Showing 39001 words to 42000 words out of 84332 words
ko kayi tunanin ni Zafar zan had'a shimfid'a da ita" ya fad'i hakan yana yatsina fuska kaman yaga kashi, shi dai Sadiq bai katse shi ba illa zuba mishi ido da yayi yana sauraron shi.
"Zanyi hakan ne kawai dan samowa kai na mafita dan haka stop dreaming cos ni *Ba sonta nake ba* as I said earlier" ya karasa fuskar shi d'auke da sansayan murmushi.
Har yanzu Sadiq ya kasa samun kalma ko d'aya da zaiyi amfani da shi ya gane abinda yake babban kuskure ne, shi kuwa hankali kwance ya zuba min ido yana kare min kallo a lokacin Maryam tana tsaye a kaina kan lalle sai mun shiga cikin masu rawa muyiwa Ya Shamsuddeen liki amma nace mata ba zan shiga zan koma gida saboda zazzab'i da naji yana son rufe ni.
Bata yarda ba sai da ta d'aura hannun ta kan goshi na taji zafi rau, a take taja kujera dake opposite da nawa ta zauna fuskarta d'auke da dumbin damuwa ta kama hannu na tace" Zareefa pls ki kwantar da hankalin ki nasan damuwa da kika saka a ranki shi ya haifar miki da zazzab'in nan,addu'a ya kamata muyi tayi Allah ya dawo dashi lafiya" duk cikin sanyin murya da tsigan lallashi take maganan.
Cikin son sakani dariya tace " ke nifa nafi ki damuwa Yayan mu ya dawo musha biki kin ga da bikin ku ne da muna can high table ba nan ba"
Ta koyi nasara dan murmushin da ban shirya ba ya tsubuce min tare da hawayen da nake shanye su tun d'azu, Maryam ba zata tab'a ganewa ba ni kad'ai ce na san yanda nake ji a cikin zuciya ta.
Rarrashi na Maryam ta fara da kyar ta samu nayi shiru ina ajiyan zuciya duk su Zafar suna kallon mu daga inda suke zaune, mikewa nayi ina gyara head tie dake kaina nace mata " zan tafi Maryam dan Allah kada ranki ya b'aci yanzu haka har na fara jin sanyi yana son rufe ni".
"No babu komai muje in raka ki but tayaya zaki tafi bayan baki da lafiya?" Maryam ta tambaya cikin kulawa.
Zan iya kada kiji komai" na bata amsa ina dafa kaina da nake jin kaman ya fashe.
"Thats d right time " cewar Zafar tare da shuran car keys d'in shi akan table , ba tare da ya juyo ba ya cewa Sadiq" zo muje".
Biyo shi Sadiq d'in yayi yana son yaga mai zai yi da yake cewa wannan shine right time, can gefen wasu flowers ya samu ya tsaya bayan ya fito daga cikin hall, Sadiq shima gefen shi ya samu ya tsaya.
Ko minti 3 basu yi da tsayuwa ba muka fito muma daga cikin ina tafiya a hankali ,har muka iso inda suke ni ban san da mutane a wajan ba naji muryan Maryam tana " Ya Sadiq ina wuni ku"
Sadiq d'in ne kad'ai ya amsa da " lafiya lau Maryam ya kuka fito lafiya kuwa?"
"Wallahi k'awa tace bata da lafiya shine na rako ta zata tafi gida"
"Subhallah Allah ya bata lafiya, amma ba zata iya driving a wannan yanayin ba ko da driver tazo?" Sadiq ya kara tambaya.
"No zan rakata bakin hanya ta hau napep ne".
"Allah ya bata lafiya" yace tare da kallon Zafar daya d'auke kan shi kaman baya jin me suke cewa alhalin duk hankalin shi yana kan mu.
Zungurin Sadiq yayi tare da yi mishi magana da ido, cikin sauri Sadiq yabi bayan mu ya tsaida mu yace " nan anguwan abin hawa yana wahala bari mu sauke ta tunda muma fita zamuyi"
Cikin farinciki Maryam ta fara musu godiya tare da jan hannu na zuwa wajan wata mota daya bud'e mana, da ido nakewa Maryam nuni da ba zan shiga motan su ba ita kuma ta min nuni da babu komai 'yan gida ne, rashin karfin jiki da hajijiya da nake ji ya bata daman tusa ni a bayan motan ta rufe tana d'aga mana hannu.
Kwantar da kaina nayi a jikin seat d'in tare da lumshe ido na fara shak'an wani fitinannen kamshi da ban tab'a ji ba a rayuwa ta, ina ji motan ya fara tafiya amma na kasa bud'e ido na can naji Sadiq d'in yana tambaya ta wani anguwan zasu sauke ni? Sai da naji a jiki na alaman ana kallo na ban damu da in bud'e ba saboda nasan sunan anguwan mu da na fad'a ne ya bashi mamaki kasancewar duka gidajen talakawa ne a anguwan.
"Sai ki nuna mana inda zamu bi mun shigo anguwan naku" muryan Sadiq ya katse min tunani, a hankali na bud'e ido sannan na nuna mishi hanya da zamu bi can nesa da gidan mu nace ya sauke ni anan.
Parking yayi daga gefe na bude kofan na sauka sauka a hankali cikin muryana mai sanyi da baya fita sosai nace " nagode jazakallahu khairan" na kama hanyan gida ina layi,da ido Sadiq ya rakani har na shige ciki.
Gyaran murya Zafar yayi wanda ya dawo da hankalin Sadiq ya juyo yana kallon shi yace" sai ka gaya min ma'anan kawo ta gida sannan dan wulakaci kaja baki kayi shiru na tabbata bata san mu 2 muka kawo ta ba.
"Mu tafi Mallam ba wai ka kama min tambayoyi ba" Zafar yace hankalin sa na kan wayan shi, girgiza kai kawai Sadiq yayi yaja motan suka fita daga layin dan wannan halin abokin nashi ya ci ace ya saba.
Da kyar na kai kaina d'akin mu na zube a gefen Inna da take kwance a kan gado,a firgice ta tashi zaune saboda ta fara bacci kuma bata ji shigowa ta ba.
"Wani irin rashin hankali ne wannan zaki shigo min d'aki ba sallama sannan kuma ki fad'o min a ka sai kace wata 'yar maye, ko daga wajan bikin kika koyo ne..." Shasshekan kuka na da taji shiya dakatar da ita daga fad'an da take min cikin fargaba ta d'ago ni ta fara dudduba jikin na tana tambaya ta meya faru???
"Inna Yaya na yau kusan sati da yin tafiya amma har yanzu babu labarin shi ga wayar shi bata shiga, Inna tsoro nake ji anya yana lafiya kuwa? Yaya na ba zai tab'a mantawa dani ba har na tsawon sati ba tare da yaji lafiya ta ba Inna kin..." Rufe min baki da Inna tayi da hannun ta yasa nayi shiru ina kallon ta hawaye na bin fuska ta.
"Babu abinda ya same shi insha Allah yana cikin koshin lafiya,bana son kina sawa kanki damuwa dayawa ki bari zuwa gobe da safe sai mu san yanda zamu bullowa lamarin" duk cikin rarrashi take min magana hannun ta kuma na kaina tana shafa gashina daya sha gyara ya kwanta yayi lub.
Jin ina sauke ajiyan zuciya kuma numfashi na fita d'aya-daya yasa ta gane nayi bacci, gyara min kwanciya tayi tare da zuba tagumi ta zauna tunani yanda zata bullowa wannan al'amarin domin babu abinda yake d'aga mata hankali kaman ganin tilon 'yar ta cikin tashin hankali, balle ma wannan na soyayya.
Kusan raba dare Inna tayi kan sallaya tana nafilfilu tare da kai kukan ta wajan Rabbi izzatti ya shiga lamuran 'yar ta ya zaba min abinda yafi alkhairi.
Koda gari ya waye da kyar na tashi daga kan gado nayi sallah na kara komawa na kudundune cikin bargo ina rawan dari saboda sabon zazzab'i da ciwon kai daya tsanan ta min, cikin matukar damuwa Inna ta had'a min tea mai kauri ta lallab'a ni na sha kad'an sannan ta b'allo paracetamol 2 ta bani tace in sha zuwa azahar in babu sauki sai mu tafi asibiti.
Cikin ikon Allah ina kwanciya bacci mai nauyi yayi gaba dani sakamakon jiya ban samu ishasshen bacci ba, gaba d'aya fita daga d'akin Inna tayi wai kada tayi wani babban motsi ta katse min bacci anan ta cigaba da ayyukan ta cikin dauriya.
Kaman a cikin mafarki naji waya ta tana ringing, da kyar na bud'e ido na da suka min matukar nauyi.
A zabure na tashi na zauna ganin sunan da na gani yana yawo kan screen d'ina, a hanzarce na d'aga kiran na kai kunne na kamin ya min magana na fashe mishi da matukar kuka kaman zan shid'e.
"Ki fito ina waje" yace min cikin wata murya da ban san shi da ita ba, amma duk da haka ban tsaya b'ata lokaci ba na diro daga kan gado dama da hijabin da nayi sallah asuba a jikina na kwanta dan haka takalmi kawai na zura na fito kofar gida ko lura da Inna dake tsakar gida banyi ba burina shine inje in saka shi a idanu na ko zanji sanyi a cikin raina.
Inda ya saba parking anan na gan shi tsaye ya juyawa kofar gidan mu baya haka kawai sai naji jikina yayi sanyi sosai a haka naja kafa na isa inda yake cikin murya na daya dashe saboda kuka da nasha nayi mishi sallama.
Amsawa yayi yana juyowa muka fuskanci juna, kasa tsaida hawayen ido na nayi ina kallon fuskar shi mai sanyaya min rai nace" barka da zuwa Yaya na aikin ne ya rike haka, wannan karon ka dad'e sosai har ya saka ni cikin matukar damuwa ga number ka bata shiga".
"Lafiya lau mana, hmmm kema dai Zareefa meye abin damuwa anan kin san in nayi tafiya bana saka miki ranan dawowa balle kice har kwanakin sun wuce ban dawo ba sannan tun a baya na gaya miki wajan babu network shiyasa bana iya kira ko a kira ni". Ya bani amsa hankali kwance.
Amsar yasa duk naji wani iri amma na daure tare da share hawayen fuska ta da gefen hijabi na ina sakin mishi murmushin da nasan yana saka shi farinciki nace" hmm ka gama komai ka yanzu dan wallahi in akayi mana aure ba zan yarda kana tafiya kana bari na ba
kafar ka kafata".
Sun glasses na fuskan shi ya gyara yana kallo na ta ciki yace" Zareefa kenan kin ga matsalar ki kenan wanda yasa nake ganin ba zamu iya zama inuwa d'aya ba".
Rass-rass naji zuciyata ta wani irin bugawa da har sai da na kai hannu na kan tsaitin wajan ido a waje nake kallon shi dan na rasa bakin magana, can dai nayi dariya kad'an ganin bai kara ce min komai ba nace " Allah Yaya na ka bar min irin wannan wasan zaka saka zuciya ta bugawa wallahi".
"Wasa!! Wasa fa kika ce, u see kina da matsaloli dayawa a rayuwar ki da in mutum ya duba koya auna ba zai fara ma kusantar inda kike balle maganan aure ya shiga tsakani, ke ko irin kunyan nan da aka san mace dashi baki da ita kullum maganan ki d'aya aure-aure mtsw..." Yaja dogon tsaki yana kawar da kai gefe kaman yaga abin kyama.
Ko kifta idona na kasa yi balle in iya cewa wani abu kawai ji nake wasa yake min jira nake in ga ya juyo yace min wasa yake amma ko kallon inda nake bai kara yiba.
Murya na rawa da son kara tabbatarwa kai na ba mafarki nake ba nace" Yaya na kaine kuwa ,nice fa kanwar ka Zareefa".
"Zareefa my foot me mutum zaiyi da macen da bata kamun kai, tunda can daure zuciya ta nake tare da saka ran zaki canza wata rana sai dai da alamu nayi kuskure dan abin naki kara gaba yake.
Pls ki bar nan in daina ganin ki ko zuciya ta zatayi sanyi saboda yanzu ko ganin ki nayi zuciya tafasa yake, dama abinda ya kawo ni kofar gidan ku kenan kada ki kara kira na a waya cos I don't have time for cheap girls like u". Yace yana min wani kallon tsana.
Wani irin kuka na fashe da shi na juya zuwa cikin gida da gudun tsiya har bana iya ganin gaba na, saura kad'an in mangaje Baban mu da yazo fita yayi sauri ya bani hanya na wuce shi zuwa cikin gida ko waiwayowa banyi ba duk da kira na da yake ta faman yi.
A masifance yace" wani d'an kwal uban ne ya tab'a ki a anguwan nan, bari inje in gani duk wanda na gani mai raba ni dashi sai Allah" ya faman gyara babban rigan shi ya nufi hanyan fita.
Da sauri ya dawo da baya yana zare ido tare da dafa kirji yace" wai-wai dama da wannan hukuman ne?????
[1/26, 7:08 AM] Golden Pen Writer's Assoc: π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉ
π¦
*BA SONTA NAkE BA*
π¦
π¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
β *β GΜΎOΜΎLΜΎDΜΎEΜΎNΜΎ PΜΎEΜΎNΜΎ WΜΎRΜΎIΜΎTΜΎEΜΎRΜΎSΜΎ AΜΎSΜΎSΜΎOΜΎCΜΎIΜΎAΜΎTΜΎIΜΎOΜΎNΜΎ* ββ
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*wΜΆΜΆΡ Ξ±rΜΆΜΆΡ Π²ΡΞ±rΜΆΜΆΡrΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓtΜΆΜΆΡ Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓdΜΆΜΆΓΟuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ pΜΆΜΆΡrΜΆΜΆcΜΆΜΆΡΓvΜΆΜΆΡ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓcΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡΞ±tΜΆΜΆΓvΜΆΜΆΡ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ* β *,Π²ΡhΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟrΜΆΜΆ ΓtΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓlΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ ΡΟuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ΖUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ΖARE!.*
Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖata namu daga farko.
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζara mana Ζarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*19*
"Masha Allah an gode ranka ya dad'e har zaku tafi kenan?" Su Zafar suka tsinkayi muryan Baban mu a bayan su, wani malalacin murmushi yayi sannan ya juyo yana yiwa Sadiq signal da ido.
"Eh Baba zamu wuce tunda jikin nata da sauki sai mun kara dawowa" Sadiq ya bashi amsa ya juya zuwa ga motan nasu.
Zafar gaban Baban mu ya dawo ya tsugunna yana wani sunkuyar da kai kaman mutumin Kwarai yace" nagodewa Allah daya had'a ni da kai Baba, dama na dad'e ina son muyi magana amma ta ki hadani da kai".
"A'a ranka ya dad'e ni kuma gani na abu ne mai sauki me kake bukata?" Baba ya amsa jiki na rawa.
Sai da ya d'an sosa keya alamun yana jin nauyin abinda zai ce yace" Abba ne yake son su zo ayi maganan aure na da ita, shine nace bari in fara fad'a maka in ka amince sai su zo" wannan karan Baba rasa inda zai saka ran sa yaji dad'i yayi ji yake kaman ya kurma ihun murna sai dai ba hali cikin sauri har muryan shi na rawa yace" kai amma yaro yaro ne meye na wani sai an tambaye ni, bayan babu inda zan je kullum ina gida. Ko yau suke so su zo ina jiran su kaji?".
"Toh Baba nagode, mu zamu tafi" yace tare da mikewa ya kara ciro wasu bundles d'in ya zubar da su a gaban Baba sannan ya mike har suka fita daga compound d'in Baba bai dawo daga suman ganin makudan kud'ad'e daya tafi ba.
Sun hau kan hanya ba tare da Sadiq ya kalle shi ba yace " Zafar it's wrong, it's totally wrong".
"And who are you to say so?" Zafar ya tambaye sh yana kara cin magani, Sadiq bai kara ce mishi uffan ba sai ma kara maida hankalin shi da yayi kan tukin da yake.
A nan asibiti kuwa Gwaggo Aisha kasa zaune ta kasa tsaye sai jujjuya ido take wai me yake shirin faruwa ne, bata gama da wancan ba kuma ace ga wani ya bullo? Ita abinda yafi d'aga mata hankali shine ita 'yan matan ta basa samun masu kud'i sai ni, shi wannan kam bayan mai kud'in ne kuma gashi balarabe.
"Wallahi ba zata tsabu ba wai bindiga a ruwa wannan karan sai ta raba ni da komai na jin dad'in rayuwa ko da duk abinda ta mallaka zasu kare ba zata tab'a zuba ido Bintu da 'yar ta su kasance fiye da ita da yaran ta ba.
Kaman wacce aka tsikare ta da allura muka ga zuruf ta mike fuuu tayi waje kaman wata kububuwa,da ido kowa ya bi ta dan tunda su Zafar suka fita babu wanda yayi magana cikin d'akin kowa da kalan tunanin da yake a cikin zuciyar shi.
Tashin hankali da Gwaggo Aisha ta tarar a waje yasa taji kaman ta kurma ihu dan bakinciki, akan idon ta Zafar ya yiwa Baba kyautan makudan kud'ad'e suka shiga mota su dashi kad'ai ta kalla ta san cewa kud'in sa ya wuce duka tunanin ta.
Ganin Baban mu ya hangame baki ya kasa dawowa hayyacin sa tunda yaga ruwan kud'i ya kara tunzura ta, ta taho a fusace ta cikin d'aga murya tace "kai Mallam meye haka?" sai a sannan yaja doguwar ajiyan zuciya ya juyo ya kalle ta,ba tare da yace mata ci kanki ba ya kwashi kud'add'en sa yayi gaba abin shi.
Sosai Gwaggo Aisha ta shak'a wato ya mai da ita mahaukaciya ko? Zasu gani zata nuna musu ainihin true colors d'in ta zasu san da ita suke zancen, sai matsayin ta na da ya dawo ta cigaba da mulkan gidan baki d'aya.
Bayan fitan Gwaggo Aisha Inna abu da Hajara suka mike sukayi mana sallama tare da yi min Allah kara sauki suka fita, cikin