Showing 66001 words to 69000 words out of 138378 words

Chapter 23 - Zakisan koni waye

09 Apr 2026

3283

Dan baki ameera ta tabe don wani haushin anty takeji
"To mom..." Sallama sukayi sannan ta ajiye wayan ta dauki sauran snickers data ci ta rage ta cigaba daci tana korawa da juice.

Bayan kaman minti ashirin wayanta yafara ringing, da sauri ta dauki wayan tana dubawa ta gane zeenat ce don dukda bata haddace digits dinta ba tasan last number, da sauri tayi picking tana cewa
"Shegiya kawas...I miss you die..." Daga chan bangaren zeenat sai jumping take tana cewa
"Babe yaushe kuka shigo kasan?" Ameera kallon gidan da take ciki tayi sannan tace
"Shekaranjiya..."
"Wayyo Allah na...ya amarci...please babe yan mi tori...."
"Ke wallahi banzace...kina nufin..."
"Yes ina nufin ki fadamin yanda first night dinki ya kasance..." Ameera shuru tayi tana tunanin abincewa
"Please babe inajinki..next week iyayen hameed zasuzo...very soon zanyi joining league naku..." Nan take jikin ameera yayi sanyi don ita hameed ya nacewa amma ta nuna ba ajinta bane shi, babu irin wulakanci da bata yi mashi ba, karfin hali tayi sannan tace
"Woww...am happy for you...." Da sauri zeenat ta katse ta dacewa
"Forget... Sis ni kawai tell me...first night da zafi kaman yanda ake cewa?" Ameera shuru tayi hawaye na taruwa idanuwanta, kaman yafadawa zeenat matsala ta takeji amma tasan muddin ta fadawa zeenat tamkar ta fadawa iyayenta ne kuma tasan ko iyayenta sunyi kadan su kwace ta daga hannun Salem.
"Babe..inajinki... Wallahi jikinna har rawa yake...hameed cewa yayi a Hilton zamuyi honeymoon... Allah sai wani irin doki yake..ni har tsoro yake bani..." Ameera goge hawayn daya gangaro mata tayi cikin sanyi murya tace
"babe mu bar wannan maganan sai wata rana..." Da sauri zeenat tace
"This voice is unlike yours...kodai sir Salem yayi maki raga2...ko kuma ince ya koya maki manners of talking.. " ita dai ameera batace komaiba zeenat tacigaba dacewa
"Anyway tunda bakison fadamin... Send me your international photos don na sanki da selfie..." Ahankali ameera tace
"Banyi photo ba..."
"Wallahi kinyi karya...keda koda shop rite muka shiga sai kinyi selfie balle Spain?...please send me jare..."
"Baya bari photo... " tafada kuma dakaji maganan kasan karya take, shuru zeenat tayi for a moment sannan tace
"Babe you are sounding weird... Ko dai wani abu na damunki?.." Ameera kallon wani katon lizard dake jikin bango dan nesa daita tayi da sauri ta mike daga gurin tana cewa
" babe zan kiraki..."
"Ya dawo ne?" Zeenat ta tambayeta
"Eh kawai tace sannan ta katse wayanta.
โค๐Ÿ’›๐Ÿ’œ๐Ÿ’š๐Ÿ’™
ZAKISAN KONI WAYE
๐Ÿ’œ๐Ÿ’™โค๐Ÿ’š๐Ÿ’›

ยฎzuwairat(ummu maryam)


4โƒฃ5โƒฃ


Daki ta shige da gudu ta rufe tana maida numfashi, arayuwa babu abinda take tsoro kaman lizard, lekawa tayi ta window taga yana gurin zaune ko matsawa batayiba, kurya ta koma don gani take yana iya binta, kwantawa tayi ta fara kuka.
"Wallahi nagaji da zama gidan nan...am feed up..." Tafada a tsiwace.
Aranan bata kara fitaba, daga baya ta kira zeenat suka shigaba da hiransu.


๐Ÿ’œโค๐Ÿ’™๐Ÿ’›๐Ÿ’š

Su Abba sunyi niyyan baro palace yau Sunday amma OBJ yace subari har sai sun ga zuwansu ameenatu, to kawai Abba yace mashi.

Abangaren su mami kam tun wayewan gari ta kara shiga sabon tashin sense, gani take korarta daga garin oba zaiyi, da wuri suka kama hanyan kwara daga Ilorin da mom sai yaranta uku tare da tawa da mami don haka aka ce masu kowa ya zo da family dinshi, daman mijin mom baya kasan. Femi ya dinga tukin mota sai kallon tawa datayi takumi, dayayi tuki kadan daya daga kai ya kalli tawa, acikin zuciyanshi yana mugun son tawa amma yasan Sam aladansu babu zancen auren zumunci, mami da mom suna baya sit din karshe sai kuka take mom na rarrashin ta.

Da wuri suka isa palace, da kyar mom ta fito da mami dake tsoron palace kaman ba gidan ubantaba, itama tawa jiki ba kwari ta fito, ahankali femi ya karasa wurin ta
"sis you look pale...what's the problem?" Ahankali ta juyo ta kalleshi sannan tayi forming murmushi karya
"Nothing... Kawai kukan mami ke tadamin hankali" hannu ya dora kan kafadanta
"Don't worry.. Everything will be alright..." Kai kawai ta gyada mashi.

Cikin palace suka shiga kowa ya nufi inda oba da mutanen sa ke zama, daidai lokacin da Abba da su OBJ suka iso, mami da sauran yanuwan ta suka shiga dukkan su sai kallon ta suke kaman ba yar uwansu ba, itakam mami sai mamakin abinda Yusuf sulaiman Abba Salem yake palace din babanta, don tasan shine baban Salem, itakam tawa batasan Abba Salem ba. Daga nesa oba ya kurawa mami ido, Abba da obj gaisawa sukayi da oba sannan suka zauna, mami sam bata daga kai ba, dukkan yaran kwanatawa kasa sukayi sauka gaida oba sannan suka zauna, Abba sai tunanin anya Salem na iya wannan kwanciya kasan, da juyawa yayi ya hangi yarinyan dake kusa da mami nan ya gane itace yarinyan data sacewa danshi zuciya
"She's adorable..." yafada cikin ranshi.
Ji yayi oba nace addua sannan ya fara cewa
"Alhamdulillah..nasan dukkan Ku kuna mamakin abinda yasa na taraku duka wurin nan..." Shuru yayi sannan yacigaba dacewa
"Kunsan am not a king with many words... Kaman yanda kuka Sani ameenatu bata cikin yarana saboda abinda ta aikata...Wanda nasan dukkanku nan kunsani..." Shuru ya kuma yi a wannan lokacin zucyan mami kaman ya fito don yanda take harvawa, ahankali oba yacigaba dacewa
"To kaman yanda nayi announcing na cireta daga cikin yayana...ta ci darajan wayan nan Nigeria legends din ..." Ya fada yan nuna Abba da OBJ da wani abu na yan sarauta dake hannun shi
"Ni oba sadiku ayodele na maida ameenatu cikin yarana!..." Aikam gabaki daya family kwantawa sukayi kasa suna nuna godiyansu, mami sabon babi kuka ta bude tayi kneeling ta rarrafa har gaban oba ta rungume kafafunshi tana kuka tana cewa
"Pami am sorry... Am sorry...." Bata karasa ba ya jawota ya rungume ta..
"I miss you.. My stubborn princess..." Cikin kuka mami tayi daria, ahankali shima yace
"Am sorry my princess... Mulki yasani son hana abinda Allah ya hada..." Mami tana rungume da jikin tsohon ta ta girgiza kai
"No..pami..." Da sauri oba yace where is my granddaughter, mami Dan janyewa tayi ta kira tawa, ahankali ta karasa wurin tayi kneeling gaban oba, abun hannun shi yadan dora bisakanta ya dinga jero adduoi dukkan yan palace na amsawa da ameen. Abba kallon natsuwan tawa kawai yake acikin zuciyanshi yana
"Alhamdulillah Dana yayi dace...Allah yasa kinada hali na gari" shikam OBJ har Dan guntun hawaye ya goge, oba kallon yara da jikokinshi dake kwance kasa yayi
"Bani zaku gaidaba..Ku gaida wayan nan" yafada yana nuna Abba da OBJ, dukkan su juyawa sukayi daga kwance suka fuskanci inda Abba da OBJ suke sukayi masu godiya.

Bayan kaman hour daya Abba da OBJ suka hau jet aka sauke OBJ a osun sannan Abba yayi hanyar yola.

Murna a family dinsu mami kaman anyi aure don gidan shika yayi da family, gasu masu hali da naira mami da tawa ne kadai suka fita daban cikin su, saukin ma kayan da mom tasa aka dayawa tawa sai man da take shafawa, don ba laifi skin dinta ya danfi da kyau da haske.
Aranan aka sauke su mami da tawa acikin wani 4 bedroom apartment dake cikin palace din, sannan aka bawa mami maidens biyu don su dinga yi mata hidima, mami cewa tayi bata bukatan su amma oba yace dole princess saida maiden. Kuma ranar oba ya sanar dasu cewa ranar asabar mai zuwa zaayi bikin maidawa mami da tawa kayan sarauta.

Abba yana isa gida Salem ya rungume shi babu kunya ya dinga jera mashi kisses a hannu
"Kai baka da kunya ko?..." Abba yafada yana daria, shima Salem daria ya dingayi yana cewa
"Am too excited.. Thanks"
"Ai naga yarinyan... She is so adorable... Gaskiya ka iya zabi..." Salem rufe fuskanshi yayi yana daria
"Abba you mean you saw Tawakaltu?..." Yafada cikin exaggeration,
"Eh mana...yanzu suna palace"
"Thank you so much Abba..."
"Son don't thank me, ka kaiwa obasonjo gaisuwa don ya taimaka sosai..."
"Hmmm..he has always been a wonderful person.. " ya fada yana budewa Abba kofan side dinshi. Abba zama yayi Salem ya nufi fridge ya dauko mashi fresh cow milk da ruwa, ruwan ya fara zuba mashi yasha sannan ya zuba mashi milk din ya mika mashi, Salem komawa yayi a zauna yana kallon Abba ya kasa daina murmushi
"Yanzu Abba next week zamu kwara?" Abba Dan kurban milk din yayi sannan yace
"Bafa wannan week dinba sarkin zumudi...I said next week Saturday..." Salem daria yayi
"To Abba... Da wa zamu?"
"Aa... Ban gane da wa zamuba.. Ga uncles dinka sannan ga friends irin su OBJ" ahankali Salem yace
"Abba kana ganin su uncle bazasu nuna tribalism ba kuwa?.." Abba ajiye cup dinshi yayi sannan yace
"Kaji zancen banza...tribalism na marasa ilimine...ai in mutum yana da ilimi yasan komai na Allah ne...kuma kasan su uncle dinka sunfi civilize saboda sun zauna wurare daban2" Dan ajiyan zuciya Salem yayi yana tunanin yanzu babu wani obstacles gabanshi dazai hanashi auren Tawakaltu, yana cikin tunani ummanshi ta shigo, Abba bude mata hannu yayi ya fada jikinshi ya sumbaceta a goshi, Salem relaxing yayi kan sofa yana kallon iyayenshi cikin shaawa da jindadi
"Umma ina nan fa..." Yafada yana daria, Umma juyowa tayi ta kalleshi tana murmushi, zama tayi gefen mijin ta tana cewa
"Alh ka dawo lafiya?"
"Alhamdulillah.."
"Ya OBJ?" tambayeshi kasancewan batasan asalin dalilin dayasa Abba zuwa kwara ba, suna nan zaune Abba ya fada mata komai gameda tafiyan da yayi, Umma shuru tayi don har cikin ranta batason danta ya auri wata yare sannan kuma har ga Allah bata ga aibun Tawakaltu ba ko kadan ita kawai alada ke batason jikokinta suyi exchanging amma who is she to separate what Allah have joined, shuru datayi yasa Salem kallon Abba da zara2 idanuwanshi sannan ya mike ahankali da niyyan tafiya part dinshi, sai lokacin Umma ta dawo hankalinta
"Son ina zaka kuma?" Ahankali ya juyo ya kalleta
"I want to go..." Cikin sanyin murya Umma tace
"Habibi dawo ka zauna" ahankali ya tako zuwa gaban Umma ya durkusa, Abba sai kallon su yake, Salem dafa gwaiwan Umma yayi
"Umma nasan har yanzu baki son Tawakaltu..." Dasauri Umma ta rufe mashi baki
"Habibi stop saying that... Batawa ke banisoba...its just the language.. Tawa is a lovely girl... Amma habibi I give you my 100% support... You have my blessings..." Da sauri ya mike ya rungume Umma
"Thanks so much...insha Allah ba zamuyi regretting ba..." Umma pointed noise mai kama da nata taja
"Allah yasa Ummas habibi.."
"Argggg... " yafada yana shafa inda Umma ta rike mashi hanci. Haka suka cigaba dari hiransu cikin jindadi, amma fa har lokacin Umma bata bar tunanin Yoruba daughter in-law dintaba...ko ya abun zai kasance?.. Oho....


_One week later_

Kowa na inda yake don ameera kam bata da friends sai lizard don tamkar sunsan tana tsoron su, most of the time tana daki, abun takaici tunda Salem yace kar akara barin hinde ta shigo bata kara shigowa ba, sai tayi kusan hour 10 tana waya da friends and family.

Salem kam ya koma aiki amma komai nashi ya koma shiririta don banda waya da princess tawa babu abinda yakeyi kullum saiya sata tayi mashi kuka hankalinshi yake kwantawa, don kullum cikin zolayanta da sabon amaryanshi yake, he's tormenting her to death and he's enjoying every part of it.

Abangaren tawa kam jiya akayi party basu right place dinsu a kwara, mutane da dama sunzo don har da yan nta da AIT, yanzu sabon rayuwa suke ciki don wata babban fashion artist CE mai dauko designer and qualitative dress ta kawo masu dresses, duk Wanda yaga tawa yasan she's royalty don da akwai bead sakale agaban goshint, sannan da akwai bead a kafafunta biyu kaman leglace sai daya a hannun ta na dama, jikin ta yayi mugun kyau amma kuma ta rame sosai don yanda Salem ke tada mata hankali don har cemata yake in yasan inda take zai kawo mata matanshi su gaisa. Rayuwan palace Sam baiyi mata dadi cos cousins dinta are so expose to life, cikin yan Matan babu mai saka normal skirt da riga saidai kaga an saga skirt abaya sosai ko kuma a gefe, datayi dressing sai su dinga cewa
"Princess toyin.. Omo Hausa" wai yar Hausa
๐Ÿ’™๐Ÿ’›๐Ÿ’š๐Ÿ’œโค
ZAKISAN KONI WAYE
๐Ÿ’›โค๐Ÿ’š๐Ÿ’œ๐Ÿ’™

ยฎzuwairat(ummu maryam)

4โƒฃ6โƒฃ

Mata dake kawo kayan sawansu ne ta kaya cike da box dukkan jikonki oba su zama saboda ya fada masu zaayi babban bako a palace,
"Duk jikokina yan mata su shirya...ranar asabar mai zuwa zamuyi bako...kuma bakon sananne ne akasan nan...kuma nayi farin ciki daya ga family din mu worthy.. Kunsan aladan mu dole yazo ya nuna mana wacce yakeso cikin Ku.." Oba yafada masu jiya wajen shagalin su mami, hakan yasa Matan ta bus shike da decent kaya, irin su jallabiya da long gowns, don oba ya bata umarnin kar ta kawo kayan banza don yasan halin jikokinshi.

A wani katon falo a juye kayan ko wacce cikin su shida sai zaba suke, sai da suka zaba sai daya ta juya ta kalli tima
"Wai ina toyin?" Sai lokacin tima ta lura da babu tawa awajen, ajiye kayan ta tayi ta nufi part dinsu tawa.


Tawa na kwance kanta kan cinya mami, sai kallon yanda mami ta chanza cikin kankanin lokaci take, daga idanuwanta tayi tana kallon mami, karaf suka hada ido, da sauri mami ta rufe mata idanuwa da hannun ta
"Ife..wayan nan idanuwan suna bani tsoro.." Tawa daria tayi, sai kuma tayi shuru for a moment sannan tace
"Mami" ta kira ta, Ahankali mami tana shafa kanta
"Yes love" ta amsa mata cikin so da kulawa
"Are you happy?..." Mami taji ta tambayeta, mami shuru tayi tana kallon ta, Ahankali ta gyada mata kai
"Yes..am very happy..na dade banji irin wannan farin cikin ba" tafada tana murmushi, tana shafa kan tawa tace
"Habibty.. A you happy?..." Tawa kara daga manyan idanuwanta tayi ta kalli mami, shuru tayi batace komaiba , Ahankali mami takara cewa
"Love are you happy?..." Ahankali ta girgiza wa mami kai, cikin sanyin murya tace
"Why love" tawa fashewa tayi da kuka tana cewa
"Mami..sir Salem is getting married!" Da sauri mami ta daga ta ta rungume
"Don't cry...kilan hakan shiyafi alkhairi.... Koda ni na amince.. Kina Iya auren Wanda ummanshi bata sonki?.." Da sauri ta girgizawa mami kai
"No..mami..I can't"
"Good... So ki mance dashi..ki koma school.. Nasan insha Allah kafin ki gama degree dinki Allah zai kawo miji na gari..." Cikin kuka tace
"But mami I love him..."
"Habibty you are too young to know what love is..." Mami tafada tana shafa bayan tawa dake kuka kaman ranta zai fita tace
"Mami.. My heart beats for him" mami dai shuru tayi tana rarrashin ta don tasan yarta da kafiya kan abu, suna cikin hakane tima tayi sallama tashigo ,
"Mami meyasa toyin bata zo daukan kayaba?" Tafada bayan ta gaida mami,
"Oh..na mance... Habibty tashi maza kije ki dauki kaya..." Tawa mikewa tayi daga jikin mami tare da goge hawayenta, tima batace komai ba don ta saba da ganin tana kuka
"Mami na meye kayan?" Daria mami tayi, ta tuna mata abinda oba ya fada jiya, komawa tayi ta kwanta
"Gaskiya mami ban zuwa...." Bata idaba mami ta katseta dacewa
"Kai...Aa ..karki yiwa oba gardama.. Kuma aladanmu dole yan Matan mu su shirya in yar uwansu zatayi introducing Wanda zata aura...." Tawa da turo baki tayi
"To mami in ya nuna wacce yakeso...sauran basu jin haushi?..." Dariya mami tayi
"Haushin me?...ai sunsan ba wurin su yazoba..kawai dai alada akebi"
"To mami yanzu Wanda zaizo wurin wa zaizo?"
"Bansani ba..tunda bamu Dade a palace ba" shuru tayi batace komai ba kuma bata mike ba
"Dalla ki taso mu tafi.." Tima ta fada mata, juyawa tayi ta galla mata harara
"Ban zuwa..."
"Come on..follow her!" Mami ta daka mata tsawa, da sauri ta mike ta bi bayan tima. Suna zuwa duk suka fara zolayanta suna cewa
"Omo Hausa oyoyo..." Tawa Dan murmushi karfin hali tayi Don ko kadan basu bata haushi, kayan ta duba taga wani beautiful Arabian gown black my golden stone ta dauka, batayi wasting time ba ta koma side dinshi.

Around 7pm mami ta tafi side din oba kaman yanda ya bukata ta dinga zuwa suna hiran bayan rabuwa, tana zuwa yana dawowa daga masjid, kneeling tayi ta gaidashi sannan ta zauna suka fara hira kaman yanda suka saba, bayan kaman minti ashirin mami tace
"Yauwa...bami..wai waye zaiyi aure cikin yaran mu?" Oba Dan daria yayi
"Nima nan bansani ba..amma abinda yafi bani mamaki shine yanda akayi Dan Yusuf sulaiman ya ga daya daga cikin jikokina..." Da sauri mami tace
"Pami you mean Salem Yusuf sulaiman ne zaizo ?"
"Eh...ko kin sanshi ne...?" Mami shuru ta danyi sannan ta fara bawa oba labarin abinda ya faru tsakanin tawa da Salem har zuwa lokacin da Umma Salem tasa aka dauko mata tawa ta ja mata kunne ta rabu da Salem, mamakine kwance kan fuskan oba
"Hmmm..wonder shall never end..so saboda yarki sukayi sasanci tsakanin mu?"
"I think so bami" har lokacin oba bai bar mamaki ba,
"Allah mai iko... Ashe rabon ki haifi Matan the richest man in Africa yasa kika bijirewa umarni na..." Mami shuru tayi tana tunanin ko oba baiji abinda tace gameda Umma Salem ba, Ahankali tace
"Bami..gaskiya na yarda yanason ta kuma itama tana son shi... Kuma tunda sunyi kokarin gani zaman lafiyanmu Dana hakura ta aureshi.. Saidai matsalan uwarshi batason danta ya auri wata yaren..." Oba shuru yayi kaman sai yanzu ya saurari abinda mami ta fada da kyau
"Ah ah..kai ai danasan haka zance yake da ban basu daman zuwaba..." Shuru yayi for a moment sannan yace
"Kuma gaskiya aure baya dadi indai uwa ta nuna ranshi son auren..sannan ko kadan bamu son abinda zai hana yaranmu jindadin zaman auren su..." Ahankali mami tace
"Yanzu bami.. Meye abinyi..."
"Kinsan we are people with principles sannan bamu karamin magana don haka bazamu hanasu zuwa ba...saidai dasun zo ta nuna bata sanshi ba...so later I can have a discussion with them..."
"OK pami" hira suka cigaba dayi amma oba sai mamaki wannan abuba.

Sai around nine ta koma part dinsu, afalo ta tadda tawa ta tafka uban tagumi, zama tayi gefen ta, tawa kaman jira take ta kwantar da kanta kan kafan mami, Ahankali mami tace
"Habibty..."
"Na'am mami"
"Inason duk Wanda yazo...da an tambayeki kin sanshi kice Aa..." Da sauri ta daga kanta tana yiwa mami kallon tuhuma
"Mami waye zaizo?"
"Kawai just do what I said" tawa maida kanta tayi ta kwanta, kaman an chunkuleta ta mike zaune sannan tace
"Mami in Salem nefa?" Mami kallon mamaki tayi mata sannan tace
"Ko waye.. After

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login