Showing 36001 words to 39000 words out of 163149 words
hisham na gode da mutuntawa da karramawar da kamin har ka furta kana sona,saidai ina mai baka haquri tare da addu'ar Allah ya baka wadda ta fini komai da komai,amma bani da ra'ayin soyayya,kayi haquri idan hakan ya bata maka rai''
shiru yayi na wani dan lokaci da alamu baiji dadin,amsar da ya samu daga gareta ba
''babu komai maryam,ita dama harka ta soyayya babu batuntilas,na gode nima da yadda kika mutuntani,amma ina nan ina jira har zuwa lokacin da kika ji jin aminta da soyayya''
murmushin yaqe tayi,ita kadai tasan me take ji cikin zuciyarya,wani irin qunci take mata,kyautar dubu goma hisham din yayi mata,da ta doje tace bazata amsa ba yace shina kam yayi niyya bai fasawa,dolenta ta amsa ta masa godiya sanna ta juya don komawa ciki
tuni an kashe qwayayen waiting parlour babu haske sai wanda ke fitowa daga sashen mami da nene,tazo tsakiyar parlour din taji an fincikota baya,razana tayi matuqa,tuni idanunta suka fito wajevta bude bakinta da niyyar qwalla qara saidai bata samu damar hakan ba,sakamakon hadata da bango da kayi aka saka wani lallausan tafin hannu aka danne bakin nata,qamshin daddadan turare ya mamaye hancinta,qirjinta ya shiga dagawa da sauka numfashinta ya soma tsere,minti kusan daya sannan taga haske kadan ya bayyana atsakninsu ,haaken screen ne na waya,fuskarsa ta fara gani abdallah ne,sanye da t.shirt fara sol cotting mai gajeren hannu wadda ta fito da murdadden damtsensa,kauda da qwayar idanunta tayi ta daina kallon fuskarshi sakamakon yadda take babu alamun rahama ko kadan a cikinta
murya a kausashe kuma qasa qasa yake fadin
''kin taimaki kanki da baki amsa masa kina sonshi ba,wallahi koda wasa kika amsa kina son wani da ya jibanceni kin shiga uku,baki kai ajin da zaki shiga rayuwar abokan huldata ba,ki qara gaba zaki iya samun wanda ke muradinki acan wata rayuwar ba tamu ba,bana aon cusa kai cikin lamura na da katsa landan tun ba yau ba na gaya miki,ki kiyaye don samun zaman lafiyarki da ci gaba da aikinki cikin gidan nan''
kamar jira ake ya kammala maganarshi haske ya mamaye falon,jdanun zubaida suka sauka kansu yayin da nashi idanu suka sauka kan fuskarta da hawaye ya aoma gangarowa,wani abu ne ya riqe mata maqogaro wanda koda an bata damar maida masa martani ba zata iya ba alokacin,saboda baqincikin da ta hadiya ba kadan bane,tsanarsa da tsanar halayensa uka sake linkuwa cikin zuciyarta
''kai din banza,abokan mu'amalar taka ma din banza,baka isa maryama ta soka ba,saboda daraja mutunci da karamci take bida ba tarin dukiya ko kyau ba''abunda take ta son ta amayar masa kenan saidai abundaya tokare tan ya hanata fada
cikin zafi baqinciki da kishi zubaida ta iso gabansu
''abdallah''abunda ta iya ambata kenan cikin karyar da kai hawaye ya soma mata zirya,sam bai damu da ganinta agun ba,duba daya ya mata ya maida idobsa kan maruam ya cire hanunshi yana jan tsaki,ya ja mayafinta ya goge hawayen ta da ya soma taba masa hannu
''indai bakiji abunda na gaya miki ba yanzu kika fara kuka''ya kewayeta da,zafinsa ya fice asashen,ita dinma gyalenta ta ja kawai ta shige sashen nasu,abida ce kawaia falo da tayi zaman kallo tana kuma dakon dawowar abdallah don yace ta zauna ta jira shi batasan gatse ya mata ba lokacin baccinshi yayi,dakinta ta wuce ta danna qofar ta rufe kana ta saki kuka,me tayi masa?,ita tace tana son hisham ne ko kuwa,ahikeban talaka ba komai bane agun wasu masu kudin,talaka bai cika mugum ba,ko talaka baisan ciwon kanshi ba,taqamarshi ta isheta,tana jingidansu zata bar masa shi yafi mata sauqi,ga fargabar yanayin gidansu ga taqama da gadararshi da wanne zata ji?
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:52 PM] 80k: *ABADAN*
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
*_Daga abu hurairah yarda Allah ta qara tabbata a gareshi yace:manzan Allah s.a.w yace:yana daga cikin kyawun musuluncin mutum,ya bar abunda babu ruwansa_*
*_a wani hadisin kuma manzan Allah s.a.w yana cewa:jibrilu bai gushe ba yana min wasiyya da maqoci,har sai da nayi tsammanin/zaton maqoci zai iya gadon maqocinshi(saboda girman haqqin dake kan maqoci akan maqocinsa)_*
washegari a makare ta tashi saboda rashin baccin kirki,kitchen ta shiga ta shirya musu breakfast,adana kebabi,tavouk koftesi a abincin turkia sairuwan shayi chips da soyayyen qwai,cikin lkkaci qanqani gidan y game da qamshi,bata bar kit hen din ba baba uwani ta shigo
''af,makara kikayi ne yau maryamu''murmushi tayi tace ''wlh kuwa baba uwani''
gaisawa sukayi sannan ta bar mata kitchen din ta koma dakin
sha biyu na rana ta fito tayi sarving nasu mami ce da abida,cikin mamaki abida ke cin abincin tana tantamar yinsa akayi ko restaurant aka je aka siyo?,abincin yan turkey a nijeria,kusan ma har yafi nasun dadi sakamakon banancin spices da muke da shi
so take ta sanarwa mami qudirinta na barin gidan saidai ta gaza,nauyinta take ji sosai,alkhairan mamin a gurinta na da yawa,da haka har suka kammala cin abincin ba tare da ta ce mata komai ba
kafin ta bar gurin mamin le sanar da ita gyaran gida da canza kayayyakin da suke duk shekara idan ya rage saura kwanaki bakwai azumi
''akwai ma'aikatan dake,zuwa,suna aikin nan da jibi zaki gansu,abunda kawai nake so kimin alfarmarshi shine zaku shiga kasuwa kiyo soyayyar kitchen dukkan abunda ya kamata wanda za'a buqaceshi''
ta dan saki murmushi''diuarki ce ni mami kamar yadda kike fadi,ba alfarma bace umarni zaki bani kawai na bi''
''na gode diyata Allah yayi miki albarka''
wanna halaye na mamin na daya daga cikin abinda ke sata sake jinta cikin zuciyarta
koda ta kammala abincin dare,sashen ta sake bari,gurin baba uwani ta kuma wuni,kiran wayarta da mami tayi da daddare shi ya fiddota ziwa,sashen mamin,a hanya suka ci karo da zahariyya na shirin fita cikin motarta,wani kallo ta jefi maryam din da shi wanda ya tilasta maryam neman tsari da ita
cikin shirin fita ta samu mamin
''maryam yau kwanan asibiti zanyi bazan dawo ba sai gobe idan Allah ya kaimu,ga gidan nan na barshi hannunki''
''to mami''ta fada tana amsar jakar hannunta don yima mamin rakiya zuwa motarta
daidai lokacin abida ta fito sanye da riga da wando,kunnenta maqale da earpiece
''mami ina zuwa?''
''af,na mamce kina cikin gidan''
hara rar maryam abida tayi
''mamee kika manta da ni amma wannan ki kasa mantawa,da ita''bata lura da hararar da take ma maryam din ba tayi dariya
''to ai kece din sarkin kwanciya,klum kina kwance a gado kamar ruwa,zan tafi asibiti ne ina kuma tsammanin kwana zanyi''
''q'nnnn,si kin dawo''ta fadi tana kwanciya saman doguwar kujera yayin da suka fice ita da maryamu
mami na shirin shiga motar taga shigowar abdallah gidan,hakan ya sanya ta dakata har ya iso inda suke ta sanar mishi fitarta ta dora da
''am....abdallah,inason in ganka daman''
''to mami ai gani''
janye jikinta maryam tayi ta koma gefe don basu damar ganawa,daidai duk da hakan tana jiyo abunda mamin ke cewa
''har yanzu banga alamun jituwa tsakaninka da bida ba abdallah me yake faruwa?''
''mami ba komai kawai dai rawan kanta ne yake bani haushi,azarbabi rashin aji da kamun kai,kuma ma ban samu zama bane kinga soaai,kwana biyin cases sun mana yawa a office,bainciken wadanda suka saci kudin talakawa''
''duka naji,saidai inaso ka ajjiye dukka wani uzirinka,ka tabbata kun fahimci juna kai da ita,maganar halayenta kuwa kana da damar canza ta tunda tana sonka,ya kamata ace i yanzu ka ajjiye iyali,don nima ina da buqatar ganin qana nan yara suna gilmawa,ina fata ka fahimceni da kyau abdallah?''
''na fahimta mami,saidai koda jikokin sunzo ta yaya wadan nan patient,naki zasu barki ki sake da family dinki,suna qwace min ke kina kwanan office''ya qarashe maganar cikin sigar zolaya
murmushi tayi don ta san dama sai yayi qorafi,haka take fama da shi duk lokacin da zata kwanan asibiti
'?idan na biye maka abdallah sai ka makarar da ni''ta dan daga murya kadan ta kira maryama,cikin nutsatstsen takunta ta iso,gidan baya mamin ta shige sannab maryama ta miqa mata jakar tana cewa
''a dawo lafiya mami''
''Allah yasa maryama,a kula da gida''
''insha Alahu mami Allah ya bada sa'a''
mamin ta juya ga abdallah dake tsaye yana jinsu,hannayenshi harde saman qirjinshi,har ga Allah yaji dadin yadda ta nuna caring wa mahaifiyarshi
''abdallah sai na dawo,banda tsokane tsokane?''mami ta fada tana dariya
''mami sai kace yaron goye,zaki jawo a raina abdallahnki fa''ya fada yana shigeqa ahima gidan bayan
''a'ah,ya haka?''ta tambayeshi
''zanje na rakaki ne mami''
''yabzun fa kaima ka dawo daga aiki,na uafe ka shiga ciki ka huta,abida na parlour tana jiranka''
''idan ina tare da mami mancewa nake da duk wata mace,a naje asibitin naja masu kunne duk wansa ya barki kikayi aiki duka dare baki runtsa ba ni da shi ne,driver muje''haka drivan yaja sauran securitu dinshi suka dafa musu baya maryam ta dawo cikin gida tana jiniina yawan qaunar dake tsakanin mamin da abdallah
a inda ta bar abida anan ta taras da ita,bata tanka mata ba,tana gab da shiga dakinta taji tace
''ke zonan,''tayi kamar ba zata kula ta ba don ta tsani irin wannan kiran sai kuma taga baquwar mami ce ko ba komai taci darajarta
''wai me kika dafawa mutane?''kafin ta kai ga bata amsa kuma sai taji tace
''jeki kawai,sai abdallah soulmate ya iso kyazo kiyi serving namu''
ta gama shirin kwanciyarta tsaf ta tuna ta manta da littafin addu'o'inta cikin kitchen,hijabinta ta zura ta fito don ta dauko
abdallah ne cikin falon gefanshi abida ce zaune ta sanya ahi a gaba tamkar zasu hade,magana auke qasa,qasa,son bata iya jiyo me suke cewa,tayi kamar ta koma sai kuma ta fasa tayi ahigewarta kitchen,tana qoqarin komawa taji tace
''ke zokiyi serving mutane,kin shige daki kin zauna sai kace baki san aikinki ba''
bata tanka mata ba sai da suka isa teburin,a sanyaye cikin jerartun maganganunta masu cike da nutsuwa
''idan baki sani ba sunana maryam don Allah ba ke ba,aiki kuma ba naki aka umarceni da inyi ba,ba don ke nazo gidan nan ba,so please don Allah mu girmama juna,tunda dukkanin mu 'yan adam ne,halitta mai qima da daraja agun Allah''
''naqi na kirakin da hakan,kuma ni ba sa'arki bace kada ki kuma hada kanki da ni,ki dubeni ki dubeki mana,tundaga sutura ai kinsan da banbanci,kada ki kuma gigin hada kanki da ni''
shiru tayi mata domin ta fuskanci abidan tayi nisa,gwana ce itama gun girman kai,amma bata jin zata iya jurewa shararta ba sam,da iliminta itama da shekarunta,ba jahila bace bare tace zata dinga shiga gonarta tayi mata kashi ta qyaleta,ta kammala zuba musu tuwon semo miyar kubewa danya sai farfeaun kan rago a plate daban,a yatsine abida ke duban abincin
''meye kuma wannan?''tayi tambayar tana duban maryam,banza tayi mata tamkar bata jita ba,don,kanta da ta gaji da shirun tace
''ni wlh soulmate bazan ci wanna abun ba,na manta wanne lokaci ne na qarshe,da na cishi,kinga malama ki ahiga kitchen ki dafa min wani abun''
''awoyin shiga kitchen dina na yau sun qare,amma babu damuwa idan zaki iya jira zuwa gobe''
daga haka ta miqe tabar musu teburin,ahi kansa abdallah dan binta yayi da kallo ganin yadda yai take maida raddi babi kinkiri,fana iya jiyo ihun abida na zage,zage da hausa mixs da,harshen nasara wani lokaci harda turkanci
''oh god,pls don Allah ki yiwa maqogoronki afuwa,baki gajiya da fada?''abdallah ya fada bayan ya tallafe kumatunta ya sanya zazzafar qwayar idanunshi cikin tata,laqwas jikinta yayi,farinciki ya maye gurbin bacin ranta,tuni ta sanya hannu ta aoma kwasar tuwon sai gashi qarshe ta bige da santi
ta cusa kanta cikin pillow ta sake rubtse idanunta akaro na barkatai,har yanzun dai bata daina jiyo tashin hayaniyar ba daga dakin abida
muryar abida ce wani lokaci data abdallah,kuka take tun kusan rabin awa das,uka shuhe,sun hanat a bacci,ta kuma gaza fahimtar meke faruwa
''wallahi abdallah ko baka aureni ba indai ka kwanta da ni burina na duniya ya gama cika,don Allah abdallah ka amince wallahi zan iya rasa raina ayau idan ban samu cikar muradina ba,muna da dama abdallah muna da lokaci isashahe,mami bata nan daga ni sai kai kawi abdallah,pls ka taimaka min''
mamaki baqinciki da takaici suka sake cikashi,gumi ya kuma karyo masa,kimanin awanni biyu yana fama ta rabu da shi amma ta qiya,tun yana lalashinta yana qoqarin fahimtar da ita har ta soma bashi haushi,da ya miqe ta yago shi,har ta rabaahi davtshirt din jikinshi sai singlate kamar tsohuwar mayya,bayason gwada mata qarfi ne amma ya fuskanci sai ya biyo,mata ta hakan
cikin zafin nama ya miqe ta sake yunqurin kamoshi,tuni ya watsar da ita ya fice kana ya maida maqulli ya rufe dakin,dai dai da fitowar maryam kenan wadda tayi niyyar barin dakin nata ta canza makwanci sakamakon hayaniyar da ta hanata sakat tasu
a tsorace ta dubeshi idanunta cikin nashi,ganinshi a jargitse ga sautin kukan abida dake fitowa cikin dakin da ya kulleta,sai ta dan ja baya kadan zuciyarta ta soma harbawa,shi din ma ita yake kallo
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:52 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶2⃣7⃣
*_ubangiji madaukakin sarki yakanyi duba izuwa filin arfa,sai yace da mala'ika jibrilu,me bayin nan nawa suke nema haka(duk da cewa shine mafi sani),sun fito cikin tsananin zafin rana da qasqantar da kai?,sai mala'ika jibrilu yace''rahamarka da gafararka,sai ubangiji yace na gafarta musu''_*
*_haka ubangiji s.w.a yake rabon irin wanna garabasar a filin idi,annabi muhammad s.a.w yana cewa''kada ku hana bayin Allah mata zuwa masallaci''_*
*_sannan yayi umarni da a fita sallar idi maza da mata yara da tsofaffi_*
*_yake 'yar uwa,kada ki bari wanann garabasa ta wuceki wadda baki da tabbas din ganin wata kamarta,Allah yasa mu dace,ya yafe mana kurakuranmu,yasa mu cikin bayinsa da za'a gafatarwa Allahumma ameen_*
*_wannan shafin sadaukarwa ne ga dukkanin al'ummar musulmi,Allah ya karbi ibadunmu_*
ci gaba yayi da lallonta kamar yadda take kallonshi,tuni oily eyes dinta suka qara sheqi da sakamakon tsoro da qwalla da ta tarar mata,zuciyarta na raya mata mummunan abu abdallah ya yiwa abida,cikin hanzadi ta juya da nufin komawa dakinta ta banke saidai taku daya biyu ana ukun ya cafkota ya maidota baya,take jikinta ya soma bari,bakinta na rawa ta soma fadin
''don.....d....don Allah kayi haquri,ka fufamin asiri''
galala yake binta da kallo,tuni ya gano manufarta,ganin taqi nutsuwa ya sanyashi daka mata tsawa
''me zayi dake da har kike tsammanin wani abu zan miki?,koyin ma zanyi kin min kadan 'yar tsakuwa,abinda nakeso dake kada ki kuskura wani yaji abinsa kika gani?,ina fatan kin fajimceni?''
kai kawai take gyadawa babu qaqqautawa,burinta kawai ya saketa ta samu ta tsere,yana sakin nata kuwa ta shige dakin jiki na rawa ta murza key
binta yayi da kallo cikin mamkin mummunar fassarar da tayi masa tashi guda,koda ya koma daki sai yaji abun ya tsaye masa a rai,ta tuhumeshi da laifin da bai taba sha'awar aikatawa ba,hasalima ya tsani mai aikata shi,gefe guda kuma tsanar abida ce fal cikin zuciyarshi,yaci alwashin koda zata rasa rayuwarta bazai iya aurenta ba,yana da tsananin kishi ya tabbatar koa ya aureta din bazaya samu kwanciyar hankali ba
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
kusan dukkaninsu kwanan zaune sukayi babu wanda ya runtsa,kowa da abunda ke yawo cikin rai da zuciyarshi,duk da hakan maryam bata kasa tashi yadda ta saba ba ta hada breakfast,saidai babu wanda yaci,bata san da hakan ba sai da mami ta dawo ta hau sama ta kintsa kana ta sake dawowa qasa don yin karin safe,abida qunar zuciya ta hanata fitowa,abdallah yayi sammakon zuwa ofgice saboda wani taron gaggawa da zasuyo wanda shi kansa bai san da shi ba sai da asubahin ranar his excellency mr presdent ya sanar mishi,saboda haka kiegin qarfe shida yabi zuwa abuja
maryama kuwa tsoro da fargabar haduwa da abdallan ne ya hanata fitowa bayan ta samu ta kammala aikin ba tare da sun hadu ba
''shi kam abdallah ai ya jima yanzun a abuja,jeki kiramin abidar dai ta karya,ya zatayita zama bata ci komai ba''
kamar tace da mami ba zata iya zuwa ba don tana fargabar halin da zata je ta taradda abidar,bata da amsar tambayar da mami zata yi mata game da abunda zata ga ya samu abidan
ba zata iya qin zuwan ba don haka ta miqe jiki a sanyaye ta nufi dakin,sai da tayi knocking sau biyar kafin a bada izinin shiga cikin qaqqarfa kuma kausa sashiyar muryar abidar
ga mamakinta sai ta tadda abidar ta fito daga wanka ras da ita,babu wasu alamu dake nuna wani mummunan abu ya faru da ita
''meye kika tsaya kikatsaya kika zuba min idanun kin nan masu zubi da na mage?''
sai a lokacin ta ankara da tsayawa tayi kallon abidar
''mami ke kiranki''tana jinta tana tambayarya ta dawo ne tayi mata banza ta wuce
da daren ranar ta sake shiga wani rudanin,a hanyarta ta dawowa daga sashen baba uwani zahariyya ta sha gabanta ,tace taje nene na kiranta
zaune take gaban nenen cikin falonta na can sama,daga ita sai nenen sai zahariyyar
''maryamu kike ko?,nasan zakiyi mamakin irin wannan kira na bazata,ba komai bane yasa na kira ki wata buqace da ni wadda nake neman taimakonki gurin cikarta,ina fata kuma zan samu hadin kanki gun cikar buri na''
''zan iya taimaka mikin indai bai kauce addini na na ba''
wata dariya nenen ta kece da ita
''idan banda quruciya irin taki ai yanzu kowa ma ba bin qa'idar addinin yake ba,biyan buqata kawai ake nema''nene ta sake qasa da murya kana ta kuma matsowa kusa da maryam
''ba wani abu nake nema agunki illa poising da nake buqata kawai ki diga a abincin abdullahi''
a firgice ta miqe har jiri na shirin kayar da ita lokacin da nenen ta gama zayyana mata buqatarta,bari kawai jikinta yake,addu'a duk wadda tazo bakinta yi take
halin da ta shiga kawai ya ishi nene amsa
''kinga zauna ki nutsu,sai kace wadda aka ce ta diga a abincin ubanta,aikin nan fa ba a kyauta zakimin ba,biyanki zanyi kudi masu yawa da nauyi,zan dauke miki dukkan wani quncin talauci da kike ciki,zan wadata ki zan yalwataki''
hawaye ne ya shiga bin kuncinta,girgiza kai kawai take cikin takaici
takaicin ha'intar managarciyar mace kamar mami
takaicin cin aman ada yaudara da sukewa mamin
takaicin son dasa baqincikin da qunci na har abada da mutanen keson dasawa a zuciyar mamin
wannan cin amana da me tayi kama?,haka mutanen duniya suke
''bazan iya ba,bazan iya cin amanar mami ba ko duniua da abunda yake cikinta zaki bani''abunda ta iya fada kenan ta juya a guje zata bar sashen
''ke,dakata''mamin ta tsaidata,har ta iso gabanta ta kasa motsawa,cikin huci take dubanta
''rashin karbar tayi na yarinya daidai yake da tangal tangal da rayuwarki,arziqi na binki tsiya ta hanaki ki ganewa,kije....ko babu ke sai na cika burina,hanyoyin