Showing 45001 words to 48000 words out of 54547 words

Chapter 16 - Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel By ashwarmediahausa.txt

16 Jul 2026

87

wahale Yace "ina gida, apart din Baki".
Ajiyar zuciya ta sauke tace "yaya plz stay calm, i cnt sleep idan banzo naga condition dinka ba, am coming right away" katse wayan tayi da sauri ta suri Hijab dinta tadau mukullin mota ta fita dakin, mutane sosai tagani palo anata hira, ta kitchen tabi ta fita waje batare da kowa yaganta ba. Mota ta shiga taja tabar gidan at 360.

Dariya sosai Mujahid yayi bayan sun gama wayan, zaune yake shida wasu cousin dinsa guda biyu a palon bak'i, duk wayar da yayi da Salma a speaker yasan ya suka ji komai.
Dayan mai suna Khaleel yace "Mjay kaci saa yarinyar nan na bala'in sonka, jifa yadda ta rud'e, dama nice nasamu Babe haka" dariya sosai yake yana maganar.
Murmushi Mujahid yayi yace "nima ina bala'in sonta, i cnt live without her, she is my everything but some scores have to be settle, Salma ta mugun wahalar dani ba kadan ba"
Harara Dayan mai Suna Abdul yamai yace "miye amfanin settling scores tunda nan da 3 dayx she is all yours, koma dai miye ka barta kawai"
Mujahid yace "aiko mi nayi mata bazata ji haushi na ba, she is madly inlove with me"
Dariya Khaleel yace "babaa wai wana irin wahala kake nufi tabaka?
Mikewa Mujahid yayi yace ina zuwa" fita yayi can bakin gate yayi magana da mai gadi sannan kuma ya dawo palon ya zauna. Labarin tun farkon haduwan su da Salma yafara basu, jifa jifa kuma yakan kalli wayarsa.

Salma na isowa Gidan wani mugun Horn tahau yi, da sauri mai gadi ya bude mata ta cilla motar ciki da sauri tayi parking ta fito... Sauri sauri, gudu gudu tayi tafara karasawa part din Baki dake can nesa da main house, takusa daf da gurin taji ana kyalkyalewa da dariya, tsoro ne yakamata tafara takawa da sauri, daidai bakin Kofar taji Muryar Mujahid na magana cikin dariya, gabanta ne ya fadi ta daskare gurin ba tare data iya kwakwaran motsi ba.

Cikin dariya Mujahid yace "kasan most funniest part of the story, bayan munyi plan da abokina nayi kissing dinta still bata bada kai ba, saida nayi fooling dinta na aika wasu Maza sukamin Duka atiti sannan fah ta waiwayeni"
Khaleel yace "gaskia kayi fooling dinta dayawa, ni yaushe zan yadda nasha duka abanza"
Mujahid yace "bayan ta fara kulani i had to pretend loving her duk dan na shuka mata rashin mutunci, kuma nasan itace same Ummi da Hajiya ta isheni saina nemo, niku kuwa na share naki nunawa Hajiya nasan wata Ummi. The next tin kawai naganta a gidan nan, kasan kuma miya faru ?
Haushi ne yakama Abdul, Khaleel kam dama player ne, kuma dadin labarin yake ji yace "what next ?
Mujahid yace "Could you imagine, yarinyar nan tasamin attarugu a shower gel dina, nikuma arashin sani nayi using, ranar ko i felt like strangling her to death"
Dariya sosai Khaleel yakeyi, abu sai kace a film, yace "Mjay gaskia ka wahalu, ya kayi kuma?
K'wafa Mujahid yayi yace "ya kuwa nayi, fooling dinta bashi da wuya, tricking dinta nayi into biliving ina sonta, ita kuma tayi saurin bada kai as usual .."
Khaleel yace "amma fa Salma ta hadu, koba laifi zaka huta da jikinta.."

Kaaa cigaba da Sauraro Salma tayi, hannu tasa kan kunnuwan ta tana fadin "innalillahi wa Inna'ilaihi rajun" hawayan Bakin Ciki data jima basu zubo mata ba suka hau ambaliya a fuskar ta, kuka sosai take tafara ja dabaya tayi tuntube tafadi kasa, ihu ta saki cike da tashin hankali.

Jin ihun Salma yasa Mujahid mikewa akidime ya fito waje, ganinta yayi zaune kasa tana rusa kukan daya jima yanason Ganin hawayanta. Da sauri ya karasa gareta yana fadin "Habibty yaushe kika zo ?
Wani sabon kuka tafashe dashi, jin sabon yaudarar dayake shirin yi mata, mikewa tayi tsaye tana kallon yadda duk ya gigice, rikota yayi cike da kulawa, wani irin feeling yaji ya ratsa jikinsa, ga kamshi jikinta sai ratsa mai gabobin jikinsa yake gabadaya.
Murya kasa kasa yace "sweetheart mi aka mike, plz stop crying, your tears are breaking my heart" janyota yayi zai rungumeta tasa hannu da karfi ta turesa baya.
Cikin kuka ta nuna shi da yatsa tace "dont you dare lay your filthy hands on my body, banza macuci, dan iskA, Allah ya isa tsakani na dakai, i hate you..", kuka sosai ya kufce mata, rike kanta tayi dake mugun sara mata lokaci gudu.
Hankalin Mujahid ne yatashi baiyi tunanin Salma zata dau komai da zafi ba ayadda takeson shi.
Matsowa yayi kusa da ita tayi saurin ja baya, kaman zaiyi kuka yace "plz forgive me, i was only joking, nasan kinji komai wlh ina sonki Salma"
Wani mugun tsanan shine taji ya diru azuciyan ta, she has never been humiliated like this in her life, kuka sosai take cike da tausayin kanta, tarasa miyasa Mutane biyu nan Abbanta da Mujahid datafiso arayuwan ta suka fi kowa kuntata mata. Innalilahi kawai take ambata aranta.
Kallon shi tayi tace "ko kana sona ko baka sona i dont give a fucking damm about it, cox ko kaine autan maza na hakura dakai, na gwamma ce na kashe kaina akan na aureka balle na zauna dakai" sautin kukan tane ya karu ta juya da gudu ta koma gurin motar ta, binta yayi shima da gudu yana kiranta, bata saurare sa tashige motar taja ta wuce ta gabansa wanda kiris ya rage bata kwashe saba, bai damu ba yabi motar da gudu amma tuni ta fice daga gate din.
Hannu Mujahid ya daura akai cike da tashin hankali yace "Am died...
Muryan Abdul yaji abayan shi yace "in life you rather learn leason the easy way or the hard way, da dukkan alamun i don't think she will ever accept you back".

Kuka Mujahid yahau yi cike da haushi abunda ya shirya dan rama abunda tamai, gashi komai ya fado kanshi.
[9/7, 12:38 AM] Xarah Bukar: ​​Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION {NWA}

Allahu akbar kulu'nafsi za'ikatu mauti, Allah yaji kanki da rahma Maman besty Yar ficika. May jannatul Firdausi be ur final destination.


63

Daran ranar Mujahid bai samu rintsawar arziki ba, ta b'angaran Salma kuwa bata san duniyar da take ciki ba, Salim kam yafi kowa farin ciki ranar, kodaya koma gida kwanciyar sa yayi yana hagon yadda rayuwarsa zata kasance tare da abun kaunar sa.

Washe gari babu wanda ya lura da Salma bata gidan, sai kuwan azahar da Kulchumi mai gyara mata jiki ta shiga dakinta yi mata wanka turare, wayam tagani babu alamun Salma tayi kwanan dakin, bandakin ta leka bata nan ta fice da azama ta fad'i ma Momy rashin ganinta. Ran Momy ne yabaci, shiga d'akin tayi dan tabbatar da zancen kulchumi, mamakine ya kamata gasgata zancen, da sauri tahau kiran nambar salma da wayar dake hannuta, ringing take bamu mai dauka.
Fitowa tayi waje ta hangi motar Salma a parke, mamakone ya kuma kamata toh ina salma ta shiga by this tym, karasawa tayi bakin motar hade da lekawa ciki ta hangi wayar Salma ajiye kan seat, bude motar tayi tadau wayar hade da duba dawa tayi waya last, sunan Mujahid tagani, ranta ne ya kuma b'acci, atunanin ta ko Salma na gidan su Mujahid, afusace ta koma cikin gida, batare da bata lokaci ba ta kira wasu yan'uwanta uku suka shiga mota zuwa gidan Hajiya.


Mujahid kam duk ya figi dare daya, tun yana jiran Salma tadau kiran wayarsa harya saduda ya zubawa wayarsa ido karshe yanke zuwa gidan su yayi Abdul ya hanashi da cewa ba lailai ne ta saurare shi balle yanzu da gidan ke cike ana hidimar buki, kumai ai Salma bata fasa auran saba tunda har yanzu basu ji bayanin komai daga bakin hajiya ba. Da wannan kalaman Mujahid yadan ji sanyi aranshi.

Annah baki har kunne, Jallabiyo yi ne matsu tsada gabanta tana zaban nasawa yau adaran Arabian nights, dakin makil yake da wasu yan jikokonta da yan'uwan ta, sai zolayar ta suke tana masu tsiya, Hajiya ce ta shigo dakin adan birkice taja Annah suka fito haraban gida kasancewar ciki makil yake da bak'i yan buki.
Cike da kidima Momy tace "Annah kinga Salma gidan nan ?
Tsaki Annah taja tace "dalilin katsamin jin dadi kenan.
Mom tace "yanzu momyta ta kirani ta tambaye ni, nace mata bata nan, da alamun kuma ba lafiya ba"
Gaban Annah na yafadi, aranta fadi take "sabon tuggu kuma yaran nan suka kulla dan karna rakashe abukin nan, toh wlh baku isa ba"
Magana zatayi sukaga an bude gate motar su Momy ya shiga da gudu, parking tayi duk suka sauko fuskar su dauke da kunci.
Babu ko gaisuwa Momy ta dubi Hajiya tace "kun mamaki wlh, a tunanin na Salma bata da wata uwa data wuce ni shine zaku rabani da ita sannan kuma kice min ke baki ganta ba, kuma ni nasan tana gidan nan"
Tashin hankali ne ya mamaye Hajiya, nanta hau kokarin fahimtar Momy da kwatakwata ta kasa gamsu wa da kalaman ta, Annah kam binsu tayi da ido tana tunanin indai dagaske Salma guduwa tayi ko sace ta akayi ba lailane ayi buki budiri ba, itakam bazan lamunci a bata mata bojet ba ayadda ta shirya juya mazauni wanga bukin. Kamar an tsikareta ta fashe da kuka hade da daura Hannu akai, duban ta su Momy sukayi adan tsorace.
Cikin kuka Annah tace "Kuyi hakuri duk laifi na na, nice na tura Salma Kano amso min may an in ciwon idona, batayi niyyan zuwa ba saida nace idan bata jeba zan hanata auran Mujahid, ba shiri ta kama hanya batare da bata lokaci ba" kuka sosai Annah ta kara fashewa dashi.
Ran Momy ya gama bacci, kasa magana tayi ta juya tace da yan'uwanta su tafi, yaukam taga matsayin ta gurin Salma da danginta.
Kirata Hajiya tayi ko kallan ta batai ba suka shiga mota yaja. Takaici ne yakamata Hajiya ta dubi Annah da har yanzu kuka take, kasa ce mata uffan tayi ta koma cikin gidan. Dariya Annah tayi tare da debo rawan shoki tana fadin "yo ina dalili kura da daukan kayan kare dashan bugu, ai baima yuyuwa ne dan ita baa ganta ba nasan halin hajiya sarai sai afasa bukin".


Da bacin rai su Momy suka komo Gida, gurin Daddy ta nufa ta tsara mai abunda ke faruwa, shikam baidau komai da zafi ba yace ba komai karta damu aci gabata kudanar da buki, inayaso ranar da Salman ta dawo shi yasan yadda zai nuna mata rashin kyautawar sanar dasu da batayi ba.
Jiki sabule Momy ta amince da hakan, ba yadda ta ita tunda shi daya kawo Salman ma baiji haushi ba.

****
Da daddare aka fara shirin Arabian night, su Mujahid kam suna zaune tare dasu Abdul harda Mubarak ba yazo, hirar su suke basu da damuwa banda Mujahid dayayi sukuku dashi, yasan ko karan hauka ne ya cize Salma bazata fito arabian nights ba, wayarta ya kuma latsawa kira tana ringing ba'a dauka ba, babban matsalan shi ma yarasa wa zai tunkara da maganar dan yasan duk wanda yaji maganar a iyayen saidai kuwa afasa auran..wata zuciyar tace miye zaka damu tunda kaji shuru kila ta hakura ayi auran, murmushi yayi zuciyar sa nagasgata masa hakan.

Arabian nyt kam yayi shagali da maana, su Junaina da Jafar ansha kyau, jamaa sai tambayan Salma suke ba kunya Annah ke dankaro karya, hajiya kam ba wata walwala tattare da ita, sam bataji dadin Abunda Annah tayi ba, ganin Mujahid bai tunkareta da zancen ba yasa bata cemai komai ba, shikam gogan baisan da wata tafiyar Salma Kano ba.

****
Bayan Kwana Biu.

Tun Ranar da Salim yakai Salma Gidan bai kara komawa ba gudun kar a zargeshi, saidai yadda yaga anata cigaba da hidimar buki yasa shi mamaki, dabara yayi ya kira momy yace zai karbi mukulli mota a hannun Salma, ita kam bata kawo komai aranta ba tacemai Salma na Kano.
Dadi yaji yafara kiciniyar hada mata passport dan guduwa da ita Ghana.

Tsoron Allah ne yakama Annah bayan an gama shagalgulan Buki, daurin aure ne kadai ya rage daza ai gobe, kullum tambayar ta ake ya labarin salma saidai tace mai magani bai gama hada magani ba, Hajiya kam taso tagano Annah karya take saidai rashin damuwan mujahid yasa tayi tunanin bakin su daya, da Yamma Annah ta fita zuwa bangaran dasu Mujahid suke, gabanta sa faduwa yake tana tsoron rashin Mutuncin zai mata, ta window ta hango su zaune da abokai suna ta hirar su tare dashi kaman babu abunda yafaru, tace "kai Mujahid fito muyi magana"
Dafe kai yayi cike da takaicin mai matan nan takeso, fitowa yayi yanai aika mata mugun kallo.
Kamar munafuka ta sinne kai tace "dama batun Salma ne, baa ganta ba nace nina aiketa kano dan kar acinye min shagali, yanzu kuma naga buduri ya k'are yasa na gayama"
Agigice yake kallon ta dan kuwa bai gane inda zancen ta ya dosa ba, "wana kano taje, bata gida ne? Ya jaho mata tambayoyin.
Tsurewa tayi tace "bansani ba, kaje ka nemo ta"
Zare ido yayi in shock yace "Annah ina take ?.
Kara tsurewa tayi tace bansani ba, bata jira cewar saba ta rugu gida da gudun dani kaina bansan yar tsohuwa ta iya ba.
Innalillahi Mujahid ke ambata, bai koma palon ba ya rugu gurin motar sa yabude ya shiga, mukullin na jiki ya kunna yaja yabar gidan.


Salma bata farka ba sai washegarin daya kaita da daddare, juyi tayi taji ta tim tafado kasan, arazane ta bude ido, wani mugun ciwon kai ke dawainiya da ita, dakyar ta mike tsaye tana karewa dakin kallo, kasa gane dakin tayi ta dafe hannu jikin bango ta fito palon, tsoro ne yakamata bata gane komai na gidan ba, wani mugun jiri taji ta fadi kasa sai bacci.
Saida tayi kusan 4 hours a gurin sannan ta kuma farkawa, so take ta tuna wasu abu amma takasa, data fara kokarin tunanin saita yanki jiki ta fadi sai bacci.
The next day ne ta kuma farkawa, da sauri ta mike koma toilet din dakin, ruwa ta kunna tasha sannan ta kirkiro wa kanta amai, saida tayi amai sosai sannan ta dawo hayyacin ta abubuwa suka dawo mata, ya Salim ta fara ayyanawa aranta, wana mugun magani ne haka yabata daga ciwon kai, ita bataji saukin ciwo ba sai hallaka da magani yasoyi, tasan kuma shi kawo ta gidan, ranta ne ta baci ta mike wani jiri ya kuma dibarta, saurin dafe bango tayi, ga wata uwar yunwa nacinta, adaddafe ta fito kofar palo taji kofar a rufe kasa jure tsayuwa tayi ta rarrafa zuwa kitchen, komai na abinci akwai, tea na ruwan sanyi kadai ta iya hadawa tasha ta kuma rararfa zuwa dakin.
Sai sannan tahau neman wayarta ta tuna a mota ta barta, kwaciya tayi akasa tana tuna Betrayal din Mujahid bata sanda kuka ya kufce mata ba, agogon shi dake hannuta ta duba taga karfe biyar na yamma. Mikewa tayi ta koma toilet, dakyar ta iya watsa ruwa tayo alwala tamai da night wear din jikinta da hijab dinta tahau rama sallolin dabata yiba. Bayan ta ida ne kuma wani mugun baccin ya kuma sace ta.

Parking Salim yayi a haraban gidan ya fito rike da ledan abinci daya kawo mata, ahankali yasa mukulli ya bude kofar sannan ya shiga, kasa ya ganta kwance a dakin ta kudundune cikin Hijab, Murmushi yayi aranshi yace wato tayi kokarin yaki da maganin.
Sunan ta ya kira ta bude ido ahankali ta kallesa, bakin magana kawai take dashi amma babu wani karfi Tattare da ita.
"my love kin tashi" ya fada yana shafan fuskar ta, murya sanyaye tace "yaya why, miyasa zaka kawonin nan ?
Murmushi yayi ya dagota zaune suna fuskan tar juna, yace "Salma ina matuka sonki, bazan iya hakura ki auri mujahid ba, cox nafishi sonki"
Dakyar ta iya sakar mai harara, tace "miyasa kace ka fini sonshi
"Salma biliv me, akwai certain time danayi confronting mujahid akan ki nace mai kin zubar da cikina, inda yana sonki dagaske bazai nemi wulakanta ki ba harya yayi kokarin daura miki kisan daba ke kika aikata ba"
Kallon mamaki Salma tamai dajin shairin da yayi mata, amma toh yaushe akayi hakan Mujahid bai taba gayamata ba, wata zuciyar tace ba sonki yake ba tayaya zai gayamaki, Ajiyar zuciya ta sauke, tana son Mujahid bazata bari Salim ya nemi aibata saba.
Bata rai tayi tace "wanda kema son gaskia baya binka da shairi, no matter how bad Ya Mujahid yayi treating dina i still love him, kaga tashi ni kamaida ni gida"
Daura fuska Salim yayi yace "keda gida har abada, you're mine, Ghana zamu tafi gobe"
Mugun kallo tamai sannan ta mike tsaye da kyar tace "you're crazy, no wonder kayi drugging dina dan ka gudu dani, toh wlh baka isa ba" afusace tayi maganar, wucewa zatayi gefensa ya fizgo ta tafada cikinsa, matse ta yayi gam yana shakar kamshi jikinta, batasan sanda wani karfi yazo mata tasa hannu ta turesa hade da kai masa kyakyawan mari.

Kallon mamaki yayi mata sai kuma ya kwashe da dariya uwa tababbe, hannu yasa cikin aljihun sa yadauki wasu kwayoyi gudu biyar ya watsa a bakin sannan ta kalleta
"Ni kika mara ?
Harara takai mai.
"Dont you dare touch me, banza marar hankali"
Murmushi yayi hade da lasar labb'an bakin sa, ya karasa daf da ita ya shako wuyanta tare da hijab dinta, zare idanuwa tayi da already sun canza launi, magana take sonyi takasa tsananin yadda taga ya koma mata uwa zaki, harshen sa yakai kan fuskar ta yana lasa, da sauri tasa k'afarta ta ture sa hade da matsawa, yawu ta hada abakin sannan ta tofa mai a fuska tace,
"wanna ba so bane, rashin hankali ne" akufule yace ni kika tofawa yawu ?" Ba tsoro tace "eh kai din, niba kare bace da zaka na lasar min fuska."



Haushi da takaici ya cika sa, ya tako gabanta tare da bata k'akk'aywan mari guda biyu a fuska, ihu ta sakani dan azaba, bakinta ya fashe yana zubda jini, yace "zan nuna miki kare ya fiki daraja"
Daukar ta yayi tsam ya wurga ta kan gado.

Ihu take tana kiciniyar kwace kanta, shikam ko kallon baiyi ya yage wuyan hijab din ya cire, danne mata hannuwa yayi yahau kai mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login