Showing 3001 words to 6000 words out of 24915 words

Chapter 2 - 'Ya 'Yan Miji Complete Hausa Novel

11 Jul 2025

1782

anan, Aisha ba bare bace itama 'yar gida ce don haka kar na kara jin makamanciyar magana irin wannan a bakinka, kai gaba dayanku ma hope you understand?", gaba daya suka ce "eh Mami". Bayan gama cin abincinsu ne suka koma daki, suna shiga Aisha ta hau tattare kayan Farid data zubar a kasa. "Ina za'a saka wadannan" tace wa Ummie, "kai mata toilet ki saka a cikin kwandon kayan wanki" ta amsata.
Da daddare ne Mami suna zaune da Daddy a sittingroom dinshi na sama take ce mishi "dazu Hajiya tazo har ta kawo mini yarinyar da zata na tayani aiki tace 'yar wata kanwartace data rasu shine ta dauko yarinyar, to ina tunanin a sakata a school maimakon zamanta a haka ko ya ka gani". Shiru yayai bai amsata ba, ita kam wannan hali na J.B sau tari yana bata mata rai don idan baiso ba duk maganar da zatayi ba amsawa yakeyi ba shine ma ya saka idan ta mishi magana taga bai amsata ba bata maimaitawa sai ta kyaleshi, don kanshi kuma idan yaso saibya dauko maganar.
Yanzun ma ganin bazai amsata bane yasa ta mike don taje tayi shirin barci. Har ta kai wurin kofa taji yana cewa "duk yanda kikayi daidai ne". Murmushi kawai tayi sannan tace "nagode bari naje nayi shirin kwanciya don barci nakeji, akwai abinda kake bukata?" Cikin ginshira yace "yeah, only you". Wata kasalalliyar dariya tayi sannan tace "hmm Daddy kenan" ta juya ta bar parlour cikin rangwada. Hannu yasa ya shafa kwantacciyar sumarshi yana mai lumshe ido, murmushi dauke a fuskarshi. Shi kam Allah ya sani yana son Zainab sosai, after all these years yana jinta a ranshi tamkar yau ya fara sonta. Tashi yayi shima ya nufi dakin din yayi shirin kwanciya.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

7
A haka dai rayuwa taci gaba da tafiya. Ga Aisha dai ta dada kame kanta daga shiga harkar Farida da Mu'azzam don ta lura akansu zaman gidan zai iya gagararta. Ita kuwa a yanda takejin dadin zama da Mami ga kuma ingantaccen ilimi duka biyu wato na addini da boko da take samu baza taso tayi abinda zai rabata da zaman gaidannan ba.
Ga kuma baby Ruqaiya da sukayi wata irin shakuwa da ita don mafi yawan lokuta idan tana wurin Aisha ko Mami bata yarda ta dauketa sai da kyar. To shima Daddy a nashi bangaren bai kara maganar mayar da ita gidan Hajiya ba, kodayake a yanzu duk fitinar Farida da neman rigimarta ta kyale Aisha ganin bata shiga harkarta.
A yanzu haka Aisha tana ss1 ne yayin dasu Ummie suke jss3. Tun zuwan Aisha gidan sau daya taje garinsu tayi hutu na sati uku. A wannan lokacin ma hutun take son zuwa sai dai kuma kasancewar ciki ne da Mami tsohi yasa dole ta hakura. Ko babu komai tana taimakawa Mami da hidimar gidan don zuwa wannan lokacin babu wani abu da bata iya ba a kitchen.
Mafi yawan lokuta zaka sameta ne a kitchen tare da Mami da sauran ma'aikatan gidan, abinda bazaki taba ganin Ummie ko Farida sunyi ba. Yanzu ma aikin abincin dare sukeyi ita da Mami a kitchen. Yaya Khalifa ne ya shigo kitchen din yace "sannu Mami, mezan samu wallahi na gaji da yawa ga yunwa na kwaso, yau tunda muka fara lectures tun 12 sai six muka gama without any interval".
"Sannu Yay Khalifa ai kana kokari wallahi Allah dai ya bada sa'a". "Amin Aisha nagode, me kukayi ne da rana? Yace bayan ya zauna akan kujerar kitchen din. "Favourite dinka ne wato faten doya bari na zuba maka" tace bayan ta dauki plate ta zuba mishi abincin sannan tace mishi "anan zakaci ne ko na kai maka parlour". "Bari kawai na wuce dashi Aisha nagode" yace yana mai tashi daga kan kujerar. Karbar abincin yayi ya fita a kitchen din. Bayan sun gama hada abincin ne Mami ta fita ta barta a kitchen din ta karasa gyarawa. Sosai take tausayawa Mami ganin duk da tsufan cikinta hakan bai hanata yin hidimar gidanta ba.
A daren ranar suna kwance suna bacci Mami ta shigo dakinsu ta tashi Aisha. "Lafiya Mami?" tace bayan ta tashi zaune. "Saka hijabinki ki taso asibiti zamuje" tace mata a yayin da take barin dakin. A hanzarce ta tashi ta daura zani akan kayan baccinta ta dora hijabi ta fita zuwa dakina Mami. Akwatin da Mami ta hada don zuwa asibiti ta dauka suka fita. Koda suka fita harabar gidan tuni Daddy ya juyo da mota, gidan gaba ta budewa Mami ta shiga sannan ta koma baya ta zauna.
A lokacin da suka isa asibitin karfe daya da rabi ne na dare. Suna zuwa direct labour room aka wuce da Mami, su kuma suka samu wuri anan rwception din suka zauna. Nesa sosai da Daddy Aisha ta zauna, duk sai tana jinta a takure don ita dai hakanan take jin tsoron Daddy bata taba sakewa dashi ba shima kuma bai taba sakar mata fuska ba tsakaninta dashi gaisuwa ce kawai.
Basuyi zaman awa daya ba a wurin nurse ta fito ta fada musu Mami ta haihu diya mace. Gaba daya annurin farinciki ne ya sauka a fuskar Daddy, mamaki ne ya kama Aisha don kuwa bata taba ganin fara'arshi haka ba. Ba'a wani jima sosai ba aka fito da Mami da babynta zuwa wani dakin. Bin bayansu sukayi zuwa dakin da aka kwantar da ita. Daddy na rike da baby sai faman fara'a yakeyi yana ce mata "sannu Zainab", ya dade a asibitin kafin yayi sallama da Mami ya tafi gida don a lokacin kausan karfe uku da rabi ne na dare. Daga Mami har Aisha basu wani samu yin barci ba saboda baby bata barsu ba. Sauki daya suka samu ma shine da safe da likita yazo ya dubasu ya basu sallama. Anyi sallamar babu dadewa Daddy ya shigo dakin hannunshi rike da kwandon kayan abinci. Da sauri Aisha ta tashi ta karbi kwandon a hannunshi sannanta gaisheshi. Yana amsawa ya karasa kan gadon ya zauna yana yiwa Mami sannu tare da amsar baby a hannunta. Breakfast kawai sukayi suka koma gida kasancewar anyi discharging dinsu tun kafin zuwan Daddy. Da isarsu gida yaran gaba daya suka fito suna ihun Murna. Rige-rigen karbar baby sukeyi, Mu'azzam ne ya karbi babyn a hannun Aisha ita kuma ta fito da kayansu suka shiga cikin gidan. Cikin kankanin lokaci gidan ya cika da baki 'yan barka don haka nema hutun da Aisha take bukata bata sameshi ba saboda hidima da tayi mata yawa.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

6
Washegari suna kan table suna breakfast Daddy ya sauko daga sama a bayanshi Mami ce rike da briefcase dinshi. Kujera taja mishi ya zauna sannan taja kujerar dake gefen damanshi ta zauna. Yaran duka suka gaisheshi ya amsasu cikin kulawa. Itama Aisha gaisheshi tayi tana mai tsugunawa. "Lafiya" kawai yace ya cigaba da magana da yaranshi. Gaba daya sai taji ta muzanta, anya kuwa maigidan yana maraba da zamanta cikin iyalinshi. Duk sai taji abincin ma ya fita daga ranta. A haka dai ta daure ta tuttura. Bayan kowa ya gama ne suka tashi suka fita, yaran suka tafi school shi kuma Daddy ya tafi office. Ya rage daga Aisha sai Mami sai ko baby Ruqaiya. "Mami kawota" Aisha tace tana mai mikawa hannu don karbar Ruqaiya. A baya ta sakata ta goya sannan ta haya sama ta nufi dakinsu ta hau gyarawa. Kayan Farida ne duk a barbaje a tsakar dakin ga alama dai Farida bata san ta cire kaya ta adanasu ba. Daga zuwanta jiya zuwa yau ta lura Farida sakaltacciyar yarinya ce saki yayi mata yawa.
Bayan ta gama gyaran dakinsu ne ta shiga dakin Mami don ta gyara. Nan kam a gyare yake tsaf don haka juyawa kawai tayi ta sauka kasa. A parlour ta iske Mami tana kallon the doctors a mbc4. "Sannu Mami" tace a yayin da take zama a kasa. "Yauwa sannu Aisha, me yasa kike son zama a kasa ne, tashi ki koma kan kujera", tashi tayi ta zauna akan kujerar. Mami tace mata "su Ummie sun tafi makaranta sun barki ko, kema inaso ki fara zuwa ina fata daikin fara karatu acan garinku". Tace "eh Mami na fara ina jss2 yanzu haka". Mami tace "Masha Allah, akwai wata makaranta a kasan layinnan zanje na duba In Sha Allahu zuwa wani satin zaki fara zuwa". Durkusawa tayi tace "nagode Mami Allah ya saka da alkhairi".
Dariya Mami tayi tace "tashi da Allah daga durkuson nan, baki daukeni uwa har yanzu ko, miye abin godiyar to ai dolenmu ne muyi miki hidima tunda dai ke amana ce a hannunmu. Jeki kwantar da Ruqaiya sai kizo mu shiga kitchen ki tayani girki ko".
A cikin satin aka gama yiwa Aisha komai na makaranta anan wata private school dake cikin unguwar sun dauketa a jss2 din da take kasancewar sun gwadata sunga tana da kokari sai dai rashin samun ingantaccen ilimi yasa turancinta yake da rauni, ganin haka nema yasa Mami ta shirya da malamarsu ta english zatana yi mata lesson akan turancin. Duk da makaranta da Aisha ta fara zuwa, wannan baisa ta daina yiwa Mami hidimar da takeyi mata ba kamar gyaran dakinta da nasu dakin da kuma wankin kayan Ruqaiya. Hakanan kuma rainon Ruqaiya na cikin aikinta idan ta dawo daga makaranta.
Sosai Mami take jin dadin zama da Aisha don kuwa yarinyar bata da kyuiya duk abinda ta sakata shi takeyi. Itama kuma Aisha tana jin dadin zamanta da Mami don kuwa Mami mutum ce mai alkhairi da kuma son mutane, gashi kuma a komai bata yin bambanci tsakaninta dasu Ummie da suke 'ya'yanta komai tayi musu itama shi takeyi mata. Ko tana da matsala a zamanta a gidan to da Farida nel data takura mata ta hanata sakat don ko wasa sukeyi da Ummie idan tazo wurin to ta barshi. Sai ko Mu'azzam shima yana takura mata amma ba kamar Farida ba, shi kam Yaya Khalifa babu ruwanshi don baya na shiga harkarsu.
A yammacin wata lahadi ne bayan malamin dake yi musu karatun islamiyya ya tafi ne suka nufi filin wasansu. Kowa da kalar wasan da yake yi, Ummie da Aisha dai lilo suka hau Ummie tana tura Aisha. Farida da Mu'azzam kuma wasan guje-guje sukeyi. Abin tsautsayi Ummie tana shilla Aisha ne ita kuma Farida ta taho a guje Mu'azzam na binta kawai tayi karo da kafar Aisha ta hantsila ta fasa hanci.
Wata irin razananniyar kara ta saka. A guje duk sukayi wurinta suna mata sannu ganin yadda jini yake fita daga hancinta duk sai suka rude. Gaba daya suka nufi cikin gidan in banda ihu babu abinda Farida takeyi. A rude Mami ta taso tana tambayarsu lafiya. Mu'azzam ne yace yana mai nuna Aisha "gatanan itace ta hankadata ta fadi ta fasa hanci". Cikin daga murya Ummie tace "laa bafa haka akayi ba, Mami ina tura Aisha ne a lilo su kuma suna wasan guje-guje sukayi karo da Aisha ta fadi ta fasa hanci", "ke yi mini shiru da bakya magana a hankali" tace da Ummie. "kai kuma matsa ka bani wuri naje na wanke mata ciwon, ai duk laifinkane don kuwa na hanaku wasan guje-guje amma bakwa ji".
Mami taja Farida zuwa bathroom ta wanke mata jinin daya bata mata fuskar sannan ta bata paracetamol tace ta kwanta ta huta. A ranar kam da Daddy ya dawo ya tarar da abinda ya faru yayi fada kamar me har yana cewa Mami shifa idan rikon bazai yiwu ba sai a maida Aisha gidan Hajiya din bazai lamunci ganganci akan yaranshi ba. Shi Daddy wani irin mutum ne mai son yaranshi hakanan baya son wani ya rabeshi, ko rikon Aishacma abinda yasa baiyi magana ba saboda Hajiyarahi ce ta kawota gidan amma da babu abinda zai sa ya karbeta. Ita dai Mami hakuri kawai take bashi don kuwa tana matukar jin dadin zama da yarinyar.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

8
Tun bayan da Mami ta haihu gidansu bai rabu da jama'a ba. Don Aisha ma ko makaranta bata samun zuwa saboda hidima da tayi mata yawa. Ga aikin jego ga kuma hidimar Ruqaiya da kacokam ta dawo hannunta.
A ranar da akayi kwana biyar ne da haihuwar da safe Aisha na zaune a dakin Mami tana shirya kayan baby data wanke Mami ta shigo cikin dakin dauke da baby. Kwantar da ita tayi akan gado sannan tace da Aisha "idan kin gama shirya kayan kawo mini kunu sai kizo ki janyo mini wancan akwatin". Bayan ta gama shirya kayan ne taje kitchen ta damowa Mami kunun gyada sannan ta kawo mata. Akwatin data ce ta janyo mata tare da budewa ta fito da kayan ciki. Laces ne guda uku sai atamfar super holland guda hudu da voiles guda uku. Mami tace "miko mini na gani" tashi tayi ta mika mata kayan. Dagawa Mami tayi ta kalla sannan tace "wai nan kayan fitar suna ne Daddy ya mini sai kace wata yarinya, nikam ai na gaya mishi babu wani taron suna da zanyi".
Aisha ta kara daga kayan ta kalla sannan tace "ai kuwa dai Mami kayan sunyi kyau, Allah ya sakawa Daddy da alkhairi, amma Mami meyasa bazakiyi taron suna ba". Dariya Mami tayi tace "kayya Aisha taron suna ai na yara ne, haihuwa ta biyar ni kuwa wani suna zanyi, don wani abu irin na Daddy ma wai baby sunana ya saka mata nayi-nayi dashi ya saka sunan Hajiya yace a'a".
Cikin fara'a sosai Aisha tace "Allah ya rayata, kuma Mami me za'ace mata?" "Zainab dinta zaku kirata don banason boye sunannan" a cewar Mami. "Ina Ruqaiya ne duk yau ban ganta ba" Mami ta tambayeta. "Tana wurin Lami tun bayan dana mata wanka ta dauketa ta goyata to inaga bacci takeyi tunda kikaga shiru bata kawo taba". Aisha ta amsa mata.
A ranar suna ne baby taci sunan Mami wato Zainab. Kasancewar Mami ba taro takeyi yasa gidan bai cika da mutane ba amma duk da haka 'yanuwa na jiki duk sunzo don haka aiki yayi wa Aisha da sauran ma'aikatan yawa don sai faman dora abinci sukeyi suna saukewa. Ita dai Aisha har ta matsu dare yayi ko ta samu ta kwanta ta huta.
Bayan suna ne da kwana biyu suna zaune a parlour gaba gayansu yaran gidan suna hira Mami kece mata idan anyi hutu sai ta shirya taje garinsu ta kwana biyu. Sosai taji dadi sai dai kuma tana tunanin udan har ta tafi yadda hidima zatayiwa Mami yawa, bata dai yi magana ba don kuwa tana kewar Babanta zataso taje ta ganshi.
Murmushi tayi sannan tace "to Mami nagode Allah ya kara girma". Kallonta Ummie tayi sannan tace "umh Aunty Aisha sai murna kikeyi zaki tafi ki barmu ko tausayinmu bakya ji bayan kinsan zamuyi missing dinki sosai". Tsaki Farida tayi hade da tabe baki tace "kedai zakiyi missing dinta nikam da zamanta da rashinshi duk daya ne a wurina don rayuwata nakeyi tamkar babu ita a cikin gidannan".
Murmushi kawai Aisha tayi ta dauke kai. Ita dai ta rasa abinda ta tsarewa Farida a cikin gidannan don ko magana idan har ba ita tayi mata ba batayi mata shima kuma ba lallai ne ta amsa ba. Wannan kuma baisa ta daina yi mata magana ba koda kuwa kullum ta mata bazata amsa ba.
Tun bayan da Mami tayi mata maganar zuwa gida ta fara shiri don ta fitar dakayanta da yawa da zata bayar a garinsu wa 'yanuwanta haka ma kuma Mami ta hada mata kayan bayarwa nabyara da yawa da zata rabar acan. A daren da zata tafi ne tana zaune a tsakar dakinsu tana shirya kayanta a cikin akwati Mami ta shigo hannunta rike da bakar kedar viva. Zama tayi a bakin gadon sannan ta mika mata ledar , jarba tayi tana kallon Mami da alamar tambaya a fuskarta. " Na Babanki ne da kuma goggonki wato matar Babanki ga kuma wannan ki kaiwa babanki inji Daddy sai kije kiyi mishi godiya" ta mika mata envelope.
Russunawa tayi hadi da karbar envelope din tace "nagode Mami Allah ya saka da alkhairi ya kara budi". Bayan data gama hada kayan ne ta nufi parlour Daddy don tayi mishi godiyar alkhairin daya yiwa mahaifinta. Daga bakin kofa ta tsaya tayi sallama, sai bayan an amsa ne tare da bata izinin shiga sannan ta shiga. Durkusawa tayi ta gaisheshi sannan ta mishi godiya ta tashi ta fita. Ruqaiya dake wasa a parlour ta taso ta biyota tana rigimar sai ta goyata. A daren ranar dai baccin Aisha rabi da rabi ne don dokin zataje taga Babanta.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

9
Tun bayan da Aisha tayi sallar asuba sai bata koma bacci ba sai ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfar mediym holland dinkin riga da zanu. Koda ta shirya sai ta hau gyaran gidan inda duk tasan ita ke gyarawa. Bayan ta gama ne ta shiga dakin Mami. Bata sameta a dakin ba don haka sai ta shiga gyaran dakin. Tana cikin yin shara ne Mami ta fito daga bandakin ga dukkan alamu wanka tayi.
"A'a Aisha har kin shirya" tace a lokacin da take zama a kan stool din dressing mirror. "Eh Mami, ina kwana" "lafiya lau, kin ma kuwa yi bacci irin wannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login