Showing 36001 words to 39000 words out of 52100 words

Chapter 13 - Hafsat Ilham Complete Hausa Novel

14 Jul 2025

5460

habarta yace "Blossom ban sanar miki banasan kukannan ba yanzu menene abun kuka,wani wurin ne yake miki ciwo? Girgiza masa kanta tayi alamar AA,yace to menene meya sakaki kuka?" Cikin shagwab'a tace "wannan abin mana" kamar be fahimce ta ba yace "Menene wannan abin?" tana kukan tace "wanda kake mun yanzu mana" k'ara rungumota yayi yace a hankali
"Blossom menene bakyaso aciki,me kike jine?" K'ara zumb'uro baki tayi ta yamutsa fuska "Yaa Abdul nifa ji nake kamar mutuwa zanyi wani abu nakeji fa" Shafa sumar kanta yaso mayi "Blossom wannan abin da kikeji fa dad'i ne ba mutuwa bane,mutuwa ai batada dad'i Elly,ki dena kuka Kizo muyi wasa kinji" batace komaiba kurin dai ta lumshe idonta ne,tana saurarenshi yana sarrafata yanda duk yaso,kuma seta tsinci kanta da mayar masa da martani batare da tasan me take ba,a haka har suka biyawa junansu buk'ata, da kanshi ya taya wanka,tace zataje gidan momy yayita mata dabara har bacci ya d'auke ta ajikinshi.....


Mom Nu'aiym
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: 🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).


22
Shine ya fara farkawa lokacin sallah asuba,be tasheta sabida yasan akwai rigima a qasa,alwala yayi ya gudu masallacin dake layinsu domin gabatar da sallah,yana fita ba jimawa ta farka aikam fitila ta kunna ta qurawa agogon bangon dake d'akin ido,da mamaki ta tashi,da sauri taje tayo alwala tayi sallah ta zauna zaman jiran shigo warsa,koda yashigo tasowa kurun tayi tafad'a jikinshi tana kuka,shikam abin dariya yabashi saboda yasan dawan garin,rungumeta yayi sosai yana patting bayanta a hankali,ganin bazatayi shiru ba ya sanya ya d'agota cikeda kulawa yace

"Kuka kuma this early morning blossom meya sameki,ko cinnaka ne ya cijeki?" Tana shashekar kuka tace "Yanzu ni me zance da momy? Allah ni bazan ma koma gidanba" Murmushi yamata yace

"Kinga blossom ki dena kuka bacci ne mafa ya sureni nima, ai kinsan dana maidaki,kuma momy Zata fahimta kinji" share hawayen nata tayi tace "Toni yaa Abdul ai inajin kunya yanzu fa dagata gammu zatace Munzo muyi wannan abin ne" gintse dariyar sa yayi yace

"Blossom aibazama tayi wannan tunanin ba,kurin dai zatace mun tafi ba sallama ne kuma zance bacci ne ya sure mu,ki kwantar da hankalinki ki dena kuka kinji? Me kikeso Kici na d'aura miki da kaina?" Hannu tasaka ta share hawayenta tace "Banajin yunwa na koshi" Jan hannunta yayi zuwa saman gadon ya d'aurata a saman cinyarsa ya saqala hannunshi saman bayanta yace

"Blossom na plss ki daure Kici abinci Allah momy bazatace mana komaiba,haba mana se kace ba miji da mata ba,zakisha chocolate?" Gyad'a masa kanta tayi tace "Zansha mana da waffles ma" Murmushi yayi

"Yauwa Inada chocolate da yawa a d'akina zan had'a miki waffles d'in yanzunnan kuma idan kika gama cin breakfast da kaina zan baki chocolate" kallonshi tayi "Toni yanzu bazanci komai ba se wannan Shawarma d'in da hot tea" dafe kanshi yayi yazeyi da Elham dolenshi ya had'a mata Shawarma d'in,dagata yayi ya kwantar da ita yace

"Oya ki kwanta idan na kammala zanzo na tashe ki kinji" batayi musu ba sabida baccin be gama isarta ba.....sanda ya kammala yayi wanka sannan ya tasheta kallonshi tayi ta zumburo baki ta yamutsa fuska

"Yaa Abdul ka tashe ni ina bacci na me dad'i mafarkin ka fa nakeyi har zaka sakamun Shawarma a baki" dariya yayi "To kiyi hakuri Kizo zan baki a bakin" tashi tayi zaune tace "yaa Abdul zakamun wanka? Yau gajiya nakeji" dafe kanshi yayi yace "Blossom nafayi wanka na,ni zaki b'atan wanka" qunquni taso mayi "Allah ni Idan bazaka munba bazan maci breakfast d'in ba,kumafa kasan banida lapia fa shine zakace nayi da kaina" Shifa har tsoron rikicin Elham yakeyi yanzu,gashi har wani dena kunyar shi takeyi ta masifar iya zuba shagwab'a da rikicin tsiya

"Oya tashi ki rage kayan jikinki na miki wankan inyaso idan kin shirya maci breakfast d'in" matsowa tayi kusa dashi ta d'aga mata hannayenta sama alamar ya cire rigar,be musa ba ya cire mata rigar ya soma mata cakulkuli,aikam ta soma kwasar dariya dak'yar ta tsagaita dariyar datake tace masa "Allah na tuba yaa Abdul, dan Allah Kayi hakuri ka dena" dena mata cakulkulin yayi yace "Gobema kya k'ara gantsarewa kina mun rigima oya muje ban d'akin" rungume k'irjinta tayi da hannayenta,wai ita a dole lallai kunya takeji,shikam wannan wawtar ta Hafsat na bashi masifar dariya be kulata ba ya wuce gaba abinshi zuwa ban d'akin bayanshi tabi tana dariya,sanda yasake wani wankan shima sannan suka dawo d'akin zamanta tayi akan bed,waigowa yayi ya kalleta "Blossom bakajin yunwa ne wai? Ki shirya mutafi mana" maqe kafad'a tayi tace "Yaa Abdul nika sha famun mai kuma ka sakamun kaya,banida lapiya fa" girgiza kai kurun yayi yazo ya Shafa mata man ya zura mata wata guntuwar riga iya gwiwa sannan suka juya zuwa dining.... Acan ma seda yasha fama da ita shi kuwa se biyewa shirmenta yakeyi,bayan sun kammala dak'yar ya lallabata ta shirya suka je gidan momy wai kunya takeji......

Agaban momy Hafsat ta kasa had'a idonta dana momy se sosai kai takeyi,momy kuwa tayi Kici kicin da fuska,bayan gaisuwa momy bata qara cewa dasu komai ba,duk sun tsargu,Abdul ne yace "Momy dama na dawo da Elham ne har jibin,jiyane bacci ya sureni,kuma tayita tashina na maidota amma baccin yaci k'arfina" wata uwar harara ta wurga masa

"Da kukaje gidan ubanme ya kaiku? Shine zaka nuna mun ka isa ka d'auke matarka ku gudu banma sani ba ko kaiga me mata? To kaje can da ita ni bazan yadda ta zauna mun kazo ka mun rashin kunya" Sosa kai yayi "momy kiyi hakuri dan Allah"

"Kabani hakuri wani laifin kamun,Allah maza ka dauki matarka ku barmun gida,kuje gidan naku da kuke d'oki" matsawa Elly tayi kusa da momy kanta a sunkuye "Momy dan Allah kiyi hakuri Allah kuwan yaa Abdul yaqi ya dawo dani" harara momy ta wurga mata "Da igiya yajaki kuka tafi kenan?" Shiru tayi ta saka kuka,ganin haka yasanya momy sakkowa daga domin fushin da takeyi ta rarrasheta sanda ta dena kukan sannan suka koma gidansu bisa umarnin momy,lura Momyn tayi da matsala idan ta riqe masa mata...... Da yamma yana wasa da yan yatsunta na k'afa lokacin ta tasashi gaba da rigima akan seya ja mata 'yan yatsunta, wayarshi ya soma ringing,inspector mansur ,ya furta bayan ya daga wayar

"Yallab'ai wlhy fa khamis ya gudu bamusan ya akayi yagudu ba" tsaki yaja lokaci d'aya sarautar ta motsa "ida ya gudu meye ruwana aciki ,wlhy Sekun nemoshi mutumin dake iyayin kisa Zakuyi sakaci dashi harya gudu daga hannunku?"

"Yallab'ai laifin yarane kuma munyi informing na commissioner yanzu haka yace abaka tsaro an Turo yan sanda susu goma zasu yi gadin gidanka" bece komai ba ya ajiye wayar ya fara masifa

"Dan Allah meya sanya en sandan Nigeria basuda hankali kuma basusan kan aikinsuba,tayaya criminal irin wannan me murder case and another attempted murder case ze gudu daga hannun su,this is unbelievable,I don't even trust there word's may be dasaka hannunshi aciki and I promise they will pay for it" rik'e hannunshi tayi tace

"Come down hubby,kanata masifa menene ya faru?" Cikeda fusata yace "Haba mana Hafsat,tayaya zasuce wai khamis ya gudu sekace wanda yake ajiye a kasuwa,yaya zasuyi Saka cin da haka ze faru? Wlhy zasu ganene idan wani abin ya biyo baya" hannunta da d'aura saman wuyanshi cikeda kulawa
"Hubby plss come down zasu nemo shine,kuma inshaa Allah ba abinda ze faru se alkhairi kaji" k'ura mata ido take ta hango masifa a idonshi wannan ya sanya tabar masa parlor gaba d'aya,ita kanta k'arfin hali kawai takeyi amma k'irjinta na dukan uku uku sabida tsoron abinda ze biyo baya,tana nan ya dazo ya sameta

"Blossom kinji wani labari mara dad'i kuma,wai khamis yayi hatsari da motar sa a hanyar sa ta barin garinnan kuma anje jikinshi kusan rabewa biyu yayi,wlhy duk Senaji jikina ya mutu Allah koda nake jin matukar haushinsa amma mutuwar nan ta dakeni har raina" zabura tayi tana salallami tace "Allah uban giji ya jikan khamis da rahamar sa,Ashe dama ajaline yake kiransa bawan Allah,nidai kam na yafe masa duk abinda yamun " Abdul dai bece komai ba shiru kurun ya mata....

*Bayan kwana goma*

Yanke mata farce yakeyi da nail cutter yana mitar rigima irin nata,"ace mutum shi komai nasa rigima ne,yankan farcen ma Senayi dagaske kice ke bazakiyi da kanki ba tsabar shagwab'a Allah momy ne ta sangartar dake" Turo baki tayi "Allah nifa tunda mukazo garinnan ka wani dena sona ni London d'in ma ba dad'i ka mayar dani gida" dariya yayi yace "jiya jiyannan fa muka zo kuma yau da yamma zamuje yawo so karki damu zakiji dad'in London sekince bazaki koma Nigeria ba" bata tanka mishi ba dai har suka gama....

*Bayan wata biyu*

Kwance take ajikinshi Wuraren k'arfe biyu na dare ta sashi a gaba da rigima "Allah ni ya Abdul seka mun Shawarma da creamy La bee's, bazan iya bacci ba yunwa nakeji" hannun shi ya sanya ya shafi fuskarta a hankali "Blossom meyasa kike da rigima ne wai,kisha yoghurt mana,I promise danayi sallan asuba zan had'a miki" shura k'afa ta somayi tana kuka "Ni idan ka gaji dani ka maidani gida sarai nasan wannan yunwar tawa bazata bari nakai safeba kuma youghurt bata k'osar dani" tashi yayi zaune bacci fal idonshi yace "muje na tashi Margie ta had'a miki" (house help nasu)

"Idan ba naka ba bazan ciba Allah" bece komai ba yatashi yaje kitchen dama sunada Shawarma bread shapshap ya hada mata da Creemy d'in ya kawo mata zama tayi ta fara shan creamy ta zauna ta cinye Shawarma din duka biyu,aikam tana idarwa se Amai,shi duk hankalinshi ya tashi ganin aman yaqi tsayawa,se Wuraren k'arfe biyar sannan tasamu bacci tausayi ta bashi ya kasa komawa bacci ya zauna zaman jiranta yayi sallah yaje ya had'a mata wani Shawarma d'in da mango juice koda yazo hartayi wanka kallon Shawarma din kurun tayi ta d'inga kwara amai dak'yar ya lafa,koda ya kamota su dawo d'akin ki tayi

"Yaa Abdul dan Allah ka fitar da abin cinnan kan na koma d'akin bana sanjin warinshi sam" ya kasa ganewa kanta sam tausayinta tamkar yayi kuka koda ya dawo harta kwanta tallafota yayi "Blossom what's wrong with you all of a sudden, me yake sakaki amai wani wurin yana miki ciwo ne?" Shiru ta masa ta kasa ansashi sanda ya kuma tambayarta sannan tace "Bana san warin wannan Shawarma d'in da komai ma" subhanallah ya fad'a shawarma d'in nawane bakyasan warinshi kuma? Tome zakici?" Shiru tayi nanma "Blossom what d u want to eat? Just tel me I will go and prepare it my self right away"

"Yaa Abdul I'm not hungry,i don't feel like eating anything" shiru yayi ya qura mata ido,sosai mamaki ya kamashi ganin batayi minti biyu dagama magana amma harta soma bacci,ba ita ta farka ba se after 12 noon, koda ta farka baya d'akin kai tsaye dining ta nufa kasancewar tanajin maso faffiyar yunwa,wanda a had'e yake da kitchen sabida ginin turawa,tana isowa wurin taji warin abincin da house help dinsu ke girka wa se wani aman ya taso ta dinga kwara rawa ba k'auk'autawa tun tana iya riqe kanta harta kwanta kasa a galabaice... Maggie ce ta taimakabta kaita dakinta ta gyara wurin Abdul yafita, aikam tana komawa d'akin se bacci koda Abdul ya dawo Wuraren la'asar tana bacci tun lokacin,Maggie ce ta sanar masa abinda yafaru

"Kina nufin blossom bataci abincin dana hada mata ba,kenan yau gaba daya ba abinda taci?" Girgiza masa kai tayi alamar hakane da kanshi yaje ya tasheta amma ina baccin takeyi cikeda wahala,seta bud'e ido Sekuma takoma baccin,ba ita ta farka ba se Wuraren magrib ta gota kad'an da uwar yunwa ta farka wannan ya sanya ta sauka zuwa dining da gudu,a parlor taga Abdul Murmushi kurun ta masa ya taso da sauri ya rungumeta "Blossom Sannu ya jikin? Wai inane yake miki ciwo haka?"

"Ba abinda yake mun ciwo nidai zanci abinci" dining ya jata ya soma zuba mata grill fish da sauce se kuma spaghetti, tunkan tafara cin abincin tasoma jin zuciyarta na tashi haka ta daure ta yanki kifin taci,aikam tunkan ta had'yeshi ta soma danna amai, haka tayi amai me yawa kuma a wurin bacci ya sure ta" zuwa yanzu ya fara tsorata musamman da wannan baccin be kawo komai a ranshi ba se mugayen dake binsu da jifa tuni,wanan ya sanya be mayi tunanin kaita asibiti ba anan yake mata aduua da karatun qurani a ruwan zamzam yake mata adua tana sha,wasa wasa Elham sanda tayi kusan kwana biyar a haka dukta rame tayi fari,sauqinta ma tanashan fresh milk da yoghurt su kadaine basa sakata amai ga uban bacci a wuni bata had'a awa uku a farke neman abinci ne kawai ke tashinta.... Yau kuma Elham rigimar lemon tsami takeyi wai da kwad'on rama,andaina samo lemon tsami amma ba zancen kwad'on rama besan inda ze fara nemo mata rama a London ba se rarrashi nta yake amma taqi dena kukan dak'yar ta yadda yamata waffles instead shima baya sakata amai...


Mom Nu'aiym
[1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

23

Riqe yake da ita tanata uban amai,shi kamma yakasa hakuri k'wallan dayake tarewa ne ya silalo,gani yakeyi tamkar anaso ne a raba Hafsat da rayuwarta sabida ya sani tako ina binsu akeyi da bak'ar mugunta,wanke mata bakinta yayi ya dawo d'aki ya kwantar da ita,abinda yafi komai tsoratar dashi shine wannan baccin datakeyi tamkar matacciya aduk sanda ta kammala amai,wanda duk tabi ta rame tayi wani mugun fari har ja takeyi,sabida abinci baya zama a acikinta,wayanshi ya janyo ya dannawa momy kira tana d'agawa yace tamkar wani k'aramin yaro

"Momy wlhy zasu kashe mun Elly na,kin ganta kusan fa sati biyu bataci batasha komai taci se amai,sannan kuma ga uban bacci awuni befi tayi awa biyu a farke ba,Allah momy ni na tsorata" nisawa momy tayi domin kuwai sarai ta fahimci ciki ne da hafsa,tace "Babana kunje asibiti kuwa??"

"Momy nasan asiri ne mezamuje asibiti muyi??"

"Kaga Babana ba'a haka,zatafa iya yiyuwa ba asirin bane ka yarda da Allah mana da khaddararsa wlhy Ko kad'an banji ajikina cewar asiri bane sam,sabida haka lallai yanzu yanzu ka kaimun Mamana gun doctor" cikin sanyi yace "Ina fatan hakanne momy,bari muje" daga nan sukayi sallama ya ajiye wayar,ba tashinta da beyiba amma bata tashiba dolenshi ya qyaleta ahaka ya d'agata zuwa asibitin, Koda Dr ya gama bincikensa se dawowa yayi da fara'arsa ya kalli Abdul dama abokinshi ne,dukanshi yayi a qirji yace "congrats dude u'll soon be a father" shi be gane inda ya dosaba riqe masa hannu yayi yace "Dr Michael what are u saying,waz wrong with her" dukanshi ya kuma yi "Ur wife is one month pregnant,wahalan datake sha kenan Buh zamu bata magungunan daze taimaka ya tsayar da aman dakuma nacin abinci bacci kuwa se yanda Allah yayi" murna a wurin Abdul ba'a magana ko kadan,ihu ya saka ya d'aga Michael yana jujjuyawa dashi......tun daga ranar Abdul ke baiwa Elham extra care ba qaqautawa Alhamdulillah kuma taji sauqi tayi kyau abinta idan ka ganta bazakace cikin ta yayi 4 month ba sabida ko kad'an be taso ba dama abinka ga doguwar mace,zaune tayi tanashan ice cream abinta datayi ordering daga green three tana sha,a ta bayanta taji an warce da fad'a yace "Wai Elham se yaushe zaki fara jin magana nane? Kinsani wannan ba me kyau bane ga Lapiyar ki dama prince na dake cikin ki,gaskia yau dai munyi fad'a bazan miki doki ba da tausa" Turo baki tayi

"Ni komai seka wani ce prince prince,inaso Inshaa dad'i na amma kafisan wannan prince me qaton hanci dani Allah ni wurin momy zan koma" hancinta yaja kad'an "kece dai me qaton hanci ba prince dina ba,kuma wannan ice cream karna k'ara ganin kina shanshi kinmaji na gaya miki" bata rai tayi sosai taqi kulashi,wunin ranar har dare bata kulashi,kuma juyin duniya yayi amma taqi cin abinci dole ya haqura ya qyaleta,cikin dare ta tasheshi

"Ka tashi yunwa nakeji,zanci noodles me yaji sosai" a takaice ya mike cikeda bacci a idonshi "idan kika kuma tashina ina bacci Allah sekinsha mari,bazan dafa noodles d'inba ina ba yanda Banyi dakeba kika k'icin abinci shine dan iskanci zaki zomun da wani raini ina bacci na" sosai ta tsorata da kalamnshi,sabida be tab'a yi mata haka ba,batace masa Komaiba ta koma takwanta shima kwantawar yayi dama acikin bacci yake masifar dama ya kwana da takaicin ta yau ta wahalar masa da prince dinsa dayake fatan samu,tashi tayi taje parlor ta kwanta tanata uban kuka shi gogan ma besan tanayiba baccinsa yakeyi,Koda ya farka da asuba bata nan,ya Zata fushin ne ya sanya ta gudu d'akinta bebi ta kanta ba yaje yayi salla abinshi,tunawa yayi da abinda ya faru daren jiya,da sauri ya zabura ya sani yau akwai yaqi, yaje room nata bata can,ya dawo parlor anan ya ganta a kwance tana rawar sanyi,mamaki yakama shi da sauri yaje wurinta,dagota yayi yace "Subhanallah blossom jikinki zafi sosai meya sameki?" Batace masa komai ba se kukan dataci gaba dayi tana rawar sanyi" hannunshi ya d'aura a saman kanta yaji wani masifar zafi da gudu ya kwasheta zuwa bedroom yafara bata taping sponge seda yaji jikin ya sauka,kanya gama tayi bacci ma,qura mata ido yai yana mamakin rigima irin nata,bata jima tana baccin ba ta farka,dashi ta fara tozali da sauri d'auke kanta,hannun shi ya saka ya juyo da fuskarta tana fuskantarsa "Blossom plss kiyi hakuri kinji,yanzu sanar dani menene kikesan Kici?" Banza ta masa yafi 10 mnt yana mata magana amma ko cikanka bata ce masa ba,tashi yayi a k'ufule yaje kitchen ya had'o mata noodles ya kula yunwa ce ke d'awainiya da ita,mugun b'ata fuska yayi sanda ya shigo ya tadata zaune ya ebo abincin ya bata,kauda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login