Showing 3001 words to 6000 words out of 39554 words

Chapter 2 - AKWAI LOKACI BOOK 2

11 Jul 2025

1686


amma hankalinsa baya taredashi

Ahmad yace wai meke faruwane Prof
Hakeem yayi murmushi wallahi baby ce take bani ciwonkai

Taki bari na rabeta Sam wallahi
Bana ganinta idan ba a gurin mummy ba

Ahmad yace zanbaka shawara idankabi yau din nan kadaina damuwa

Hakeem yabada hankalinsa sosai

Ahmad yace bakace agurin mummy take wuniba prof yace a

Ahmad yace sallar ishar dazakaje yau kabari kawai kamuku jam'i

Kana shiga kacewa mummya da daddy da ciwon kai kadawo

Idan kaga zata tashi saikace jirani mutafi tare agaban mummy nasan bazatayi musu ba

Hakeem yace kuma wallahi sai dai kuma yau laila ce da kwana

Ahmad yace saikayi hakuri yau da gobe ai duk dayane yayi dariya

Hakeem yace a a baduk dayabane wallahi kai bakasan halin danake cikibane shiyasa


Ahmad yace kai haba mai mata biyu fa amma kana fadin haka ai saika kabani tsoro nakasa
kara tabiyu

Hakeem ya harareshi



Husnah falonta suna waya da ummanta da ya shamsu da anty kubra

Bayan sunagama wayarne ta dauko mayafinta zata koma banngaren mummy

Sai taji Laila tana waya amma bata San dawa take ba

Laila tace dadin abinma fa yarinyar baso shi take kullum a dakinta take kwana
amma wannan aikin bokane yace bazai taba bari harya kusanceta ba

Yanzu fa kusan sati uku kenan amma suna wasan buya bata ma bari yaganta

Shikuma na mamajo kina gani shi kisan yana cikin damuwa

Can ta matse mishi kinga haka malam zaicire mishi sonta aranshi kwatata

Dan nima yace karnabari ya kusanceni har sai yarinyar tabar gidan

Kinga kuwa ai yana cikin matsala dannima bana zuwa bedroom dinsa harsai ranar da wannan
aljanar yarinyar tabar gidan

Nan dai sukayi sallama da kawartata

Ta kalli suby tace insha Allah saura kiris yarinyar nan tabar gidan nan

Daga nan kuma sai mufara shirin yadda zamuyi mukasheshi idanba haka ba wallahi wata
zaisake hangowa


Suby tace wallahi da dai yafikam

Dan wallahi nima inason naga munfara fantamawa fa anty

Laila tace kidai yishirunki kawai saura kiris


Husnah toshe baki tayi sai kuma wani jiri data ji yana dibanta dakyar tasamu takai kanta kan
kujerarta

Tace innalillahi qainnairraihirraju'un nashiga uku meya musu suke son kasheshi


Gaskiya bazantabari kuyi nasara da yardar Allah

Kuma mijina zaisamu abinda yakeso insha Allah

Allah yakaimu gobe nashiga ukuna ni husnah wani irin zunubi na daukarwa kaina

Tabbas yaya Hakeem bai can canci wannan sakaiyar daga garaniba kayafemin Dan Allah duk
da banasonka nayi alkawarin faranta maka kamar yadda kake faranta mana nida iyayena

Duk wannan maganar da husnah take yi tanayinsane itakadai

Hmmmmmmmm


Next page

Your comment is needed fan's. Love u all

Duk wacce bantaba bata page ba

Tayi comments mezafi next page natane 踫踫


踫踫踫踫踫踫
[05/05, 8:59 PM] UMMU AFAN �: 潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤
潤潤潤潤
潤潤潤
潤潤

BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer


UMMU AFAN

踫踫踫踫踫踫踫



�FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION�


�� (F.C.T.W.A)��



�HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION�




潤I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MAMAN ISQAH Allah yabar zumunci gaskiya ina alfahari
dake wajen comments keep it up d潤






潤AKWAI LOKACI 潤





潤PAGE 106 to 110潤

Husnah ce a kitchen din mummy tana ta aikin abinci Dan yau abincin ma special ne

Sakwara takeyi da spinach soup Wanda yasha ganda

Kamshi ya kauraye koina


Sai data gama komai tasaka a flasks dama ta hada
Hadaddan zobonta meshegen dadi da kamshin kayan hadi

Ta jera komai a dining din mummy hafsat yayin da me aikin mummy take gyaran kitchen da
wanke wanke

Husnah ta duba agogo taga karfe biyar dai dai ta haura sama gurin mummy

Direct dakin mummy ta wuce tasameta itama tagama shirin ta tana ma shirin saukowa kasane


Mummy hafsat ta kalleta tace
Sannu da aiki 'yar albarka ina ta sauri nasauko naga me ake girka mana gida duk ya dau
kamshi


Husnah tayi murmushi tace abinda kikace min dadi yafiso shinayi yau mummy


Mummy hafsat tace sakwara kenan fa Husnah tadaga kai

Mummy tayi murmushi tace ai masu son suna dayawa harda son iyayen ci

Yau zakiga santi husnah tayi murmushi

Tace mummy ina son zanje nayi Dan gyare gyare ne

Mummy tace bakomai 'yar albarka ai kina kokari Allah yayi albarka

Husnah tace amin mummy

Husnah harzata Fita mummy hafsat tace kiwuce muku da naku can kawai tunda nasan kinyi aiki
kingaji ba lalle kisamu daman dawowaba

Husnah dama abinda takeson mummy tace kenan

Tayi murmushi tace to mummy sai da safe

Mummy tace Allah yabamu alkairi


Husnah tafito tawuce part dinsu tana shiga falon taga su hajiya rukayya harda hajiya suwaiba
yauma sunzo

Dan kusan kullum suna gidan

Husnah tace ina wuninku hajiya
Kosusan Allah yayi ruwan tsiranta

Ita kuwa husnah ganin ba Wanda ya amsa mata yasa ta tashi tayi ciki abinta

Direct kitchen dinta tashiga tafito da sabbin food flask masu kyau da tsada tayi part din mummy
tazuba musu abinci

Tadauki jug din flask din tazubo musu zobo maisanyi Wanda dama tasaka a fridge

Harda fruit salad din data hada duk ta deba tayi part dinsu

Ganinta da flask duk suka bita da kallo tayi dakinta dasu tajerasu a dining table dinta


Kafin ta fito tasawa kofar ta key nan ma su Laila suka bita da kallo abin mamaki gani sukayi ta
haura saman Abdul Hakeem


aikuwa Laila da suby suka kalli juna sukabita da kallo

Tana shiga tasa hanu ta murda aikuwa tayi sa a ba akulle bane
Tashiga wani makeken falo ta gani har yaso yafi nakasa kyau sai dai duk yayi kura Dan dagani
bayasamun kulawa


Dakuna biyu ta gani cikin tabude nafarko taga nan ma wani hadaddan bedroom ne amma
Daga ba anan yake kwanaba

Tabude dayarma tagashima yahadu iyahaduwa
Kuma dagani nan yake rayuwa

Shiga tayi harta kan bed dinma ba agyare yake ba
Kuma bata ga laifinsaba zaiji da office ne kozaiji da da gyaran gidanshi

Nan dai duk wasu kayanshi datake tsammanin yasaka tahadasu a gefe Dan bazaka gane dattin
ba saima kamshi dasuketashi Daga miki su tana cikin binko kayansa wani Dan akwati ta gani
yamata kyau sosai

Garin ta gyara mashi zama sai yafafo kayan ciki cuka zubo

Ba abinda tafara gani sai fuska(masks)/kuma da ya mu'alim yake kama sak abin har yaso
yabata tsoro zata gudu idonta yakai kan nokia yarsa wacce tasha dauri da roba

Cikin tsananin mamaki husnah tace badai ya Hakeem shine ya mua'allim dina bansaniba

To meye hujarsa na boye kansa
Tasake bincika kayan taga zoben data bashi Wanda sukayi canji yabata tabashi


Nan tasake tabbatarwa kanta ya Hakeem shine ya mu'allim

Taga wani diary kamar yadda taga anrubuta a bayan littafin

Nan ta hau karanta abinda ke rubuce

Nan ta tababbatar Abdul Hakeem shine ya mu'allim dinta

Kukan dadi suka gangaro mata

Sosai tayi kuka ammafa na murna ne
Tace meyasa zaka cutar da kanka har haka meyasa baka fada minba kabari har na dauki
alhakinka ya mua'llim

amma bakomai insha Allahu zakasan kayi auren soyayya
Ya Allah ka karemin mijina Daga sharrin wadan nan mutanen tabas a labarin dake rubuce cikin
diary dinshi mummy hafsat da daddynsa sunbata tausayi

Dole ya mua'llim yayi taka tsan tsan gurin sake Neman matar
Baka da laifi kuma na tabbatar kosu umma da ya shamsu bazasu zargekaba idan sukaji Kaine
ya mua'llim kuma suka ji dalilinka

Wani irin son mijinta yadawo sabo fil azuciyarta tareda tausayinsa Dana iyayensa tashare
hawayenta tashiga yin abinda yakawota cikin farinciki da dokin dawowar mijinta

Acikin mitoci kadan daki yakoma kaman bashiba kafin tashiga bathroom dinsa ta wanke mishi
kayansa tsaf da kananun kayansa na ciki

Taje farandar saman shi ta shanyasu tsaf tasaka abin kamawa ta kamasu karsu fadi kasa

Tagyara bathroom dim ma tasaka kayan kamshi koina ya San anayi

Kafin kuma ta koma falon tagyara tsaf yadawo kaman bashi ba sai sanyayyar kamshin dake
tashi akowani lungu da sako na falon

Sai da ta tabbatar ba inda bata gyara ba kafin tafito key din dake jikin kofar tacire ta cire ta kullo
saman abinta

Ta wuce da keyn har yanzu su Laila suna inda tabarsu

Zata shige dakinta hajiya rukayya tace ke zonan yanzu agidanku haka kikewa manyanki

Husnah tadago ido takallesu

Batayi magana ba tayi shiru Dan taga ba abokan yinta bane

Suby tace ke 'yar marasa kunya ba magana akemikiba

Husnah ta kalle suby sama da kasa tace kekuma fa 'yar masu kunya ya akayi

Laila tace kutuman uba lalle yarinyar nan ma kinsamu guri

Uban me yakaiki saman dakin mijina

Husnah ta tashi tsaye ta kalli Laila sama da kasa tayi dariya
Tace ai gwamma da kika nuna min kece matar gidan Dan gaskiya na kasa tan tancewa acikin
Ku hudun nan
amma yanzu kinga nasani

Maganar miji kuma point of correction mujimmu zakice please kina saka munjaye idan zaki furta
kallma kamar haka


Kafin ta kalli suby ta banka mata harara tace kekuma 'yar cin arziki banda lokacinki

Tabuga tsaki tashige part dinta ta banko kofar

Cikin tsananin tashin hankali Laila tace me yrinyar nan take nufi da wai bata San matargidan
acikin muhuduba

Hajiya rukayya cikin takai ci
Tace abinda kunnenku yabiya muku shitake nufi harda mukenan namuke nan ai mu hudu

Suby ta yashi tana haki tayi kofar husnah tashiga bugawa da karfi

Tace kifito Dan ubanki kiga yadda ake rashin kunya karamar 'yar iska yar talakawa kawai
shasha


Ita kuwa husnah ko jima batayi ba saboda tana bathroom tashiga wanka


Hajiya suwaiba da tsufa yakamata sosai tace kai kai kedawo nan bakuda hankali ko

Duk abinda kuka mata za ace mu ne muka saku

Kuma kunga zasugane ba tuban Allah mukayiba

Abinda nakeso daku kibari sai randa bama nan bamuzo ba sai Ku hadu kumata shegen duka
dakanta zata gudu

Kunga idan mukazo sai murufeku da fada sosai akan abinda kukayi Baku kyauta ba


Hajiya rukayya tayi murmushi tace kai hajiyata Ashe haryanzu da sauranki a tunani kuma
wallahi wannan shawarar tayi dari basa Dari

Suby tace ai gaskiya idan nakama yarinyar nan saina fasa mata baki wallahi wai nice 'yar cin
arziki


Nan dai sukata gulmacensu



Husnah kuwa wanna tafesa cikin wani tsadaddan material Wanda ummanta ta kawo mata Daga
Sudan

Ya hadu iya haduwa gashi dinkin ya kwanta ajikinta Daga tundaga samanta a matse yake

Sai Daga kasan gwaiwarta aka sake irin dai dinkin amare idan zasu dinner

Ta gyara gashinta cikin mayuka masu kamshi da dadawa

Tasaka ribbon tadauki sarka ta metsada tasaka

Rabin kirjinta awaje suke amma cikin net Wanda akayi ado dashi har wuyanta Wanda akecewa
high neck

Sai da tagama komai tay sallar magriba Dan taji anata kira

Ta dauki tiren abinsu tayi waje saida ajiye akasa tasaka ta kullo sashinta kafin tayi saman mijnta

Dining din saman tajera komai cikin wayewa da Jan hankalin mecin abincin

Kafin ta dauko remote din TV kunna ta dauko tasaka tashar sunna TV

Kafin ta fito bayan ta kullo kofar da key guri tasamu itama zauna a falon ganin ta zauna yasa
duk suka dawo da kallonsu kanta


Itakuwa husnah bata San Allah yayi ruwan tsiransu ba

Tadauki wayarta tana watspp tashiga group din mutuniyarta wacce tazama mata kamar roll
model dinta wato ummu afan

Wani littafi ake turowa maisuna 'YAN BIYU NE kuma husnah tana bin novel din daki daki

Tana balain son NANA DA SAMHA jarumar cikin novel dinne
Gaskiya itadai zata iyacewa novel biyune sukamata a rayuwarta Daga 'YAN BIYU NE

Sai kuma 'YAR MAKARANTA wacce ficacciyar marubuciyar nan ta rubutashi wato UMMY
KHALEEL
Gaskiya mutanen biyu tana matukar alfahari da littafinsu


Tana ta karatunta na novel dinta inda Nana tama Hussain karyan rashin sallah


Sai kawai taga ankarbi wayar an rada da kasa

Husnah tabi wayar da kallo kafin ta kalli wacce ta karba wayar

Laila ce tsaye tana karkada jiki tace nafasa kozaki yi magana nane

Husnah tayi murmushi tace kodaya abinda baninasayaba

Wanda yasai wannan shizaisaje sayan wani kinga kuwa ai basai nayi magana bako


Laila tayi tsaki saiya saya mugani ai wallahi bai isa yasai miki waya a gidan nan ba saidai
kizauna haka ba wayar

Husnah tace to Allah yakawo sauki

Kafin Laila tace wani abu prof yayi sallama yashigo

Idonshi direct kan babynsa suka sauka itakuwa Husnah ta shi tayi cikin tafiyanta mai kara
rikitashi

Ta isa gurin prof ta fada kirjinshi
Cikin tsananin mamki Prof ya ajiye jakar hanunshi shima ya rungumeta da kyau yana ajiyar
zuciya

Husnah tadago kai tace sannu da dawowa

Kasa amsawa yayi saboda mamakin Husnah

Itakuwa husnah ganin haka yasa ta sunkuya tadauki brief case Dan daya yar takama hanunshi
shikuwa prof binta kawai yake harzasu haura sama husnah tace sweet baka gaidasu hajiya ba

Har ga Allah prof bema san da mutane a falonba

Laila datayi suman tsaye baki kawai tasake da ido tana kallon ikon Allah

Hakeem yayi murmushi yakalli su hajiya suwaiba da hajiya rukayya ya ce sannunku hajiya
hankalina yayi gaba bangankuba Sam

Hajiya rukayya tace inazaka ganmu
ai hankalin ka baya taredakai

Nan ya gaishe su kaman karsu amsa amma dai gudun tuhuma yasa suka amsa mishi

Suby tsabar haushi ko gaishe shi batayiba bare uwar gayya datakasa magana

Kota Kansu baiyiba yajuya zai haura sama saiyaga wayar Husnah a tarwatse akasa

Yace garin yaya kuma wayarta yafashe

Caraf hajiya rukayya tayi tace ai da gangan tafasashi munata mata magana tace ai tagaji dashi
tana ce Kasai mata wata zaka saya

Shine fa Laila ta mata magana akan abinda tayi fa almubazzaranci ne shine fa tahau zagin Laila

Laila zatayi magana nace tabarta yarinya ce ai


Tana gama was Hakeem wannan bayani

Yayi murmushi yace oh baby rigima aidata fada ma da nataho matadashi

amma bakomai barin ci abinci nayi wanka saimuje nasaya mata wani

Ya kalli Laila yace kekuma data zaga kiyi hakuri kamar yadda hajiya tabaki hakuri Dan
yarinyace


Ya kalli suby yace ke tashi kigyara wajen data fasawayar

Yayi haura sama abinshi Dan tunda yatsaya gaisuwa husnah tashige da brief case dinsa


Yana shiga falomshi nasama yaji wani sassanyar kamshi mai ratsa zuciya

Tabbas yasan aikin husnah ce wannan Dan tunda aka zuba kujerun falon nan yana jinma ba
ataba share waba duk da ba azama sosai amma ai yana bukatar gyara


Yana shiga bedroom nan ma mamaki yakasheshi ganin yadda komai tas

Ya kalli koina fes

Husnah tafito Daga bathroom din shi tanufo shi tashiga cire mishi takallmimsa da cire mishi
bottle din suit dinshi

Har neck tied ita tacire mishi

Shidai Abdul mamakinta yakeyi kuma yakasa magana saida yarage saura farin naciki da
wandon suit din

Ta kwashe Sauaran ta ajiyesu Indayakamata

Kafin tace kashiga wanka kafito kacin abinci

Tana fadar haka tayi hanyar kofa

Hakeem yayi wuf yakamota
Suna fuskantar juna ya kureta da ido takam takasa kallonshi

Yakai bakinshi kun nan ta yace thanks my wife

Husnah dai kanta a kasa yazaunar da ita bakin gado yace bana son kitashi kijirani harsai na
fito OK

Husnah tadaga kai

Ya sumbaceta kafin yashige bathroom

Husnah tana dubawa kan side bed taga phone dinshi

Tadauka tahaye gadon tana kallon hotuna duk yawancin hotunan natane abin ya matukar bata
mamaki yaushe yasamu wadan nan hutunan Dan itadai bata san lokacin daakayisuba

Ganin hotunan meenat taredashi ranar graduation dinsu

Abin yamatukar bata mamaki

Kardai AMINA ABDUL HAKEEM

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login