Showing 27001 words to 30000 words out of 56336 words

Chapter 10 - NANA KHADIJA COMPLETE

13 Jul 2025

17316

don Allah Nene wai meyasa bakya son ki zauna damu ne ba fa kya zuwan mana da kinzo ma zaki ce zaki tafi don Allah ki zauna damu mu ma muna bukatarki anan"


kallon ta Nene take tace "wannan ce maganar dama ,? to in zauna inyi muku me na bar dakina nazo na tare anan can ma "yan uwa da Abokan Arziki suna bukatata" Nene tafada tana dada gyara zamanta hankalinta kwance


"mu munfisu bukatar ki wallahi muna so mudinga ganin ki kullum Nene" Na'ima tafada tana karyar da kai domin ta fuskanci in ba haka tayi ba Nene bayadda zatayi ba



"ke bazan zauna ba nace wai tashi kibani guri wato hada baki kukayi ke da "yar uwarki itama tazo tagama ke ma kinzo kina yi ko nace bazan zauna ba ehe!
shima Aliyu zai zo yasame ni domin ai bahaka mukayi dashi ba mutumin banza babu wanda zai sakani in zauna a wata uwa duniya "yan uwana suna can wani guri ni ina wani guri gashi suna bukata ta sosai sabida haka bari Abban naku ya dawo gobe zamu kama hanya mutafi na fasayin sati dayan dana ce zanyi to kaji"""""



kallon ta kawai Na'ima take tana kunshe dariya domin Nene sai wani masifa take batasan ko kasa da sama zata hadu babu wanda zai mai data sai dai in ta tafi ita kadai


"to tunda kin ce bazaki zauna ba kibar mana Dija anan don Allah" Na'ima tafada cikin rarrashin Nena


banza Nene tayi da ita tana cigaba da laziminta


ita ma Na'ima bata kuma cewa komai ba illah zubawa Nene ido da tayi


kusan minti goma babu wanda ya kuma cewa komai cikinsu ita Na'ima tana tunanin yadda zata bulluwa abin ne yayin da Nene take tunanin yadda zata iya zama ba tare da tana ganin "yan uwanta ba domin dai Nene maca ce mai zumunchi kusan kullum atafe take kai wa Jan kai was "yan uwa ziyara da Abin arzikinta shiyasa sukan su"yan uwanta suke ji da'ita domin tana tai maka musu ba kadan ba to a zahirin gaskiya tasan nan dinma suna da bukatarta to Amma gwara nan domin su Acikin dadi suke kuma basu ne mi komai sun rasa ba tasan Allah ne mai ciyarwa da shayarwa Amma mutanen da take taimakawa da abinci suna dayawa kama daga dafaffe zuwa danye.yanzu ya zasuji in sukaji zamanta ya dawo nan gabada daya


tashi Na'ima tayi tace "Allah ya huci zuciyar uwar dakina ni dai zan gayawa yaya Ali cewar kin ce bazaki koma ba kin fison nan yafi dadi dabida haka ke kar Asake a mai dake kano"


Na'ima tafada cike da tsokanar Nene itakam Nene bata ce komai ba har Na'ima ta karaci neman maganarta ta fice daga dakin


to har dare Dija taki kula Nene tasaki ranta tana walwala da kowa Amma taki zuwa inda Nene take


har Abba yadawo yagama sabgoginsa asama ya sauko cin Abinci Dija bata cewa Nene kala ba gashi An hadu a babban falon Anata hira cikin nishadi jameel sai tsokanar Nene yake yana dariya kowa sai dariya yake Amma banda Dija wacce ta kame Akan kujera tana faman zumzumbura bakinta


Nene kam itama ko kallonta batayi ba tace kyayi kyagama ni ko A mafarki ma ban yi zaton zaki.ce zaki zauna Anan ba sabida rashin sabonki da jama'a Nene take fadar haka cikin zuciyarta








jameel ne ya kalli inda Dija take zaune yace "ke wai me A kayimiki kike ta faman cin kunu tundazu"

banza Dija tayi dashi ta dauke i danunta daga inda suke zaune dariya yakama yace "wa kike harara da wannan kwala kwalan i danun naki " ?


harararsa ta yi tace "tubarkalla masha Allah "
ta dauke i danunta da ga kansa dariya ya kuma yi A karo na biyu yace "zo kiga wata sabuwar game mai dadi ce " yafada yana kokarin ciro wayarshi daga Aljihun gaban rigarshi banza tayi dashi bata ce komai ba


ummi dake zaune tun dazu bata ce komai sai yanzu tace "dan Allah ka kyale ta mana kazo kabi ka damu mutane da surutu ba gaira babu dalili"


murmushi yayi yace "wai don Allah ummi me A kayi mata ne"?


"ina ruwanka to" ummin tafada tana harararsa


fa'iza ce da sauri tace" ita da Nene ne fa wai baza ta barta A nan ba "


kallon Nene yayi yace "kamar yaya bazata barta A nan ba"?

ita ma Nene shi take kallo tace" e bazan barta A nan dinba ka wani zuba min ido "


"to ke ina zaki da ta keso kibarta Anan din"?

"bansani ba gobe in sha Allah zan kama hanya na koma in da nafito tunda A bin yazama haka" Nene tafada tana kara kallon inda Ummi take zaune


dariya jameel yake yace "wasa ma kenan Ai sai dai kitafi ke kadai Amma Dija baza ta biki ba tunda tana son zama A nan "


ko kallonsa Nene batayi ba ta ciga da kallonta hannuta rike da carbinta


Abba ne yai sallama domin kai tsaye da ya sauko bai zauna A falon ba masallaci ya nufa sai da ya jira yi isha'i sannan yai A ddu'oinsa sannan ya bar masallacin



kallon jameel din yake yace " ba ka wuce masallaci ba kanaji A na sallah ko"?

"eh Abbah yanzu zan tafi" jameel din yafada yana sunkuyar da kansa


"Ai sai dai kayi taka kai kadai tunda yanzu babu masallacin daza su tsaya jiranka " Abba yafada yana kokarin zama kan kujarar da take fuskantar Nene


tashi jameel din yayi yana faman sosa kansa ita kam Nene harara tabishi da shi tace "sai Aukin surutu jam'i yana huce ka"



bai ce komai. ba ya fice gaba daya daga gidan


to suma su Na'ima ta shi sukayi bayan sun sake gaishe da Abbah

A kabar Nene da Abba A falon Ummi kam tun lokacin da Abbah ya shigo ta tashi ta nufi daynnig domin ta hada masa Abinci


gaishe da Nene Abbah ya kuma yi yace "munyi lafiya Nene"?

cikin kulawa Nene tace " lafiya lau ya Aiki da fama da jama'a"???






"lafiya lau Alhamdulilah "Abban yafada


"masha Allah Allah ya taimaka yayi jagora "

"Ameen ya Allah Nene"

"dazu kina magana babu lokaci ko" Abbah yafada yana kara mai da hankalinsa kan ta


"eh ni da Dija ne baka ga irin rashin kunyar da takewa yarannan ba suna Na'ima ita da wannan yarinyar matar Ali"


"Assha "! Abban yafada yana gyara zamansa hankalinsa gabadaya Akan Nene


"yawwa sai magana ta biyu tasa rigimar wai sai nabarta Anan wai kace zakasa ta A makarntar da fa'iza ta ke zuwa to Ai acan din ma tana zuwa makarantar sabida haka gobe nace dama zamu kama hanya mu koma tunda kun zugata da kai da sauran yaranka"


murmushi Abba yake acikin ransa yace "nasan za Arina dama "


kallonta Abba yake cikin rarrashi yace "haba dai Nene Ai munyi da ke cewar sati biyu zakiyi sai in sa A mai dake ko ni in mai da ke da kaina ko"


"kwarai kuwa haka nace to yanzu na canja shawara gobe nake so in tafi tunda Abin ya zama haka dama kadade kana so ka dauke min Dija daga gaba shine yanzu kuka taro da kai da yaranka kuke zugata yarinyar da bata so natafi ko ina na barta yau ita ce take cewa baza bini ba"


dariya ta kama Abba ganin yadda Nene ta wani hakikance ita fa da gaske tafiya.zatayi


yace "kiyi hakuri Nene kikara kwanaki ko sati ne kiyi don Allah kuma ina rokon Alfarma kibar min Aron Dija don Allah in hadata da "yan uwanta guri guda tana gama skull zan mai do miki da ita "



"wai karatu duk ba karatu bane da za ku wani dame da zancan karatu ehe Acan din ma Ai tana zuwa makarantar "

"Ai nasani" Nene Abba yafada cikin rarrashinta

sannan yace "karatunmu.na nan ba daya suke.da na can ba nan zatafi samun kulawa sosai sannan tana ganin "yar uwarta zatafi mai da hankali"


Shiru Nene tayi bata ce komai ba Abbah yace "ke nake sauraro Nene in baki Amince ba sai kutafi babu damuwa tunda tana debe miki kewa yarinyar"


Ajiyar zuciya Nene ta sauke tace 'shikkenan Ai tunda kun matsa sai ta zauna Amma nasan halin Dija zata iya bijerewa in An kwana biyu tace A maida ita to wannan ne ban Amince ba tunda har kun zabi zamanta Anan din ita ma tana so to sai dai in ce Allah ya bada mai Amfani ilimin"


"Ameen" Abba yace fuskarsa cike da Annuri bai zaci zai shawo kan Nene cikin sauki haka ba


yace "in sha Allahu haka baza faru ba Nene Dija zata zauna samu ilimi mai Amfani"


"to Allah yasa gobe kasa A mai dani Ai mun gaisa ko to zaman me zanyi"

"Aa ' Nene kikara hakuri kiyi mana sati daya mana"
Abba ya fada


kan Nene tayi magana Ali ne yayi sallama cikin falon fuskarshi babu yabo babu fallasa shigowarshi kenan wata irin yinwa yake ji tun safe rabonshi da yasa wani Abin Abakinshi don haka,da ya shigo gidan bai nufi bangarensu ba ya shigo gidan so yake ya fadawa ummi cewar tasa Akai masa Abinci can domin wanka yake son yayi


tun A mota ya cire rigar saman yabar ta cikin wacce suke daura rigar kakin Akai wata mai yan kakakke hannu don haka A hannu ya shigo da rigar

daya hannunashi rike da wayoyinshi da key din motarshi da ma loptop dinshi A motar yake barinta


sun kuyawa yayi yana kwance igiyar ta kalmin shi wanda tun da ya sashi bai cire ba sai dai in zaiyi Alwala


kara sowa yayi tsakiyar falon ya karasa in da Abbah yake zaune yana mika masa hannu


shima Abba hannu ya mika masa sukai musabaha A junansu Alin yace "Abbah barka da dare Abbah"


"yawwa barkanmu dai haidar ya Aikin na ku" ?


"Alhmdulilah mun gode Allah Abba, gobe ma Insha Allah zamu wuce can jahar taraba jalingo domin kwantar da wata tar zoma da ta ke faruwa"

"to masha Allah Allah yakiyaye ya bada sa'a"

"Ameen Ameen" Alin yafada to duk wannan Abin da suke hannayensu nanan rike da na junansu kamar wasu Abokai wannan shakuwar haka take tsakanin Abban da Aliyu



cikin murmumushi Abba yace" yawwa sai ka zauna ka rarrashi uwargidan naka gatanan tace wai gobe take so ta tafi"


kallon inda Nene take zaune Ali yayi yana dan ya mutsa fuska na sabo


ita kam Nene tana zaune zukudinm tana mamakin wannan shakuwa tsakanin uba da dansa kamar wasu Abokai


ita ma shi take kallo tace "meya ka tsareni da wa "yannan ida nuwanan naka kamar na masu jin bacci ko ince kamar na mashaya sai ka dinga faman kikkiftamin ido eh ! , nace zan tafi kuma bance kai zaka mai dani ba ehee!"


kallonta yake fuskarshi A hade sabida dama shi haka yake in dai ya gaji ba ko wane yake gane gajiyarsa ba sai umminsa ita ce take fahimtarsa in dai tanganshi babu wal wala duk da cewar dama ba kasa fai yake dariya ba


cikin ransa kuwa cewa yakecewa wannan Nene masifarfiyace dubi sai wani masifa takewa mutane


fuska babu walwala yace mata "Nene kin Wuni lafiya"?
Ya bar maganar da take tabi ruwa






"lafiya lau " Nene ta fada tana dauke i donta daga kan sa


ta daura A kan Abba sannan tace " ka tambayeshi ya muka yi dashi da yaje tawo damu "


kallon Alin Abbah yayi yace" to kai kaji yaya kuka yi da ita ne"? Abbah ya nuna kamar bai son Abinda suka shirya mata shi da Alin ba lokaci da zai je daukota



cikin yanayin maganarshi yace " bangane A tambaye ni yaya mukayi ba ke ce fa kika ce zaki zo sabida kin dade bakiga danki ba da sauran jikokinki " Alin yafada ida nunsa Akan Nene gashi fuskarsa A hade kamar da gaske


kallonsa Nene take tace "Af Ai ka kware wajan kulla sharri kamar wata mace kai wata macen ma in kana guri duk sharrinta sai ta kauce " Nene tafada tana faman hakikancewa


wata dariya ce ta so ta subucewa Ali Amma ya dake yana yinta A zuciyarsa ganin yadda Nene take kokarin fadowa daga kan kujera sabida masiba


Abba dake gefe shima dariyar ke cinsa Amma ya dake yana kallon Alin
yace "kai bana son shirme tambayarka nake ya kukayi da ita lokacin da kaje dauko ta"


gyara zama Ali yayi yana duba A gogo dake daure A hannusa.sannan ya kalli Abba yace "lokacin danaje ne Abba na tarar da yarinyar nan suna dambe da yara gashi lokacin makaranta Nene bata tura ta da nai mata magana sai tace,Ai makara tayi shiyasa bataje ba,to A dan zaman danayi na lura da yarinyar bata son karatu gashi bata da kunya shine nace kace in tawo da itanan zaka sata A makaranta shine fa,Nene tace ita ma zata zo to kaji yadda mukayi fa Abbah"


kafin Abbah yace komai Ali yaji saukar Abu Ajikinshi kallon gurin yayi romot din tv ne Nene ta cillo masa tana faman harararsa kamar idanta zai fado ita kam bazata iya da sharrin Ali ba ta fada cikin ranta



murmushi yake yana kallonta sannan yace "me nayi miki daga fadin gaskiya kefa kika ce in fadi yadda mukayi dake"


banza Nene tayi dashi bata ce komai ba'shi kam Abbah mai da hankalinsa kan Nene yayi yace "kiyi hakuri Nene duk yadda kika ce haka za'ayi Amma ina neman Alfarma A karo na biyu kiyi hakuri kiyi mana sati daya Anan don Allah in ya so sai in mai dake da kaina "


shiru Nene tayi bata ce komai ba ta mai da hankalinta kan tv da take ta faman yi.ita kadai


wannan ya nunawa Abbah cewar Nene Ta Amince da hakan



Ummin ce ta sakkon daga sama yayin da Dija da fa'iza suke biye da bayanta kara sowa tayi falon tana kallon Ali tace "kai kuma yashe ka dawo"?



kallon Agogo dai ya kara yi Akaro na biyu sannan ya kalli inda umminnasa take yaca "ban jima da shigowa ba ummi kinyini lafiya"?


"lafiya lau nayi ni ya Aikin"?

"Alhmdulilah Ummi. " ya fada

"masha Allah Allah ya tsaremana ku duk inda zaku shiga" 'Ameen ummi"


"gobe in sha Allah zamu tafi jahar taraba can jalingo ummi kiyimana A ddo'a " kallonsa ummin tayi tace " Addu'a kam kullum cikin yinta muke insha Allah zakuje lafiya kudawo lafiya"


"in sha Allahu " Abbah ya fada yana kokarin canja tasha hankalinshi na kan tv


fa'iza dake kusa da Abbah tun zamanta A gun kallon yaya Ali take cikin kayan sojoji sai taga kamar sojojin da suke gani A tv mussaman A tashar mbc 2


bakinta na rawa tace" yaya Ali ina wuni 'kallon inda yaji A na gaidashi yayi dan yasan muryar fa"iza ce Amma bai san sanda ta shigo falon ba sai waccan marakunyar ya gani tunda gurin zaman su daya da umminsa


kallon f'iza yayi fuska babu yabo babu fallasa yace " lafiya lau fa'izan Abba
"

mikewa yayi tsaye yana kallon Nene wacce tayi gurum A zaune ta tsurawa tv ido kamar wata mai fahimatar Abinda suke fada 'yace "wai haka A ke yi An barni ko ruwa baza 'A bani ba in magana Ace duk wacce tazo sai dai tazama bora ni dai babu ruwana duk wacce tafi kyautatamin itace mowa A gurina"


ko kallonsa Nene batayi ba domin ta san neman magana yake dariya yake kasa kasa wanda nene ce kawai ta fahimci Abinda yake


kallon ummi yayi bayan ya mike yace " ummi kisa Na'ima ta kai min Abinci zanje nayi wanka " "to.ummi tace 'kan tarufe bakinta ma sai ga Na'ima sun fito ita da siyama dama sallah suka shiga yi



jiki na rawa Na'ima take kallon Ali wanda ya ke kokarin fita daga falon tace " yaya Ali barka dare Andawo lafiya"?


yana kokarin sanya takalmansa yake Amsawa "ita kam siyama jikinta ne ya mutu tun lokacin da taga Ali cikin kayan sojoji domin bakaramin kyau su kayi masa ba sai. taga kamar bashi ba domin Allu Arjun ya ko ma mata na kasar hindu dan haka da wani irin mayataccan kallo ta bishi har ya fice da ga falon bata samu damar gaisheshi ba domin kasa motsa bakinta tayi sabida tsabar mutuwa da jikinta yayi



jiki A sanyaye Siyama taje tasamu guri ta zauna zuciyarta sai wani irin bugawa take jikinta yai bala,in sanyi sabida wani irin kwarjini da yaya Aliyu yayi mata



kallonta Ummi tayi tace " Siyama zo muje ki kai wa yayan ku Abincinshi domin Ummi bazata tura 'Na'ima ba kamar yadda yace Sabida dalili Siyama ita ce yafi dacewa ta kai masa domin ita yake shirin Aura 'tashi Siyama tayi har yanzu jikinta babu kuzari A ranta take fadin ga bikin zuwa Amma babu zanin daurawa dan ita yanzu shakkar tun karar yaya Aliyu take wallahi



bayan Ummi tabi kchin din tana ta faman zancan zuci


sai da Ummi ta kammala hada masa komai sannan ta kalli inda Siyama take tsaye tace ''gashinan ko"


"to" siyama tafada tana tana kokarin daukar Abinci da Ummin ta hada cikin wani kwando mai kyau



gabanta na faduwa ta fara bubbuga kofar dakin

yana zaune gefen katifarshi daga shi sai gajeran wando 'wani irin gashi duk yayiwa fatar jikinshi rumfa dama tun Asali shi mutum ne mai gargasa A jiki tun yana yaro



rigarshi yake kokarin ya jawo wacce take gefe A ajiye fitowarshi kenan daga wanka ya zauna yana tsane jikinshi da towol ya ji wayarshi tana kara shine ya zauna yana Amsa kiran wayar



kafin ya saka rigar yaji An turu kofar dakin An shigo

me zai gani Siyama ce A tsaye rike da kwando Abincinsa''ita kam siyama da taji An yi shiru ba 'a ce mata ta shigo ba shine kawai ta yanke shawarar shiga domin ita A tunaninta ko yana toilet ne sabida haka shine kawai tai tunanan bari ta shiga ta A jiye masa ta tafi domin har yanzu bata gama da wowa daidai ba tun ganin da tayi masa dazu



Wani irin kallo Ali yake wa siyaman gashi ya tsareta da idanuwanshi masu rikirkikita mata lissafi'"fasa sanya rigar yayi ya mayar ya A je a inda take 'har yanzu idanunshi yana kan siyaman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login