Showing 39001 words to 42000 words out of 140483 words

Chapter 14 - 'YAN UKU COMPLETE

11 Jul 2025

19392

wato Alhaji Sammani so kamar yadda ku ka sani babu Wanda a cikin mu yasan shi wanene wannan Alhaji Sammani a fuska domin ko yaushe b'oye fuskar sa yake yi yana aikata ta addanci sannan yana kashe bayin Allah da basu ji ba basu gani ba da hanyar magungunan da ake sai da su ba tare da k'a ida ba da kuma shigo da makamai suma ba bisa k'a ida ba saboda shi ya mayar da hakan sana'ar sa to wannan karon yana shirin shigo da cocaine k'asar nan tare da makamai kimanin guda dubu d'aya da d'ari biyu da hamsin Wanda mun samu wannan information d'in ne daga jami'in mu da muka tura dubai domin bincike sannan wad'an nan makamai da hodar iblis za'a turo su ne ta jirgin ruwa kamar yadda ku ka sani Alhaji Sammani yana da mataimaka wad'anda bamu san suwaye ba amma muna bincike bakin k'ok'arin mu domin gano su kuma mu d'auki mataki a kansu,"




Wani cikin sojojin ya ce "But sir ta ya zamu gano su bayan komai a b'oye suke yi?"


"Zamu iya gano su amma idan har anyi nasarar kama wad'an nan kaya da kuma wad'an da suka d'auko kayan,"


Wani daban cikin sojojin ya sake cewa "Sir yanzu wanne mataki za a d'auka?"



"Kusan baza mu tab'a bari a cigaba da kashe al'ummar mu ba saboda haka kamar yadda ku ka sani kuma ku ka shaida sannan ku ka yadda da k'warewa da kuma gogewar rundunar MG Abdul-maleek akan aikin su da kuma jajircewar su saboda mun samu nasarori da dama ta sanadin su saboda haka wannan lokacin ma su kasance cikin shiri domin zamu turasu duk wata hanya da mukasan wad'an nan kaya zasu shigo,"



Gyad'a kai kawai Maleek ya yi domin yasan rundunar sa na musamman ne sun samu horo na musamman suna da k'warewa sosai akan aikin su.




Nan suka cigaba da tattauna ta yadda aikin zai kasance kowa na bada tasa shawarar.




Su Sabeeha kuwa suna zuwa ta sauka a mota ta nufi gidan su su Salman na biye da ita ta d'aura nik'af sannan ta shige gidan su.



Faruk dake zaune akan benci Salman ya ba hannu suka gaisa Faruk d'in nayi musu kallon tsoro ganin su sanye da uniform d'in sojoji.




Salman ya ce "Dan Allah muna tambaya ne," Faruk ya ce "To Allah yasa nasani," Salman ya zauna gefen sa ya tare da nuna masa gidan da Sabeeha ta shiga ya ce "Kasan wata yarinya a gidan can mai suna Sabeeha?" Gyad'a kai Faruk ya yi ya ce "Eh nasan ta k'anwata ce Allah dai yasa ba laifi ta yi ba," murmushi Salman ya yi ya ce "Ba laifi ta yi ba amma ita da su waye a gidan?"




Faruk ya ce "Ita da 'yan uwan ta ne Sameeha da Sabreen amma yanzu dukan su basa nan sunyi tafiya sai Mahaifin su kad'ai a gidan," jinjina Kai Salman ya yi ya ce "Amma mamar su fa?" Ajiyar zuciya Faruk ya sauke ya ce "Mamar mu bata nan gaskiya," Nan Faruk ya labarta musu labarin b'atan Mamar su Sabeeha.



Salman ya ce "Mun gode sai anjima," daga haka suka yi sallama suka juya suka tafi.





Sabeeha kuwa da sallama ta shiga gidan su ta samu Abban su zaune akan tabarma yana jan carbi zare nik'af d'in fuskar ta ta yi Abba yana ganin ta yaji wani farin ciki a zuciyar sa domin tun tafiyar su kullum tunanin sa a kansu yake yana tunanin wanne hali suke ciki shin suna lafiya ko a'a sunci abinci ko a'a wataran har kuka yake yi saboda ba mahaifin da zai so 'yan'yan sa suyi nesa da shi bayan ba aure suka yi ba kuma 'ya'ya mata ba maza ba dole hankalin sa bazai kwanta ba.


Itama Sabeeha tsayawa kallon mahaifin nata ta tsaya yi cikin tausayin sa ganin ya rame sosai.




Bayan ta Abba ke lek'awa domin ganin ta ita kad'ai k'arasawa ta yi ta zauna gefen sa ta ce "Abbana Ina wuni?" cikin murmushi ya ce "Lafiya qalau Ina sauran aminan nawa?" Dariya ta yi ta ce "Abba ba tare muke ba suna gida sunce na gaida Kai sosai kuma suma ai zasu zo wataran," ya ce "suna lafiya dai ko?"



"Lafiya k'alau Abba dama bamu zo tare bane saboda Kar Kawu ya samu labari," shiru Abba ya yi sannan ya ce "Amma me ku ke yi a can d'in hankalina yak'i kwanciya," murmushi ta yi ta ce "Abba ka kwantar da hankalin ka aiki muke yi a wani gida Abba mutanen kirki ne sosai suna kula damu sosai Wallahi Abba matar kamar ita ta haife mu," Abba yaji dad'in hakan sosai ya ce "Alhamdulillah ko dai a can za a samo mun surukan nawa?" Dariya Sabeeha ta yi ta ce "Aikuwa Abba Sabreen dear saurayin ta a gidan yake,"



Abba ya ce "Masha Allah," nan suka cigaba da fira Sabeeha ta ce "Yawwa Abba ya aka yi da Sadam kuwa?" Abba ya ce "Yaya ne ya zo har gida yaci mun mutunci sannan daga baya ya aurawa Zainabu shi," tab'e baki ta yi ta ce "Allah ya basu zaman lafiya," Abba ya ce "Ameen," tashi Sabeeha ta yi ta fara kiciniyar d'ora girki domin tasan Abban nasu ba abinda yaci.




Tana girki suna fira har ta gama ta zuba musu tare suka ci suka k'oshi sannan suka yi sallar azahar.




Su Salman kuwa suna komawa NDA suka wuce direct office d'in Maleek suka wuce suna shiga suka samu yana duba wasu files d'aga kai ya yi ya kalli Salman ya ce "Salman zauna mana," zama Salman d'in ya yi Maleek ya ce "Me yake tafiya?"




Salman ya ce "Mun je kamar yadda ka sani 'yan uku ne sannan su kad'ai ne wajen iyayen su sannan a meyere suke sannan su da mahaifin su kad'ai ne a gidan su,"



"Mamar su fa?" Maleek ya tambaya yana kallon Salman.



Salman ya ce "Gaskiya nemar ta aka yi aka rasa ba asan inda take ba kuma tun suna 'yan 3years," tsayawa da abinda yake yi Maleek ya yi yana kallon Salman sannan ya ce "Ina da abubuwa da yawa amma jibi zamu je k'auyen," Salman ya ce "Angama," daga haka Maleek ya tashi suka nufi gida.
[10/25, 7:42 PM] Autar Marubuta: ❤️'YAN UKU❤️





RUBUTAWA DAGA
HAFSAT MAGAJI DABO (RUHAZ)







SADAUKARWA GA
MY DAUGHTER SABEEHA
BILKISU Z.YA'U (🅱️K)
AISHA MAGAJI DABO (AMA)




Page 12


Sabeeha kuwa sai yamma sannan ta yiwa Abban su sallama ta tafi bayan ta ba shi kud'i mai yawan gaske da Ummi ta bata a bashi sannan taje gidan zuwaira mai abinci ta k'ara mata wasu kud'ad'en.




Abba kuwa sai godiya yake yi yana sa mata albarka haka ta tafi tana jin ba dad'i haka ma Abba ji ya yi kamar kada ta tafi domin ya ji dad'in zuwan ta sosai ranar ya ji shi cikin farin ciki.




Sai dare sannan ta isa Kaduna mai keke napep ta samu ta shiga zuwa gida.




Maleek ne tsaye a compound d'in gidan sai kai da komawa yake yi sannan lokaci zuwa lokaci yana kallon agogon hannunsa ji yake yi kamar ya bita k'auyen meyasa zata yi dare haka?



Salman ne ya k'arasa wajen sa ya ce "Ranka ya dad'e da alama fa ta iso sai dai tana gate d'in farko domin bincike," k'aramun tsaki Maleek ya ja sannan ya ce "Kira mun Adam a waya," Kiran sa Salman ya yi sannan ya mik'awa Maleek wayar.



Maleek ya ce "Adam ka barsu su shigo kasan dai abinda ya dace," Adam jin muryar boss d'in su jiki na rawa ya ce "Ok sir," katse wayar Maleek ya yi.




Adam jiki na rawa ya hau mota har wajen Sabeeha ya bud'e mata ta shiga ya ja motar.


Sarai tasan wannan umarnin Maleek ne dan haka sai zuba ido take yi ta ga ta inda zata ganshi amma babu shi sai k'amshin turaren sa da ya cika wajen Adam na tsayar da motar ta bud'e ta fice tunanin fal zuciyar ta domin zuciyar ta fad'a mata take yi Maleek ya hak'ura da ita tunda gashi ko son ganin ta baya yi.




Abinda bata saniba kuwa Maleek baya son su had'u ne saboda ya tabbata idan ya ganta sabuwar soyayyar ta ce zata k'aru a ransa sai dai baya buk'atar hakan tunda har ita bata son shi.




Da sallama ta shiga falon su Sabreen da gudu suka rungume ta suna yi Mata sannu da zuwa har k'asa ta tsugunna ta gaida Ummi cikin fara'a ta amsa tare da tambayar ta hanya da kuma Abban su tace "Lafiya lau Ummi yace na gaida ki," Ummi ta ce "Masha Allah Ina amsawa yanzu kije ki watsa ruwa kici abinci ki huta," ta ce "To Ummi," ta fad'a tare da mik'ewa ta nufi d'akin su.


Bin bayan ta su Sameeha suka yi tana shiga d'akin ta cire hijabin jikinta ta ajiye gefen gado sannan ta cire bak'ar doguwar rigar jikin ta ta d'aura towel.




Su Sabreen ne suka shiga d'akin har suna had'a baki wajen cewa "Abba yana lafiya dai ko?" Murmushi ta yi ta ce "Lafiya k'alau yake yace yana gaishe ku," a tare suka sauke ajiyar zuciya Sameeha ta ce "Ya b'angaren su Kawu fa?" Kallo mai kamar harara Sabeeha ta yi mata sannan ta ja tsaki ta ce "Oho bansani ba amma dai ya aurawa Sadam Zainabu," tsalle Sabreen ta buga ta ce "Wayyo dad'i gaskiya kan Kawu naja irin wannan had'i haka dama yana da wata macen sai ya aurawa Dauda," dariya Sameeha ta yi ta ce "Allah ya shirye ki ai Dauda yana nan yana jiran ki 'yammata," wata uwar harara Sabreen ta makawa Sameeha ta ce "Ya ishe ki malama," juyawa Sabeeha ta yi ta shige toilet tana dariya ganin yadda Sabreen ta yi kicin-kicin da fuska.



Itama Sabreen juyawa ta yi ta nufi k'ofa tana cewa "Kuma yaseen ki ka yi wasa sai na fad'awa ya Fauwaz domin yasan zaman da zai yi dake," da sauri Sameeha ta rik'o hannun ta ta ce "Haba sister mie kinsan fa ni dake ba fad'a tsakanin mu Dan Allah karki fad'a masa harna fara jin kunyar sa tun kafin ki gaya masa ai Sabreen sister sai ya Fauwaz Wallahi ke da shi ba rabuwa wallahi ke da shi ba rabuwa bazar kowa bazar kowa da bazar sa ke kike taka rawa da bazar sa ke ki ke taka rawa," aikuwa Sabreen ta fara taka rawa domin wak'ar Sameeha ta faranta mata sosai.




Dariya Sameeha ta yi ta fice tabar Sabreen ta tik'ar rawa ita kad'ai.


Washe gari Ummi na zaune a falo tana yin waya aka bud'e k'ofar falon aka shiga falon da sallama kallon wajen Ummi ta yi mamaki ne k'arara ya bayyana akan fuskar Ummi domin ganin Umman Nasreen a part d'in ta domin rabon ta da part d'in an dad'e kuma idan har an ganta a b'angaren to ba alkhairi ne ya Kai ta ba, katse wayar ta yi tare da amsa sallamar.



K'arasawa cikin falon Umman Nasreen ta yi ta zauna gefen Ummi ta ce "Aysha Ina wuni," ta fad'a tana washe baki kamar gaske Ummi ta ce "Lafiya k'alau ya yara?"




Umman Nasreen ta ce "Wallahi lafiya k'alau ya su Abdul-maleek?" Nan ma da kallon mamaki Ummi ta bita domin wannan tambayar tafi komai bata mamaki domin tana da tabbacin duk duniya ba wanda Asiya ta tsana kamar Maleek amma yau ita ce ke tambayar lafiyar sa abinda bata tab'a ba kenan tun kuwa Maleek d'in na jariri.




Kawar da tunanin Ummi ta yi ta ce "Yana lafiya,"




"Masha Allah," cewar Umman Nasreen sannan ta cigaba da cewa "Aysha dama zuwa nayi na k'ara baki hak'uri akan abubuwan da suka faru a baya nayi nadama Dan Allah kiyi hak'uri," cikin farin ciki Ummi ta ce "Haba Asiya komai ya wuce," Ummi ta fad'a zuciyar ta fal farin ciki domin dama bata da burin da ya wuce su had'a kansu ba ma tun yanzu ba dan dai kawai ita Umman Nasreen ta nuna ba hakan a ranta ne.


Rinaz da Sameeha tare da Sabreen ne suka yi sallama a falon gaishe da Umman Nasreen suka yi suka wuce banda Rinaz da ta d'auke kai kamar bata ganta ba duk da hararar da Ummi ke aika mata suka haura stairs.



Umman Nasreen ta ce "Aysha wad'an nan tagwayen fa?" Murmushi Ummi ta yi ta ce "Ai 'yan uku ne," nan Ummi ta bata kad'an daga cikin labarin su Umman Nasreen ta ce "Allah sarki ko zaki bani aron d'aya ta dinga zuwa tana yi mun aiki dama Huwaila taje unguwa?" D'an jim Ummi ta yi tana tunani sai kuma ta yi tunanin kar ta hana Umman Nasreen ta yi tunanin wani abu sai kawai ta ce "Shikenan sai Sameeha ta dinga zuwa tana yi miki," Umman Nasreen ta ce "To bakomai nagode," murmushi Ummi ta yi ta ce "Bakomai wallahi," daga haka Umman Nasreen ta yiwa Ummi sallama ta tafi.



Bayan tafiyar ta ne Ummi ta kira Sameeha ta fad'a mata cewar zata dinga zuwa part d'in Umman Nasreen tana ta ya su wasu ayyukan kafin Huwaila ta dawo duk da akwai wasu 'yan aikin Sameeha ta ce "To Ummi,"




Da daddare Sameeha ta samu su Sabeeha a d'aki ta fad'a musu cewar ita fa zata fara zuwa part d'in su Nasreen domin yiwa Umman su Nasreen aiki a d'an razane Sabeeha ta kalle ta saboda tasan dole akwai abinda Nasreen da mahaifiyar ta ke k'ullawa a kansu amma sai bata nunawa su Sameeha ba ta ce "Allah ya kaimu amma sun fad'a miki sanda zaki fara zuwa?" Sameeha ta ce "A'a," Sabreen ta ce "Kai nifa ba abinda Umman Nasreen d'in nan tayi mun amma duk na tsane ta Wallahi," Sabeeha dai bata ce komai ba.



Washe gari da wuri Maleek ya shirya domin zuwa k'auyen su Sabeeha k'arfe 9 ya fito daga part d'in sa ya matuk'ar yin kyau cikin light blue shadda kansa da bak'ar hula yayi kyau iya kyau kullum kamar k'ara masa kyau ake yi wayar sa ya zaro k'irar iPhone 12 pro max ya yi kira.



Sabeeha na kitchen tana k'arasa had'a breakfast Rinaz ta lek'o ta saman bene ta ce "Ummi Yaya yace na fad'a miki zai je unguwa ya k'ira wayan ki bai samu ba," Ummi ta ce "Ooh ni son mai part d'ina ya yi masa da bai son zuwa Allah ya dawo mun da shi lafiya," Rinaz ta ce "Ameen,"




Sabeeha na jin haka ta fice ta k'ofar baya dake kitchen d'in da gudu domin bala'in son ganin sa take yi rabon da ta gansa har ta manta sai dai tana fita lokacin an bud'e masa mota zai shiga bata ga fuskar sa ba sai bayan sa ta hango Salman ya bud'e masa k'ofa ya shiga an rufe sun ja motocin da gudu.



Had'adden k'amshin sa ne ya daki hancin ta da ya sata lumshe ido wanda hakan yaba hawayen da ya taru a idanunta damar zubowa a ranta tace shikenan na rasa shi na tabbata yanzu ba soyayya ta a zuciyar sa haka ta juya ta koma direct d'akin su ta wuce ta sha kukan ta ba tare da kowa ya saniba.



Tana cikin kukan ne bacci ya d'auke ta ta dad'e tana baccin sannan ta farka Sabreen ce ta shiga d'akin tasha kyau sosai cikin riga da skirt na less maroon mai adon flowers silver color ta kalli Sabeeha ta ce "Sabeeha dear kin tashi dama zamu fita ne da my love," jinjina Kai Sabeeha ta yi sannan a hankali ta ce "Sai Kun dawo," kallon ta Sabreen ta tsaya yi sannan ta ce "Dear mai yake damun ki?" Girgiza Kai Sabeeha ta yi ta ce "No bakomai," Sabreen ta ce "Kinsan nasan ki nasan yanayin ki Dan Allah ki dena saka komai a ranki idan har kina son farin cikin mu," Murmushi Sabeeha ta yi ta ce "Bakomai fa kawai kaina ke mun ciwo,"




Sabreen ta ce "To ki sha magani ni na tafi," Sabeeha ta ce "Ok," fita Sabreen ta yi zuwa falo ta samu Fauwaz zaune ya ci ado ba k'arya ta ce "My love muje ko," tashi ya yi ya ce "Ok let's go my heart Ummi sai mun dawo," hararar su Ummi ta yi ta ce "To marasa kunya," dariya suka yi dukan su har Sameeha dake zaune kan kujera tana buga game a wayar Rinaz.



Wayar Ummi ce ta fara ringing ta d'aga tana gama wayar ta mik'e ta kalli Sameeha ta ce "Daughter d'auko mun d'aya a cikin key's d'in motana a bed side drower zani hospital ne Ina da patient," Mik'ewa Sameeha ta yi ta ce "To Ummi," ta nufi stairs bata dad'e ba ta dawo sannan ta d'auki hand bag d'in Ummi ta ce "Ummi muje na raka ki motor," Ummi ta ce "To muje," har mota Sameeha ta raka ta sannan ta koma direct stairs ta nufa d'akin Rinaz.




Tana haurawa stairs Sabeeha ta fito daga kitchen daidai lokacin d'aya daga cikin 'yan aikin Umman Nasreen ta yi sallama.




Amsawa Sabeeha ta yi sannan 'yar aikin ta ce "Dama Hajiya ce ta aikoni ta ce gashi a bawa Sameeha lokutan da zata dinga zuwa aiki ne," tab'e baki Sabeeha ta yi sannan ta karb'a ita Kuma 'yar aikin ta fice.





B'angaren su Maleek kuwa suna zuwa k'auyen sojojin sa suka diddiro daga motocin su suka nufi motar da yake ciki suka zagaye ta Salman ne ya bud'e masa mota ya fito.




Gani ya yi 'yan garin sun taru suna kallon sa har da masu lek'e ta katanga sai dai ana cewa kett zasu gudu saboda kallo d'aya zaka yi musu kasan a matuk'ar tsora ce suke.



Kallon Salman ya yi ya ce "Kayi mun sallama dame gidan," zauren gidan Salman ya shiga ya yi sallama Abba dake zaune bisa tabarma ya amsa sallamar sannan ya ce "Bismillah shigo,"



Shiga suka yi da Sallama Abba ya amsa tare da nuna musu tabarmar da yake zaune ya ce "Ku K'araso ga guri," zama suka yi sannan suka gaida shi ya amsa cikin fara'a sannan ya ce "Sai dai bangane ku ba?" Maleek ya ce "Abba ni sunana MG Abdul-maleek Hamza mai dala wannan Kuma Salman," a tsorace Abba ya ce "Lafiya dai ko?" Domin Abba yasan MG a radio k'arara mamakin ganinsa a gidan sa ya bayyana a fuskar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login