Showing 21001 words to 24000 words out of 54547 words
Chapter 8 - Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel By ashwarmediahausa.txt
ba ta kawar da tunanin kasancewar taje gidan shi kuma bata ga alamu yana da yan'uwa ba.
Shuru ne ya ratsa tsakanin su har taxi ya iso gidan su.
Kallon shi tayi, gabadaya baya cikin hankalinsa, tabosa tayi, adan firgice ya kalleta, murmushi tayi tace "kana da abun dariya, kodai dukan yafara tab'a kane.."
Murmushin k'asaita yayi, irin wanda yake fizgar zuciyar wanda aka yiwa.
Yace
"Kije ki huta, i'll call you later"
Okay, bye ta fada ta fice a mota.
Gobe Birthday na 👯👯👯👯👯👯💃🏿
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: : Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkar
41- 43
Gidan su fa'iza ya wuce amsan motarsa. Isketa ta yayi tsaye haraban gidan jingine bisa motar. Da ganin sa tahau cika da batsewa, cikin koya kula da yanayin ta yace tabashin mukullin. Kaman zatayi kuka tace "Mjay miyasa zaka min haka gaban yarinyar nan, shikenan ta gama raina ni yanzu gani zatayi daidai nake da ita tunda kana kulata"
Kallon takaici yayi mata.
"Keda ita ba d'aya bane, you're my friend ita kuma she is nothing.."
Cikin rashin gamsuwa da kalamansa ta tab'e.
"ban yadda ba saboda dazu kallon da kake mata baiyi kama da babu komai ba, kuma na tabbata ka fara sonta"
Murmushi gefen baki ya saki wanda shi kadau yasan manufarsa, yace "tabbas na kamu da sonta saidai son da nake mata baikai na kasance tare da ita ba, kin dauka zan barta taci bulus ne bayan tamin rashin mutunci "
Nisawa Faiza tayi, aranta batai na"am da koma mai yake niyyan yiba, tunda har ya furta yana sonta ba lailai ne ya rama abunda zaiyi ba
"What are you planning ?
Girziga kai yayi yace "i dont know yet, ina dai tunani gagarinmin abunda zanyi na koya mata hankali, so nake tayi kuka da idanta"
"Daganan kuma saika rabu da ita kenan ? Faiza ta fadi.
Tsaki yaja
"Kinga enough of your questions, you're just a friend banaso ki wuce limit dinki" ya fada, amshe mukulli hannuta yayi ya fada motar yaja ya barta nan tsaye baki sake cike da takaici.
Salma na shiga Gida daki ta wuce ta kwanta, zuciyar ta fal da farin ciki, tunanin Mujahid take tana tuna farkon haduwa su izuwa yau, kwata kwata takasa gane kanta, shin sonshi take komi, kullum dashi take kwana ta tashi, girgiza kai tayi, sam babu lissafi soyayya aranta, bata tab'a yi ba saidai na baya data gani sun wahalu daga karshe ma tsana ce ta biyo baya shiyasa take bala'in tsoron fadawa soyayyar wani. Tana son Mujahid amma bazata nuna mai komai ba ayanxu har saida tabbatar he won't break her heart.
****
Tun daga ranar lamari ya canza tsakanin su, soyayya da kulawa sosai Mujahid yake nunawa Salma saida bai fito yace yana sonta ba, har ilah yau bai kuma canza kudurin sa na koya mata hankali ba, ta bangaran Salma kuwa zuciya daya take zaune dashi takan yi mamaki sai kace ba kwanakin baya suke casa juna ba, aranta takanyi tunanin anya kuwa Mujahid baida wani mugun nufin akanta, saurin kawar da tunanin take saboda tsananin yadda yake damuwa da lamarinta.
Daddyn Salma ne tare da Ja'afar a office dinsa. ja'afar yana daya daga cikin lauyoyi da Alhaji Abbas ya aminta saboda tsananin rike gaskia da Tsoron Allah da yake azuciyarsa, sau tari yawan idan zaiyi harkar canji da dollars ko euro yafi yadda da damk'awa jaafar takardun shaidan komai dan yasan bazai cucu saba.
Zaune suka suna magana akan wani fili daya siya a Kaduna, copy na takardu shaida da komai ya mikewa Jaafar, karba yayi yana dubansu
Daddy yace "ka adana su da sauran"
Hade takardun jaafar yayi cikin briefcase nasa sannan ya mike da niyan yimai sallama, dakatar dashi Daddy yayi hade da cewa "ya maganar mu ta kwanaki, naji shuru baka kara waiwayar zancen ba.."
Zama jaafar yayi had'e da kirkiro murmushi dole, shikam yama manta da zancen, shuru yayi yana tunanin zancen da neman amsar bawa Daddy, bazai yaudari zuciyan saba dan kuwa yana son Junaina, saidai kuma ba damuwa tayi dashi ba ga kuma Daddy da yakeson ya hada shi da Diyar shi dako sanin ta bai yiba balle ma yasota, shi kuma auran bayama cikin lissafinsa yanzu kokarin Nemo Ummi kawai yake dan farin cikin hajiyarsu kuma baima isa ya tunkareta da sunan yana son aure ba, ana takai wa yake ta kaya.
Ajiyar zuciya ya sauke yace "Alhaji wani hazari ba gudu ba, maizai hana mu hadu da diyar taka, idan ta amicin dani saina yadda karya zamana ko tana da wanda takeso"
Farin ciki sosai ya lulube Daddy, kasancewar ta bangaran Salma ba matsala koda batason Jaafar yasan zata mai biyayyah, kuma ma baiyi tunanin Salma nada wani da takeso ba.
yace "ba matsala, gobe kazo gidana mu kara tattaunawa saika ganta
Yake jaafar yayi aranshi yace "Allah yasa karta aminci, afili yace "saidai yau nazo, saboda gobe da safe ina da aiki a Kaduna"
"ba damuwa, Allah ya kaimu zuwa dare" acewar Daddy.
Godiya yama Daddy sannan sukai sallama ya fice azama.
Tun ranar da Hajiya ta kira Mujahid tace yazo gida bai samu daman zuwa ba sai rana ta yau acewarsa aiki yamai yawa bacin kuma da gangan yaki zuwa.
Fuska ba yabo ba fallasa Hajiya ta tarbeshi, nan tahau mai fadan barin sa gida akan abunda baikai ya kawo ba, Mujahid kam shuru yayi yana sauraran ta dan ya kagara ta gama ya wuce aikinsa, tace "Bani hotunan Ummi dana baka kwanakin baya"
Sosa keya yayi alamun marar gaskia yace "mi zaai dasu, an ganta ne ?
Hajiya tace " baa ganta ba, kawai hoton zaka bani tunda ba nemo ta zakayi ba, tuni Jaafar ya dukufa da nemo ta kuma am sure zai samota aduk inda take"
Ware ido Mujahid yayi adan kidime yace "jaafar zaki bawa hoton ?
Mugun kallo takai mai, tace "ko babu hoto Jaafar yasan fuskan ta, kaida ba saninta kayiba yasa na baka hoton"
Gabansa ne ya fadi, fatan shi Allah yasa kar Jaafar ya hadu da Salma, nisawa yayi yace "Hajiya basai jaafar ya nemo taba, nida kaina zan kawota gidan nan very soon."
"Ka ganta ne" Acewar ta.
Kai ya girgiza alamun a'a, aranshi yace "ki bani time very soon zaki ganta amma saina koya mata hankali yadda idan ta shigo gidannan bazata yadda ki had'ata aure da niba".
Tashi yayi ya mata sallman zai wuce office ya fice waje, nan suka hadu da Junaina ta dawo daga gidan wata kawarta dan tuni sun gama Neco.
"Yaya kyan tafiya dawowa" ta fada tana dariya.
Tabe baki yayi yace, "ce maki akayi nadawo"
"Oh Allah, he will never change, ni ina can ina missing dinshi amma koya kula dani" aranta tayi maganar, Afili tace "yaya akwai abunda nakeso kasani, sumtin is going on in this house"
Kallon gefe yayi babu mai dubansu sannan ya jata gefe danjin wana abu ke faruwa, sau tari dama ita ke kaima rohoton abubuwan dake faruwa agidan dan ba zama yake ba.
Murya kasa kasa tace "bansan full story dinba, naji dai Hajiya na Waya da Aunty Bilkisu akan wani abu, i dunno ko kudi ne ko gida ko kuma ince sumtin is missing i dont really know, naji Hajiya tace tunda kai kaki nemo wa idan ya jaafar ya nemo shi zata
bawa ta fasa baka"
Hankalin sane ya tashi danya gane inda Zancen ya dosa, saidai bazai bari Jaafar yaga Salma ba much less ya yadda da auran suba.
Dakewa yayi yace "little sis kinsan mi zakimin"
Kur tayi tana kallon shi, yace "inaso ki sawa Jaafar ido, idan kinji yana waya akan wata mace ko bincike ki bani feedback kinji"
Kai ta girgiza alamun toh, murmushi ya sakar mata. "yauwa my beautiful sister, you know i like you alot"
Dariya tayi tace "nidai yaya kadawo gida plz, wlh i missed you alot".
"Karki damu nakusa dawowa"
Dadi sosai taji, sun jima yana biyeta sai shagwaba take zuba mai daga bisani ya lallab'a ta ta tafi ya koma motarsa yaja yabar gidan.
Tuki yake yana neman mafitan yadda Jaafar bazai hadu da Salma ba, idan yayi sake kuwa yanaji yana gani zaiga Salma a gidansu, dabara ce ta fadowa mai yadau waya hade da dailing no din Salma.
Alokacin kuwa had'e book dinta Salma tayi cikin jakarta sannan tabar dakinta, gurin Mom ta shiga ta mata sallama ta fito cikin sauri, library na skull takesan zuwa karatu saboda jibi ne zasu fara exams.
Kokarin bude motar tayi taga kiransa, murmushi tayi ta dauka.
Daga can Bangaran cikin sweet voice dinshi yace "Angel of my life, son kowa kin wanda ya rasa"
Dariya tayi kasa kasa, tace "ka fara koh, how am i even sure am your angel"
Yace "believe me, ba karya nake ba, idan ma baki yadda ba God knows it.
"Kaga ni library zani, inada exam jibi, kana ina?
Yaji dadi abunda tace, aranshi yace "perfect, nasan abunda zanyi"
Afili yace "ina driving, ki jirani nazo nayi picking dinki saimuje inda babu wanda zai dameki dan kisamu kiyi karatu, nasan ki da tsokana kar kije kiyi dambe da mutane a library" karashe maganar yayi cikin zolaya.
Shagwabe fuska tayi kaman yana ganinta, tace "nifah bani da tsokana, ko dambe ban taba yibaaa.."
"Hmm, kedin, ki jirani am coming" katse call din yayi, ta fita can bakin gate jiran shi, baafi 20 mins ya karaso ta shiga motan ya kama hanyar office dinsa, tagane hanyar, tace "lailai ma office dinka ne bazaa dameni ba?
Wani shumin kallo yayi mata da saida taji shi a kwakwalwar kanta, murya kasa kasa yace "duk wanda ya dameki cikin cell zan wurga shi..
Ware ido tayi adan tsorace, "cikin cell sai kaca a film"
Dariya yayi bai kuma cewa komai ba ganin yadan tadan tsorata, suna isa parking yayi, suka fito suka shiga elevator har zuwa cikin office dinsa, ita batama san akwai elevator ba kasancewar ta stair security yabi da ita kwana kin baya.
Office din babba ne mai shegen kyau can gefe inda Couch da center table yake takarasa ta zauna shi kuma yA karasa gurin table dinsa ya zauna kan kujerar sa hade da fara aikin danna laptop din gabansa, sosai yaci serious da abunda yake batare daya dubi Salma ba.
Itakam abunda take so kenan, bude handout dinta tayi ta dukafa da karatun General studies da suke dashi.
Bayan kaman awanni uku Mubarak ya shigo office din, ganin Salma yasashi dariya, zama yayi gurin mujahid yana zolayar shi murya kasakasa, b'ata rai Mujahid yayi, yafara magana cikin fad'a, duk ahankali suke magana, Salma bataji komai ba kuma bata damu dason jiba, sund'an jima sannan Mubarak ya fice office din.
Gyaran murya yayi, Salma ta dubeshi
Yace "bani labarin samarin ki ?
Dariya tayi
"Banda saurayi, infact ni bana soyayya"
"Miyasa ?
Ajiye pen din hannuta tayi hade da yin tagumi, amaraice tace "Sanadin So Ummata tasha wahalan rayuwa, daga karshe ma Abbana ya rabu da ita da tsowon ciki, bansan lokacin ba, bansan anyi ba amma ayadda naji labari yadda komai ya faru yasa kwata kwata na cire so araina"
Kallon tausayi yayi mata, tunda yake gida bai tabaji labarin Ummanta abakin Hajiya ba, saidai zaiso sani..
Kaman wanda baisan da rasuwan Umman ba yace "ina umman take ?
Kaman zatayi kuka tace "ta rasu, lokacin daban santa ba, i was 3years old tym din".
Maida dubansa Mujahid yayi bisa laptop din yace "bai kamata ki cire so aranki ba, tunda iyayan ki daban ke daban"
"Hmm, am sacred banso ayi breaking heart dina"
Shuru Mujahid yayi baice komai ba, bayason cikata da surutu, bari yayi sai kuma gobe ya kara jeho mata wata tambayar.
Cigaba da karatun Salma tayi, lokaci Sallah azahar nayi ya nuna mata toilet dake office din sannan yafice zuwa masallaci, bayan ya dawo ya tura aka kawo wa salma abincin take away, godiya tayi.
Karfe bakwai Daddy ya dawo Gida, nan ya tsarawa Mom batun zuwan Jaafar, sosai taji dadi da batun daddy dan kuwa ta kagara Salma tayi aure ko zata nutsu, nan daddy ya shaida mata bayan Sallah Isha'i Jaafar zaizo ganin Salma, dadi sosai taji, wayarta tadauka dan kiran Salma.
Bayan Salma ta idar da sallar Magrib, Qur'an dake ajiye a office din tadau ta karanta sannan ta ijeye ta cigaba da karatunta, lokacin Mujahid yafita masallaci bai dawo ba, kirar Mom tagani tayi azaman dauka.
Aladab ce ta gaidata, Mom ta amsa sannan tace "Salma kibar duk abunda kike kidawo gidan yanzu nan, Daddy zai baki wani Surprise"
Farin ciki ne ya kamata, tace "momy miye ne, dan Allah gayamin i cnt wait saina zo"
Dariya momy tayi tace "idan kinason sani kizo maza yanzun nan, kuma kiyi sauri" katse call din Mom tayi, cike da Murna Salma tahau tattare books dinta ajaka, Mujahid ne ya shigo, ganin tana hade komai yace "keda kika ce sai 10 zamu tafi, kin fasa ne ?
"Eh nafasa, kaini Gida" cigaba tayi da hade komai zuciyar ta fal murna.
8.20 Jaafar ya iso gate din Gidan Daddy, bai tab'a zuwa gidan ba yasa yakira Daddy awaya dan tabbar da gidan ne, nan take Daddy ya kira mai gadi aka budewa mai gate ya shigo gidan, cikin palo gidan Daddy yamai iso, ya shiga yagaida Mom aladabce, sosai mom ta yaba da hankalin sa, sun gaisa sosai, mai aiki ta kawo mai na shasha baki, shikam Jaafar gaban sane keta faduwa, har yayi dana sanin kowa kanshi gidan.
Mom kam murmushi kawai take tana saurara isowan Salma....
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta
~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
®NWA
43 - 50
Murmusawa Mujahid yayi ganin yadda take cikin walwala. Table dinsa ya k'arasa yadau wayarsa tare da mukulin mota. Ficewa sukayi daga office suka nufi ma'ajiya motar, Salma na tafe tana waya da Mom, cikin sauri tayi gaba ta tsaya bakin motar. Wayar sace tayi ruri, ya duba yaga Junaina da kuma miss call datai mai wanda bai lura ba sai yanzu, tsaye yayi nan inda yake batare daya karasa inda Salman take ba ya dauka.
"Little sis ya ake ciki ?
Kaman munafuka Junaina tahau duben ko ina a palo gudun kar wani yajita, murya kasa kasa tace "yayA naga ya jafs ya fita, kuma naji yana waya da wani zaije ganin wata yarinya, i dont know wace yarinya ce"
"Yaushe ya fita ?..
"Yadan jima kuma bai cewa Hajiya Komai ba"
"Okay Sis, ki cigaba da samai ido, i'll call you later" katse call din yayi ya karasa motan suka shiga, sai sannan ya tambayi salma dalilin tafiyar ta, bata boye maiba ta fadi mai Mom ke kiranta kuma it urgent.
Shuru Mujahid yayi yana tunani anya ba gidansu Salma yaje ba, wata zuciyar tace it cnt be possible, miye zai kaishi gidan, saidai surprise da Mom zata bawa salma ne ya tsaya mai arai, zuciyar sam bata aminta da hakan ba, kuma baiji yana son tafiyar Salma ayanzuba. Kallonta yayi da gefe ido yaga tana latsar wayarta fuska ta dauke da murmushi..
Murmushi yayi sannan yaja wani wawan burki da saida ta tsorota, afirgice ta kalle shi, gani tayi ya daura kansa bisa steering hannusa dafe kan gefen cikinsa, murkutsutsu yahau yi tamkar wanda zai mutu.
Tsabar gigita bata san sanda takai hanunta bisa bayan saba tanai tambayarsa maike damunsa, kasa magana yayi banda cije labb'a da yake, fita tayi motan ta zagayo gurin sa. Tambayarsa ta kuma tayi, murya ciki ciki yace "am sick, can you drive ?
Kai ta gigiza alamun eh, taimaka mai tayi ya koma dayan sit din sannan ta shiga taja motar.
Kaman mai shirin kuka ta kalle shi, "wana asibiti zamu ?
"Kaini gida kawai" ya fada yana lumshe ido, shingidewa yayi akan sit kaman wani marar lapian gaskia.
Hankali tashe tahau driving ba tare data tuna kiran da Mom ke mata ba, suna isowa gidanshi ta taimaka mai suka shiga ciki ayayinda sai faman cemai sannu take, shikam dariya ke cinsa yana gimtsewa. Zaunar dashi tayi kan two sitter sannan ta dube shi, murya cike da tausayi tace "sannu yaya.."
Yi yayi tamkar baiji taba saima rufe ido dayayi, itakam tanason tafiya ga dare yafara lulawa, gyara zama tayi ta fuskan ceshi tanai karemai kallon aranta tanai kara jin sonshi. Sunkai 20mins ahaka kafin nan ya bude ido, suna kallan juna, lumshe ido yayi yace hado min tea nasha magani"
Ba musu ta mike ta shiga kitchen ta hado ta kawo mai, k'insha yayi ya ajiye akan yayimai zafi da yawa, zama tayi tanai jiran tea yayi sanyi tanason tafiya saidai bata iya barin sa cikin larura.
Har kafar Tara su Daddy da jaafar na zauna suna jiran salma, shuru babu labarinta, sau kusan hudu Daddy na kiran wayarta babu respond, ransa ne ya bacci, nan yahau tambayan Mom, cemai tayi skull ta shiga karatu saboda exams da zasu fara, jin shaanin karatu yasanya Daddy yayi calming down, dan yasan lokacin exam Salma bata wasa. shikam Jaafar dadi yaji, amma aransa mamaki yake ace yarinya har yanzu bata dawo ba, jinjina kai yayi "anya ta arziki ce kuwa" azuci yayi maganar.
Hira kadan suka tab"a Daddy yace mai yayi hakuri idan ya dawo daga tafiyar sai yadawo kafin nan diyarshi ta gama exams sai ayi magana, Jaafar kam bai damuba, gaba ta kaishi gobarar titi a Jos, san samu ma kar Daddy ya kuma mai zancen. Sallama yayi masu yabar gida.
Mujahid kuwa shiriritar da Salma yahau yi, bayan tea yayi sanyi k'insha yayi wai zaiyi amai, saida ta kuma had'amai Black tea sannan yadan sha kadan da maganin bayan tasha walaha da lallaba shi sannan ya iya shan pill na magani guda daya, acewarsa daci yayi yawa. Bayan nan kuma ta tashi da niyya tafiya ya langwabe da ciwon kai, saida ta tayi zaman kusan 30 minti tanai mai sannu.. Karshe dai saida yaga 11 tayi sannan ya koma normal, tace mai zata tafi dare yayi, ba kunya yace suje ya kaita gida, itakam mamaki ne ya kamata mutum sai kace mai aljanu, tunani tayi anya ba raina mata wayo yake ba. Haka dai tabishi suka shiga mota, sai janta yake da hira, kasa magana tayi tsananin yadda taganshi garau, wayarta ta duba