Showing 12001 words to 15000 words out of 154708 words
WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
_Wannan shafin naku ne My Fans kuji daɗin ku, Allah yabar ƙauna._
.
*EPISODE Eight*
*MONDAY*
Ɗahira ce tsaye gaban mirror ta buɗe locker ta ɗau ɗan siririn glass ɗin ta tasanya a idanuwan ta sannan ta juya ta ɗau jakan ta ta fice, Direct ɗakin Maman ta ta nufa, tana shiga ita kuma tana fitowa daga Toilet
Kallon ta tayi tace, "Ke har yanzu ashe baki tafi ba?"
Ɗahira tace, "Eh Mama ban gama shiryawa bane yanzu zan tafi".
Aunty Amarya tace, "to ki kula sosai abinda ya kai ki shi za kiyi, Allah ya tsare".
Murmushi Ɗahira tayi tace, "Ameen Mama na tafi bye".
Ta juya ta fice, a parlour ta tarar da Umma tana zaune
"Umma sai mun dawo".
Umma kallon ta tayi sannan tace, "to adawo lafiya".
Amsa mata kawai tayi ta fice cikin sauri, parcking space ta nufa ta buɗe motan ta da ta kasance ash colour ta shige tabar gidan
Mintuna 15 ya ɗauke ta kafin takai Babban Hospital ɗin wato *AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL* tana shiga tayi parcking motan sannan ta ɗau jakan ta tare da rigan aikin ta tafito, rufe motan tayi kafin ta juya ta doshi cikin Asibitin cikin tafiyan ta na yanga, Lifter ta hau yakai ta hawa na uku kasancewar anan ne Office ɗin ta yake, ko wani Doctors akwai sunan sa agaban office ɗin sa, itama haka an saka Dr. Ɗahira Al'ameen Al'ameen, sai da ta kalli sunan nata tasaki kyakykyawar murmushin ta kafin ta buɗe tashiga ciki, ahankali ta taka har ta'isa kan kujera ta zauna tana ajiye jakan ta tare da rigan aikin ta, files ɗin da ta gani azube akan table ta soma buɗe wa tana dubawa, sai kuma ta miƙe tsaye da nufin fita taji anyi nocking
"Yes come in". Tafaɗa tana kallon ƙofan
Baffa ne ya shigo hannun sa riƙe da wasu files, murmushi suka sakarwa juna kafin ya'iso ciki ya zauna, itama ɗin komawa tayi ta zauna tana cewa
"yayana Barka da safiya".
"Yauwa my sweet sister, hope dai kina enjoyed aikin?"
Murmushi tasaki cike da farin ciki tace, "Yes sai dai ban fara ba zuwana kenan".
Shima murmushin yasaki cike da ƙaunarta a ran sa yace, "Ok ga wasu files ɗin; su ne waɗanda zaki duba anjima da ƙarfe 10:00am, waɗannan kuma na gaban ki na petiens ɗin ki ne Big Dady ya kawo miki, idan kin shirya sai muje in nuna miki Rooms ɗin da suke".
Ɗahira kallon sa tayi har alokacin da murmushi a face ɗin ta tace, "Tom muje".
Miƙewa yayi itama ta miƙe tana ɗaukan farar rigan aikin ta tasaka, sosai rigan yayi mata matuƙar kyau fiye da tunanin me karatu, eyeglasess ɗin ta tagyara tana me bin bayan sa
bayan sun fito atare suka jera suna tafiya suna hira sai zuba murmushi duk kan su suke yi.
⚫⚫⚫
Buɗe ƙofan tayi ta shigo bayan da Shakira ta bata umarnin shigowa, ahankali ta ƙariso ciki tana karairaya cike da son burgewa ta samu waje ta zauna tana kallon Shakira da itama ta zuba mata idanu tana kallon ta, murmushi ne kwance a face ɗin ta tace
"Suna na Dr. Ayush Abdulkarim, Ni ce office ɗina ke kusa da naki kuma nima ɗin ina cikin wanda Hospital ɗin nan suka ɗauke ni aiki ranan Waliman ku, am.. shine nace bari na shigo mu gaisa".
Sai alokacin Shakira tasaki fuskarta tace, "ok Ni kuma Dr. Shakira Abubakar Al'ameen".
Murmushi Ayush tayi tace, "idan babu damuwa zan so mu zama Friends coz tun alokacin Walima naga kin burge ni".
"Why not". Shakira tafaɗa tana ɗage kafaɗa
"Thank you, bari inje zan sake dawowa idan na gama aiki".
Murmushi Shakira tayi mata tace, "ok babu damuwa".
Tashi Ayush tayi ta fice tana me rufo mata ƙofar, murmushi ta saki tana cije leɓe afili ta furta
"Da sannu Burina zai cika, da sannu mafarki na zai zama gaske, tabbas sai na cika burin zuciyata".
Juyawa tayi ta shige office ɗin ta dake kusa da na Shakira.
⚫⚫⚫
Ɗahira bayan ta gama duba petiens ɗin ta ne ta juyo ta nufi office ɗin ta, ta zo karya kwana kenan su kayi karo da wata matashiyar budurwa har files ɗin hannunta suka zube, cikin sauri atare suka ce
"Sorry".
Sai kuma su kayi murmushi sannan Ɗahira tariga ta cewa
"Kiyi haƙuri fa".
Budurwan me suna Safna tace, "no babu komi".
Sannan ta duƙa ta soma kwaso ma Ɗahira files ɗin, itama duƙawa tayi ta taya ta har suka gama kafin ta'amsa na hannun ta ta wuce
Bayan ta Safna tabi da kallo har ta ƙule sannan ta saki ajiyan zuciya tana murmusawa a ranta tace, "Tana da sauƙin kai ba kamar wancan bugaggiyar da mu kayi karo da ita ba".
Juyawa tayi taci gaba da tafiyan ta har ta'iso wajen lifter ta buɗe zata shiga, ji tayi an bangaje ta an shige, tana ɗago kai taga Yusra, a ran ta tana mamakin halinta, yanzu suka gama karo da ita ta balbale ta da tsiya but gashi yanzu ta buge ta bata ce mata tayi haƙuri ba. ɗauke kai kawai Safna tayi ta shige ciki tare da danna Number liftern ta rufe.
Yusra ta soma sauka kasancewar office ɗin ta a hawa na biyu yake sannan ita kuma Safna ta sake latsa number yakai ta ƙasa, wasu files taje ta'amso a reception sannan ta sake hawa ya maida ita block 4 inda anan ne office ɗin ta yake, tana ɗaya daga cikin waɗanda aka ɗauka sabbi.
⚫⚫⚫
Ƙarfe 01:00pm. Ta gama duba marasa lafiyan ta, miƙewa tayi ta shiga Toilet ɗin cikin office ɗinta ta ɗauro alwala ta fito, sallaya ta shimfiɗa ta gabatar da Sallah sannan ta miƙe ta ɗau duk abinda take buƙata ta zuba cikin jaka ta fito ta rufe office ɗin, lifter ta hau ya kaita upstairs na 5 inda anan ne office ɗin mahaifin ta yake, Direct office ɗin ta nufa tayi nocking aka bata iznin shiga, tura ƙofan tayi ta shige da sallama a laɓɓanta
Abbu ganin ƴar shi da yafi ƙauna cikin ƴaƴan shi a office ɗin sa yayi matuƙar saka shi farin ciki, cike da fara'a ya'amsa mata yana cewa, "Mama na".
Ɗahira da itama take faman doka murmushin ta ƙariso ta zauna tana cewa, "Abbu Barka da aiki".
"Yauwa Mama na ya naki aikin?"
"Alhmadulillah Abbu".
Abbu yace, "masha Allah haka ake so, har kin tashi kenan?"
"Eh Abbu, nazo ganin ka ne sai mu wuce tare".
Murmushi yayi yace, "Mamana kenan ai ban tashi ba, ina ga yanzu sai zuwa 04:00pm.".
Gyara zaman ta tayi tace, "to Abbu bari in jira ka sai mu tafi tare".
"A'a tashi kije gida ki huta Mamana ba na son ki zauna nan, kin ma ci abinci?"
"A'a Abbu".
Coolarn dake kan desk ɗinsa ya turo mata yace, "ɗauka ki ci".
Duk da ba ta jin yunwa bata yi masa musu ba ta ɗauka ta soma ci, kaɗan taci ta tsame hannun ta ta shiga Toilet ɗinsa ta wanko hannu ta dawo
Lokacin ne Abbu ya ɗago kai daga rubutun da yake yi yace, "Kin ƙoshi kenan?".
Gyaɗa masa kai tayi sai kuma tace, "Abbu ko ma ban ƙoshi ba idan na koma gidan zan sake ci ai".
"To shikenan Allah ya miki albarka ki kula kinji".
"To Abbu byee".
Ta ɗaga masa hannu sannan ta fice tana murmusa wa, tana fita haraban asibitin ta shige motan ta taja tayi gida, bayan tayi parcking ta fito ta nufi Part ɗin su, sai da ta soma shiga ɗakin Mamanta ta sanar mata dawowar ta sannan ta nufi ɗakin su, wanka ta soma yi ta shirya cikin wata koriyar atamfa ɗinkin Buba ta ɗaura ɗankwalin shi, eyeglasses ɗin ta tasanya ta fito ta nufi kichen, abinci ta ɗiba ɗan kaɗan ta fito parlour ta zauna tana ci, lokacin ne itama Fadila ta dawo
Ɗahira amsa mata sallaman ta kawai tayi taci gaba da cin abincin ta idanuwan ta na kan t.v, bayan ta gama ta tashi tamayar da plate ɗin kana ta wuce ɗakin Mamanta, tana tura ƙofan da sallama Aunty Amarya ta ɗago kanta daga karatun Hisnul Muslim da take yi, ta kalle ta tana amsa mata sallaman
"Mama bari inje wajen Kaka".
Gyaɗa mata kai kawai Maman tayi ta maida hankalin ta kan littafin ta, ita kuma Ɗahira ta fice.
[5/23, 3:55 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
*NASIHA*
_Sallar natsatstsu ba ta samuwa sai an kare sallar daga duk wani abu mai shagaltar wa, a kuma yi ta cikin lokatai waɗanda ba su hana yin Sallah da zuciya ɗaya kuma ba su zama shamaki tsakanin zuciyar sa daga kome ban da tunanin Allah, sai Allah ya haskaka masa zuciyar sa, ya sami basira ya ji daɗin saduwa da Ubangiji. Daga nan sai ka ga Bawa kullum yana mayar da hankali sosai ga wanda yake ganawa da shi. Wannan ma ya fi ƙarfi cikin sujada domin kuwa Bawa ya fi kusa da mahaliccin sa lokacin da yake cikin wannan hali. Don more wa shi wannan muƙami an ji Manzon Allah yana cewa, "Bawa ya fi kusanta ga Ubangiji. Saboda haka ya yawaita addu'a."_
.
*EPISODE Nine*
. Cikin siririyan muryan ta tayi sallama tana shiga ciki
Kaka dake zaune saman Wheel chair ɗin sa yana karatun jarida ya ɗago yana kallon ta, sannan ya'amsa mata sallaman yana cewa, "Maraba lale da matata abar ƙaunata, yau ga matata ta zo gare Ni".
Murmushi me burgewa Ɗahira ta saki tana takowa wajen sa ta zauna a gefen gadon sa tana cewa, "Kakus kenan baka rabo da tsokana ta, sai kace ka daɗe rabon da ka ganni".
Smile yayi yace, "Matata kenan ke baki san yanda nake ji dake bane, yau gaba ɗaya ba na jin daɗin rasa ki kusa dani, Allah da ba don kar in so kaina da yawa ba, da sai ince ki zauna a gida abinki ba sai kinyi aiki ba, tunda gani Mijin ki Ina son ki kusa dani".
Dariya sosai Ɗahira tayi kana tace, "Kaka kenan hmm Mijin kwali ko, don dai a kan ka dai bazan iya ajiye aiki na inzo in tare a wajen ka ba".
Zaro idanu yayi yace, "au kina nufin ban kai matsayin da zan iya auren ki bane na zama na ƙarfen?".
Sai kuma ya girgiza kansa yana dariya yace, "to bari kiji Ni ɗin Ni ne dai Mijin ki da zaki yi alfahari dashi nan gaba don babu wanda zai so ki fiye da yanda nake ƙaunar ki, har da wanda kike son min gori akan sa".
In ban da dariya babu abinda Ɗahira take tiƙawa, sosai Kaka yake ba ta dariya idan suna zancen nan, kuma sai ya fuske tamkar da gaske ne maganar tasa
"Hmm ci gaba da min dariya, ban da abinki ma ni fa taimakon ki zan yi, kin san Real Matata tafi ki komi baza ki haɗa kanki da ita ba".
Wannan karon murmushi tayi tace, "Kakus nawa Ni kaɗai, kaima ban da abun ka me zan yi da tsoho irin ka, idan har matarka ta fi ni komi ai nima Mijina ya fi ka komi, kuma idan kace ƙarya zan kawo maka shi ka ganshi".
Cike da jin daɗi Kakan yace, "yauwa Jabun Matata ki kawo min shi dama na daɗe ina burin ganin sa, kin ga sai a gwada aga wanda yafi kyau cikin mu, ke kaɗai ce dama ban san saurayin ki ba, amma kin ga su rasa kunya ɓeran tanka duk sun kawo min su na gani".
Numfashi Ɗahira taja tana kallon sa don ita bata san ma me zata ce mishi ba, ita da bata taɓa yin saurayi ba taya zata kawo masa wanda zata aura?
"You are silent my wife? I love to see who you will marry more than the other children. Burina kenan inga Mijin ki inga wanda zai iya riƙe min ƴar ƙwai na da amana". Kaka ya ƙarike maganar tasa yana kallon ta da alamun dagaske yake yi
Hannu ta saka ta dafa Wheel chair ɗin sa tana kallon sa, cikin murmushi tace, "to karka damu Kaka, idan ma tsoro kake ji karka mutu baka ga aure na ba ka kwantar da hankalin ka, zan roƙa maka Allah ya barka da ranka har zuwa ranan da zaka ga aure na, me kake ci na baka na zuba Tsoho na?"
Kaka dariya yayi yana jan hancin ta yace, "ja'ira kin ganki".
dariya tayi itama tana kai hannun ta kan hancin nata
"To ki nuna min shi ko a hoto ne mana".
Zaro idanu tayi tace, "kaiii Kaka is so expensive, wannan dalilin ya saka na hana sa yin hoto kar ma wata ta mallaki hoton a rashin sani, don shi ɗin yafi ƙarfin ko wace mace idan ba Ni ba, but idan kana son in ɓurɓusa maka wani abu daga cikin labarin sa nima sai ka bani labari me daɗi ta yanda zanji daɗin baka labarin shi".
"To shikenan yanzu bari in Baki labarin Matata abar alfahari na".
Murmusawa Ɗahira tayi ta gyara zaman ta da kyau har da buga tagumi tace, "to ina ji bani nasha".
Sai da yayi dariya kafin yace, "to tashi ki buɗe drowern can ki ɗauko min jakan ciki, ga ɗan mukullin acikin locker".
Yayi mata nuni da Lockern dressing mirror
Ɗahira da har ta tashi tsaye tanufi wajen ta buɗe ta ɗauko keeys ta kawo masa, shi ya cire mata na drowern ta'amsa taje ta buɗe ta ɗauko masa jakan ta dawo
Zuge jakan yayi hotuna ne da yawa aciki, ya zaro ɗaya daga ciki ya nuna mata
"You see this".
Amsa tayi tana kallo, shi ne tare da Baby a manne da juna, ga duk kan alamu anyi hoton ne lokacin da ake party, murmusawa tayi tana shafa hoton ta ɗago kai tana kallon sa tace, "Wow Kaka gaskiya kun yi kyau sanda kuke Matasa".
Murmushi yayi yace, "ke ma kin faɗa ai, mun yi hoton nan ne lokacin da ake Dinnern bikin mu, hmm bazan taɓa manta wannan lokacin ba, Matata har yanzu na kasa manta ta har yanzu kuma ƙaunar ta na nan daram cikin raina batare da ko ɗigo ya fita ba duk da kuwa ba ta a raye, kin san kowa da irin ƙaddaran da Allah yake jarabtan bawan sa dashi, to Ni soyayyarta shine ƙaddara ta, na so ta matuƙa fiye da tunanin mutum, haka zalika taso Ni fiye da tunanin me tunani, Allah Sarki Baby".
Sai ya saki murmushi yana komar da hawayen idon sa
"I will never forget her in my life. har yanzu zanen halin ta na nan daram cikin raina".
Murmushi kawai Ɗahira take yi tana kallon Kakan nata, sai da ya dasa aya a maganar nasa sannan tace, "Grandpa tell me about the day you first met her".
Sai ko Kaka ya saki dariya me sauti, ga duk kan alamu ya tuna wani abu ne, cikin murmusawa yake cewa, , "This is the day I will never forget in my life, ranan da na haɗu da Babyna matata abar ƙauna ta, lokacin da naje Hospital ɗin da nake aiki, a bakin Hospital ɗin na kusa bige ta da motata, hakan ya saka ta tsorata har ta faɗi taji ciwo a hannu sannan kuma nayi mata asaran shinkafan da take siyarwa".
Ƙwalalo idanu Ɗahira tayi tace, "Kaakaa Talla?"
Dariya yayi yace, "eh Talla, ai talla naga take yi lokacin da muka fara haɗuwa, Hmm my Baby taga rayuwa duk da kasancewar ta ƴar gata don mahaifin ta me kuɗin gaske ne.."
"To amma Kaka ya akayi ta koma yin talla?" Ɗahira ta katse sa da tambayan nan
"Ƙaddara, ko ince canjin rayuwa".
"To Kaka ya kuka ƙare da ita kuma wani kalma ta soma shiga tsakanin ku? And kuma lokacin ne ka soma sonta?" ta sake tambayan sa cike da zumuɗi da son jin labarin
Murmushi Kaka yayi yana lumshe idanun sa, sai ya buɗe a kanta yace, "kalman da ta soma fitowa a baki na shine haƙuri na bata, sannan ne ta ɗago ta kalle ni, tabbas kallon farko da nayi mata na kamu da matsananciyar ƙaunar ta, kuma sai na nemi alfarman tabi ni inyi mata dressing hannun, da farko bata da ninyan bi na but mutanen da suka taru wajen ne suka saka ta taje, kalman da na soma ji a bakin ta har ta tafi sunan ta kaɗai ta faɗa min".
"Kaka kasan me?"
Girgiza mata kai yayi yana kallon ta
Murmushi tayi da ya bayyana ƙananun haƙoran ta tace, "abinda yake bani mamaki da burgewa yanda ka auri Mata har uku masu suna ɗaya, ko a Film da littafai ban taɓa ganin hakan ba, kuma har kayi rayuwa dasu alokaci ɗaya".
Shima murmushin yayi yace, "Allah kenan shi ya ƙaddara hakan, gashi ke kuma kin zo a ta huɗu".
She laughed and said, "Show me the other pictures, ka ga har yanzu bansan sauran matan naka ba ko a hoto ka ƙi ka nuna mana, wancan ƴar uwan taka da tayi aure a ƙauye kawai nasan zan iya tunawa, tunda nasan ta muna yara kafin ta rasu".
Jakan ya buɗe ya kuma zaro wani hoton ya miƙa mata
Hoton ta'amsa tana kallon matashiyar da aƙalla zata kai shekara 19 zuwa 20, fara ce sol kyakykyawar bafulatana, da sauri Ɗahira ta ɗago kai tana kallon Kaka tace, "Laa Kaka wlh wannan sak Big Dady, ba su da maraba kamar tayi kaki ta ajiye".
Murmushi yayi yace, "Matata ta farko kenan *UMMEE NAFEESA,* Mace ƴar aljanna me tsananin haƙuri, dattako da sanin ya kamata, bazan iya fasalta miki kyawawan halayyan ta ba, wannan hoton anyi sa ne gab da