Showing 15001 words to 18000 words out of 24915 words

Chapter 6 - 'Ya 'Yan Miji Complete Hausa Novel

11 Jul 2025

1783

lallai ne ya ci ba yasa tace tayi shinkafar don tasan baya cin abincin masu aiki.



Ya shigo gidan ne wajen karfe bakwai da rabi. Bai tarar da kowa ba a parlour kasa don haka ya wuce sama maybe kuma suna dakunansu. Dakinshi ya wuce, sai da yayi wanka yayi Sallah sannan ya fito don yaci abinci. Zuciyarshi fal da tunani Aisha yana mamakin abinda ya hana ta zuwa yi misgi sannu da zuwa. A take maganr da Farida tayi mishi jiya ta fado mishi a rai.



Baiyi wata-wata ba ya nufi dakinta don ganin lafiya. Tunda taje gidanshi a matsayin matarshi bai taba shiga dakinta ba sai yau. Tana kwance a kudundune cikin quilt. Da sallam a bakinshi ya shiga sai dai ganinta a kwance ta lulluba har kanta yasa bai san lokacin da ya karasa gaban gadon ba yana cewa "lafiya Aisha kika kudundune cikin bargo a zafinnan gashi ko fanka ko ac baki kunna ba".



Jin muryarshi ne yasa ta yaye rufarta bude idonta da suka kada suka yi jawur. Tsikar jikinshi ce yaji ta tashi hada idon da sukayi. Zama yayi a bakin gadon sannanyace "baki da lafiya ne, tun yaushe ne bakida lafiya" ya tambayeta yana mai kai hannu jikinta.



Da sauri ya janye hannunshi jin yadda jikinta yayi zafi. "Bari na canja kaya sai muje asibiti" yace a yayin da ya mike daga kan gadon. Baifi minti biyar da fita ba ya dawo yana sanye da shadda getzner kalar light brown dinkin tazarce.



Bargon ya janye sannan ya saka hannu ya dagota. Zaunar da ita yayi ya janyo hijabinta dake ajiye akan sallaya ya saka mata ya mika mata takalmi ta saka ya mikar da ita.



Tana rungume a jikinshi suka fita. Har sai da ya zaunar da ita a cikin mota sannan ya zagaya ya shiga ya tashi motar suka fice. Asibitin da suke da family folder suka je.



Ba wani bata lokaci suka sami ganin likita. Tambayr ta yayi abinda ke damunta tace mishi zazzabi ne sai jiri da take fama dashi sai kuma tashin zuciya. Test ya rubuta ta malaria da kuma ptegnancy test yace suje lab ayi yanzu su kawo mishi.



Bayan sunje sunyitest dinne sun kawo mishi result din ya duba yace "its as i suspected she's 12 wks pregnant sai dai kuma akwai malaria a jikinta. Wani irin farinciki ne ya ziyarci Daddy jin cewar zai samu Baby.



Gaba daya fuskarshi ta cika da annuri har mamaki ya dinga bawa Aisha don bata taba ganinshi a cikin farinciki kwatankwacin wannan ba. Bayan sun karbi magungunanta ne suka tashi suka tafi.



Motsi kadan idan Aisha tayi sai yayi mata sannu, mamakinshi ne kawai ya kamata don bata taba sanin wannan side din nashi ba.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

17

Akan Aisha Daddy yayi watsi da policy dinshi na cewa iyalinshi bazasu ci abincin masu aiki ba don kuwa a yanzu kowa na gidan girkin Lami suke ci don laulayi ya sako Aisha a gaba komai taci sai ta amayar dashi.



Sosai take ganin kulawa da tarairaya a wurin Daddy abinda ya kara assasa wutar kiyayyarta a zuciyar yaran don sosai suke bakin cikin ganinta da ciki tun ma dai ba Farida ba.



Sai da cikinta yayi watanni hudu sannan ta samu saukin laulayin. A lokacin ne kuma ta karbi hidimar gidanta duk da dai Daddy yaso ta bari Lami ta cigaba da kulawa da komai amma ta dage akan zata iya don haka ya kyaleta.



A kwance take akan gadon Daddy sai shagwaba take zuba mishi wai jikinta na mata ciwo. Shi kuma ya biye mata yana mata tausa hade da yi mata mitar aikin da take yi ne ya saka mata ciwon jikin shine kuma dalilin da yasa tun farko ya hanata yin aikin taki ji.



Tun tana mamakin kulawar da take samu daga Daddy har ta dain don da farko ma kasa sakewa tayi dashi sai da taga dai da gaske yake janta ajikinshi sannan ta sake ta bar yin dari-dari dashi.



"Um Daddy kana jina" tace mishi cikin muryar shagwaba. Bata fuska yayi yaja kunnenta kadan yace "bana hana ki ce mini Daddy ba, ni ba Daddynki bane Daddyn baby ne" ya fada yana mai shafo cikinta. "Gara ma tun wuri ki daina kirana Daddy nan don banaso, kirani da sunana Ja'afar yafi mini, ok".


"Owch da zafi fa Dad... ow sorry, nifa gaskiya bazan iya kiran sunanka ba gatsau, haba ai babu ma tsari wallahi" ta fada tana mai cuno baki.



Sunkuyowa yayi yay kissing din lips dinta lightly sannan yace "to ki kirani da wani sunan amma ba Daddy ba". Tace to shikenan zanyi tunani, ni kasa na manta me ma zance maka, yauwa dama so nake nace'maka inason zuwa gidan Hajiya na gaisheta".



A take ya bata fuska yace "nifa bana son yawo, ke da baki da lafiya wane fita kuma zakiyi. Ina ce'kuma kusan sau uku Hajiyan tana zuwa dubaki bare kice kin dade baki ganta bane yasa kike son zuwa".



Jikinta ne yayi sanyi jin abinda yace sai dai kuma bazata iya mishi musu ba don kuwa bata saba musu dashi ba komai yace da to take amsa mishi. Sai dai kuma har cikin ranta bata ji dadi ba don har fuskarta sai da ta nuna bacin ranta.



"Fushi kikayi don nace bazaki fita ba" tace "a'a me ka gani" yace "gashinan kin bata rai kin daina magana bayan da hira mukeyi". Yake kawai tayi tace "a'a ba fushi nayi ba ai nasan hakanan bazaka hanani zuwa wurin Hajiya ba dole kana da naka dalilin kuma ma ai ka fada cewar bani da lafiya. Babu komai wata rana sai naje idan na kara samun sauki".



Dole ba don taso ba ta ware take janshi da hira don ta kawar mishi da shakku a zuciyarshi sai dai har ga Allah bataji dadin hanata zuwa gidan Hajiya da yayi ba. Tunda aka kawota gidan a matsayin matarshi bata taba fita ba sai lokacin da sukaje asibiti kusan watanni bakwai.



Tana son zuwa gaya ma amma sanin cewar ba lallai ne ya barta ba yasa ta kasa tambayarshi bare kuma yanzu data samu cikinnan komai takeyi idonshi nakai, ita har mamakin son yaranshi takeyi.



Da safe ne bayan sunyi breakfast yake ce mata ta shirya taje gidan Hajiya amma karya dade don baya son kaiwa yamma a unguwa. To itama tasan policy dinshi ne tun lokacin Mami nada rai bata wuce karfe biyar a waje.



Kitchen ta nufa ta hada abincin rana. Alkubus tayi da miyar taushe sai farfesun kayan ciki. Bayan ta shirya warmers ne ta zuba wanda zata kaiwa Hajiya ta hada a cikin basket sai toma dkinta don ta shirya.



Kafin ta shirya dama sai da ta tura Zainab don ta fadawa Mallam Adamu cewa zasu fita. A sitting room dinshi na sama ta iske shi ta mishi sallama sannan ta fita.



Lokacin da ta isa harabar gidan sai ta iske babu Mallam Adamu babu motar kuma, cikin daurewar kai ta tsaya tana kallon wurin daya saba ajiye motar. To ko dai Zainab bata gaya mishi cewa zasu fita ba.




Komawa tayi cikin gidan, a zzaune a parlour Ruqaiya da Zainab ne suna kallo a tashar disney. "Zainab baki fadawa Mallam Adamu cewa zamu fita ba ne" ta tambayeta bayan ta zauna akan kujera.



Tace "na fada mishi, su Yaya Ummie da Yaya Farida ne suka ce ya kaisu gidan kawarsu kuma ya fada musu cewa tare zaku fita suka ce idan ya kaisu ya dawo ya kaiki".



Ok kawai tacewa Zainab. Tasan da gayya suka fita bayan sun sanccewa fita zatayi don a gabansu ta tura Zainab ta shaidawa Mallam Adamu zata fita shinw suka rigata ficewa ta kuma san ba lallai ne su barshi ya dawo yanzu ba.



Tashi tayi ta haya sama don ta sanarwa Daddy cewa bata tafi ba. Tana shiga sitting room din yace mata "ya kika dawo ko mantuwa kikayi", gyada kai tayi tace "a'a na samu su Farida sun fita tare da Mallam Adamun ne". "Baki gaya mishi zaki fita bane suka fita ba tare da sun jiraki ba", tace "na aika Zainab ta gaya mishi maybe sunyi zaton ba yanzu zan fita bane".



Cikin fada yace "zancen banza kenan yasan zaki fita amma ya biye tasu Farida ya fita dasu, wa ma ya basu izinin fita. Ko sun sanar dake zasu fita. Girgiza kai tayi tace "um-um maybe kuma ba nisa sukayi ba shi ya saka basu sanr ba".



Tashi yayi ya shiga daki ya canja kaya zuwa kaftan ya dauko kwy din mota ya fito. "Tashi mu tafi" yace mata. Tashi tayi tabi bayanshi suka sauka kasa. Suna shiga parlour ta cewa Ruqaiya da Zainab su dauko takalmi da gyale suzo su tafi.



Juyowa yayi ya kalleta jin abinda tace yace "dama dasu kika shirya tafiya" tace "a'a na gani ne gidan babu kowa sai su Lami kaga ai bai kyautu a barsu su kadai ba".



Bai kara cewa komai ba sai dai kuma har cikin ranshi yana Jin dadin yadda take kula mishi da yaranshi yasan hadda wannan yasa mishi sonta a zuciyarshi.



Suna saukowa suka fita, yaran na baya ita kuma ta kame a gaban mota. Jefi-jefi suna hira har suka isa gidan Hajiya. Yana tsaida motar yaran suka fita da gudu don ko motar basu rufe ba.



Murmushi kawai Aisha ta dauki basket dinta ta fita ta nufi hanyar cikin gidan. Horn din da yayi mata ne ya sakata juyowa. Fitowa yayi ya kulle motar sannan yace "ki jirani mana mu shiga tare".



Ita dai kunya takeji yanzu kawai sai Hajiya ta gansu sun jero, shine fa dalilin da yasa tayi saurin fita don ta rigashi shiga amma ya tsaida ita.



Gaba ya wuce ta bishi a baya. A tsakar gida suka iske Hajiya a zaune akan tabarma su Ruqaiya sunyi matashi da cinyarta. Haka nan yau sai taji tana kunyar hada ido da Hajiya.



Cikin sanyin jiki ta karaso ta zauna akan tabarmar tana gaida Hajiya ita kuma tana tambayarta jikinta. Sai da ya bri suka gam gaiswa sannan ya gaida Hajiya ya tashi yana mi kallon Aisha yace "zan tafi sai da yamma zan dawo, inasu Zanab ne suzomu tafi kunsan yau akwai islamiyya" tace mishi "to nagode Allah ya kiyaye".



Bayan tafiyarsu ne Hajiya tace mata "tashi ki shiga cikinima yanzu nima yanzu zan shigo, tashi tayi ta koma parlour ta zauna.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

19

Yau kwanankin Aisha uku a asibiti kuma yau dinne ake saka ran za'a bata sallama. A cikin kwanakin nan gaba daya su Farida sai wasan buya suke yi da Daddy ko da wasa basu bari sun hadu dashi ba.



Shima kuma baibi takansu ba don a yanzu ba abinda ke gabanshi ba kenan. A yanzu ta lafiyar Aisha yakeyi, ya bari ne sai sun koma gida sannan ya zauna dasu dukkansu don yaji miye musabbabin hatsarin daya faru.



Baya so ya zurfafa zarginshi akan yaran sai dai kuma yanayinsu a lokacin ya nuna tabbas basu da gaskiya. Gashi kuma tun ranar bai kara sakasu a idanunshi ba abinda ya kara assasa zargin da yakeyi na cewar sune ke da alhakin kada Aisha har ta kusa tayi loosing yaranta.



Mutanen gaya ma sun samu labarin haihuwar Aisha don haka sukayita tururuwar zuwa dubata, Yakumbo Dije kuma ta zauna don ta kula da lafiyarta data jariran.



Koda aka sallameta gidanta aka wuce da ita duk da dai Hajiya taso ta tafi da ita gidanta amma Daddt yace a'a tunda dai ga Yakumbo Dije babu bukatar sai ta koma wurin Hajiya.



Koda suka dawo daga asibitin su Ummie basu je sun mata sannu ba bare suga babies, Khalifa ne kadai ya shiga ya dubata a daren ranar sai kuma su Ruqaiya da suka tare a dakinta basa motsawa ko nan da can.



Bayan kwana biyu da dawowarsu daga asibiti ne Daddy ya tara su a parlourshi na sama, tun daga kan Khalifa da ba ma ya nan abin ya faru har zuwa kan Farida. Ruqaiya da Zainab ne kawai babu.



Hatta da Hajia a ranar sai da tazo don tun suna asibiti ya gaya mata cewa yana so za suyi magana amma bai gaya mata akan miye ba sai kuma a yau yayi mata waya yace ya tura Khalifa ya daukota.



Gaba dayansu sun taru a parlourshi har Aisha. Ga Mu'azzam da Farida kuwa gaba daya sun rude don sun tabbatar da wannan zaman akansu akayi shi, hatta da Ummie a tsorace take.



Kallon wurin da suke Daddy yayi yaga yanda sukayi tsuru-tsuru kwata-kwata basa cikin nutsuwarsu.



Bayan wasu 'yan mintuna ne Daddy yayi gyaran murya yace "abinda yasa na taraku duka anan shine dan na sanar daku abinda ya faru kwanaki biyar da suka wuce na samun Aisha da nayi kwance a cikin jini bata cikin hayyacinta sai kuma wadannan da na samu a tsaye akanta wanda bana raba daya biyu sune sukayi sanadin dana sameta a halin dana tarar da ita" ya fada yana mai nuna su Mu'azzam.



Yaci gana da cewa "shine yasa na taraku anan don ina son sanin asalin abinda ya faru, Aisha ko zaki gaya mini yanda akayi kika fadi akan cikinki har yayi sanadin da sai da aka miki aiki aka ciro babies?"




Sunkuyar da kanta tayi ta kasa magana don sai yanzu da yayi maganar ne ma taji ciwon abin sosai. Bata taba sanin kin da suke yi mata har yakai yanda zasu yi mata lahani ba sai yanzu.



Tasan da gayya Mu'azzam ya cilla mata ball dinnan a cikinta abinda bata taba zaton zasu iya yi mata ba. Jin shirun nata yayi yawa ne yasa Daddy yace mata "Aisha kiyi magana mana, nace ko zaki iya fada mini abinda ya faru a ranar na tarar dake a kwance cikin jini".



Girgiza kanta tayi sannan tace "a gaskiya bazan iya tunawa ba na manta". Hajiya ce ta ce "wanne irin kin manta kina nufin baki san yadda akayi kika fadi akan cikinki ba da har yay sanadin da akayi miki aiki aka ciro yaran dake cikinki, kenan kin samu shafewar tunani da bazaki iya tuna rayuwarki ta baya ba".



Nanma Aisha cewa tayi "a'a Hajiya ban samu shafewar tunani ba kawai dai na manta abinda ya faru ne a ranar". Hajiya zata sake magana Daddy yayi hanzarin cewa "kyaleta Hajiya tunda tace ta manta shikenan saukinta ai ba ita kadai bace a wurin da abin ya faru don haka kai Mu'azzam kaine babba ko zan iya sanin abin d yaru da har nazo na iske Aisha a kwance yayinda kuke tsaye akanta kai da kannenka".



Mummunar faduwar gaba ce ta ziyarci Mu'azzam don har ga Allah yana tsoron Daddy yasan cewa shine ya cilla mata ball a ciki duk da dai yana tunanin Daddyn yasan cewa sune shine ma dalilin da yasa ya tara su duka anan wurin.



Ganin yayi shiru ya kasa magana ne yasa Daddy ya juya akalar tambayarshi wurin Ummie, itama shiru tayi ta kasa bashi amsa haka ma Farida.



Ranshi yayi mummunan baci, shirunsu ya kara tabbatar mishida zarginshi na cewa sune sukayi sanadin da Aisha ta kwanta a asibiti.



Cikin masifaffiyar murya yace "kunsan me shirun ku yake nufi, yana nufin zargin da nake yi akanku ya tabbata don ko rantsuwa zan iyayi akan cewa kune kuka yi sanadin da Aisha ta fadi. Yanzun its either ku fada mini gaskiyar abinda ya faru ko kuma nayi bincike na gano yanda abin ya kasance don kada ku manta ba wai ku kadai bane a wurin a ranar da abin ya faru kun kuma san Zainab bazata gaya mini karya ba. So its better you start talking right now".




Mu'azzama ne yayi karfin halin cewa "Daddy don Allah kayi hakuri wallahi tsautsayi ne",cikin tsawa yace "comeon ka fada mini abinda ya faru don bawai na tara ku anan don kuyi mini yawo da hankali bane".



A haka dai Mu'azzam ya daure ya fadi abinda ya faru sai dai yayi kokarin ya nuna cewa laifin na Farida ne don ita ta kauce bata bari Aisha ta dafa ta ba abinda yayi sanadin data kifa akan cikinta.



Gaba daya Farida rikicewa tayi jin Mu'azzam na neman ya juya laifin kanta ita kadai bayan kuma da ace bai fara jefa mata ball dinba da duk haka bata faru ba.



Sosai ran Hajiya ya baci da jin abinda ya faru. Fada sosai ta hau yi tana cewa "wannan ai rashi imani ne ku jefi mace da tsohon ciki, me kuke so ku zama ne yarannan".



Khalifa ma ranshi ya baci dajin abinda sukayi, ya rasa me ke damun yarannan wai har Mu'azzam da yake babba kuma namiji ace yana abu irin na jahilai yana biyewa su Farida.



Daddy kam takaici ne ma ya hana shi magana sai zuwa can ya ce"yanzu magana guda daya ce zanyi bazan yi tolerating iskancinku ba acikin gidana dole ne kuyi respecting matata don disresoecting dinta yana nufin disrespecting dina. Aisha da kuke gani matata ce and its a must for you to accept her as a mother, babu ruwana da wani grudges da kuke holding against her wannan damuwarku ce.



Abinda na sani shine cewa nine mai gida kuma dukkanku a karkashina kuke so dole kuyi accepting ko waye na kawo na ajjiye a cikin gidannan, don haka this should be the first and the last time da wani abu makamancin wannan zai kuma faruwa.



Abu na gaba kuma shine ke Ummie da Farida ku fito da miji auren zan yi muku tunda na lura har da kyaleku da nayi kun zaune mini a cikin gida babu aure yasaka kuke mini iskancin da kuka ga dama, don haka sai ku shirya auren Khalifa da za'ayi tare da naku za'a hada".



Kai kuwa Mu'azzam babu abinda zan ce maka don kuwa a shekarunka idan har baka tsawatarwa da na kasa dakai ba bazaka biye musu kuyi abinda kukayi ba amma kuma unfortunately kai ne kake nuna musu ko miye ma sukeyi, abu daya zan gaya maka shine bazan dauki rashin da'a a cikin gidana ba. Bazan yadda da ganganci irin wannan ba ayi terming dinshi as tsautsayi".



"sannan kuma inaso dukkanku ku bawa Aisha hakuri tare da alkawarin makamancin irin wannan bazai kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login