Showing 84001 words to 87000 words out of 226733 words
kayanki ne? Ko na barcin wannan ai ya yi sutura, Shuwwa kar ki ce min bakya kwana a dakinsa tunda kika zo?"
SHUWWAR ta zuba mata ido bata ce komai ba a kasan zuciyarta tana ayana' Du tunani take wannnan mutumen wani mutun ne mai sauki kai ko? Ko du ji take kowani namiji da zarar ka saka matsatsu ka yi tafiya a gabansa zaka dauki hankalinsa ne?, Bata san cewa wannan mai kama da aljannun ya fita taurin kai bane, bama wannan ba bata san cewa baya cikin burikanta ne?'
"Kina nufin har yanzu baku yi....." Nahidt ta fada tana kallonta da zarro ido.
SHUWWAR ta dafe hab'arta tana fadin" kin ga matsalata da ke fa kenan, kin gani fa ko?"
Nahidt ta taba hannu tana fadin" Ko bashi da lafiya? Ko kece yar iskar? Shuwwa mijinki ne fa? Kwana har biyu daga ke sai shi a cikin gida ko shedan din bai samu galaba a kanku ba hala? Innalilahi na shiga uku na lalace Shuwwa du uban kudin da na kashe na dudura maki magungunna har yanzu bai fara kaikaitawa ba? Ke ina safarki? Ban hannaki zama ba safa ba?, Wayo duniya Shuwwa kina kallon kato yana shiga yana fita koda baya so ki masa dole mana?"
Wannan Karro SHUWWAR sai kawai ta zuba mata ido ta gaza ce mata komai sai da ta dasa aya ta ce" Wai me ya kawo ki ne?"
Nahidt ta dan kalleta, ta dan yi tsam sai kuma ta gyara zamanta tana murmushi ta ce" Na k'auro fa, ai mun ma yi magana da shi kin ga ya sa an saukeni baki ga yadda aka amshi kayana aka min maraba aka ce ga dakina da komai da komai, Shuwwa kin samu duniya Allah baki k'iyama."
Shuwwar ta zaro ido tana kallonta ta ce" Kin k'auro ina?, Ni da nake shirin tafiya sai ki k'auro? Waye ya sauke kin ? Ba dai wancen dunkum d'in ba kau? Nahidt tsakani da Allah me yake yawo a kwakwalwarki ke kin san ai ba zama zan yi da mutumen nan ba, na san kin gane da ba zama zan yi da shi ba, shine zaki kauro kema?, Innalilahi wa inna ilaihi raj'une Nahidht ina yayan namu yake yo? Gaskiya sai dai mu koma wajensa tare, waima me yasa baki zauna a wajen yayan namu bane?"
Nahidt ta zaro idanuwanta da fada fada ta ce" Ke da barin gidan kun ci uwaku! Na ce kun ci uwaku!, Kuma da kike cewa wai ina yayanmu yana nan baima san na kauro ba, ni ba zan iya zama a gidansu ba sai kumbiya kumbiyar munafurci suke yana sando baya so a ga zai je dakin Fauziya, itama wai ni take jin kunya dan wani tsohon munafurci, ke ni gidansuma ba hayaniya walahi ni kuma na saba ana haya haya ko yayane kau? Shuwwa wai ko dai korata kike ne? Kudi kika yi kike korata ne?"
SHUWWAR ta rafka tagumi da hannayenta bibbiyu tana kallon yayar tata, wai irin abin nan take yi na daukaka karamin abu dan ta sakata a uku, wai da wani yare NAHIDT take so ta kwatanta mata dala dala waye MUHAY ne?, Da yaya take so ta kwatanta mata shi din ba kalar maza yan soyaya bane? MUHAY bai yi kama da wanda zai iya tatalin mace ko ya nuna mata yana sonta ba, domin shi matan suke yiwa haka ta yaya shi zai fara yiwa wata? Shikenan ita sai ta zama banza a banza kenan? Ta zauna da k'aton sai dai ita ta ringa rarashinsa shi ba zai rarasheta ba? Ai ba haka bane rayuwa gaba daya ba haka bane ba, ita burinta ta samu namijin da zai kasance mai yawan maimaita mata kalmar so, wanda zai ringa fada mata ba dare ba rana cewar itace so dinsa, wanda zai zama tamkar redio idan tana gefensa, aman wanna mutumen idan ya budi baki dan ya mata masifa ne, a kwana biyun nan da ta yi da shi zata iya cewa kyautata masa b'ata masa rai yake!
A hankali Nahidt ta ce" Da kin san abinda ya koro ni gidan nan da sasafe da baki nemi na koma ba, dan na san ranki sai ya baci Shuwwa."
Shuwwar ta cire taguminta tana kallonta ta ce" Wani abu aka yi maki?"
Nahidt ta sauke ajiyar zuciya tana aron jarumta zata fara magana wayarta ta shiga kuka.
Kin dubawa ta yi domin a tunaninta yayansu ne ko Fauziya, bata san cewa Malan bane, da ta dauka ta gindaya masa sharudan da ta gama zanawa ranta sannan ta fada masa ya ji kunya wollah, ta danne wayar ta hade hannayenta ta ce" Abanki, Shuwwa Abanki ne ya ba matarsa waya ta zageni ta ce min karuwa?"
Gaban SHUWWAR ne ya fadi tana kallonta ta ce" Aunty, kalle ni, kalle ni, dan Allah ki fada min gaskiya kin ji? Aban nawa?"
Nahidt ta taba hannu tana fadin" To karya zan maki ne?, Na rantse da Allah tsakiyar dare muna maganarki da shi jiya kawai ya tashi ya kai mata wayar dakinta ta aniya duran ashar harda mamanmu da abanmu ta zaga, ta kuma ce min karuwa wai ina kiran mijinta tsakiyar dare!"
Zuciyarta ce ta fara tafasa a zaunen da take tana kallon auntynta ta dan wara zamanta tana kallonta ta ce" Nahidht, dan Allah ki rufa min asiri ki fada min yadda abin ya kasance kin ji? Kar ki saka na aikata abin kunya, domin idan matar nan ta taba ni ta kwana lafiya banda ke, bana tunanin zan iya kyaleta a yau Nahidt, me ya hadda ku waya da Abahna? Kin tabata shi ya kai mata waya? Abana ba zai aikata haka ba Nahidt, ki fadan yadda abun ya kasance."
D'auke hannunta ta yi daga na ta hannun da mamaki ta kalleta tace "Kai! Shuwwa a ganinki k'arya na fad'a? Zan miki karya ne dama ? Wallahi gaskiya nake fad'a miki, ke abun kunya fa Abanki ya riga daya aikatashi, sai dai fatan kiyaye na gaba kawai."
A zafafe take kallonta har ta muskuta ta gyara zamanta, wara k'afafunta tayi sosai irin zaman nan wanda ko masifa kake za ka ji dad'in jijjiga jikinka yanda kake so, hannun rigarta d'aya ya fad'i har ya sauko kan damtsenta, ba wai dan ta mata yawa ba sai dan kalar zaman da ta yi ta dafe hannunta d'aya akan cinye.
Kafin ta ce wani abu suka ji takon saukowarshi daga sama, da d'an sauri sauri yake saukowa saboda wasu takardu da ya ke son ba wa d'aya a cikin yaransa ya kai masa ofice.
Sam bai kula da tsiyarsu dan yi yayi kamar bai gansu ba ya nufi hanyar ficewa daga falon gaba d'aya, a yanayin neman fitina da rigima ba tare data gyara zamanta ba tace "Ji mana."
Har zuciyarshi bai yarda da shi take ba, dan haka ya wuce abinsa har ya kama k'ofa zai fita ta d'aga muryarta yanda zai ji ta ya kuma fahimceta tace "Ji mana malam soja."
Cak ya tsaya hannunshi na kan hannun k'ofar amma ya kasa jawowa ya bud'e, a saib'ance ya juyo ya zuba idanunsa akan ta.
Nahidt da ke kallon Shuwwa da mamaki ta rarako ido ta rufe baki mamaki na neman kasheta tace "Muhammadu Rasulillahi sallalahu alaihi wa sallam! Allah ka jik'aina tun man mutu ba."
Sassauta muryarta tayi a hankali tace "Shuwwa ashe dai haukan da na ji ana rad'e rad'i a kan ki gaskiya ne? Yanzu ke dan ubanki wannan d'in ne daga zaune kike kira da ji mana...Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un!"
Zunbur ta mik'e ta d'auki mayafinta tace "Bari in koma d'akina, wannan lamari na ki sai addu'a."
Kallon fuskar Nahidt yayi sanda ta kawo kusa da shi, d'an kaucewa yayi kad'an tare da sakin hannun k'ofar ta rab'a ta fita, saida ya ji ta rufe k'ofar ya dawo da dubanshi a kan ta.
Tasowa tayi tana gyara hannun rigarta daya fad'i ta kai kusa da shi sannan ta tsaya, kallon fuskarshi tayi tace "Dama ina so zan fita ne anjima, zan je wajen Abana."
Gefensa ya d'an kalla yana sakin murmushin gefen labb'a mai ciwon gaske, yayin da zuciyarsa ke ci gaba da raya masa duk Dady ne ya ja masa wannan wak'i'ar, amma yanzu zai wa tubkar hanci ta yadda za ta banbance aya da tsakuwa.
Damatsenta ya damk'a da k'arfin da ya san za ta iya d'auka, ihu ta saki na balakin daya ziyarceta amma sai ta ji bakinta ya sake yin d'uff ta kasa furta komai.
Gaba d'ayanta ya d'agata, irin d'agawar nan dake raba mutum da k'asa, kuma gata a hannayenshi ya rik'e damatsenta, wutsil wutsil da ta ji k'afafunta na yi a doron k'asa yasa ta duk'ar da kanta dan ta tabbatar wai gaske d'agata ya yi, duk'awar da ta yi ce ta sa hular kanta fad'owa har saida ta shafi fuskarshi kafin ta dire k'asa.
A kid'ime ta d'ago dan ta kalli fuskarshi ta rok'eshi Allah Annabi ya sauketa k'asa dan yanzu ta tabbatar a sama take.
D'agowar da ta yi da sauri ta sa gashinta daya fincike tsabar jijjigar daya fara mata ya rufe masa fuska, iskar bakinshi ya huro da k'arfi ya hure gashin daga fuskarshi, hakan yasa ta rintse ido saboda iskan daya huro mata a fuska.
Ido cikin ido suka kalli junansu wanda ita na ta suka rarako waje su d'an d'auki launin ja, bakinta dake bud'e alamar tsoro da firgita yake kallo, d'an tsurut da shi amma a haka take iya yanko masa magana iri iri.
Jijjigata yayi, kamar dai yanda zaka zazzage shinkafa ko dankali a cikin buhu, hakan yasa Shuwwa rintse ido kan ta ya shiga gigil gigil gaba d'aya jikinta na d'aukar jijjigar musamman k'afafunta dake sama, a k'asan mak'oshinta ta dinga fad'in "Aaaaaa! Kakkkkk...sssory."
Dakatawa yayi daga jijjigar da ya ke mata yana kallon fuskarta dan samun gamsuwar ta jijjigu ko da saura, daga tsayen nan ba tare da ya rusuna ba ya saketa da tunanin ta fad'o yanda zata d'an samu karaya ko shida ce a k'afa, amma ikon Allah sai ta fad'a kan k'afafunta amma rashin k'warin jiki da kuma dawowar da bata yi ba daidai saboda wannan shocking da ya bata, sai kawai ta yi zaman yan bori k'asa har saida ta sake lik'e idanunta gam ta dafe k'ugunta tace "Washhhhh!"
A hankali ta fara bud'e ido har ta bud'esu fes akan shi, zabura tayi ta Waro ido da zulumin me ye kuma na sunkuya gabanta yana kallonta, tsugunno yayi irin na maza yana k'are mata kallo yana so ta dawo hayyacinta sannan ya fad'a mata abinda ya ke son fad'a mata.
Marairaicewa tayi ta tank'washe k'afafunta tana sake rik'e k'ugunta da nufin ko ya tausaya mata idan yayi tunanin ya karya mata k'ugu.
Nunota yayi da yatsa fuskarsa a kausashe yace Ke! Kin san wa ye ni? Ke wacece da za ki dinga neman ja na a k'asa? Wane irin aljanu ne a jikinki? Idan na kirasu za su tashi?"
Hannu ya kai zai kamo gashinta da niyyar ya kira aljanunta ya ce su tashi dan su yi cin uwa da su ko zai ji daidai, ita kuma a tsorace ta ja baya tace" Na ce sorry ko."
Cak ya tsayar da hannunshi yana kallon fuskarta, kallon daya tsareta da shi yasa ta sadda kanta a marairaice tace" Ka yafe min dan Allah, in dai babu abinda ka sha ka k'yale ni haka."
_Ta kuma._😂💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥
*ALK'ALAMIN K'ADDARA TA*
💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥
*The Hero writer*
*SAJIDA*
_Bismillahir rahamanir rahim_
PAGE:. 2️⃣8️⃣
*P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽*
*S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ*
*S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞*
*T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻*
1 *yar mahaukaciya*
2 *Banida zabi*
3 *Duk karyar kada*
4 *Baka ce*
5 *Daga tafiya daukar soja*
6 *Kutkale*
7 *Makauniya ce*
8 *Mage mai kwanciyar daukar rai*
9 *Duk nisan jifa*
10 *Dutse*
11 *Idan Ka Raina Inda Kake*.
12 *Neman Na Kaina*
13 *WATA KOKOWAR*
*The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA*
*WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓*
Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748
Amina Maikudi Abdullahi
GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.
Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar
08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.
Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
Yunk'urawa yayi zai mik'e da wani mugun sauri Shuwwa ta rigashi mik'ewa, d'aurin k'irjin da tayi ne ya warware hakan yasa da sauri a rikice ta dafe k'irjin, a tunaninta sake shak'o wuyanta zai yi, dan haka ta juya da gudu ta shiga haurawa sama har tana juyawa dan ta ga wai shin ya biyota ne ko kuma ya ya ya.
Mahuydeen dake tsaye yana bin ta da kallo da fari mamaki ne ta bashi, amma da ya ga tsakaninta da Allah gudun ceton rai ne take da mugun tsoron nan, yanda take taka matakalar da mugun gudu ba ta ko tsoron ta kifo k'asa, yanda take rik'e da zanin a hannunta ga d'uwawunta dake ta gudun su ma daga cikin zanen duk da ba d'auri ne ta masa da ya fito da surarta ba.
Me zai yi in ba dariya ba? Haka kawai ya ji dariya ta sakosa a gaba dalilin mahaukaciyar yarinyar nan, abinda ya jima bai yi ba sai gashi har da neman k'yak'yatawa yake.
Lokaci d'aya kuma sai ya yi gum da bakinshi kamar dama dole aka saka shi dariyar, wani basaraken murmushi ya saki yanzun tare da jinjina kai a zuciyarshi ya ayyana "Haka ya kamata ki kasance kina gudun fanfalak'i idan kin ganni."
A hankalce ya juya dan zuwa aiwatar da abin da ya fito da shi, sai dai a jikinshi yake ji ko ya kwanta yanzun na zai samu bacci ba saboda makirar yarinyar can, dan in dai ran shi a b'ace yake baya iya samun bacci, duk da ma dai ya d'an samu nishad'i tunda har ya yi dariya, amma hakan ba yana nufin zai samu bacci ba ne yanzun
_________________________________
Kamar jiya, yauma haka suka wuni sunna aiki, yau aikin yaa sha bamban da na jiya domin daidai da girkin ba an dafa ci idan ka yi niya bane, an dafa da ka kaleni zaka soni ne, watau irin girkin nan da zarar mutun ya kalla zai ji sha'awar ci ko yayane, hakan ya saka Shuwwa shiga a cikin takaicin aikin da Nahidt ta dage suke yi har sai da ran Nahidt din ya baci da gannin tana aiki ba kaza kaza ta ce" Ke wai me haka yake nufi ne? Aikin uban gidanki kike yi a haka ne? Yuaushe kika koma yin aiki da munafurci ne?"
Shuwwar ta dakata tana cire safar hannunta da ta saka take faman aiki a kusa da tukwane ta dauki tissu ta share dan gumin da ta tarra tana kallon kicin din da tunanin wai ina hanyar da iska ke dan fita ko shigowa ta dubi auntynta ta ce" Mah, wahala ce fa muke yi, domin a tsamtsamce yake da abinda zai kai bakinsa"
Da dan mamaki take kallonta ta ce" A tsamtsamce kika ce?, Yaya aka yi kika sani?"
Shuwwa ta watsa hannayenta tana kallon yamboll din da NAHIDT ta sakata dakawa dan fitina ta ce" domin jiyama na yi girki a gidan nan, kuma bai taba komai ba, daidai da liptona dinsa sai da ya tarda ni dakina ya sakani sha sannan ya tafi da shi, na tabata ritsani ya yi dan ya ga idan zan iya sha ne ko me........, Ina tsoron ko yana tare da tsoron cin abincin kowa a rayuwarsa "
Nahidt ta dan kura mata ido na dan lokaci sai kuma ta saka yar dariya tana fadin" Kin san me ya fado min a rai? Marin da kika sha a lokacin da kika ajiye abincin Rislane ya zo taba maki nono kika kiya uwarsa ji take abincin ne kika ki ci ta wanka maki mari, kai a ranar kin daku shuwwa"
Shuwarma ta saka yar dariya tana zarro idannuwanta ta nunota da hannunta ta ce" Kema ai kin dakun kin manta da kika cewa uwar jaka kema ta wanka maki mari? Aman mun masu tsiya kai da bamu bato saudiya ba sanadiyar kayar da uwar nan da muka yi da sai an yanke mana kai a tsakiyar gari dan a kiyaye gaba"
Yar dariyar raha suka yi tuna ranar da sukai gudun ceton rai,
Daga bisani Nahidt ta dubeta da kyau ta ce" ribar aikatau din da muka yi menene Shuwwa?"
Shuwwar dake zaune saman yar karamar kujera ta dan sake kura mata ido tana kallonta aman ta ki ta ce da ita komai, hakan ya sa ta sake sakin murmushi ta ce" Ribarsa shine, naci wa farin cikin uban gidanmu, girkawa ba tare da tunanin za'a taba ko dan tsakure ba, girki da soyayar abinda muke dafawa...........Shuwwa karasa min mana?"
Shuwwar ta lumshe idannuwanta tana tuna rayuwarsu a sanyaye ta ce" naci da maimaici a kan lokaci, tsafta da kwanoni masu fuzgar maganadisun kwalon idannu, kula, hankalta da yannayin wanda ya ajiyemu, shi abu mai daraja shi yake janyowa kansa daraja ne"
Dan murmushi Nahidt ta yi a sanyaye ta ce" Ba lallene ace dan ya ki ci ko dan ya saka ki sha yana tare da tsatsamcin cin abinci, ta yiwu damuwarsa ta tsafta ce, ta yiwu a matsayinsa na baba ba lallene kai tsaye ya aminta da girkin macen da ta shigo da niyar zaman aure da shi ba, dole yana da bukatar yarda da ita, yana da bukatar gane hannunta, idan har ya sha Lipton dinki na jiya zan iya ce