Showing 33001 words to 36000 words out of 110979 words
kuwa kullum suna gidan.
Kwata² tadaina gyarama Bobo d'akinsa, tun ranarma bata sake kallon ko hanyar d'akinba, su khairiyyane suke gyara masa idan sunzo.
Dama bawani shiga harkarsa takeba, to akwana ukunnan ma talura yana matuk'ar busy, Dan kullum yana danna laptop, wani sa'inma saiyakai 10 baidawo gidanba.
Dukda abin na damunta tanason kuma tambayarsa abinda ke faruwa?, amma tana tsoron wulak'ancinsa, Dan haka ta shareshi itama, tanadai tayasa da addu'a samun nasara akan abinda ya burkitashi haka.
+++
A6angaren bobo kam ya ajiye komai gefe, gaba d'ayan hankalinsa yabada akan shari'arsu da Haneef, bak'aramin shiri yayma shari'arba, Dan yayi bincike na musamman akan halayyar haneef, wannan yasa yakeson ceto sauran yara daga gudun fad'awa tarkon Haneef d'in na gaba, Dan ance mai halin bata barin halinsa.
Tun washe garin daya kai Rahma asibiti taga muheebat kuma yaji tasanta, da safe yakar6i address d'in gidansu Idris, tare sukaje shida ya Hamza da ya sulaiman har gidan suka maida muheebat.
Dangin hebba sunyi murna da dawowarta garesu, sunkuma sakama su bobo albarka gameda taimakon dasuka bama yarinyar, saidai sunyi kuka sosai akanjin k'addarar data afka mata.
Nansu ya Hamza sukaita lallashinsu, sukace sukwantar da hankalinsu zasu kwatoma Hibba hak'inta dukda dai budurcinta yatafi bazai dawoba.
Sunji dad'i sosai tareda yimusu k'yak'yk'yawar addu'a.
Bobo ya ce, " zamu tafi, amma ga no. d'ina Indai dawata Matsala sai'a kirani, sannan akan rashin maganar heeba d'in kodama tanada wannan matsalar?.
Eh damacan bata iya magana tun bayan ciwon k'yanda datayi lalurar ta sameta, amma tanajin abinda ake fad'a cewar baba Hamisu mahaifinsu hibba da idris.
ALLAH sarki, amma baba kunta6a d'aukar mataki akan hakan?. Dr sulaiman ya tambaya?.
A'a yaro, gsky bamuta6a yiba kasancewarsa kada muyima ALLAH shishshigi.
Hakane baba amma yana da k'yau anema mata magani, Dan naga zata iya samun lfy, ban yimata aikin bane dama saboda inaso saida izininku, amma insha ALLAH zamu yimata wani aiki komai zai dawo daidai, Dan matsalarta bata cika tsananiba.
To shikenan mungode ALLAH yasaka muku da alkairi, yayma Rayuwarku albarka, ALLAH yajik'an mahaifa.
Ameen suka fad'a suna mik'ewa, sukai musu sallama suka tafi akan sai suhad'u a kotu ranar talata.
*.......................*
Washe gari talata su bobo suka shiga shari'a.
Tun azaman farko hankalin lauyan Haneef yatashi, dan tabbas yasan Bobo kwarone tunda bayau suka fara karawaba, yasan kuma bobo baya tsayama Mara gsky koyaya suke kuwa, komin k'arfin alak'arsu.
Zaman nan nafarko kawai bobo yakawo hujjoji da dama wad'anda suka saka mutane dayawa yadda Haneef ya aikata abinda ake zarginsa dashi, amma dayake alk'ali yaci kud'i saiya d'aga shari'ar sai nan da sati biyu masu zuwa.
Anan lauyan Haneef yanemi Belin haneef amma bobo yace Sam bai yardaba, Alk'ali yasan halin bobo dabin kwakwaf dama kuma bawani shiri sukeba, Dan haka yace k'orafi bai kar6uba, zasucigaba da rik'e Haneef.
Ran Alh Sunusi ya6aci, sai kallon miye haka?, yakema Alk'ali.
Alk'ali kuma yanamasa magana da ido akan subi ahankali.
Duk abinda ke faruwa bobo yana kallonsu, Dan haka yasaki murmushin sa na mugunta, Wanda Ammar kankira da yafi saukar Boom ban tsoro, amma ga Wanda yasan ma'anar murmushin ga bobo kenan.
Suna fitowa daga shari'ar gida bobo yay shirin tafiya, daka gansa Kasan yana cikin farinciki, bud'e motarsa yayi zai shiga Alh Sunusi da masu tsaronsa suka k'araso wajen, bobo yaja sirin farin gilas d'insa k'asan ido Wanda yadawo k'arshen hancinsa ya tsaya.
_( na ce, "anyi shirin rashin arzik'i kenan��)?._
Alh Sunusi ya watsama bobo harara, yaro har yanzu kanka yana rawa ko?.
Murmushi bobo yayi, tareda bud'e motar yawatsa kayan hannunsa a sit d'in baya, yarufe murfin sannan yajingina da motar yana kallon Alh Sunusi cikeda basarwa.
Alh wai minayi maka hakane dazafi? kasaka rayuwata agaba.
Yakamata ka lura dawani Abu, ni lauyane mai zaman kansa, banida banbanci dad'an kasuwa, so saina gadamar saida maka hajata, idan banida ra'ayi saikaje gaba kasiya, Alhaji karik'e girmanka, banaso mufara game tare dakai, Dan akwai matsala.
da d'anka nake shari'a bada kaiba, so ka kalli gabanka kada katsaya kallon ruwa kwad'o yayi maka k'afa wlhy.
Yana gama fad'a yashige mota, Alh Sunusi kuma yana zabga ruwan masifa da bala'i, jiyake yak'ara tsanar yaronnan.
Fuuuuu bobo yaja mota tareda bud'ama Alh Sunusi k'ura, by Alhaji sai zama na biyu, bobo yafad'a yana figar motar yabar harabar get d'in.
Kwafa Alhaji Sunusi yayi, tareda fad'in zakasan koni waye yaro.
.×.×.×.×.×.×.×.×.×.×.
Da sallamarsa yashigo falon, saidai shiru babu kowa, yakalli agogon hannunsa 12:15pm Nawal bata dawo school ba, aransa yace to ina momynta?.
K'arar Rahma yajiyo daga d'akinta, da sauri yanufi d'akin, hakan yayi daidai dafitowar Rahma dagudu daga bayi, daga ita sai tawul, jikin bobo tafad'a tana rawar jiki, bashida za6i saina rungumeta, yanda jikinta kerawa kawai ya isa kasan wani abune yabata tsoro.
"K!, miya farune?."
Dadyn Nawal Dan ALLAH kataimaka ka kashemin shi wlhy inajin tsoronsa, kataimakeni plzzz, tafad'a tana kuma ruk'unk'umesa, tamkar zata fasa jikinsa tashige.
Bobo ya girgizata "k kinutsu kifad'amin minene mana?.
d'agowa tayi tana d'an hakki, tuni idanun nan NATA masu kasheshi sun wani sake fitowa, yakula duk yanda yarinyar tashiga rud'ani ko tsoro idonta baya canja kala..... Tunani takatse masa da nuna hanyar bayi.
Hannunta yakama suka nufi bathroom d'in, kinga Nutsu ki nunamin banason shirme, abayansa ta mak'ale, tashiga waige² Neman abinda yatsotata saidai wayam yabar wajen.
Yaja tsaki yarinyarnan ALLAH kinyi mugun rainani, yanzu inbanda raini minene a Bathroom d'innan?.
Wlhy naganshi da idona, saidai idan ya 6oyene, harara ya watsa mata yayo baya zai fita yad'an matseta da bango.
Sukur² taji abayanta, Dan haka tayi saurin turashi takalli bango, wani k'ara takuma fasawa tatafi luuuu zata fad'i.
Da sauri yatareta tafad'o jikinsa, Tawul d'in jikinta ya kwance, yakai dubansa ga abinda tagani, wata 'Yar k'aramar k'adan garuwace, (Tsaka), da alama ta'inda zata fita ma take nema, yamaido kallonsa kan Rahma wadda yakeda tabbacin ta suma, runtse idonsa yayi Yakuma bud'ewa a kan k'irjin Rahma, shima jikin nasa rawa yafarayi, da sauri yakauda kansa yaja tawul d'in ya rufe mata jikinta, d'aukarta yayai cak, jikinsa dukya mutu yafito da ita zuwa kan gado.
Zama yayi yadafe kansa Dan yau surar Rahma ta tsokalishi, babu abinda yake ambata sai _"Hasbinallahu wani'imal wakil"_, tuni idonsa yakad'a yay jajur, zumbur yamik'e yafita kafin yayi aika², kichin yashiga yabud'e firij yakwaso lemon tsami har biyar, jikinsa har rawa yake wajen yankawa, dandanan yamatse ruwan lemon akofi yashanye, ko azababben tsamin baijiba.
Yadire kofin saman tebird'in tsakkiyar kicind'in, yadafe hannayensa biyu tareda runtse idanu, yakai minti10 ahaka sannan yabud'e ido yaja d'aya daga kujerun kicind'in yazauna yana sauke ajiyar zuciya, tamkar jinjirin daya kwana ya wuni baisha nonon mamansaba.
Nanma kwantar da kansa yayi atebir d'in, yad'an jima ahaka sannan yatashi jikin a sanyaye yad'auki ruwa mai sanyi ya kwankwad'a, yakusa shanye gora d'aya kafin yacire yana sauke numfashi, goran ruwan yad'ago ya kalla sannan yafice daga kicin d'in.
d'akin Rahma Yakoma, har yanzu tana nan inda yabarta, yak'arasa gaban gadon ya zauna, yayyafa mata sauran ruwan hannunsa yayi, ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, saikuma tamik'e zumbur ta kwakumeshi tana fad'in dadyn Nawal plzzzz kaje kafiddata wlhy banason ganinshi wayyo ALLAH ummi kizo ki ceceni na bani.........
Ganin yanda take gogamasa jikinta gashi tabi ta k'adandaneshi, idan suka k'ara d'aukar lokaci ahaka bazai iya jurewaba, sai kawai yadaka mata tsawa.
k!!!!!!!, dallah ki nutsu banason shashanci, miye abin tsoro a tsaka?, duk kinbi kin wani rud'a kanki har kina k'ok'arin illatamin lafiyata Mtsooooow, yaja tsaki.
Tuni Rahma tashiga hankalinta, amma har yanzu jikinta rawa yakeyi, harma batasan Tawul d'inta ya k'ara zamewaba.
Gaba d'aya hankalin bobo yakuma tashi, yatsurama k'irjin Rahma ido tamakar zai cinyeta d'anya.
Ganin kallon k'urillar dayake mata yasa itama ta kalli jikinta dantaga miyake kallone haka..... Idanu tawaro tareda jan bedsheet d'in ta k'udun dune jikinta.
Mik'ewa Bobo yayi yayo kanta................
������typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
4⃣3⃣
Safna ga sir Hamza canfa yazo, baseera tafad'a tana kallon Safna data rafga tagumi kamar wadda akace ummi zata mutu yau.
Zumbur tamik'e tana fad'in habadai?.
ALLAH kuwa yanzu yashiga office d'insa.
Kinga tashi muje kirakani.
Mubari Zeenat ta iso mana tunda ta ce, "tana hanya.
Mtsooow dallah shareta tashi muje, kinsanfa bakomaine take Goya mana bayaba.
Mik'ewa Baseera tayi tana kakka6e doguwar rigarta, hakane kuma wlhy, kinsan zeenat ya ustaz CE.
Aii saitaji da ustazancin ta ita kad'ai.
Saida suka kwankwasa yabasu izinin shigowa, sannan suka shiga, bayan sun gaidashi baseera ta ce, " Sir mun biyo sawune.
Kallonsu yake cike da mamaki, amma baice komaiba yarubuta musu number Bobo, ya d'ago yana kallonsu, ban tanbayesaba Dan ina mantawane, amma baridai yau nabaku Dan kun fara bani tausayi, dukda bansan mizakuyi da no. d'in *Abdulmaleek!* ba.
Wlhy bawani mugun Abu zamuyi da itaba, kawai zamu sada zumincine.
Girgiza kai kawai ya Hamza yayi, yamik'a musu number, gashi to, nadai baku number sa gama gari tunda bannemi izinin saba bare nabaku number sa mai muhimmanci, amma insha ALLAHU zaku samesa da wannanma.
Mungode sir, ALLAH yak'ara girma.
Amin yafad'a yana binsu da kallo atak'aice, shifa mamaki suke bashi wlhy, koda yake basuda laifi k'anin nasa ya had'u, ga k'yau ga iya wanka, uwa uba kamun kai.
Cigaba yayi da aikin gabansa kawai.
A can kuwa suna fita Safna ta daka tsallen murna tareda rungume Baseera, wayyo k'awata yau na mallaki number Bobona.
Dariya baseera tayi, kinga Laila karki karyani nikam.
Miye kuma laila?, safna tafad'a tana yatsine fuska.
Dariya baseera tayi, laila majnun mana, aigara mufara kiranki Laila kafin bobo yazama majnun.
Dariya Safna tayi tareda Jan hannun Baseera suka nufi class.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Baya Rahma tashiga matsawa tana fad'in inna'lillahi wa'inna ilaihirraji'un.
Ina Bobo baisan tanayibama, kanta kawai yayo tamkar wani zaki maijin yunwa.
Gadon ya hawo yafincikota jikinsa, jikinta sai Rawa yake, ga kukanta ya k'aru, bakinsa da nata ya had'e yashiga wasa da harshenta tamkar yasamu alawar lollipop, agefe kuma hannunsane ke murza ko ina najikinta, Rahma dai sai dukansa da tsungune takeyi, amma baimasan tanayiba, shidai sak'o kawai yake burin isarwa.
Yakai tsawon minti 13 yana Abu d'aya, tuni Rahma tabar kukan tsoro saidai na ceton kai.
Shikam Bobo idonsa yarufe baimasan mi yake aikatawaba, shidai kawai burinsa yake son cikawa, jin hannunsa a k..... Yasata k'ara rikicewa.
Shima da sauri yasaketa danjin pad alamar tana period kenan.
Zubewa yayi agefe sai wani wahalallen numfashi yake saukewa, Rahma tayi saurin sauka daga gadon takoma jikin bango ta mak'ale tana kuka, sai kallon yanda Bobo yake fidda numfashi tamkar zai mutu takeyi, nan take kuma tausayinsa yakamata, jitai hawayenta sun k'aru.
Tanaso taje ta taimakeshi amma tana gudun karya k'ara damk'arta.
Sunkai minti15 ahaka, shi yana cikin wahalar ciwon mara ko magana yakasa mata, itakuma tana cikin tsoro da abinda yamata gakuma halin dayake ciki abin tsoro.
Bobo ya daure dak'ar ya ce, "ki matsemin lemon tsami please zan mut u..........yak'arasa maganar da k'yar danji mararsa da kansa tamkar zasu fashe."
Da gudu tafita zuwa kichin, cikin sauri tamatse lemon tsami wajen takwas, dama tasaka ruwan zafi kad'an awuta, tajefa lifton uku dantaga wani sa'in haka yakecewa ta dafa masa, juyewa tayi akan ruwan lemon tsamin tad'auka tanufi d'akinta yanata turiri.
Da k'ar ya iya tashi yakar6a, dukda zafin da shayin yake dashi bai sauraraba yakafa kai ya shanye kamar yasamu ruwan sanyi.
Mik'amata kofin yayi yakoma yakwanta, jikinsa har Rawa yake, ya ce, " lullu6eni sanyi nakeji, kuma ki kashemin AC.
Duk abinda yace tayi masa da saurinta, sannan takoma gefe tazuba masa ido.
Lumshe idonsa yayi, danda nan zazza6i ya rufeshi, jikinsa yad'auki azababben zafi kuwa.
Rahma sai kallon sa takeyi tana hawaye, yanzu ba kukan abinda yaymata takeyiba, kukan halin dayake cikin takeyi, tarasa yanda zata fassara al'amarin nasa.
Idonsa alumshe yake amma yana kallonta ta k'asan idonsa, saiyaji tama k'ara bashi haushi.
Tunda yake baita6ajin abinda yaji yau ga mace ba sai akan Rahma, shekararsa wajen 5 babu mace, dukda yasan yana cikin buk'atar macen, amma hankalinsa bai ta6a tashiba irin yau, yarasa wace irin mace ce Rahma da jikinta yazame masa tamkar wani magana d'isu, jiyake tamkar zai mutu Dan azaba, amma lemon tsamin data kawo masa yad'an rage masa azabar dayakeji, yamanta tsawon lokacin daya d'auka rabonsa da zazza6i mai zafi kamar haka, yarintse idonsa yana ambatar sunayen ALLAH.
Zuwa wani lokaci kuma sai barci ya saceshi.
Rahma ta sauke ajiyar zuciya, yanzu kuma matsalarta d'aya shine a ina zatayi wanka?, Dan bazata sake shiga bayin taba sai an kashe tsakar can.
Zuciyarta ta ce, "kije d'akin mijinki tunda barci yakeyi.
Aiko tayi na'am da wanga batu, d'akinsa tanufa ta shiga bayinsa tayi wankanta sannan tafito.
Harta shirya yana barci, kichin taje tafara girki, zuwa 2:00pm tagama takuma gyara ko ina, tana falo zaune tana kallon Hausa film Nawal tadawo, direbanta ya d'akkota.
Dagudu tashigo gidan tana kiran momyna! Momyna!!, Rahma tamik'e da sauri Nawal tafad'a jikinta, d'agata tayi tana juyi da ita afalon suna dariya.
Hayaniyarsu ce ta tada Bobo, yamik'e dak'yar Dan Marar tasaki saidai zazza6in shima kad'an, falon yafito, sukam bama su gansaba sunata murnar ganin juna itada Nawal d'inta.
d'an murmushi yayi yashige d'akinsa, ko babu komai yanajin dad'in yanda Rahma take kula masa da yarinyarsa, idan ba fad'a maka akayiba bazaka ta6a cewa ba ita ta haifetaba, saidai kawai idan ka kalli Rahma d'in zakaga yarinyace batakai ta haifi kamar Nawal ba, ammafa duk wata kulawa irin ta uwa akan d'anta Rahma tana k'ok'arin bama Nawal, kuma har zuciyarta takeson yarinyar.
Kama hannunta tayi suka shiga d'akin, tabi gadon da kallon mamaki to ina yaje?, tafad'a azuciyarta, tad'an lek'a bayi daga nesa taga wayam, inaga to yana d'akinsa.
Da wannan tunanin tacirema Nawal kayan makarantar.
‘Nawal!.’
Na'am momy.
Kije d'akin papa kigani barci yakeyi, idan barci yakeyi muje can namiki wanka.
Lah momy bayinmu fa?.
Akwai ojuju aciki ina tsoron shigane.
Kai, momy kema kinajin tsoron Ojuju.
Dariya Rahma tayi ta ce, "kinga kedai jeki duba kidawo.
Tamata hakane Dan tambayar ta tsaya haka.
Da gudu Nawal tafita sai d'akin Papanta.
Fitowarsa kenan daga wanka, yana zaune abakin gado yana shafa mai, Nawal ta shigo aguje tafad'a jikinsa.
Uccch yafad'a yana rungume Nawal d'in, saboda yaji zafi data fad'a jikinsa.
baby bana hanaki guje²n nan bane?.
Sorry papa nadaina.
Yalumshe idanunsa yana kad'a kai, toya School?, harkun dawo?.
Eh papa, tad'ago tana kallonsa, papa kaima bakada lfy kamar momy?.
Kallonta kawai yakeyi yakasa magana, ta girgizashi kaji papa, ajiyar zuciya ya sauke, a'a baby lafiya ta k'alau, itama momy aita warke ko?.
Eh mana ta warke, yanzuma catayi Nazo naduba idan kana barci saitazo tamin wanka a bayinka, wai bayinmu akwai ojuju tanajin tsoronsa.
Papa dama idan mutum yay babba yanajin tsoron ojuju?.
Bobo dake shafa mai yanajin zancen Nawal yayi murmushi, baby Momynki tacika tsaorene, amma zan koya mata yanda zata daina, jekice mata tazo tamiki.
Papa nima zaka koyamin Dan nadaina tsoron ojuju d'in?.
Eh zan koya miki, jeki kirata.
Fita Nawal tayi kiran Rahma.
Momy tahoto kimin.
To Babyna, amma papa fa?, yananan ad'akin.
Atunanin Rahma yana barci Nawal take nufi Dan haka takama hannunta suka fito zuwa d'akin bobo.
Kanta tsaye tashiga d'akin, saikuma tatsaya cak Dan ganin bobo tsaye yana saka ma6alin rigarsa, baya tayi zata koma, batareda ya kalletaba ya ce, " kizo kimata wankan mana.
Rahma tayi k'asa da kai kamar wata munafuka tanufi bayin rik'eda hannun Nawal.
Shikam baki yata6e yad'auki brush yana k'ara kwantar da sajensa bak'i sid'ik, yak'ara fesa turare sannan yafice daga d'akin.
Masallaci yanufa, saida yayo sallah yadawo sannan ya d'auki Jakar aikinsa daga fallo, yamanta a can yabarta, yacire laptop d'insa da wayoyi ya ajiye a tebird'in tsakkiyar falon sannan yakawo jakkar d'aki Yakuma fita.
d'akin Rahma yashiga, yanufi bayimta danya kashe matsa tsakar, dube² yahauyi, can yahangota kwance a bango, tsintsiya yasa yabugota tafad'o, Yakuma bugunta