Showing 15001 words to 18000 words out of 138378 words

Chapter 6 - Zakisan koni waye

09 Apr 2026

3230

nan zaune, yana fita Abdul yabi bayan shi da sauri.


๐Ÿ’›๐Ÿ’™๐Ÿ’š๐Ÿ’œโค๐Ÿ’œโค๐Ÿ’›

"Mami kin san abinda ya faru wajen aikina yau?" Tawa ta tambayi mamanta, Matan girgiza kanta tayi sannan tace
"Ya zaayi in sani tunda ba wurin aikimki nakeba" Matan ta amsa mata da yarensu itakuma tawa tana magana da hausa kasancewan tanajin yarensu Amman bata Iya yinshi itakuma Maman bata Iya hausaba sosai, tawa ta cigaba dacewa
"Mami wata yarinyce ta mari wani babban mutum a gaban restaurant dinmu..wai dan ya dan gogi motanta da taxi dinshi... Wallahi mami mutum saida jini ya fita a hancinshi... Ni kuma nayita zagin yarinyan...." Da sauri mami ta katseta dacewa
"Kini...meye ruwan ki ?..kinason ki ja manako?" Dan turo baki tayi
"Mami mutum zai girme brother tajudeen fa..."
"Ina ruwanki koya girmi babanki...please karki jamana matsala... Kinga ta abinci muke ..." Ahankali tawa tace
"Yes mami.. Gobe zan saya maki inhaler ki don madam ta cire daribiyu cikin kudin aikina don na sayawa mitumin da aka Mara cotton wool... Kuma mami cotton wool din ashirin na tsaya Amman Dan zalunci ta cire min Dari biyu" ahankali Matan tace
"Naji Allah ya saka maki..Amman karki kara shiga abinda ba ruwanki"
"Yes mami" tafada sannan ta mike ta sauke abinci dake kan stove cikin Dan karamin tukunya ta zubawa mami sannan ta dauki mafici tana hurawa mami suna labari kaman yanda suka saba.


๐Ÿ’™๐Ÿ’š๐Ÿ’œ๐Ÿ’›โค๐Ÿ’š๐Ÿ’›โค

Aranar da ameera ta mari Salem taje office din babanta take bashi labarin abinda yafaru da kuma yanda ta maka mashi mari, dad dinta jinjina mata yayi yana cewa
"That's daddy's angel" wuri ta samu ta zauna acikin daya daga cikin wasu relaxing sofa dake office din dad, sannan ta kurawa photo Salem da dad dinta dake manne jikin bango. Da alaman Salem baisan ana daukanshi photon ba Amman still he's looking breathtaking. Kurawa photo ido tayi tana tunanin
"Wannan mijin mai rabone" tafada tana lumshe idanuwanta
๐Ÿ’šโค๐Ÿ’›๐Ÿ’œ๐Ÿ’™
ZAKISAN KONI WAYE
๐Ÿ’™๐Ÿ’šโค๐Ÿ’›๐Ÿ’œ
ยฎzuwairat(ummu maryam)

1โƒฃ4โƒฃ

Sai tunani take tana cewa
"Duk wacce Allah ya zaba amatsayin matan wannan bawan Allah ta huta...imagine being married to the most handsome and the richest guy in africa...kam kome kakeso a hannunka..ka hau the latest car...ka saka the latest version of clothes and kaci abinci daga the best cook in Nigeria sannan ka zauna in the best house Kuma ka maida kasashen waje kaman zuwa toilet..." Tana cikin tunanin wata zuciya tace mata
"Ameera ki farka daga mafarkin da kike...don sam baki da chance... Kilan bazaki taba ganin shi ba har ki mutu" bakinta ta tabe tare da gyara kwaciyanta, sai dab da magrub suka koma gida, motan dad dinta gaba nata bayan nashi.

Bayan sun gama dinner wayan dad yayi ringing, yana ganin mai kira ya gwalo idanuwanshi tare dacewa
"Allah ya sa lafia.." Yafada yana picking wayanshi
"Hello sir..good evening.." Shuru dad yayi yana sauraron abinda oganshi yake cewawa sannan yace
"Sir ban bude emails dinava " mutum magana yayi kafin dad yace
"OK sir ..bari in duba emails din" sannan ya kashe wayan.
Ameera ya kira ta dauko mashi laptop dinshi, emails dinshi yafara dubawa, nanfa yaga takardan sallama
"inna lillahi waina ilaihi rajuun..." Ya fara maimaitawa da karfi, mom da ameera sai affan suka nufeshi da tension,
"Lafiya?" Ko wannensu ke tambayanshi.. Amman
"Inna lillahi.." Kawai yake ta maimaitawa... Da kyar ya samu cewa
An koreshi daga aikinshi, ko waccensu salati ta saki, ameera kam hannu ta dora bisa kai tana kuka. Mom kam neman hawaye tayi tarasa, shikam affan kallonsu kawai yake dukda yasan rashin aiki matsalane, hannu dad na rawa ya dauki wayanshi yayi dialing number oganshi, bayan ringing kaman biyar ya amsa
"Me nayi kuka yimin haka...meye laifina?...ple..." Bai gamaba mutum ya katseshi dacewa
"Calm down.. Sir Salem ne ya bada umarni...kuma yace yana kano..so zansa secretary dina ya turo maka details sai kayi amfani da car navigation ka nemi gidan shi..." Da sauri dad ameera yace
"My car don't have a navigation... "
"OK don't worry.. Bari in kirashi..in ya bada address dinshi zan baka sai ka sameshi"
"Thank you... Thank you.." Kawai dad ameera keta maimaitawa ayayinda zufa ke ta keto mashi.

๐Ÿ’œ๐Ÿ’›โคโค๐Ÿ’š๐Ÿ’™

Salem kam bayan sallan ishai ya zauna yana jiran abinda zai biyo baya, bai Dade da zamaba wayanshi yafa ringing, yana dubawa yaga Nigeria head ne ke kiran shi, ajiye wayan yayi bhai dagaba, saida yayi mashi kusan 3 miss call sannan ya daga tare dacewa
"Ya akayi kuma?" Ahankali mutum yace
"Sir..wannan alh umar Adam din yace motan shi baida navigation.. So sir in babu stress ka dan bani address dinka..." Bai karasaba Salem ya katseshi dacewa
"Listen to me...bani da lokacin raba address dina...in bashi da navigation then ya samo ma kanshi sabon aiki...and tell him zan bar Kano jibi..in har na bar Kano kar ya nemeni..." Kas ya katse wayan shi yana murmushi mugunta..Abdul dake zaune a falon yanajin abinda Salem ke cewa yasan ba abu arziki bane.

Abangaren dad ameera kam oganshi na gaya mashi yanda sukayi da Salem ya dora hannu bisa kai yanacewa
"Ina zan samu kudin siyan mota mai navigation... OK bari inkira kB mai motoci.." Yafada kaman wani Mara hankali, kiran kB yayi bayan ya daga yake gaya mashi ko suna da babban mota mai navigation, mutum yace da akwai, dad ameera ya tambayeshi nawa, kB yace 70millions,baki dad ameera ya bude kafin yace
"KB in na kawo jeep dina dana Hajiya sai murano ameera nawa zaka saya?" Daga dayan bangaren kB yace
"Gaskiya alh..tunda Kaine zan sayi jeep dinka dana hajiya million 12 each sannan na ameera million 2..."
"Haba kB wurinkafa nasayi nawa dana Hajiya million 20 each..."
"To alh ai kasuwane..." dad yaga ko an sayi dukkan motaccin gidan bazai saya mashi motan da yake bukata ba,
"To kB don Allah alfarma nake nema...zan baka million 1 ka aramin motan...gobe kawai zanyi amfani dashi sai in maido maka..." Shuru kB yayi kaman mai tunanin wani Abu sannan yace
"To alh Amman million 2 zaka bada..kasan in ba kaiba babu Wanda zan yarda inyiwa wannan alfarman..." Ba musu dad ameera ya amince.

Wacegari tun gari bai wayeba dad ya tafi wurin da kB ke saida exotic car a sharada. Yana nan zaune har karfe tara kafin yaranshi su bude wajen, suna budewa kB yasa yaranahi suka karbi jeep din dad sannan suka bashi wani dunkullen jaguar, da agreement din cewan dad zai kawo million 2 inzai dawo.

KB ya taimaka mashi sukayi activating navigation din motan, cikin kankanin lokaci ya nuna mashi address din Salem, babu bata lokaci dad ya hau motan ya fara tahowa, yana tafiya motan na nuna mashi inda zaibi har ya iso wani makeken gida, horn yayi, mai gadin gidan ya dan bude, rufewa yayi yashiga cikin gidan , falo ya tarda Abdul nan ya fada ga wani mutum chan waje yanason shigowa, Abdul mikewa yayi yaje side din Salem, a lokacin Salem na zaune yana waya da first love dinshi , Salem dan kauda wayan yayi
"Alh Abdul ya akayi?"
"Sir wani mutum ne yake son shigowa..da alaman wurinka yazo..." Salem yasan alh umar ne don babu Wanda yasan address dinshi
"Go and tell him...bani da lokaci yanzu..." Yana kaiwa nan ya cigaba da waya da ummanshi.
Abdul komawa yayi ya fadawa maigadi sakon shikuma mai gadi ya fadawa dad ameera
"Ai kam ba inda zani...zan jirashi har sai ya sami time din" ya fada cikin ranshi.

Salem kam bai fitaba kuma baisa aka kiramashi dad ameera ba, har lokacin sallan zuhr sannan ya fita, shida Abdul, dad ameera na ganin an bude gate ya fito daga cikin mota da sauri ya nufeshi da sauri shima Abdul ya tare oganshi, Salem na daga kai ya ganeshi bata fuska yayi kaman baitaba dariyaba, cikin girmamawa dad ameera yace
"Good after noon s...."
"Who are you?" Salem ya watsa mashi tambaya batare da ya amsa gaisuwanshiba. Dan runtsunawa dad ameera yayi kafin yace
"Sir nine umar adam ..."
"And so?"
"Sir kaikace inzo..."
"Katafi gobe ka dawo am busy..." yana kaiwa nan ya juya ya barshi nan tsaye. Jikin ba kwari dad ameera ya juya yabar wurin, Salem dan juyawa yayi yaga yanda jikinshi yayi sanyi
"Don't give up...cos yanzu na fara treating dinku" ya fada ciki ranshi.

Haka dad ameera yaje ya biya million biyu bai samu biyan bukata ba.
Wacegari ma ya koma Amman da motan shi kasancewan ya riga yasan gidan, kaman jiya ma Salem cewa yayi bashi da time ya tafi gobe ya dawo.
Atakaice saida dad ameera yayi sati daya yana zuwa sannan Salem ya bashi daman shiga falo, yafi hour uku zaune kafin Salem yafito, fuskanshi Sam babu walwala. Zama yayi ya dora kafa daya kan daya yana kadasu ahankali
"What can I do for you.. Don yan kwana kin nan ka hanani sakewa.." Ahankali dad ameera ya dan rutsuna sannan yace
"Sir..aikina..."
"Please mister man...bani da time..talk fast" yafada babu alaman wasa amuryanshi
"Sir ban yi komai ba kuma an aikomin da emails wai anyi firing dina...."
"Bakayi komaiba...kana kirana mara adalci kenan..."
"No sir ba abinda nak...." Salem ya kara katseshi dacewa
"Yes mana...you are telling me ban san aikinaba tunda bakayi komaiba na koreka...anyway nazo garin nan kuma na duba ayyukanka sam batayiba...sannan abubuwan daya kamata abawa local hospitals kyauta saida masu akeyi..." Dasauri dad ameera yace
"Sir ba haka bane...."
"Mr umar are you by any means calling me a liar?..." Da sauri dad ameera ta girgiza kai
"No sir...am sorry.."
"Sorry for your self" yafada yana daria cikin ranshi don yanda mutumin ya zama abin tausayi cikin dan kankanin lokaci
"As I was saying before you interrupted... In na gayawa Bill Gates abinda akeyi azone dinka INA tabbatar maka da komai naka zaa amshe..." Da sauri dad ameera ya runtsuna
"Sir ka rufamin asiri kaman yanda Allah ya rufa maka asiri.."
"Zan rufa maka asiri on one condition..." Da sauri dad ameera ya kara cewa
"Anything sir..." Salem balance yayi kan sofa sannan ya fara cewa
"Na san kasani bani da mata...kuma daga ganinka kana kama da mutanen arziki..so inason acikin family dinka koma yanuwanka ka nema min yarinyan da zsan aura batare da bata lokaciba...and dana so auren yarka saidai bansan ko kanada yarinyan data isa aureba" tunda yafara magana dad ameera ke murnan cikin zuciyanshi.. Imagine ace sir Salem surukinshi ne
"Sir ina da yarinyan data isa aure mana.."
"Really?.." Yafada yana tunanin
"Nasan zaayi hakan" dad ameera yacigaba dacewa
"Yes sir..na baka ita...kuma bana bukatan sisinka..." Cikin ranshi yace
"Daman bani da niyyan kashe sisina kan lalatacciyan yarka..." Dariya karfin hali Salem yayi kafin yace
"That's wonderful of you...Amman wani hanzari ba guduba...bata da Wanda take so?...kar a samu matsala"
"Babu kowai..yanzu yaushe kake bukatan akawo maka mata?" Shuru Salem yayi for a moment sannan yace
"Zan gaya maka..ka amshi number ta wajen guard dina sai ka kirani"
"OK sir" dad ameera har ya mike sai kuma juyowa
"Sir yanzu ina iya komawa bakin aikina?"
"I will let you know" ya amsa mashi atakaice. Dad ameera fita yayi ranshi fal don anashi tunanin ko da bashi da aikinyi ba zaiyi talaushiba muddin yana da Salem amatsayin surukinshi. Sai Allah Allah yake yaje gida ya bawa angel dinshi labarin.

Yana fita Salem ya kira agent dinshi, bayan sun gaisa Salem ya fara cewa
"Inason ka samomin fili a kauyen abuja.."
"Karami ko babba?"
"Girmanta yayi 100by100 sannan kasa afara ginashi right away...sannan ka tabbatar fence din yayi tsawo kaman na prison... Kuma ayi ginin ciki da pure kasa no cement.."
"Sir no cement kuma?"
"Are you deaf?...nace banda cement ko kadan..."
"OK sir...daki nawa?" Shuru Salem yayi kaman bai tunani sannan yace
"Daki biyu sai very small kitchen sannan bathroom da toilet waje daya"
"Alright sir" mutumin yafada sannan Salem ya katse wayanshi.
Dariya ya farayi yancewa
"This is going to be marvelous..."
๐Ÿ’œ๐Ÿ’›๐Ÿ’š๐Ÿ’™โค
*ZAKISAN KONI WAYE
* ๐Ÿ’™๐Ÿ’š๐Ÿ’›๐Ÿ’œ๐Ÿ’›
ยฎzuwairat(ummu maryam)

1โƒฃ5โƒฃ

Dad ameera sauri yake don ya isa gida, yana shiga gidan ko parking kirki baiyiba ya shiga ciki.

Direct dakin mom ya shiga, mom juyowa tayi ta kalleshi kafin tace
"Alh lafia? Ko yauma baka samu ganin shi ba?" Hulan kanshi ya cire yana cewa
"Hajiya.. Ameera ta tayi goshi..." Mom na jin ya kira sunan ameera ta dan bata fuska kaman ba ita ta haifetaba.
"Me akayi kuma?" Dad cire babban riganshi yayi yana cewa
" ameera ta tayi goshi wallahi... Saidai yan bakincik su mutu" dan tabe baki mom tayi
"Wai me yafaru?"
"Ai naga kin bata fuska daga kiran sunan ameera.. To albishirinki"
"Ni ka gayamin abinda ke faruwa" zama dad yayi kusa da mom tare da dora hannunshi kan kafadan mom sannan ya fara cewa
" sir Salem yace yanason ameera da aure kuma na bashi..." Zumbur ta mike
"Haba alh..yace yanasonta ko ka kaimashi tallanta...kuma yarinyan da ba ganin kowa da gashin arziki zaka bawa shugabanku gaba daya ta jawo mana zagi?" Ta danyi shuru ta hadiyi wani abu sannan ta cigaba dacewa
"Gaskiya alh ka sake shawara.." Shima mikewa yayi
"Daman nasan haka zakice...wallahi da ba gabana kika haifeta ba da sai ince bake kika haifetaba...to aure anyi angama...cewa yayi zai kirani..yana kirana yau zansa a daura masu aure a tafi da ita gidan Hutu...ban taba ganin inda uwa take bakin ciki da karuwan yarta ba sai a kanki...rubbish" mom baki ta tabe kafin tace
"Ni ina ruwana...daman tsutsun daya ja ruwa kanshi yake karewa....ayi lafiya" dad baice mata komai ba ya fice, direct dakin ameera ya tafi ,nan ya zaiyana mata yanda sukayi da Salem, dad bata gamaba tayi daka tsalle ta fada jikin dad dinta, shima rungumeta yayi.

Bayan dad yafita, kwantawa ameera tayi kan gado tana cewa
"Daman haka Allah yake biyawa bawanshi bukata? Daman duk abinda mutum ke in har kasa abun cikin ranka zaka samu?.. Imagine me as Salem wife , imagine me as surukin former President... Woowww" tafada da karfi tana tsalle kan gado, wayanta ta dauka tafara dailing number zeenat.

โค๐Ÿ’œ๐Ÿ’™๐Ÿ’š๐Ÿ’›

Bangaren Salem kam hankalishi kwance don yanzu kwana uku da maganan shi da dad ameera, gini kam ana chan anayinta abinka da mai naira har an gama fence din kuma da aka turowa Salem hoton cewa yayi yayi kadan akara tsawon fence din, wani irin dogon fence mai kama da tower akayi sannan aka fara ginin ciki, shima har sunkai tsakiya aka turawa Salem hoton, shima cewa yayi dakunan sunyi girma a ragesu.

Yau yana kwance murmushi ne kwance a fuskanshi.. Kona meye oho, wayan shi ya dauka yasa Abdul ya kira Makeup artist dinshi.

Around 5pm suka bar gidan, suna zuwa daidai inda ameera ta mareshi ya fara kallon wurin kawai sai ya hangi kaman yarinyan data siya mashi cotton wool lokacin da yake nasal bleeding, kallon Abdul yayi kafin yace
"Alh wancan kaman yarinyan data siyamin auduga ko..." Shima Abdul kallon wurin yayi
"Yes sir..itace kuma kaman abun hawa take jira...kilan ta tashi daga wurin aiki" Salem rage gudun abun hwanshi yayi yana cewa
"Wane aiki take?" Abdul murmushi yayi
"Sir bakaji sanda madam din datakewa aiki tana zaginta wai ta kashe mata kudi har da cewa saita biyata..." Shuru Salem yayi kaman mai tunanin wani abu sannan yace
"Sam banjiba ai yarinyan nan tana marina wuta ya daike min Amman naga sanda ta sayi auduga ta baka...Amman baka gayamin aikn datake ba" suna zuwa daidai inda take Abdul nacewa
"Inajin abinci suke saidawa don naji matan nacewa tawuce ta bawa mutane abinci" Salem tsaida taxi yayi inda take, tawa na ganin taxi ya tsaya sai tadanyi baya kadan, Salem dan fiddo kanshi yayi ita kuma ta kura mashi ido tana tunanin ina nasan wannan mutum, Salem zai bude baki yayi magana ta fara cewa
"Lah...Ashe kaine..ina wuni"
"Lafia lau...kinyi tunanin na mutune?" Dan murmushi tayi Wanda ya bayyana one side dimple dinta
"Aa..kawai banyi tunanin kai bane"
"To naji..zo in baki lift"
"Aa nagode..." Kura mata ido yayi for a moment kafin yace
"I insist.. Ko kina tsoron kar..." Dan daria tayi ya dan saci kallon hakoranta
"Meye na tsoro.. Kawai dai nagode.." Shima Salem Dan daria yayi itama tawa tadan kalleshi tayi saurin kauda kanta
"Please ki shigo in ajiyeki" kallon Abdul tayi kafin tace
"wannan passenger da ka dauko fa..kar mu shiga hakkinshi..." Abdul murmushi yayi
"Kar ki damu ni abokinshi ne..." Tawa Dan tsayawa ta yi kaman batason shiga kuma da ka ganta da akwai Dan alaman tsoro tare daita, kara daga kai tayi ta kallesu suka hada ido da Salem, cikin ranshi cewa yayi
"Wannan yarinyan da akwai manyan idanuwa kaman na mage" ahankali ta bude bayan motan tashiga , tana shiga ta dan kwantar da kanta bayan seat da alaman gajiye take, Salem juyawa yayi ya kalleta
"Hajiya ina zaa kaiki?"
"Oh sorry...tukuntawa zaa kaini"
"Babu nisa ma" inji Abdul, Salem fara tuki yayi, yana cikin tafiya yadan saci kallon ta ta mirror yaga sai lumshe ido take ahankali, cigaba da kallonta yayi har ya mance da tuki yake, saida ya kusa bige wani sannan yadawo hankalinshi, bai dade ba yakara kallon ta wannan karin itama ta daga kanta sukayi ido hudu dashi, murmushi yasakar mata kafin yace
"Nagode da taimakonki fa..."
"Haba ba komai...Amman kabani mamaki..." Daga kanshi yayi ya kalleta
"Da nayi me?" Cikin irin jin haushin nan tace
"Da baka rama marin datayi makaba...mazan hausawa da akwai hakuri wallahi da mazan yarenmune da yarinyan nan bata kara marin mace yaruwanta balle namiji" Salem Dan murmushi yayi yana tunanin
"Bakisan abinda ke faruwa don ina tabbatar maki when am done with her ko dabba bazata iya tabawaba balle mutum" dan murmushi yayi
"To ya zanyi tunda ni talaka ne...wai ke wace yaraece?" Ya tambayeta, Ahankali tace
"Yoruba" ido Salem ya kwalo don sam bata kama da yare
"Kambu " yace cikin ranshi sannan yace
"Yoruba? Amman meyasa kike Hausa kaman bahaushiya?"
"Nan aka haifeni"
"Wow..ya ake cewa kina da kyau da yarenku?" Dan daria tayi shima Abdul yayi
"Ni ban iyaba Amman inaji"
"Baki iyaba kwata2? " Dan girgiza kanta tayi sannan tace
"Naiya few words" Dan daria yayi sanda Abdul ya nuna mashi hanyan dazasu bi, saida yabi hanyan sannan yacigaba dacewa
"To ya ake cewa my friend da yarenku?" Ahankali tace
"Ore mi" dan daria yayi kafin yace.
" zaki zama oro mi?" Cikin daria tace
"Ba oro mi naceba...I said ore mi" dukkansu daria sukayi kaman sun wani dade na sanin nuna
"To naji..zaki zama ore mi?" Shuru tayi kaman bada ita yakeba.
Saida ya kara cewa
"Baki bani amsaba?" Kallon shi tayi ta mirror suka hada ido tayi murmushi tare da kauda kanta
"Cewa nayi will you be my ore mi" ahankali tace
"You are funny.. Ka taba ganin inda mace

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login