsi nasan ya rasa Mai zai cemin ne hakane yasa na fara k'ok'arin mik'ewa mahfuz yayi sauri ya Sha gabana ya zube akan gwiwar sa idonsa ya Kada yayi jajjur kiriss yake jira ya saka kuka"Lubna dan Allah badan halina ba kiyi hakuri,wlh tallahi sharrin shaidan ne kema kinsan Ina balain kaunarki wlh na hadu da shaidaniyar mace ne,banyi niyyar kaita gida ba wlh Allah haka ta dagemin har ta shawo kaina" Bayan ta maka kiss kaji tudun kirjinta a bayanka sabida kwarto ne Kai dole ta shawo kanka nifa Mahfuz da kasan irin tsanar da na maka wlh Tallahi da baka tsaya a gabana da Sunan bani hakuri ba idan har baka San tonan asirinka ka aikomin da takardata ko ka bani yanzu idan ba haka ba wlh tallahi hisba Zan Kai ka Kuma kasan naje can dole na fada musu abinda kamin dayasa nake neman takardar saki,wlh bama kada kunya mahfuz,har gidanku ka Kai Hadeeza da baka Santa zaka kaita gidanku dan ta gaida Ammi ne,duk siyayyan nan da ka ringayi Ashe duk sabida ita ne Allah ya Isa tsakanina da Kai mahfuz ka rubutamin takarda sakina idan ba Haka ba wlh jibin nan Zan Kai ka hisba suma Dole ka bani takarda ta domin bazan Kara Zama da mazinaci ba" Na fara k'ok'arin kewaye shi na wuce dan yayansa har ya fice daga palon Mahfuz ya rike kafata gam dan duk abinan da ake Yana tsugunne akan gwiwarsa "Wlh bani na Kai Hadeeza gidanmu ba,ita ta Kai kanta ki yarda dani,Wlh wasu Abubuwan da ta fada Miki karyane so take ta rabamu lubna ki dubi soyayyar dake tsakanina dake ki yafemin" Ba abinda nake sai k'ok'arin fusge kafata amma ya rik'e gam har sai da na hada Masa da duka Ina ya sakeni. Karar bugun da nake Masa ne ya fito da mummy daga d'aki da sauri tayo wajena tana ke Mai haka ka cika ta mahfuz. Sai a lokacin ya cika ni na kewaye shi na shige dakinmu ya hau rokon mummy akan ta bani hakuri yayi nadamar abinda yayi na Masa kowane irin hukuncine,mummy ce masa tayi yaje gida zata min magana godiya ha hau yi Mata yace mata Yana San ganin Mimi,Mummy tace Masa bacci take. Ina Jin Yana Mata sallama akan zai dawo daddare,mummy tace ba sai yazo ba ya bari a kwana biyu har yanzu Ina Kan zuciya ne. Koda na Shiga d'akin Ina Kara tuna abinda mahfuz yamin ne ina Kara Jin zafi a zuciyata. Mummy kuwa data shigo rarrashina ta hau yi tana nayi hakuri,mijina na sona kila ma asiri Hadeeza ta Masa baa hayyacinsa ya kaita gida ba" Murmushin takaici nayi dan nasan an Sha rainawa Mata wayo da Sunan asiri aka yiwa mazajensu bayan karyane ba wani asiri zalar iskanci ne ko asirine ma asiri na tada hali. Wayata ta mikomin akan shi ya kawomin Na kuwa karba nayi blocking lambarsa. Miscall din Abdul nagani rututu har dasu text Koda na bud'e text dinsa hakuri yaringa bani da rantsuwar baisan abinda Mahfuz yayi ba kenan da bai kawota ba. Ban Masa reply ba dan ba amfanin hakan ban Kuma wani ji haushinsa ba dan ada na dauka da hadin bakinsa amma tunda ga lokacin da nasan ba ruwansa naji ban rik'e sa a raina ba. Har a raina so nake bayan sallah idan har Mahfuz bai kawomin takarda ta ba hisba Zan Kai sa. Wasa Wasa sai gashi kullum mahfuz sai yazo gidanmu duk da bana fita,haka ya ringa kawomin mutane iri iri akan su bani hakuri ciki kuwa har da mijin mmn Iman da yace mahfuz Yana neman zarewa na yafe Masa yayi nadama. Sam bana Jin mahfuz a Raina dan Mummy ma yanzu tausayinsa takeji,ita ta ringa hanani zuwa hisba. Daidai da zainab kanwata sai da ta fara tausayinsa amma niko Ina nan Ina Jin haushinsa har yanzu Ina kwanta bacci Ina tuno yanda na gansa da Hadeeza. A irin wanan lokacin Ina da wata daya da sati daya a gida Abdul yazo bayan dogon nasihar da yamin da waazi da roko akan na komawa Mahfuz na dage Masa na gama auren mahfuz,dan ko na koma wlh bazai ji dadin Zama dani ba dan mutuncinsa ya zube a idona na har abada ba Kuma na jinsa a zuciyata balle har na iya kyautata Masa. A takaice dak'yar da nasiha da rarrashi dan mahaifiyata da ta sakoni agaba da mmn Iman na yarda Zan koma baa san Raina ba Ina jimanta irin zaman da zamuyi da mahfuz da ko kad'an bana kaunarsa, indai Zan gansa sai na tuna abinda yamin zuciyata tayi ciwon abinda yamin,sabida na bashi wahala nace Masa bazan zauna a gidanmu ba dan indai Zan kalli d'akin da Hadeeza ta zauna sai na tuna ta. Take ya nemo gidan haya ya Kama mana sai rawar jiki yake yabi ya rame Kamar bashi ba,bana ma jinsa a Raina nasan bazaiji dadin Zama dani ba,dan.bazan tab'a yarda ya kusanceni ba dan bazai zo ya shafamin cuta ba...... Duk wayanda suke min sharing na barsu da Allah MG'S SKINCARE In akaji gangami labarin kidane,sun shahara sun tumbatsa sunkai sunwuce tunanin duk wani meson Adama dashi aharkar gyaranfata d walwalinta, Yar uwa haske ko qyalqyale kikeso kiyi Abu yaci tura? Kyan fuskarda ko yar uwarki mace kance dama dama kikeso? Kokuma ke kuraje d tabbuna suka lahanta mki fuska har ake ganinki d wani idon n daban, Nankarwace tayimiki zanen kura a kyakyawar fatarki? Kokumade Mai kikashafa be amshekiba yasa duk kika koma ruwa biyu Nan fari Nan baqi? To duk kuzo insha Allah kudai naku y qare gdan kukazo, Munkawo shahararrun kayangyaran jiki Sabulu, Man shafawa, Man fuska, Scrub, Cleanser, Glow oil, Dukdan qawarmaku d matsaltsalunku, Da 11k kachal zatasa kihaske kizama kalar madara qirar models, Set 11k Sabulu 3k Student package:7k Munakuma bayarwa in pieces duk afarashin mesauki.kayanmu bbu fariya ko tutiya angwada andawo,ankumayi farinciki d hkan,Kuna iya samummu d wadannan numbobin, WhatsApp, 08062991549 or 07046881166 or 07067210195 Call only 08064532391 Instagram: glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Idanba wadannan numbobinba to gaskiya b mg's bane, available in Kaduna and Kano only, thanks for always trusting us,our returning customers we really do appreciate wadanda sukeda burin Siya munamaku fatan alkhairi ubangiji ybaku yenda zakuyi,Allah Kuma yqaro mna dukiya me amfani ta hanyar halalinmu. *WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min SHARING bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi* Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 07046881166 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare *WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min SHARING bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi* *Page 18* "Lubna Wai Mai hakane dan Allah dan Annabi so kike sai na kwanta jinya ko na kashe kaina kafin ki hakura" Ya cigaba da jijjiga k'ofar daya dameni ma na kunna karatu a wayata bansan Mai yasa zuciyata ta k'ek'eshe ba mahfuz ganinsa na Yan mintina ma batamin rai yake abinda ko kusa bazan yarda ba shine yace zai tabani da sunan zai samu nutsuwa dani, bayan ya kwanta da Hadeeza da ita kanta bata San adadin mazan da suka nemeta Ina matarsa ta sunna ya tsallakeni ya tafi wajenta hmmm macen data Kama mijinta da laifin cin amanar irin na mahfuz kawai zata Gane mai nakeji a zuciyata,ko kishiya aka ma kana dadewa cikin Jin Haushin mijin ka ballantana Wai budurwa naja dogon tsaki na Kara gyara kwanciyata dan idan har zan tuna sai naji kamar a yanzu abin ya faru ina jinsa ya bar bugun k'ofar. Bansan a Ina ya Kwanta ba har bacci yayi awon gaba dani. Mahfuz Yasan yayi wa Lubna laifi amma wulakanci da take Masa ya fara isarsa,ya bata hakurin yayi rarrashin yayi kukan,baisan Mai takeso yayi ba har rantse mata yayi akan ya rabu da Hadeeza duk abinda takeso zaiyi amma Sam Taki saurarensa k'arfi da yaji yake neman zaucewa rabonsa da wata ya mace tun lokacin daya sadu da Hadeeza,wata wajen biyu kenan da sati,tunda yayi aure,bai tab'a sati ba mace ba ko period lubna take takan Masa dabaru ya samu nutsuwa amma sai gashi Yana fama da matsanacin shaawa sai aukin Shan kanwa da yake,a dawowar nan da tayi ya d'auka zata barshi ya samu nutsuwa ko Yaya ne amma sai gashi ko ta kansa bata bi ba ta kulle k'ofar,ya balain saka Rai da samun nutsuwa da ita,Koda ya kwanta juyi kawai ya ringayi,yanda zai samu nutsuwa kawai yake nema, wajen daya ya Kara mik'ewa ya nufi d'akin Lubna ya hau bubugawa amma lubna ko kulashi batayi ba balle ma tasan ana kwankwasa sai gajiya yayi da bugun k'ofar ya koma dakinsa. Hannunsa dafe a mararsa ya d'auko wayarsa shi kansa bai san dalilin dayasa ya dauko wayar ba. Tsintar kansa yayi da shigar da lambar daya haddace a kansa ya hau Kira bugu daya yaji ta d'auka tare da Jan dogon ajiyar zuciya "MahfuZ Kaine ko mafarki nakeyi"? Ta fada can kasan makoshi daya sa yaji ta kara daga Masa hankali Sam bai iya magana ba a ransa Yana tunanin dalilin dayasa ya kirata da bashida burin daya wuce ya yakiceta daga rayuwarsa amma a Yanzu gani yake tunda lubna taki sauraransa zai iya samun nutsuwa a wajen Hadeezan. Cikin kukan kissa da shagwaba ta fara magana tana Jan numfashi Wanda hakan ya tilasta masa rub da ciki dan ji yayi kamar mararsa za ta fashe ba abinda yake dawo masa sai abinda ya shiga tsakaninsu a karshe, kafin ta bar gidan Can kasan murya kamar Mara lafiya yace "Hadeeza banida nutsuwa kimin abinda zan samu na fitar da abinan dake marata pls" Wani irin kuka ta saka mishi daya saka shi wawuro pillow ya kankame a kirjinsa,yanda Hadeeza keyi yasa shi imagination ya ringa wani irin abu,shima ya ringa yi gurnani kasa kasa,Hadeeza kuwa ta cigaba da zuba masa kuka dayasa cikin Yan mintuna ya fara vibrating dan Kamar Yana tare da Hadeezan haka yakeji. (KUYI HAKURI BANSO NAYI BAYANI DALLA DALLA KAMAR NAYI BATSA NIMA WANAN DIN KAMAR NAYI DIN NAKEJI🙂🙂) Numfashi kawai yake mayarwa Yana Jin Hadeeza tana "Karka cutar da kanka ka cutar dani Mahfuz ka turo gidanmu muyi aure na ringa faranta maka nayi missing dinka mahfuz" Sai daya dawo daidai yaji kamar ya rufe kansa da duka baiso Sam ya Kira Hadeezan ba duk da bata gama fita a ransa ba,amma bayajin zai iya aurenta,a yanzu yafisan ya samu ya rabu da ita cikin sauki,tunda dama bashida burin Kara Auren Lubna ta ishe shi rayuwa. Bai san ma mai zai cewa Hadeeza ba dan lalura ce tasa ya Kira ta Kuma duk lubna ce ta jawo masa kashe wayarsa yayi gabad'aya batare da yacewa Hadeeza uffan ba. Ya lumshe Idonsa dan sosai yaji shi sakayau kamar an cire masa nauyi a jiki. A hankali ya fara tuno wayar da yayi da Hadeeza yanda ta ringa kuka Kamar suna tare da Sunan ita budurwa ce a Ina to koyo irin wadanan Abubuwan. Dan lubna har yau bata iya nuna Masa wani abu idan Yana tarayya da ita Wai kunya takeji,sai da ya zaunar da ita ya nuna Mata hakan da zatayi ne zai saka yaji dadi,yasan tana Jin dadin tarayyarsu,a hakan ma ba sosai take iya yi ba,taya duk Hadeeza ta iya Abubuwan Nan,ya tuno ranar daya fara kusantarta,hadin kai ta bashi ba kadan ba,Taya ma zai soma aurenta,a yanzu ya riga da yasan ba a budurwa ya sameta ba Tama goge a harkar har Lubnar ma tafi ta gogewa,yasan a yanzu zata cigaba da addabarsa da waya gashi lubna ta dawo shi.yasan a duk ranar da lubna ta ga Hadeeza ta kirashi yasan komai zai fada mata ba yarda zatayi ba,Kiran nan daya mata duk lubna ce ta jawo Masa. Haka yayi ta sake sake har bacci yayi awon gaba dashi ba dadewa ya hau mafarki da Hadeeza Wai a kwancen da yake ta shigo dakin da yake kwance har ya kwanta da ita, lubna ta fado d'akin da wuka a hannunta aguje tayo kansu ya farka a gigice. Ganin mafarki yake yasa ya koma ya kwanta,ya zama dole yayi taka tsantsan dan a yanzu ma tsoron Lubnar yake. Baccin da bai koma ba kenan har aka Kira sallah asuba ya Shiga toilet yayi wanka ya dauro alwala ya fito har zai kwankwasa wa Lubna Kuma ya fasa dan yasan tana tashi itama. Lubna Ina jinsa ya fita massallaci dan tun hudu na farka ban Kara komawa bacci ba sabida mumunan mafarkin da nayi wai Hadeeza ta shigo gidan ta window naje na rutsa ta a d'akin mahfuz,duk na dauka a gaske ne sai da na farka bansan Mai yasa Hadeeza ta tsaya min a rai ba,na balain tsanarta a dawowa nan da nayi so nake ko Yaya ne na kamashi ma Yana waya da Hadeeza a ranar sai mun rabu,nasan mace bata Isa ta tsallaka kaddararta ba,amma ko da mahfuz na da rabon Kara aure na gwammaci ya auri kowa Banda Hadeeza,a duk ranar daya auro Hadeeza na gama Zama dashi kenan har abada. Wajen shidda naji shigowarsa sanin ranar asabar ne ba fita yake da wuri ba yasa na koma nayi kwanciyata. Karar tv da na jiyo ya kunna yasa na san Yana palon na Kuma tuno tv nan yake kunnawa ya yaudareni na dauka Yana Palo Ashe yana can d'akin Hadeeza na cije lebbena dan takaici,Nima tuna Abubuwan Nan ma hawan jini yake neman doramin amma bansan ya Zan hana zuciyata tunawa ba. Wajen karfe takwas na fada bandaki nayi wanka na fito na dan shafa Hoda da man lebbe sai parking da nayi, wani yellon doguwar Riga nasa da bai jemin har kasa ba ya kwanta a jikina sosai nayi kwalliya ne dan kaina ba dan wani mahfuz ba,ban fito daga d'akin ba sai da na yiwa mimi itama wankan na shiryata na sabota a kafadata na fito. Ina bud'e kofa Muka hada Ido dashi Yana kwance a doguwar kujera sanye yake da farar jallabiya. D'auke kaina nayi daga kallonsa na kwantar da mimi a 2 seater. Nayi hanyar kitchen zanyi Masa komai amma bazan yarda ya tabani ba. Sam banji shigowarsa ba sai ji nayi an rungumeni ta baya,so nake na fusge jikina daga nasa da sauri amma rukon da yamin ma bazan iya kwakwaran motsi ba yasa kansa a wuyana Yana "Haba Lubna haba matata shikenan mutum bazai yi kuskure a yafe mishi ba,kinsan halin da nake ciki kuwa nayi kewarki lubna dan Allah ki yafemin ya riga da ya wuce nasan nayi kuskure bazan sake ba ki manta da komai mu cigaba da rayuwar mu kamar da" Duk maganar Nan da yake k'ok'ari kawai nake dan na fusge daga jikinsa,amma yaki bani damar sai wani lasar min dokin wuya yake, ada Yana min haka duk girman laifin da yamin sai na sauko amma bansan Mai yasa ko kad'an maganrsa bata shigeni ba,har idan Yana Sona bana Jin zai ci amanata nasan Mai yasa yake ta lallabani so yake kawai na barshi ya kwanta dani. Tuni ya hau yamutsani.ya hadani da bango ya dagemin riga Sama ya hanani ma motsi idan ya kawo bakinsa bakina sai na cije shi. Ganin ya dage gaske a kitchen yake san yamin dole yasa na handaka.dashi da balain k'arfi Ina "Dan Allah mallam rabu dani, Mahfuz Wai kana tunanin bayan abinda ya faru cikin sauki zan iya yarda dakai,taya zan yarda.da Kai bayan baka je kayi gwaji ka tabbatar da lafiyar ka ba" "Lubna naje nayi gwaji fa kikace"? "Eee kaje kayi gwaji nace dan bazan zauna ka shafamin cuta ba,tunda ita budurwar taka ba kai ka fara saninta ba,itama kanta bata san adadin mazan da suka nemeta ba to akan me zan bari ka tabani bakayi gwaji ba idan har kaga na bari ka tabani a gidanan wlh sai na tabbatar da lafiyarka" "Lubna yanzu wulakanci naki har ya Kai haka zargina ma kike zan saka Miki cuta,shikenan dan shaidan ya rinjayeni nayi abinda zanyi sai kice Ina d'auke da cuta" "Wnan kuma matsalarka ce kaje asibiti dan ka tabbatar da lafiyar ka dan kaima kasan budurwar ka karuwace zata iya yuwa tana da cuta" Yanda idonsa ya Kada yayi ja yasa na tabbatar da yaji haushi ko a jikina na dauko doya na fara feraye wa ya gaji da tsayuwa a kitchen ya fice ya bani guri. Ko kad'an banji a raina abinda nakeyi ba daidai bane ba Har na gama soya doya da kwai na dafa Mana ruwan shayi. Sai da na zuba nawa daban na Kai sauran palo,ban ganshi a palon ba. Hakane yasa na samu waje na zauna na fara karyawa,har na gama ci bai fito ba dan Ina Jin motsinsa a d'aki. Koda na gama ci wayata na d'auko ina lallatsawa naji motsin bude kofa ban daga kaina ba amma kamshin turarensa da naji yasa nagane wanka yayi,na dauka zaiyi zuciya yaki cin abincin ta gefen ido na ringa satar kallonsa ya zauna ya fara cin abincin. Daga ni har shi ba wanda yayi wa wani magana har ya gama ci ya mik'e Yana "Ni Zan fita zanje gida daga nan zanje asibitin nayi gwajin kamar yanda Kika bukata idan har gwajin ne zai kwantar miki da hankali zanyi" "Idan ma wajenta zaka je ba damuwata bace ba gwajin Kuma idan kayi dan lafiyarka ne ba nawa ba" "Allah ya kyauta wanan halin da Kika tsiro dashi ba Mai kyau bane ba karki manta aljannarki na tafin kafata karki ringa daukar wa kanki zunubi lubna" Wayata na cigaba da latsawa ya gama surutunsa ya fice ko fitar da yayi sai da naji kamar wajen Hadeezan za shi ni nasan mawuyancin abu ne ya rabu da ita,idan shi zai rabu da ita wanan mayyar yarinya bazata rabu dashi cikin sauki ba,a zaune da nake sai zuciyata take saka min sai ya biya ta wajenta ma ya ganta. Mahfuz Yana fita daga gida ya kunna wayarsa a fitar da yayi har layi yayi niyyar canzawa dan a yanzu baya san su samu sabani da lubna,yasan ya kirawa kansa ruwa jiya Kiran da yayi wa Hadeeza yanzu zata sake Sako shi agaba,wayar na kunnawa sai ga texes dinta yafi Goma a wayar Yana k'ok'arin bud'ewa ya karanta sai ga kiranta a wayarsa yasan zaa rina Kuma bazai dauka ba. Hakane yasa ya saka wayar a silent ya jefa a aljihunsa, gidansu ya fara zuwa Koda ya gaida Ammi bata amsa gaisuwar da ya mata ba sai cewa tayi "ka dai rantse sai ka dawo da yarinya nan ko?ka rantse sai nayi azumin kaffara ka dage ban Isa da Kai ba ko"? "Ammi dan Allah dan Annabi Mai lubna ta Miki da zafi haka ?Ammi ni.na mata laifi fa" "Zaka ga mai ta min ba dai ka dawo da ita ba tom ka fara shirye shiryen aure dan wlh Tallahi sai ka Mata amarya idan bazata iya ba sai ta Kara gaba" "Ammi banida halin Kara Aure yanzu ni lubna ta isheni rayuwa" "Idan ma asiri ta maka zaka dawo hankalinka Zan nuna Mata na Isa da Kai ni na haifeka ba ita ta haifamin Kai ba MahfuZ ka fara shirye shiryen turawa gidansu yarinya Nan Hadeeza" Gwallo Ido mahfuz yayi Yana "Ammi wlh bazan iya aurenta ba haba Ammi dan Allah ni bama nida niyyar aure" "Bazaka iya aurenta ba amma zaka iya kaita gidanka ko toh wlh sai ka aureta mu zuba mugani" Duk Yar muryar da mahfuz ya ringayi wa Ammi ko kulashi bata karayi ba haka ya mike ya bar gidan ransa a bace shi Kam rabonsa ma dayaji shi cikin kwanciya hankali da farinciki har ya manta. Daga gidansu asibitin da suke zuwa yaje. Da zuwansa ya fadawa likita gwajin da yake.so ayi.masa, Cikin awa daya aka Masa gwajin yasan bashida wani cuta ko Hadeezan ma bai zargi tana da wani cuta ba dama. A hanyarsa ta komawa gida ya siyi layi Mai register ya saka a wayarsa ya cire tsohon layinsa dan yasan Yana kunna wayar Hadeeza zata kirashi. Duk da yasan sai lubna ta fada Masa bakar magana haka ya tsinci Abubuwan da take so ya tafi dasu. Wajen karfe uku ya Isa gidan. Lubna Nasan asabar ba office yake zuwa ba idan gidansu ne ma da asibiti yaci ace ya dawo,amma har na gama girkin rana Bai dawo ba,haka.kawai naringa Jin kila zance.yaje wajenta idona na zubawa agogo Ina kirga sakanni da mintoci,wajen karfe uku sai gashi ya shigo,ciki ciki na amsa sallamar da yayi Ina Jin idonsa a kaina.har ya samu waje ya zauna yana "Sannun ki da gida" "Yauwa" "Ammi tana gaisheki" "Ina amsawa" "Lubna naje asibiti nayi gwajin ga result din bana d'auke da kowane cuta" "Toh yayi kyau" "Ki karba ki gani Mana" Ko kulashi banyi ba Ina jinsa ya saki murmushi Yana "ai duk ta Inda Kika biyomin daidai nake dake yau dai baki Isa ki gujemin ba sai kin bani hakkina lubna rabona dake fa tun ana washegari zaki haihu watan Mimi yanzu nawa ta tafi hudu fa" "Rabonka Kuma da Hadeeza fa"? "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Lubna Nagaji daga yau Kar na sake Jin sunan Hadeeza a bakinki wanan wane irin masifa ne Abu kad'an sai kice Hadeeza Abu kad'an sai kice Hadeeza ba dama nayi magana sai kin Kira sunanta" "Da baka kawota gidanka ba Zan santa ne ai ba karya nayi ba da kake cewa rabona da Kai an dade.ai Naga Ina nan ka wuceni kaje wajen Hadeeza ai lokacin Ina da tsarki ko nawane baka marmari sai nata,dan haka.kaje wajenta ta cigaba da baka" "Inaga dan banyi maganinki bane shiyasa kike kiramin sunan ta kafin na ankara ya iso wajena ya danne ni da k'arfi ya fara kokawar ciremin riga. Karfinsa da nawa ba daya bane duk yanda naso na hanashi kasa wa nayi,haka ya hau jagwal gwalani,Yana dab da cimma burinsa na hau tuno abinda yamin da yanda ya binne kansa a kirjin Hadeeza "idan kasan Kai dan halak ne ka kyalleni idan Kuma ba dan halak bane Kai sai kayi amma inaso kasan ba abinda zakayi naji Dadi a raina bakin ka nake gani har yanzu Ina hango ka a kirjin Hadeeza Tunda na fara magana ya tsaya cak Ina idda magana ya dagani idonsa yayi jajjur Kamar jini yace "Lubna ni dan halak ne Kuma Zan nuna Miki nidin dan halak ne" Ya dauke gajeran wandonsa da sauri yayi hanyar d'aki.... Mg's cakes nd more For the lovers of cake,Ina masu biki ko suna ko wani shagali na musamman ko dan jin dadinku da morewar ku ko kuma akwati kuke Shirin ansa zaku bayar matsayi tukwaici,tofa nesa tazo kusa domin kuwa zamu tabbatar mun fidda ku kunya mun kuma gamsar daku da hadaddun abubuwa kamar su,cake nd cupcakes,meat pie,fish roll da kuma egg rolls,to me ya rage muku ai kawai ku tuntube mu ta number nmu kamar haka 07067210195,08062991549 cika alkawari shine taken mu,adade anayi sai gaskiya *WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min SHARING bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi* *Page 20* Lubna Koda na Kira Mummy na fada mata fitar da mahfuz yayi da girkin da na masa yaki ci cikin kuka na Kara da "mummy wlh mahfuz a yanzu baya sona hankalinsa ba'a kaina yake ba, shiyasa nace miki bazan dawo ba wlh dan biyan bukatarsa ya dawo dani, yau kwana biyu da dawowa gidansa har ya fara fita wajen budurwarsa wlh abinda na dauka a baya bazan iya dauka ba yanzu, tun daga lokacin da na kamashi da budurwarsa ya fice min a rai mai kaunarka bazai tab'a maka haka ba dan haka wlh mummy bazan iya zama ba zan hakura da aurensa yafimin alheri" "Shikenan Lubna mijinki bazai fita ba sai kice zance yaje?wai wanan wane irin abune kinfi so tun kina karamarki a ringa kirga miki aure? Kin isa ki canja abinda ya faru ne? Idan kina haka zai goge abinda ya riga da ya farune?,shikenan dan kin kama shi da laifin cin amanarki duk wani motsi ko fita da zaiyi cin amanarki yake"? Lubna bazaki ki kwantar da hankalinki ba ko?bakya Jin magana ko?kinaso ki nuna ban Isa dake ba ko?to ki kashe auren naki tunda bazaki iya zama ba " Kit naji ta kashe wayar. Nabi wayar da kallo hawaye na zubo min mummy ta kasa fahimta ta ta kasa gane halin da nake ciki,duk abinan da mahfuz yamin taya zan iya mantawa da wuri,har na iya sakin jikina dashi,ko zan saki jikina dashi sai na tabbatar da rabuwarsa da Yar iskar budurwar sa da ni nasan bazai iya rabuwa da ita ba idan har yasan bazai iya rabuwa da ita ba ya aurota ya sakeni,dan bazan tab'a zama da Hadeeza da Sunan kishiyata ba,ko fitar da yayi ban yarda abinci yaje nema ba nasan wajen Hadeeza ya tafi,idan har Yana Sona dan nayi fushi akan abinda yamin,bai Kamata yayi fushi ba har yak'i cin abincina. Haka bakin ciki ya cikemin zuciya Ina kallon agogo har tara ta wuce ko uwar abinci yaje ci yaci ace ya gama ci ya dawo idan ba wulakanci ba da Rana ai da yayi zuciya da abincin zuwa yayi ya dafa bai fita nema ba. Tara da rabi na wucewa na mik'e naje na kulle k'ofar ba inda yaje sama da wajen Hadeeza dan me ya matsamin na dawo bayan Yana tare da ita. Na dauki Mimi muka Shige daki muka kwanta ni kadai nasan bakin cikin da nake ciki,mahfuz ya Raina min hankali. Ina kallon agogon har goma ta wuce da minti goma anan na yanke sai dai ya koma wajen Hadeeza ya kwana amma ko ya dawo bazan bude masa kofa ba Kuma sai ya bani takardar sakina ko yanaso ko bayaso gwara ya sakeni yaje ya karata,idan ya ga dama ya auri Hadeeza idan yaga dama ya kawota gidan ta zauna na dindin din wanan matsalarsa ce amma matsawar Ina amsa sunan matarsa ina zaune a gidanan wlh sai dai ya zabi Hadeeza ko zama dani tuna duk abinda nayiwa mahfuz daga lokacin da muka hadu zuwa na aure shi nayi hawaye ya hau zubomin,na tuna akwatin Aurena da ba kayan arziki ya zuba min ba haka kawayena sukayi tayi dani,ko damuwa banyi ba dan Ina kaunarsa,duk wani abu Kuma da nayi da mukayi Aure rabin hidimar mummy ke bani kudin dan duk wata inta dauki albashi haka take binmu da kudi ba iya ni kadai ba dani da Zainab dan tana d'aukar albashin da yawa gashi dagani sai zainab da yayata da nake bi. haduwata da mahfuz yasa ban cigaba da karatu ba dan yace kishine dashi,haka nake zaune sai mummy ce ma take cemin na bari idan na haihu zata bani jari na kama Sana'a,ban tab'a b'atawa mahfuz rai da gangan ba,duk wani abu da nasan Mahfuz naso Ina iya k'ok'arina na Masa koda ni banaso amma sakayyar da mahfuz zaimin shine ya kawomin budurwarsa har gida ya munafirceni,ya fifitani akanta ya Kuma Sakani hidima da ita,dan Nagano shi nayi fushi shine zaiyi fushi shima,Mai amfanin zama da mahfuz, mutumin da hankalinsa ya koma kan budurwarsa da taki aurensa sabida bashida abin duniya,banma san Yana da rufin asiri ba sai da budurwarsa tazo gidan har ya iya bata Dubu ashirin kudin kitso da kunshi,har a yanzu dubu ashirin a dunkulle bai tab'a bani ba. Na kara kallon agogon naga goma da minti talatin da biyar adaidai lokacin da naji bugun kofa na maida idona na rufe dan dagaske so nake ya kwana a waje idan gari ya waye yayi zuciya ya bani takardar saki na. Duk bugun da yake Ina jinsa har Kiran da yake min a wayata da nasaka a silent. Idona biyu bai fasa buga kofar da Kiran waya ba har daya na dare yayi. Haushin karnuka kawai nake jiyowa a waje burina ma su cije shi buga kofar da naji ya daina na tsawon mintuna yasa na bud'e idona,wayata dake ta kawo haske na leka naga mummy ce take kirana,da sauri na mike zaune na daga wayar "Lubna yanzu mijin naki Kika kulle a waje innalillahi wa Inna ilaihi rajiun dama haka kike a yanzu na tabbatar da kina da matsala a yanzu na yarda akwai mugayen Abubuwan da kikeyi dayasa yarinya nan ta d'auke masa hankali wlh idan baki so naci ubanki kije ki bud'e Masa kofar nan" Kuka nasaka Ina k'ok'arin Magana ta kashe wayar. Na duro daga kan gadon nayi waje a fusace na bud'e k'ofar na ja da baya Ina jiran ya shigo. Sai daya dade kafin naji Yana kokawar shigowa da machine dinsa. Ina tsaye har ya shigo fuskarsa a balain had'e,kamar yanda nima nawa yake a had'en. Yana saukowa na fara shakar kamshin turaren Hadeeza daya saka kirjina wani irin bugawa na tabbata ko hauka nake ba'a hayyacina nake ba idan naji kamshin turaren Hadeeza nasani. Dagaske mahfuz wajen Hadeeza yaje daga dawowa ta bai ma iya daga kafa na kwana biyu ba tunda na hanashi kaina gwara yaje wajenta ta bashi,nama bashi yaje wajenta ballantana yanzu da na hanashi. Wani irin zafi naji kirjina namin daya kusanto wajen da nake tsaye a fusace ban bari ya karaso ba na daka tsalle na isa wajensa na cakumo wuyan rigarsa sosai yake kamshin turaren hadeeza "Bani takardar sakina mahfuz na balain tsanarka cutar da kayimin Allah ya Isa ban yafe maka ba bani takarda sakina mahfuz" Wani irin fincike hannuna yayi daga rukon da nayi masa cikin hucci yace "Ni kikayi wa laifi amma zaki zo ki cakumi wuyan riga na kice na sakeki" "Mahfuz mai yasa ka dawo dani gidanan bayan kasan bazaka iya rayuwa ba Hadeeza ba? yau Zan kwana biyu da dawowa amma mahfuz har ka koma wajenta idan har kasan kana santa haka Mai yasa ka dage min na dawo"? "Ke fa dama idan Kika tashi haukarki bakya lissafi da tunani ni nace miki wajen Hadeeza naje"? "Ko baka fadamin ba mahfuz ga kamshin turaren ta nan a jikinka ga Jan baki nan a kwalar rigarka dan Allah bakaji kunya ba Mahfuz na tsaneka ka sakeni kaje ka aurota idan Kuma dawo da ita gidanan zakayi sai ka dawo da ita mahfuz amma ni lubna na gama zama dakai ka rubuta min takarda ta mahfuz wlh na gama aurenka" Nace cikin ihun kuka tare da Kara cakumo rigarsa Mara gaskiya ko a ruwa yake gumi yakeyi Ina cewa Yana kamshin turaren Hadeeza ya hau zare Ido,gumi na tsatsafo masa ya jawo kwalar rigarsa ya hau dubawa bai kalleni ba ya runtsa idonsa na cigaba da jijjiga shi Ina ya sakeni "Ki yarda dani ba wajen Hadeeza naje ba abokina ne ya fesa irin turarenta yarsa da na dauka yasa na goge janbakin bakinta" "Kutumar uban abokinka da yarsa baka ma iya karya ba mahfuz,yaushe maza suka fara fesa turaren mata mahfuz bana kaunarka bana San ganinka idan baka so na tara.maka jamaa ka bani takardar sakina gobe da safe na bar.maka gidanan kaje kayi duk abinda kaga dama da Hadeeza" "Lubna dan sakeni dan Allah dan annabi karki manta dare yayi mu Shiga ciki muyi magana" "Bazan sake ka ba sai ka bani takarda ta mahfuz wlh dak'yar nake numfashi sabida ganinka da nakeyi mahfuz ka bani takardata" "Lubna na rantse da Allah bazan iya sakinki ba Ina kaunarki dan Allah ki tsaya mu fahimci juna wlh indai Hadeeza ce zan rabu da ita wlh sabida na faranta miki rai na canja layin wayata yanzu ma na saka layin ne dan na kwafi lambobi dan Allah kiyi hakuri ki cikani" "Mahfuz idan kaga na cikaka wlh ka furta kalmar saki a gareni mahfuz yau kwana daya da wuni duk abinda kayimin duk baka ga girmansa ba daga dawowa ta ka Kara koma Mata,Ina san da kake min yake mahfuz ka daina yaudarar kanka,Hadeeza kake so ba lubna ba dan haka Zan hutashe ka ka bani takarda ta ka aurota ko kuyi zaman daduron duk abinda ka yanke yayi daidai nidai ka sakeni" "Toh ki cikani mu Shiga ciki na rubuta miki" Da sauri na sake shi yayi hanyar palo da sauri nabi bayansa Ina Jin kamar na shako shi dagaske ba abinda nake burin gani sama da takardar sakina Muna Shiga palon ya shige d'akina na bishi har d'akin da shigarsa ya daki ya duka a kasa duk wani abu da mahfuz zaiyi yanzu bakinsa nake gani,ba abinda zai fadamin da zai Shiga kunnena duk rokon nan da ya ringayi na dawo ashe na munafirci ne daga dawowa ta ya tafi wajen budurwa bazan zauna mahfuz ya saka min hawan jini ba,ban damu da durkusawan da yayi ba na hau dube duben inda Zan samu takarda da biro,drawers din dake gefen mudubi na nufa da sauri,na hau watso da tarkacen ciki jikina sai rawa yake tamkar yanda na kamashi da Hadeeza zuciyata ta ringa Kuna haka nakeji a yanzu dan Koda bangansu a taren ba kamshin turaren da yake da dan janbakin gefen wuyansa ya tabbatar min da wajenta yaje babu ma ja "Lubna dan girman Allah ki nutsu muyi magana Lubna ko kasheni zakiyi bazan iya sakinki ba Ina kaunarki lubna wlh sanki bai tab'a raguwa a zuciyata ba daidai da second guda" A zabure na jawo drawer na jefa masa cikin ihu Ina "Karya kake Yi mahfuz da kana sona bazaka ci amanata ba,da kana sona bazaka kawomin budurwarka har gida ka ringa kwanciya da ita,da kana sona bazaka fifita budurwarka a kaina ba Ina matarka ka wuceni ka barni a gida kaje wajenta dan kawai na hana ka kaina bayan duk abinda kamin mahfuz,kwana biyu da dawowa ka Kara koma mata Ina San yake anan ka fadamin mahfuz ka maidani shashasha ka wulakantani kaci mutuncina ka nunawa budurwar ka banida wani matsayi a wajenka har gidanku ka kaita mahfuz sabida tsananin san da kake mata duk abinan daka min ka dage na dawo daga dawowa ta ka Kara komawa wajenta,Mai na maka dana cancanci haka daga wajenka mahfuz,dame na rageka da ka fifita budurwarka a kaina laifi ne dan na soka na aureka har yanzu ba muyi shekara biyu ba mahfuz" Kukan da yaci karfina yasa na kasa cigaba da magana sosai nake Jin ciwon abinda mahfuz yamin Zafin da kirjina yakemin yasa na dafe kirjina da hannu biyu bansan lokacin daya iso ba sai ji nayi ya kamkameni cikin rawar murya Yana "Baki rageni da komai ba Lubna wlh duk abinda ya faru sharrin shaidan ne bansan Mai ya hau kaina ba Hadeeza shuuma yarinya ce bansan ya akayi ta ja raayina har na kawota ba wlh ba wai bana kaunarki bane Ina sanki wlh Allah kiyi hakuri ki yafemin ki bani dama na gyara kuskure na nayi alkawari duk abinda kikeso shi zanyi a gabanki zan karya layin Nan da Hadeeza ta sani dashi" Rashin kwari yasa bama zan iya kwace kaina daga rukon da yamin ba kamshin turaren Hadeeza da nake Shak'a a jikinsa yasa nake Kara Jin zuciyata na zafi "Wane irin kalamai ne baka min kafin na dawo ba wane irin ban hakuri ne baka bani ba kafin na dawo daga dawowata mahfuz ka koma gareta mahfuz ka daina wahalar dani kana wahalar da kanka ka sakeni kaje ka zauna da Hadeeza dan Allah ka daina azabtar dani ka rabu dani na bar Mata kai duniya da lahira" "Bani naje wajenta ba lubna ita tazo ta sameni a wajen da naje cin abinci" "Shine ta danneka ta maka fyade ko mahfuz"? "Dan Allah kiyi hakuri Lubna ki tausaya min ki kwantar da hankalinki" "Kwanciyar hankalina shine ka bani takardata dan bazan iya zama da fasiki ba" "Toh naji ki kwanta gobe da safe sai na rubuta miki" "Bazan iya kwanciya ba sai ka bani mahfuz babban burina ka bani takarda ta" "Wlh Lubna Zan rabu da Hadeeza duk abinda kikeso wlh Allah zanyi na Miki na farko na Miki na karshe idan kin Kara kamani da ko waya Ina Yi da ita nayi Miki alkwarin Zan sakeki" Haukace masa nayi akan lailai sai ya sakeni,ya dage da magiya kaina danajin Yana baranazar rabewa biyu yasa na samu waje a gefen gado na zauna, Yana k'ok'arin nufoni na daka Masa tsawa akan ya fice min daga d'aki. Ya fita da sauri na koma na kwanta Banida burin da ya wuce garin Allah ya waye na hada kayana,mahfuz ya Saba da Hadeeza ko min daidaita bazai fasa nemanta ba banga amfanin zamana dashi ba. Sam bacci bai ga idona ba sai wajen karfe hudu bacci yayi awon gaba dani. Mahfuz So yayi tana bude k'ofar ko bai dauketa da Mari ba zai jijjigata har shi zata kulle a waje , sam dabaran Kiran mahaifiyar lubna bai fado masa na sai dayaga dagaske Lunbna ta shiryawa ya kwana a wajen hakane yasa ya Kira Aunty nurse duk da bashida tabbacin zata dauki wayar ga mamakinsa a kira na biyu ta dauki wayar bayan ya gaisheta ya fada mata kulleshi da lubna tayi a waje a san ya kara Kare kansa yace Mata abinci ya tafi nema kafin ya dawo ta kulle tunda lubna ta dawo take masa rashin mutunci jiya ma koroso tayi daga d'akin,daga yanda take sallati yasan ta fusata hakuri ta bashi akan bari ta Kira lubna Yana zaune ba dadewa yaji an bud'e k'ofar. Ransa a b'ace ya shiga gidan so yayi ya zubawa lubna rashin mutunci Yana parking ya doshi wajen da take tsaya ga mamakinsa kafin ya Isa wajenta ta iso wajensa tare da cakumar rigarsa tana ya bata takardar sakinta haka kawai yaji gabansa ya Fadi har ga Allah inta furta sakin nan sai yaji hankalinsa ya tashi Dakewa yayi ya mata martanin ita ta Masa laifi amma itace zata ce ya saketa Kamshin turaren Hadeeza data ce yanayi da Jan bakin da tace Yana kwalar rigarsa yasa gabansa faduwa ya Kai hancinsa jikinsa ya kuwa shako kamshin turaren Hadeeza ya kuma ga jan bakin da bai san garin yaya ta shafa Masa ba duk wani kwarin gwiwar daya shigo dashi ya sace wani irin kunya ya lullube shi bazai yi saurin shiru ba ko yayane gwara ya Kare kansa Hakane yasa ya yanko mata karya Amma baiga alamar karyarsa ta Shiga ba hakane yasa ya yanke bata hakuri duk hakurin da ya ringa bata haka ta ringa botsarewa akan dole ya fito daga d'akin ya shige nashi d'akin duk hankalinsa a tashe, idan har baiyi dagaske ba zai iya rasa lubna bai Kuma shirya rabuwa da ita ba lubna ta riga da ta Zama Rabin jikinsa baisan Mai yasa baya iya danne kansa akan Hadeeza ba,Sam baiyi niyyar komawa Hadeeza ba tunda bashida niyyar aurenta zafin da lubna ta hada masa yasa ya kirata a waya gashi turaren da ta fesa ya tona Masa asiri ya zama dole ya Kira mahaifiyar lubna ya fada mata abinda ke faruwa ya Kare kansa Haka yayi ta sake sake sallah asuba akan idonsa,sai a lokacin ya Shiga bandaki yayi wanka ya daura alwala ya fito a hankali wai Kar ma Lubna taji motsinsa. Ana iddar da Sallah ya fito daga massallaci ya samu waje ya zauna ya Kira Aunty nurse a waya Yana Kira ta d'auka bayan ya gaisheta cikin marairaicewa ya hau bata labarin abinda ke faruwa a tsakaninsa da lubna ya hada rantswar shi bai hadu da Hadeeza ba tazo ta taimaka Masa ta bawa lubna Baki ya rantse ya rabu da Hadeeza. Aunty nurse kuwa ranta ya balain b'aci da abinda lubna tayi inda ta bawa mahfuz hakuri akan tana nan zuwa" Sai a lokacin mahfuz ya samu kwanciyar hankali ya koma gida karfe bakwai daidai sai ga sallamar Aunty nurse. Mahfuz har kasa ya duka ya gaisheta yayi kasa da murya yana "Dan Allah mama banaso ki mata fada sosai so nake ki kwantar mata da hankali ta daina furta kalmar saki mutuwa nakeso ta rabamu mama,wlh Ina kaunarta bansan Mai takeso nayi ba na riga da nayi kuskure na Bata hakuri amma ta dage sai na saketa wlh na rabu da yarinya nan mama bansan Mai lubna take so na mata ba "Jeka kiramin ita" "Wlh tsoron zuwa d'akin nake mama" A fusace Aunty nurse ta mike tana a wane daki take Mahfuz yayi sauri ya nuna Mata ta nufi d'akin lubnar da k'arfi ta tura k'ofar tayi Ido biyu da lubna dake zaune akan sallaya idonta ya kumbura gefenta ga akwatin kayanta Lubna Nayi matukar ganin mummy da sassafe yanda ta had'e rai nasan Mahfuz ne ya kirata,banason yanda Mahfuz ke neman hadani da mahaifiyata A hankali na Mik'e nayi waje Dan muna hada Ido ta juya ko gaisuwar da na mata bata amsa ba ta rufeni da fada har tana k'ok'arin kawomin duka,da wane zanji kuka kawai nake idan Ina k'ok'arin Magana sai ta tareni,a karshe sai ta saka kuka akan batasan Mai yasa nakeson dora Mata hawan jini ba idan na Kara yiwa mahfuz ba daidai ba bata yafe min ba idan na kashe Aurena Kar nazo Mata gida. Bata tsaya taji ta bakina ba ta mike da sauri tayi waje mahfuz ya mike ya bita a baya........ *Page 21* A ganina mummy kawai ce zata iya gane halin da nake ciki mummy ta d'auka kishi ne yasa na kasa kwantar da hankalina,bana jin ko aure mahfuz zai Kara ko yayi zai jefani a cikin tsananin bakin ciki haka, tsanar mahfuz nake ji a kowane sassa na jikina yanzu mummy ce kawai nake ganin idan nayiwa bayanin halin da nake ciki zata karfafa min gwiwa tace na hakura da aurensa tunda har ya kasa rabuwa da budurwarsa bazai daina fasikanci ba mummy da ta barni nayi mata bayani abinda ya faru amma Sam taki saurarana,Allah ne yasan kalar karyar da mahfuz ya mata,da har zata min Allah ya isa idan ban kyautata masa ba har yaushe iyaye zasu gane gaskiya su daina danne yayansu akan su zauna a gidajen mazajen su Idan basajin dadin auren,akwai cutuwa a zamana da mahfuz,dan nasan bazan iya Kara Masa biyayya ba,zan tayin abun da zan jawowa kaina zunubi ne. Ina nan a zaune hawaye na zubo min har Mahfuz ya dawo palon Yana satar kallona,Allah yasan ko ganinsa bansan yi balle har mu zauna waje daya. Mik'ewa nayi na nufi dakina Ina shiga ciki naji motsin sa a bayana gefen gadona na zauna na sunkuyar da kaina kasa har lokacin hawaye nake,da zalincin mahfuz zanji ko da hadani fadan da yayi da mahaifiyata. "Lubna dan Allah kiyi hakuri wlh nasan na miki ba daidai ba,dan Allah ki tsaya mu fahimci juna ki cire komai a ranki insha Allahu bazaki Kara kamani da laifi irin haka ba,bana Jin dadin irin zaman da kikeso muyi wlh gwara ki hukuntani kowane irin hukuncine indai zamu koma yanda muke ada" Mai zancewa mahfuz babu dan ba sabon kalma a maganarsa maimaici ne,kafin na dawo yamin kalamai da suka fi haka amma duk da haka bai fasa koma Mata ba ko dan daga kafa baiyi ba. Mike'wa nayi na shige bandaki banasan ma jin muryarsa. Har a yanzu kirjina zafi da ciwo yake min, wanka nayi dan naji sanyi a jikina bansani ba Yana bandakin ko baya nan, towel din dake rataye a bandakin na daura na fito ko ban kalli mudubi ba nasan fuskata a kumbure yake,Yana nan a zaune a gefen gadon ya dora mimi a cinyarsa ban nuna nasan Yana d'akin ba a nutse na shafa mai na zura doguwar riga na bar masa d'akin idan ya ajiye mimi sai na dauketa na mata wanka. Tunda har ya dage bazai rabu dani ba bazai ji dadin Zama dani ba,kwanciya nayi a 3 seater dan karfe tara nake san Shiga kitchen,na samawa kaina abinda zanci tunda jiya yaki cin abincina na Sha alwashin bazan sake girki dashi ba. Fitowarsa daga d'akin yasa na lumshe idona sai nake hango shi a kirjin Hadeeza,a jiya Abubuwan da yake min yake mata rudewar da yakeyi idan muna tarayya haka yakewa Hadeeza ba aurenta yayi ba jiya ma Allah ne yasan iya abinda sukayi ahaka mahfuz yakeso na share komai mu cigaba da Zama Kamar ba abinda ya faru. Nayi saurin goge hawayen daya zubomin ta gefen idona bansani ba Yana palon ko baya palon dan idona a rufe yake, Saukar numfashinsa naji a fuskata kafin na bud'e idona ya kamo bakina da nasa ya tsotse lebbena kafin na Mik'e ya hau ruwan cikina Yana "Dan Allah Lubnata ki taimaka min komai ya wuce wlh banasan ganinki cikin damuwa wlh tallahi zan rabu da Hadeeza ga wayata nan ki kirata duk abinda kika ga dama ki fada mata na miki alkawari bazan sake kulata ba" So nake na saka ihu na tureshi huccin numfashinsa a jikina kamar garwashin wuta haka nake ji amma kalmar mummy ke dawo min na bata yafe min ba idan na kara Masa ba daidai ba hakane yasa na Kara runtse idona,shi kuwa hakan da yagani yasa ya cigaba da min magana Yana bin fuskata da sumba, na d'auka zan iya daurewa ya kashe kishinsa a kaina na riga da nasan jikina yake yiwa nasan abinda yake so ya samu kenan,bama zai iya hakurin a kwana biyu ba,ko zuwa lokacin zan daina Jin zafin da nakeji a kirjina,kansa kawai yasani bai damu da halin da nake ciki ba,bansan mai yasa idan har zai tabani sai na Tuno yanda na gansa da Hadeeza da Kuma yanda ya shigo jiya Yana kamshin turaren ta idan har yasan Ina da matsayi a wajensa ai ba yanda zaayi yaje wajenta jiya. Wani iirn hankada na amsa adaidai lokacin da yake kokawa da wandona A gigice ya taso yana "lubna karki min haka wlh idan na sama miki nutsuwa Zaki yafemin komai zai wuce a wajenki dan Allah kibari mu farantawa juna,ki barni na gwada miki kaunar da nake Miki wlh Zaki yafemin lubna" Ya Kara yowa kaina gadan gadan Sai a lokacin na dago idona na kalleshi "Mahfuz ka rabu dani idan kana so na sauko mu daidata dan Allah ka nisanceni har zuwa na samu nutsuwa ka riga da ka dage sai ka zauna dani bazaka bani takarda ta ba,kaje ka hadani da mummy Mahfuz har tana ikrarin bazata yafemin ba idan na maka ba daidai ba mahfuz kamin adalci kenan?mahfuz aure anayi ne dan Jin dadin,a yanzu bata ni kake ba ka samu wacce ta fini ka sakeni Mana ka koma gareta ka samu nutsuwa nima na samu sabida me kakeso kaga kayi ajalina ta hanyar doramin hawan jini,jiya da kamshin turaren ta.ka shigo gidanan" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun lunbna dan Allah kicire komai a ranki idan kina tuna baya wlh bazaki iya yafemin ba karki manta Allah ma muna masa laifi mu nemi yafiyarsa ya yafe Mana haba lubna mai yasa kike da ruko haka dan Allah ki manta da duk abinda ya faru wlh na Miki alkawari na rabu da ita har abada" Haka kacemin a gida jiya Kuma ka koma wajenta mahfuz da aurenka kake aikata zina,ban rage ka da komai ba sabida rashin godiyar Allah, ka bar matarka ta suna ka tafi wajen da zaka kwasowa kanka zunubi inaso na yarda shaidan ne ya rinjayeka daka kawota har gida jiya Kuma fa"? "Wlh ban yi komai ba jiya lubna wlh bacin rai ma yasa na kirata muka hadu turarenta nada k'arfi shiyasa kikaji kamshinsa a jikina" Mik'ewa nayi fadar ma ya hadu da ita bai san.mai hakan ke haddasa min bane. Na shige kitchen sai gashi shima ya shigo kitchen din,bai bar kitchen din ba har na dafa farar taliya na yanka cabbage dan mai da yaji nakeso naci. Koda na zubo haka ya saka hannu ya fara ci,so yake ya ringa abinda Zan tanka shi hakane yasa ko kulashin banyi ba Ina gama cin abincin na dauki Mimi nayi daki da ita na mata wanka. Zamansa a palon yasa nayi kwanciyata a d'aki. Ban Kara Jin motsinsa ba har bacci ya saceni bansan tsawon lokacin da na dauka Ina bacci ba sai ji nayi ana hura min iska a kunne na bud'e idona a hankali sai da na wartsake na kalli gefena da alama wanka yayi sai kamshin turare yake D'auke kaina nayi daga kallonsa na matsa sabida Rabin jikinsa ya kwantar a jikina. "Lokacin sallah yayi ki tashi kiyi sallah ga abinci nan na siyo mana yau ba sai kin wahalar da kanki wajen girki ba daddare sai mu fita" Da a baya yace zamu fita inaga sabida doki bazan ma iya cin abincin ba dan a rayuwata Ina balain san naga mun fita,irin rayuwar nan na matukar burgeni,ban ce masa komai ba na sauka daga kan gadon na shige bandaki na dauro alwala na fito. Kafin na iddar da Sallah ya fita daga d'akin ya dauko plate da cokali Ina sane nayi zamana akan sallaya bazan cutar da kaina ba zanci dashi nake fushi bada cikina ba. Ina satar kallonsa har ya zuba Miya akan sakwaran dake a mulmule yasan Ina balain San sakwara inaga hakane yasa ya siyo,duk abinan fa da yake yi da wata a zuciyarsa na girgiza Kaina Ina danne zuciyata dake san bijiromin da tunanin Hadeeza. Yana gama zuba miyan ya kawo sakwaran ya ajiye a gabana ya dauko ruwan wanke hannu da ruwan roba ya zauna tare da tankwashe kafarsa Yana "Bismillah" "Na koshi" "Lubna dan Allah ki bari, fushi da zuciya bazai canza abinda ya riga da ya faru ba dan Allah ki sauke fushin nan haka haba lubna" Ya yanko sakwaran ya kawo bakina na kau da kai K'arfi da yaji ya dage sai ya bani a baki hakane yasa na wanke hannuna na fara cin sakwarar Kamar ana min dole,har ga Allah Kuma yamin dadi,fuskata a hade har na gama cin Wanda Zan iya ci Yana Jana da hira nidai ban tanka masa ba har na wanke hannuna na Mik'e na dauki mimi nayi Palo na zauna. Shi ya kwaso kwanukan ba jimawa yazo palon shima ya zauna shi kadai ya ringa hirarsa da eee Aa kawai na ringa binsa bana san fushin mummy ya tabbata a kaina. A haka har aka Kira sallah la'asar yayi alwala ya fita massallaci nima nayi sallah na sake wanka tare da canja kayan jikina nayi zamana daki na dauko wayata na kunna data na hau WhatsApp. Grps na Shiga nake dan bin hirar mutane har ya Kuma shigowa d'akin ya zauna Yana yiwa Mimi Wasa Ina latsa wayata Ina satar kallonsa idonsa na kaina sai sauke numfashi yake, na riga da nasan duk abinda yake yiwa bana san na cigaba da dorawa.kaina zunubi Addu'a nake Allah ya bani ikon daurewa idan ya sake nemana. Bai bar dakin ba sai da aka fara kiraye kirayen sallah magriba da ya fita bai sake dawowa ba sai da aka yi sallah Isha. A Palo ya tarar dani a zaune idan ta nice a koshe nake,sai dai ya nemowa kansa abinda zaici. Yana shigowa yace na tashi mu dan fita baa machine zamu fita ba a machine Mai kafa uku zamu fita ya hada da na tayashi da Addu'a akwai kudin da yake sa rai idan ya shigo zai siyi mota. "Idan ma aure zakayi wanan damuwarka ce ba inda zani sai ka dawo" Ya dawo gefena da sauri ya zauna Yana "Lubna ba dan halina ba dan Allah ki tashi mu tafi" Banza na bawa ajiyarsa ya cigaba da magiya yanda ya dagemin yasa na shige daki na canza kayan jikina zuwa doguwar Riga na yane mayafin akaina. Shi ya goya mimi da jakar goyo ta gaba sai kallona yake ni kuwa na hade rai nasan so yake yace mayafin dana yafa yayi kadan ban saurare shi ba nayi gaba har muka fita titi ya tsayar Mana da abin hawa ya fada mishi inda zai kaimu. Wayata nake latsawa har muka iso wajen da ake Shan ice cream yasan ni mayyar ice cream ce rabon ma daya siyomin tun Ina amarya. Nidai binsa nake kawai a baya har muka iso wajen zama na zauna, ya miko min Mimi yaje ya fada musu kalar ice cream din daya keso a kawo daga Inda nake zaunen na ringa Kare Masa kallo. Shigar kananan Kaya na balain yi Masa kyau so nake naga muninsa,amma na shagala da kallonsa Yana k'ok'arin jiyowa na d'auke kaina da sauri ya dawo ya zauna. Muka hada ido ya sakar min murmushi na d'auke kaina aka kawo Mana ice cream din. Ya mik'o hannu Yana na bashi Mimi naji dadin Shan ice cream din Ban musa masa ba na mika masa Mimi na fara Shan ice cream din a hankali,har ga Allah naji dadi a raina, amma ban nuna hakan a fuskata ba sai ma Sha da nake a hankali kamar yamin dole,da alama masoya Nan suke zuwa har nawa namiji zai kashe ya kawo matarsa nan ya faranta Mata,mazan mu basa Mana adalci haka suke ajiyemu a gida su fito nan da Yan matan su waya sani ma ko ya kakawo Hadeeza nan take na hade rai naji ice cream din na neman fita a raina. A hankali na saci kallonsa naga yana kallon wani waje hakane yasa na juya dan naga mai yake kallo,mace da namiji ne zaune macen ta bani baya yanayin jikinta Kamar na Hadeeza take naji gabana ya Fadi,na maido da kallona Kan Mahfuz da har lokacin yake kallonsu na Kara juyawa na kallesu,a daidai lokacin da namijin yake bawa yarinya ice cream a baki hannu daya mika yasa nagane a baki yake Bata amma banga fuskar macen ba,na Kara dawo da kallona Kan Mahfuz daa yanzu yake juya cokalin ice cream din ba Kuma Sha yake ba ni kuwa na zuba masa Ido Ina karantarsa hada Ido da mukayi yasa ya sakar min murmushi da a idona na yak'e ne yace "Kiyi ki gama mu tafi dare yanayi ko Kar Mimi ta kamu da mura" Juyawa nayi na kara kallon wajen da dazu yake kallo sai dai har lokacin namijin kawai nake gani,macen bata jiyo ba,bansani ba ko hancina ne sai naji kamar kamshin turaren Hadeeza. Kishi wata mahfuz keyi a gabana kenan take naji raina ya b'aci Yana k'ok'arin Magana nace "Sabida kaga Hadeeza da wani shine ka hade rai Mahfuz" Ya gwallo Ido waje Yana "Kamarya lubna akwai wacce zanyi kishinta bayan ke ne ai babu dan Allah ki daina kiramin sunan ta ki gama Sha mu tafi" "Na Gama" Na juya na Kara kallon bayan yarinyar da Zan so ta juyo ba ma ja Hadeeza ce kamar na kwalla Mata Kira ta juyo Wanda kake kauna kake kishi,mahfuz ganin ta da wani ne yasa ya kasa Shan ice cream din,take naji zuciyata na min zafi daya barin Kuma sai naji dadin ganin daya Mata da wani duk abinan dai ban tabbatar da itace ko ba ita bace. "Kaje wajenta Mana mahfuz Zan jiraka a waje" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun haba lubna" Ya dan fada da karfi idona na Kan yarinya dan burina ta juyo na ganta aikuwa muryar mahfuz da taji yasaka ta juyo, gabana yayi wani irin faduwa. Bana Jin tagani ganin mahfuz yasaka ta mik'ewa tare da gwallo ido tana mahfuz gadan gadan tayo wajen mu har lokacin bata gani ba, Kafin ta karaso mahfuz ya daka mata wani uban tsawan daya saka ta tsayawa cak "Karki sake ki matso kusa dani,ki fita daga rayuwata Hadeeza daga yau bani bake, matata ta isheni rayuwa ki rabu dani Hadeeza idan Kuma kika k'i duk abinda na miki ke kika jawowa kanki" Bansan Mai yasa naji sanyi da Dadi na ratsani ba,Koda baa har zuciya MahfuZ ya fadi haka ba ya faranta min dan ya disgata a gaban katon Alhajin da tazo dashi haka ma a gaban mutane. Ido muka hada da ita idonta ya ciciko da hawaye na sakar mata murmushi na tsinci kaina da karasawa wajen da take tsaye Ina "Idan ke din ba jaka bace Kuma karuwa mai bin mazajen mutane sai ki hakura ki daina bibiyar mijina haka banza balagaza karuwa" So nake tayi magana na d'auke ta da mari batayi magana ba har Mahfuz yazo ya janyeni Muka bar wajen muna fita na fusge hannuna Ina "Wlh duk kishi yasaka kayi maganar da kayi,mahfuz ni ba yarinya bace wlh kana san yarinya nan ka sakeni kawai ka aurota" "Lubna bansan Kuma Mai kikeso na miki bayan wanan ba agaban idonki dai kina ganin kashedin dana mata duk sabida na faranta miki rai haba lubna" Ya kuwa faranta min din banaso na nuna masa ne ban Kara ce masa komai ba har muka Isa gida. Da isarmu gida ya ajiye ledojin da ya dan yi siyayyarsa a ciki har dasu balangu a palo ni kuwa daki na shige na canjawa Mimi Pampers na bata abincinta ta Sha ta koshi Kafin na Shiga bandaki nayi wanka na saka kayan bacci na haye gado raina fes dan na fara yarda mahfuz dagaske yake zai rabu da Hadeeza. Shigowarsa yasa nayi saurin lumshe idona yace "bazaki ci balangun ba"? " A koshe.nake" Bai Kara cemin komai ba ya fice daga d'akin ba dadewa ya dawo d'akin Ina jinsa ya rufe kofa yazo ya kwanta a gefena a hankali ya matso kusa dani yamin rada a kunne "Ina bukatar ki pls kimin wanan taimakon dan Allah" Ban motsa ba ya juyo dani,jiki da jini Ina karbar sakonsa amma haka na kwanta kamar ruwa na d'auka yi zaiyi sai ji nayi ya dagoni idona a rufe yake Ina k'ok'arin bude Idona naji jikinsa a bakina Yana shafa kaina. Har ga Allah abinan amai yake Sakani nayita tofe tofen yawu har garin Allah ya waye janye kaina nayi na koma na kwanta,hakane yasa ya hakura jikinsa sai rawa yake kamar Wanda tab'a sanin mace ba har ya samu nutsuwarsa naji bacci ya d'auke shi nima Ina rufe Ido bacci yayi awon gaba dani... MG'S SKINCARE In akaji gangami labarin kidane,sun shahara sun tumbatsa sunkai sunwuce tunanin duk wani meson Adama dashi aharkar gyaranfata d walwalinta, Yar uwa haske ko qyalqyale kikeso kiyi Abu yaci tura? Kyan fuskarda ko yar uwarki mace kance dama dama kikeso? Kokuma ke kuraje d tabbuna suka lahanta mki fuska har ake ganinki d wani idon n daban, Nankarwace tayimiki zanen kura a kyakyawar fatarki? Kokumade Mai kikashafa be amshekiba yasa duk kika koma ruwa biyu Nan fari Nan baqi? To duk kuzo insha Allah kudai naku y qare gdan kukazo, Munkawo shahararrun kayangyaran jiki Sabulu, Man shafawa, Man fuska, Scrub, Cleanser, Glow oil, Dukdan qawarmaku d matsaltsalunku, Da 11k kachal zatasa kihaske kizama kalar madara qirar models, Set 11k Sabulu 3k Student package:7k Munakuma bayarwa in pieces duk afarashin mesauki.kayanmu bbu fariya ko tutiya angwada andawo,ankumayi farinciki d hkan,Kuna iya samummu d wadannan numbobin, WhatsApp, 08062991549 or 07046881166 or 07067210195 Call only 08064532391 Instagram: glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Idanba wadannan numbobinba to gaskiya b mg's bane, available in Kaduna and Kano only, thanks for always trusting us,our returning customers we really do appreciate wadanda sukeda burin Siya munamaku fatan alkhairi ubangiji ybaku yenda zakuyi,Allah Kuma yqaro mna dukiya me amfani ta hanyar halalinmu *WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min SHARING bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi* *Page 22* Dagani har shi makara mukayi sallah asuba sai a gida yayi sallah asuba. Sanin zaije aiki tunda ranar Monday ne yasa ban koma bacci ba na fara k'ok'arin zuwa kitchen na sama Masa abinda zaici. Sai dai Ina zuwa na gansa a kitchen Yana soya kwai Ido da muka hada dashi yasa ya kanne min Ido Yana "Na hutasheki farin cikina jekiyi kwanciyarki kiyi baccinki" Ina karya Zan wuce na Kulle Miki gidan idan bazaki iya girkin rana ba Zan siya na Aiko miki dashi" Hmm kawai nace tare da barin Kitchen din nasan duk Yana hakane dan na manta abinda yamin,nima zanso na manta din amma bansan Mai yasa nakeji kamar bazan iya sakin jikina dashi kamar a baya ba,ban koma d'aki ba na zauna a palo,ya fito daga kitchen din da plate din kwai da kofin shayi. Ya zauna a gefena yana ci Yana min hira nidai biyesa kawai nake har ya gama ya jawoni ya Kara jagwalgwalani san ransa banda ma naki nasan karawa zaiyi ya shige daki ba dadewa ya fito a shirye Yana kamshin turare ya ajiyemin Dubu biyu a gefena Yana "bari naje kar na makara" "A dawo lafiya" Ya sunkuyo yamin kiss zai juya nace "Idan har ka sake cin amanata Allah ya isa ban yafe maka ba idan bana kallonka Allah na kallonka" Murmushi yayi Yana "Mahfuz bazai ci amanarki ba mahfuz nakine ke kadai ki kwantar da hankalinki a gabanki dai jiya kina kallon irin gargadin da nayi mata" Yarda daya ce amma ba abinda mahfuz zai cemin yanzu na yarda da Ido na bishi har ya fice daga gidan. Na Mik'e na koma daki na kwanta bacci ya Kara awon gaba dani. Mahfuz Sosai yaji shi cikin farinciki dan a yanzu yasan ya samu ya shawo Kan lubna zaiyi iya kokarinsa wajen gujewa duk wani abu da zai saka su samu sabani. Take yaji shi cikin b'acin rai daya tuno ganin da yayiwa Hadeeza da wani jiya,tunda yake da ita bai tab'a ganinta da wani ba baisani ba ko hakane yasa jiya yaji ransa ya b'acin da ganinta da wani,Ashe karya take da tace masa bata kula kowa Ashe karya take da tace shi kadai ne saurayinta,a yanzu ya Kara tabbatar da zarginsa akan fuska biyu gareta,dama hanya yake nema da zai yakiceta,dama hanya yake nema da zai ce Mata bazai iya aurenta ba, a yanzu Kuma ya samu hanyar tunda ya ganta da wani jiya. Sai da ya isa office ya dan kammalla wasu ayyukan kafin ya Nemo lambar Ammi ya kirata dan su gaisa,dan ba mai wanan sabon layin nasa. Sai dai Ammi na Jin muryarsa ta rufeshi da fada tana "Wulakanci ne yasa ka kashe wayarka tun jiya nake neman layinka a kashe" 'canja layi nayi Ammi shiyasa na kiraki da sabuwar Dan na daina amfani da wancan" "Sabida me ka canja layin da tun kana Saurayi kake amfani dashi"? "Haka kawai na canja layin Ammi" "Karya kake yi kace min matarka ce ta saka ka canja layi sabida Kar mu ringa samun ka a waya mahfuz kasan dai ba ita ta haifamin Kai ba ko"Anya yarinya nan ba asirice ka tayi ba naga alama so take ta rabaka da kowa ta hanaka muamalla da kowa to wlh wanan ne bata Isa ba dan ko dawo da ita da kayi bada yawuna ba,amma tunda ka dage wlh sai ka Kara aure Ina nan akan bakana Kuma kafin na Saba maka ka mayar da layin nan da kowa yasanka dashi,ba ruwana da wanan sabon layin jibi kazo Ina san ganinka" Kit ta kashe wayar yabi wayar da kallo,ya riga da yasan halin Ammi idan baiyi abinda tace ba kadan da aikinta tace zata maka baki, mayar da layin nan da tace yayi zai iya haddasa Masa matsala da Lubna yasan halin Hadeeza da azababben naci ko yayi blocking dinta sai ta kirashi da wani layin ba Kuma lalai duk bayanin da zai yiwa Lubna akan ita take nace Masa ba ta yarda,zancen Karin Aure Kuma da ta dage sai yayi sam bai shiryawa wani aure ba,Koda zaiyi ba yanzu ba Hadeeza ce dama ta matsa Masa yaji Yana San ya Kara auren,a yanzu Kuma bazai tab'a iya aurenta ba. Layin ya mayar a karamar wayarsa dan yasa a babbar wayarsa sai Hadeeza ta kusa cika mishi waya da magana ta watsapp. Yana sakawa ko minti goma baayi ba sai ga Kiran Hadeeza a wayarsa ya riga da ya haddace lambarta a kansa baiyi wata wata ba ya danna Mata blocking sai yake hango ta a idonsa yanda ta dame ko'ina a jikinta wani katon da a haife ya haifeta ya ringa bata ice cream a baki. Texes ne sukayi ta shigowa da wani lambar zain ko bai bud'e ba yasan itace tayi amfani da wani layin Duk message din na ban hakuri ne da bayanin ba saurayinta bane wani dan uwansu ne ya bata dama su had'u bata ji dadin wulakanci daya mata ba jiya ko bacci batayi ba,Kar ya manta irin san da take masa,Kar ya manta irin dukan da ta Sha a hannun matarsa bai dace ya Mata haka ba. Tsaki yayi ya goge duk messages din ya Nemo lambar lubna a waya dan so yake ya goge komai a zuciyarta sai da Kiran ya kusa katsewa kafin yaji ta d'auka hira ya hau janta dashi amma daga yanda take amsa wayar yasan ba so take ba,dariya ma yanzu take bashi ita a lailai fushi take dashi,bayan yasan balain San shi take dannewa kawai take katse wayar yayi ya tutura Mata text ya ajiye wayar. Kiransa da Hadeeza ke tayi da layin zain din da ta ke ta Masa texes ya danna a block Yana Jan dogon tsaki,har yanzu hangota yake da wanan katon yana bata ice cream ya rasa ma mai yasa yake Jin haushi idan ya tuna. Wajen karfe daya ya mik'e dan so yake daga massallaci ya biya ta restaurant yayi take away guda biyu ya aikawa lubna daya shima yaci daya. A bakin k'ofa ya ci Karo da Hadeeza da ta sha bak'ar doguwar Riga har kasa kamshin turare kawai take. Da sauri yaja da baya cikin mugun hade rai,Yana "Mai ya kawoki office dina ban hanaki zuwa wajen aikina ba Wai Mai yasa bakida hankaline wane kallo kikeso a ringa min ne bana ce miki ki rabu dani ba" Ba ko alamar fushi a fuskarta ta rufe k'ofar tana "Mahfuz taya zan rabu dakai bayan Ina sanka nasan kaima kana Sona, Mahfuz Ina duk alkawarikan da kayi min,na zaka aureni,duk wahala da na sha da dukan da naci a hannun matarka ya tashi a banza kenan a yanzu zaka ce na rabu da kai,bayan kasan banida kowa Wanda ka gani dashi a jiyan cousin dina ne ba saurayina bane" "Hadeeza ada ni nace zan aureki a yanzu Kuma na fasa ba Kuma ki isa kimin dole ba,har ni zaki rainawa hankali kicemin wanan katon da na ganki dashi jiya cousin dinki ne?cousin dinki ne yake baki ice cream a baki?wane irin rantsuwa ne bakimin akan bakida saurayi ba ni kadai gareki,nasan irin wayanda kike hulda dasu taya zan aureki kina biye biye wlh Hadeeza Sam ban yarda dake ba na dade Ina zargin badani kawai kike muamalla ba jiya kuwa idona ya gane min dan haka a yanzu ban yarda da ke ba bazan iya aurenki ba ki daina kirana a waya Hadeeza karki hadani fada da lubna inasan matata" Akan gwiwarta ta zube hawaye na zubo Mata Tana "Wlh mahfuz dakai kawai nake hulda ka yarda dani ba komai tsakanina da wanan da kagani dashi jiya,san da nake ma yasa nake ma duk abinda nakeyi bawai dan halina bane ba Zan iya maka komai dan na faranta maka rai" Kamar an fusgo maganar daga bakinsa dan ya dade Yana san ya mata tambayar "Hadeeza bani na fara saninki ba wa Kika fara bawa kanki"? "Fyade aka min a lokacin Ina secondary mahfuz shiyasa kaji haka amma wlh ba na muammalla da kowa" Tasan ta hanyar da take Kama mahfuz hakan kuwa yasa ta cigaba da kuka cikin kirsa tunda taga yayi shiru ta cigaba da kuka cikin shagwaba taja gwiwar ta zuwa wajen da yake tsaye ta mike tsaye tare da rungumeshi. Har zai janyeta ta Kara kankame shi. So take ko Yaya ne ta rinjayeshi tunda ya fara botsare mata hankalinta ya tashi bata da wata hanya da zata samu ya fito ya aureta sai ta wanan hanyar da idan ta samu cikar burinta ya gama zuwa hannunta,so take ta nunawa lubna tayi kad'an bata Isa ta hana aurenta da mahfuz ba,so take ta nunawa lubna iyakarta a jiya ko runtsawa batayi ba burinta kawai mahfuz ya aureta. Yanda ta fara kunna shi yasa mahfuz janye jikinsa da sauri Yana "Dan Allah ki tafi gida Hadeeza nan karki Manta wajen aikina ne" "Bazan tafi ba sai ka tabbatar min da zaka zo gidanmu idan ba haka ba wlh haka zan ta zuwa nan" "Hadeeza Dan Allah ki bari na samu nutsuwa zanzo ki daina kirana a waya bana so ki haddasa min wata fitinar har yanzu ban gama shawo Kan lubna ba Kuma kinsan duk abinda ya faru ke Kika jawo min,kema kinsan bazan samu wani kwanciyar hankali ba har nayi tunanin wani aure idan bana zaman lafiya da lubna" Kamar ruwan zafi yake watsa mata haka ta ringa ji amma haka ta daure tana "toh idan ban kiraka ba kai zaka kirani"? "Eee karki sake ki Kara kirana a waya Hadeeza da kaina Zan kiraki Kuma Dan Allah ki daina fesa wanan turaren yanzu lubna tasan kamshin turaren ki idan har kinaso mu cigaba da muamalla ya zama dole ki kiyaye Abubuwan da na fada miki na Kuma gaya Miki gaskiya a yanzu banida halin aure idan har matsuwa kikayi da auren sai dai ki nemi wani idan Kuma Zaki iya jirana toh sai ki bini a hankali" Murmushi ta sakar Masa tana "Duk yanda kace ayi haka za'ayi Ina kaunarka Mahfuz" Ta Kara rungumeshi,mahfuz da kyar ya Kai zuciyarsa nesa bai biye mata ba amma har kasan ransa yaji yana san kasancewa da Hadeeza dan wani irin salo take masa dake gigita shi. A haka ya samu ya Koreta yana maida numfashi sai yake ganin kamar Lubna zata gane ya had'u da Hadeeza wayarsa ya d'auko ya Kira lubna Koda ta d'auka hira ya ringa janta dashi da alama ta fara saukowa dan ta dan biye Masa har take tambayarsa mai zata dafa mishi daddare sosai yake jinsa cikin farinciki saukowar da tayi hira Suka dan tab'a kafin ya kashe wayarsa ya sake alwala a bandakin office d'insa yayi sallah Koda ya iddar cire rigarsa yayi ya wanke a bandakin ya rage daga shi sai vest da dogon wando dan gani yake Yana zuwa gida lubna zata ji kamshin turaren Hadeeza a jikinsa a yanzu tsoro yake lubna ta gano Yana tare da Hadeeza bai san Mai yasa zuciyarsa taki bashi hadin Kan ya rabu da ita ba tana da tsara shi shikenan. LUBNA Tunda mahfuz ya kirani a waya ban Kara komawa bacci ba na tashi na nemawa kaina abinci naci na gyara ko'ina nayi wa mimi wanka na dawo Palo na zauna haka kawai nake Jin wani irin kadaici da ace a wancan unguwar muke da yanzu na Shiga gidan mmn Iman mun Sha hira. Wayata na dauka dan na kirata Ina kuwa kiranta tace min yanzu takeso ta kirani akan ta shigo layin gidana. Kasa hakura nayi ta shigo na fita waje na tsaya har ta karaso cikin farinciki na rungume ta mmn Iman nada wani irin matsayi a zuciyata Ina kaunarta sabida tana kaunata duk wani abu da ya shafeni tana daukarsa da mahimmanci damuwata damuwarta ce, duk da ta girmeni ko jinina ce ita sai haka. Hira muka barke dashi ta hau tsokana ta akan nayi fresh anya daga dawowata mahfuz bai yiwa Mimi kanwa ba,nariga da nasan halinta ban biye mata ba Na Shiga kitchen na dora Mana abincin muna hira Ina girkin har na sauke na zubo Mana muna cikin ci nake bata labarin duk abinda ya faru daga dawowata gidan har ganin da mukayi wa Hadeeza jiya da wani ban b'oye mata komai ba Cokalin hannunta ta ajiye tana "Lubna ki ajiye duk wani fushi ki cire komai a ranki a yanzu ya Kamata ki zage wajen kyautatawa mahfuz wlh yarinya nan shaidaniya ce,duk da kince ya mata kashedi a gabanki zata yi duk abinda zatayi dan ta dawo rayuwarsa ke Kuma kisan yanda zakiyi ki hana hakan faruwa,yanzu balain da ake ta fama dashi kenan wlh shekaranjiya Abban Iman ya bani lambar wata da ta sako shi a gaba yace na kirata na nace mata ta daina kiransa a waya bakiga zagin da nayiwa yar iska ba,yau ma Yana Kira a wayarsa ya mikomin yace min itace tanajin muryata ta kashe" "Toh mmn Iman ke mijinki Yana Sanki baya iya Miki boye boye,mahfuz bazai tab'a bani wayarsa na zagi Hadeeza ba wlh nasani,wane irin kyautata wa ne banyiwa mahfuz ba mmn Iman a karshe dai sai da yaci amanata har gida ya kawomin budurwarsa wlh ko yanzu na tuna sai naji zuciyata namin zafi, fushin mummy ne banaso shiyasa na bar shi ya samu nutsuwa dani,amma wlh na kasa manta abinda yamin" "Idan har kina tunawa dole kiyita Jin zafi amma Ina shawartarki da ki manta da komai wlh mijinki na kaunarki shuumar yarinya ya hadu da ita" Shawarari mmn Iman tayi ta bani ta bud'e Jakarta ta fito da lodin magunguna mata akan na ringa amfani dasu,na jawo mijina jikina na yafe Masa abinda yamin tariga da tasan bazan iya mantawa ba amma na daure. Muna taren mahfuz ya kirani, ita ta ringa min rada har na biyewa mahfuz muka tab'a hira har na tambayeshi abinda zan dafa yace na dafa koma mene zaici. Ina jin farinciki a muryarsa har ya kashe wayar sai ga text dinsa nan a wayata Zuwan mmn Iman da shawawarinta ya faranta min sosai hakane yasa na cire komai a raina na Kuma dauki shawararta akan na sake karkato da hankalin mahfuz kaina. Magungunan da ta kawomin wayanda zan iya sha na Sha na matsewa na matse nayi abincin da yake so karfe shidda ya dawo da kwalliya ta yazo ya Sameni. Sakin fuskar daya samu da tarbar da na mishi yasa sai da ya samu nutsuwa dani har mamakinsa nake dan kamar karo jarraba yayi. A ranar guduwa ne banyi ba dan sai daya kusa fanshe watani da baiyi ba. A wanan gabar na Kara jawo mijina jikina duk wani abu na kyautatawa Ina masa,lokaci zuwa lokaci shaidan kaso bijiromin da cin amanar da yamin sai nayi saurin yakicewa balle idan naga bai dawo da wuri ba. Wayarsa kuwa Yana ajiyewa zan d'auka na hau Masa bincike duk binciikena dai ba abinda nake gani hakane yasa na saki jikina Ina tunanin dagaske ya rabu da Hadeeza. Mahfuz......