Showing 6001 words to 9000 words out of 62695 words

Chapter 3 - YAR HANNU BOOK COMPLETE

Zee Md   

11 Jul 2025

3839

ta tunda koda yaushe suna da wuta , sai dare ya tsala
sannan take hawa Online tafara chat da Mutanenta , duk irin wannan d'abi'a ta Aysha baisa ta
yi sakaci da ibada ba , tana azumin litinin da Alhamis ga Yawan yin Nafila tare da Azkar ......

Tuni Alhaji Ubale Ghana ya shedawa Aysha ya sauka yana Tahir Gate palace , tuni Aysha
dabara ta fad'o mata tacewa Gogal Shugaban Makarantar datake koyarwa yace taje suna da
taron malamai , aikuwa Gogal batare da ja ba ta amince dan ta yadda da Aysha d'ari bisa d'ari ,
dan duk kud'in da Aysha ke samu a wajen maza tanayiwa Gogal k'aryar Albashin tane na
Makaranta da ake bata shiyasa bata ganewa , kowacce hidima ta gidan nasu itace take d'aukar
nauyin ta , Gogal duk tunanin ta Albashin datake samune take musu wannan hidimar dashi ,
Asalima Makarantar ba zuwa takeyi ba sai taga dama , sannan ba'a biyansu ko ficika kawai
suna kyarwa ne saboda Allah .......

Aysha tayi wanka ta shirya cikin wasu riga da siket na material , sosai d'inki ya kamata
tamkar zatayi motsi kad'an su yage , ta d'auki Hijab d'inta kalar kayanta tasa tare da d'aukar
Nik'af tasa ta d'auki jakar ta wacce tasa wayoyinta tare da kud'in Napep ta fito , sallama tayiwa
Gogal ta kama hanya ta fice daga cikin gidan....
Yauma kamar kullum tana zuwa wucewa ta Majalissar su Jabir , a lokacin daga Jabir sai
wani Abokinsa a zaune , yana ganinta yafara kallonta harta gifta ta gabansu , koda ta wuce
Jabir ya dubi Abokinsa yace " wallahi mutumina ina son ganin wannan matar ko sau d'aya ne ,
koda yaushe zuciya ta tana kwad'aituwa da son ganin fuskar ta tare da cikakkiyar Halittar ta ,
Abokin nasa ya dubesa yace " haba Abokina taya kana ganin mace da irin wannan shigar ta
kamala zaka ce kanaso kaga fuskarta , inkuma ta kasance matar aure to meye ribar ka na
ganin fuskar ta ta ? Murmushi Jabir yayi sannan yace " bazaka gane ba Abokina nifah a jikina
inajin wannan ba matar aure ce ba , kuma dole saina bibiyeta nagano ko wacece ita , Abokin
nasa yace "aikuwa ka had'a kanka da aiki Allah yataimaka , Jabir yace Ameen tare da mik'ewa
yabi hanyar da Aysha tabi........

Aysha na fitowa titi ta tsayar da Napep ta hau tare da gaya masa inda zai kaita , bayan ta
sauka ta bashi kud'insa tare da shigewa cikin Hotel d'in....
Dama tuni Alhaji Ubale ya gaya mata Room number d'in d'akin , tana zuwa tashige batare
da fargabar komai ba , tana shiga tasamesa daga shi sai boxer da singlet yana kwance yayi d'ai
d'ai dashi , yana ganin ta a haka ya tashi yana fad'in " yakuma naga haka Babyn Dad'i ? kinyo
shiga tamkar zakije gidan mutuwa , cire hijab d'in tayi tare da Nik'af take surar ta ta bayyana ,
tuni Alhaji Ubale ya zabga wani ihun murna tare da cewa " wow Babyn dad'i wallahi kin had'u
sosai , ashe haka kike da kyau kika sa banzo gareki da wuri ba ? yau zansha wadak'ata da
wannan lafiyayyen jikin , Wani fari da ido Aysha tayi tana dubansa sannan tayi k'asa da murya
tace " zakaji dad'i mutuk'ar nima zaka jiyar dani , mik'a masa hannunta tayi tana fad'in ciniki
yafara fad'awa sai kaji dad'in , Alhaji Ubale yayi murmushi yace " me kikeci na k'asa na zuba
Babyn dad'i ? ai kome kikeso zanbaki shi basai mun tsaya wani ciniki ba , kinsan Allah bantab'a
ganin mace me irin wannan surar taki ba , nayi aure aure na mata dayawa amman bantab'a
karo da me irin wannan zubin halittar taki ba , mezai hana bazan miki b'arin nera ba kuwa ,

kawai kizo muji dad'in mu Babyn Dad'i Zuma kike ga zak'i ga harbi , wani murmushi Aysha tayi
tare da hayewa ruwan cikin Alhaji Ubale tafara susuta shi , ihu yake tamkar wani k'aramin yaro
ga sambatu dayake mata tamkar wanda yau yafara sanin mace , saida tabari ta birkitashi
sannan suka afka ta'asar su ......
Sosai Alhaji Ubale ya rik'e mata wuta , duk irin Jarumtar Aysha sai da tasha jiki a hannun
Alhaji Ubale , dan shi mutum ne me k'arfin sha'awa sosai da sosai , gashi kwata kwata baya
gajiya tamkar wanda yasha zak'ami , Bayan ta gasa jikinta ta fito ta saka kayan ta har lokacin
Alhaji Ubale a jarabar sa yake , gashi yace shi soyake ta kwana a gurinsa , Aysha duk iskancin
ta bata tab'a kwana a hotel ba ko kuma gidan Namiji , ta yadda tazo ku yini tare zungur amman
bata son kwana sabo da Gogal , Aysha tasaka Hijab d'inta tare da Nik'af tadubi Alhaji Ubale
tace " zan wuce gida kaga Magriba tayi kuma bantab'a kaiwa haka a waje ba , Alhaji Ubale
yace " haba Babyn dad'i saikace wata k'aramar yarinya da zaki dunga tsoron gida , kawai ki
saki jiki mu kwana tare injik'aki da nera , murmushi tayi sannan tace " bazaka gane ba ne
shiyasa banason ko kad'an in b'ata ran kaka ta , dan itace wacce tayimin gata har nazama
hakan kuke tarayya dani , dan haka idai tafiya zanyi kawai ka sallameni , Alhaji Ubale yace
turomin Account number saina tura miki kud'in aciki, take Aysha tatura masa account d'inta ,
dubu d'ari biyar ya tura mata ta mik'e ta fice batare da ta waiwaye saba .......


Sauri takeyi tunda ta sauka daga Napep dan lokacin har anfara kiran isha'i , gani tayi
ansha gabanta ana k'ok'arin d'age mata Nik'af , da sauri taja baya tana fad'in " bawan Allah
lafiya zaka tare ni ? Jabir ya matso daf da ita yace " inason ganin fuskar ki ko sau d'ayane a
rayuwata , Aysha tace " a dalilin me yasa zaka ga fuska ta inkuma ina da aure fa ? murmushi
Jabir yayi sannan yace " nasan ked'in ba matar aure bace , haka zalika nasan wacece ke dan
haka ki nunamin fuskar ki , Aysha tace " wacece ni to kuma meyasa zaka sakamin ido ko
natare maka wani Abun ne ? inaso kabani Hanya zan wuce ina da Abubuwan yi , ta zagayesa
zata wuce da sauri yace " Nasan bakisan waye ni ba to nasan wacece ke , kece aka kira da
*Aysha Babyn Dad'i Zuma kike ga Zak'i ga Harbi ,* wasu kuma da dama suna kiranki da *'Yar
Hannu* , take Aysha ta tsaya tsaf wata zufa na karyo mata ajiki , tabbas ko waye wannan
yagama saninta , dan wad'an nan sunan sune wanda ake kiranta dashi a Social Media , Abinda
yabata tsoro taya wannan mutumin yasanta harya bibiyeta haka ? kuma gashi Uwa Uba acikin
Unguwar su yake , wato kome takeyi akwai masu bibiyar ta kenan ? tabbas saita san waye shi
kuma taya yake bibiyarta haka.........



*Banga Comment ba* ν Ύν΄’


*'Yar* *Mutan* *Kanawa* _Ce_😍🌹
[11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR* *HANNU*
ν Ύν΄’ν Ύν΄’

_NA_
*Zee* *MD*



*Hamdala* *Writer's* *Association* ν ½ν²ͺ
https://www.facebook.com/111403834371046

✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨


*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*




_Page._ 6


Sai Bayan wani lokaci sannan Aysha tafara motsa jikinta a hankali , da k'yar ta iya
sakko wa daga kan katifar datake , a hankali ta mik'e tamkar ana yanka mata jikinta haka takeji ,
d'aukar kayan ta tayi tasaka a jikinta sannan ta tako a hankali ta fito , lokacin data fito bata sami
kowa a cikin wajen ba haka ta fice zuciyar ta nayi mata k'una.......
Tana tafe a hankali tana bin hanya tamkar wacce akayi wa shayi , haka ta k'araso bakin titi
ko gaban ta bata gani , jitayi wata mota tayi ciki da ita tun daga nan bata sake sanin inda take
ba ....

Acan gida kuwa Gogal hankalinta ba k'aramin tashi yayi ba na rashin dawowar Aysha ,
tasan halin Aysha duk inda taje bata gota Magriba take shigowa amman gashi yanzu har Isha'i
ta wuce , tuni zuciyar ta tafara tuhumar ta akan barin Aysha su tafi tare da Farouq d'in batare
da ta bisu ba , a hankali Gogal ta furta " tabbas nayi wauta dana barki kikabi wanda ko asalinsa
bamu sani ba , Allah yatsareki a duk inda kike Aysha , Allah yasa ba macuci bane ko kuma
matsafi.......

Da gudu Hameed ya fito daga cikin motar sa yana salati , mutane suka yi ca ana fad'in "
Innalillahi Allah yasa bata mutu ba , tuni Hameed yace " dan Allah kusamin ita a motar inkai ta
Asibiti , haka aka saka Aysha a motar suka nufi Asibiti da ita.....

Suna zuwa aka bata taimakon gaggawa saboda buguwar da kanta yayi , jini sai zuba yake
da k'yar suka mata allura ya tsaya , ruwa suka sa mata tare dayi mata allurori , Hameed

dayake likita ne shima yana tsaye har suka gama yi mata komai , duban sa Dr. Maheer yayi
yace " Dr. Hameed Baffa yaushe kadawo k'asar tamu bamu da labari ? Hameed yayi murmushi
yace " wallahi yau kwana na biyu da zuwa wani program , ashe tsautsayin indawo ne in kad'e
wannan baiwar Allah , Dr. Maheer yace " Allah yayi sai hakan tafaru shiyasa kadawo , amman
ai babu matsala tunda har ciwon bamai girma bane , Hameed ya dubi gadon da Aysha take
kwance sannan yadubi Dr.Maheer yace " ina ganin kamar akwai wani Abun dayake damun ta
bayan wannan buguwar kan , inaso kabani waje dan Allah zan duba ta , Dr.Maheer yace " ok
badamuwa bari naje office duk abinda kake buk'ata kamin magana , Dr. Maheer ya fice daga
cikin office d'in...

Yana fita Hameed ya k'arasa kusa da Aysha yashiga duba ta , ganin wani farin zuwa ya
bushe gefen k'afar ta yasa yashiga duba jikinta , yana bud'e zanin ta yaga irin ta'asar da akayi
mata , da sauri ya rufe jikin nata yana salati tare da fad'in " su waye suka mata wannan aiki ?
nan ya fita daga cikin d'akin da saurin sa , ba'a fi minty 5 sai gashi da kayan aiki ya dawo , yana
zuwa yashiga yi mata wasu Allurai tare da goge mata jikinta sannan yayi mata wata allura a
gaban ta .......

Sai Bayan awa d'aya sannan Aysha ta farka daga bacci , tana tashi taji duk jikinta yadaina
mata ciwon dayakeyi , kanta ne kawai yake mata ciwo shima kuma kad'an kad'an yakeyi ,
hannu tasa tana tab'a kan nata jitayi ansaka bata bandeji , sai a lokacin ta tuno da Abinda
yafaru da ita tunda ga kan abinda su Farouq sukayi mata har izuwa lokacin da aka kad'eta da
motar , da sauri ta tuno da Gogal dan tasan yanzu tana can hankalin ta atashe mik'ewa tayi da
sauri tana dirowa daga kan gadon , Hameed tunda ta tashi yake kallon ta batare da yayi
magana ba har saida yaga ta diro daga kan gadon , cikin sauri yace " baiwar Allah ina zuwa
haka wannan dirowar da kikayi ? da sauri Aysha ta dubi gefensa sukayi ido biyu dashi ta tsaya
tana kallon sa , shima ita yake kallo har tsawon wasu minty na kafin tace " dan Allah ka k'yaleni
intafi gida nasan Gogal nacan na nema na , Hameed yashiga lallab'ata akan tayi hak'uri zuwa
anjima , Aysha kwata kwata tak'i yadda saboda hankalin ta a tashe yake sosai , duk wani
Namiji yanzu bata son k'ara mu'amala dashi koda ta magana ce , tuni Hameed yaje ya anso
sallama suka fito daga Asibitin , koda suka fito yayi yayi da Aysha ta hau motar sa amman firr
tak'i hawa , haka ya hak'ura ya k'yaleta ta fito tahau Napep ta fad'i inda zai kaita ......


Hameed a baya yake binsu batare da Aysha tagane ba , ana kawota har k'ofar gida ta
shige da gudu batare da ta tsaya ta bashi kud'i ba , me Napep tuni yafito da niyar bin Aysha
cikin gida Hameed yayi saurin tarar sa , nan ya yabashi kud'in motar sa ya shige yatafi...

Hameed duba agogo yayi yaga k'arfe goma ta gota sai sannan ya tuno da abinda ya fito yi ,
da sauri ya nufi mota ya d'auko magun gunan Aysha yadawo k'ofar gidan yatsaya zai k'wan
k'wasa , me shagon gidan sune ya fito da buta a hannu , koda Hameed ya gansa sai yayi masa
sallama sukayi musabiha sannan yabashi maganin yace " dan Allah kamik'awa wata budurwa a
cikin gidan nan , yana bashi ya shige ya nufi motar sa yashiga tare da jan ta yana barin
unguwar......

Koda Aysha ta shiga gida samun Gogal tayi sanye da Hijab sai kai kawo take , tana ganin
Aysha ta taho da sauri tana rik'e ta tare da fad'in " Alhmd Ina kika shiga haka Sayyada ? duk
hankalina ya tashi sosai narasa ina zan nufa , Aysha kasa magana tayi sai kuka data shiga yi a
jikin Gogal , nan danan Hankalin Gogal yatashi tashiga tsoro da farga ba tana fad'in "
kigayamun meya sameki ina Farouq d'in ? ganin yadda Gogal ta furgice yasa Aysha ta
sassauta kukanta tace " hatsari mukai Gogal nida Farouq , Sai sannan Gogal taga bandejin
dake kan Aysha , salati tashi ga yi tana fad'in " shi yanzu ina Farouq d'in yake ko shi ya mutu ne
? sallamar me shagon gidan su itace ta katse Gogal suka kalli k'ofar shigowa , gaisawa yayi da
Gogal sannan yabasu ledar magani yace " gashi inji wani a waje yace abawa Aysha , Gogal ta
ansa yayi musu sai da safe ya juya ya fita.....

'Daki suka shiga baki d'ayan su Gogal nasan jin halin da Farouq d'in yake , ita kuwa Aysha
ko maganar Farouq bataso ayi mata dan duk duniya bawan da ta tsana sama dashi , dan ko
Khalid bataji tsanar sa irin hakan ba , Gogal tace " Sayyada inaso sanin yadda jikin Farouq d'in
yake , Aysha ta lumshe ido saboda takaicin jin sunan Farouq tashiga girbowa Gogal k'arya "
yana can Asibiti shima baiju ciwo sosai ba , dan nafishi jin ciwo sosai Gogal kuma tunda akamin
allura naji sauk'i , yanzu bari nayi wanka nayi sallah na kwanta dan Dr. Yace in samu hutu
saboda ciwon dayake kaina , da sauru Gogal ta mik'e tana fad'in " bari na had'a miki ruwan zafi
sai kifi jin dad'in jikin naki , Allah ya kiyaye gaba mungode Allah ma dayasa ba'aji Babban ciwo
ba ......

Koda Ayaha ta shiga wanka sai data gasa gaban ta sosai , tanayi tana hawaye tare da jin
tsanar duk wani namiji a duniya , tabbas tasha jin yadda k'awayen ta ke bada labarin akan
Macen data kai budurcinta gidan miji , Budurcin mace shine k'imar ta darajar ta da kuma
mutuncin ta a idon mijin nata , yau gashi ita tuni angama bud'e mata shi a titi , yau wai itace
maza hud'u sukayi amfani da ita , Khalid shine na biyar d'insu wanda kuma shine wanda yafara
bud'eta , yanzu meye amfanin aure a gurin ta ma ? meye amfanin tayi aure mijinta yaji ta ba
cikakkiya ba , tabbas sunriga sun b'ata mata rayuwa sun cuceta cuta me muni , dan haka saita
zama *'Yar* *Hannu* yadda zata zamewa duk wani Namiji Mazinaci masifa arayuwar sa , sai ta
d'au fansa akan su Khalid da Farouq da sauran Abokansa , wani murmushi tayi me ciwo tare
da goge k'wallar idanunta tace " *Yan zu zamu fara wasan*, *Mazinatan maza ku shirya tarar
Aysha 'Yar Hannu* sai na zamar muku masifa yadda bazaku k'ara sha'awar aikata zina da
Yaran mutane ba.........




*Nadawo daga yajin aikin Rashin yin Comment*, _amman zan maida Book d'ina na kud'i
tunda bazakuyi Cimment ba_ ν Ύν΄’ν Ύν΄’ν Ύν΄’ν ½ν±Šν ΌνΏ»ν ½ν±Šν ΌνΏ»

*'Yar Mutan Kanawa* _Ce_ 😍🌹
[11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR* *HANNU*
ν Ύν΄’ν Ύν΄’


_NA_
*Zee* *MD*



*Hamdala*

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login