Showing 27001 words to 28895 words out of 28895 words

Chapter 10 - GIMBIYA YUSRAH

12 Jul 2025

1659

hanunta rike da leda



Sabeer tausayin su yakeji hakama Fahad


Saida yusrah tayi kuka Mai isanta kafin tayi shiru


Tatashi Ido a kumbure yusrah tace waziri da maimuna Allah ya Isa tsakani na daku kuncuce iyayena kuncuci umma na da kakata Allah saiya saka musu Kuma kusani asirinku ya tonu



Dama ance inzaka Gina Ramin mugunta kaginashi daidai Kai Amma kun Gina Wanda yafi karfinku



Yusrah tace aminiyata Miko ladar hanunki



Ansha kasar yusrah wacce tayi amfani da face din yusra tatashi takawo Mata ledan


Yusrah ta zazzago abinda yake ciki layune dakuma Killin leda Mai dauke da gashin da ake bukata



Yusrah takalli abban ta tace Abba wannan gashinkane da na umma Tamika mishi yabude tabbas kuwa hakane mamaki yakamashi


Bai ankaraba yaji takara cewa abban wannan ma gashin Kane Dana matarka shima Tamika mishi


Tunaninsu ya akayi suka samu gashin su



Wani leda tafitar shima gashin ne aciki tace wannan Kuma gashin wa innan azzaluman ne dasuka cutarmin da iyaye



Takalli waziri da maimuna da buhari Wanda gaba daya hankalinssu baya jikinsu



Sannan taciro wani laya da garin magani tace



Abba umma Mai martaba dakuma umman abbanta


Tace wannan maganin da kuke gani anbani ne Akan nayi kokarin na hadashi da gashinku nakone


Idan harna konesu to tabbas kingama Shan iskar duniya


Anyi asirin da ba Mai iya warwareshi Sai Allah sannan Kuma Ni inzama sila


Inhar bani nanemo wa innan maganinva to bayadda za ayi su umma susarke sukoma kamar da



To alhamdulillah Allah yakawo Mana komi cikin sauki



Yusrah taci gaba dacewa Abba inbaku mantaba nataba cemuku zandawo Amma kuyi hakuri da halin da zancanza



Alokacin kawai nafada ne Amma bansan me zan aiwatarba sabida


Watarana nazo hutu natafi ingaishe da wannan makirar matar wato maimuna


Sai naji suna kulle kullen yadda za ayi akasheku Dan wannan tsohon muna fukin ya hau mulki



Koda naji maganar sai hankalina yatashi alokacin kamar zan juya nakoma Amma saina fasa sabida wasu kwararan dalili Wanda Yaya sabeer yake koyar Dani wato tauheed


Danagama saursrsnsu nakoma lambu nazauna nabasu kamar minti 30 kafin nashigo gidan da murna na rungume wannan munafukar matar



Ahaka kullum burina nasan abinyi Amma nakasa sanin komi Dan Haka kullum sainayi salla da addu.oi Akan Allah yakaremin iyayena



Ahaka harlokcin komawata kano yayi nakoma Amma kullum a cikin tunanin ku nake saidai Yaya sabeer yariga yakoyar Dani tauheed Dan Haka nakara amincewa da cewan Babu Wanda ya Isa yacutar da bawa batare da yaddan ubangijiba



Ahaka zucciyata take tafiya kullum Dan Haka nadogara da Allah

Watarana inajin daddy Yana waya Yana tambayar jikin ummana da umman ka Koda natamvayeshi saiyace Wai ummana zazzabi kedamunta Amma da sauki Dan Haka na hakura Amma alokacin kullum acikin muggan mafarkai nake


********

Yusrah taci gaba dacewa tunda nagama secondary nake ta planning yadda zancimma burina gurin ganin nakawar da sharrin da ake son kullawa awannan masarautar Mai tarin albarka


Kai tsaye abokin shawarana nanema wato Yaya sabeer nasanar mishi abinda akeciki


Tare muka zauna muka shirya planning yadda zamu samu motona ma wa innan makiran asiri ta wannan hanyar da na bullo muku



Yusrah tanuna Aisha tace Abba wannan qawa tace wacce mukayi secondary da ita tun daga jss one tasan komi nawa nasan komi nata Dan Haka takuduri niyyar taimaka min da ita Mike shawara hakama Yaya sabeer da amininshi



Dan Haka Koda nsamu makatanta a kasar waje bakaratun yakainiba Yaya sabeer yanema min wani malamin da yakoyar Dani addu.oi da yadda zan fuskanci makiya sukasa gane a irin suffar da nazo musu dashi


Dan Haka namakda hankali na ga abinda naje koya Haka Kuma alhamdulillah nayi sa.a sosai



Innagama wannan training din na dumfaro gida anan nasoma aiwatar da duk Shiri na


Dukwani Abu da kukaga nakeyi dama nariga na tsara shi ko ince muntsara



Abba sabeer tare dashi mukaje neman maganin kauci alokacin da naji munafukin Nan Yana fada ma munafukarnan wato waziri da maimuna


Nanne na umurci Aisha wacce take acting a matsayina takulamin daku



Kuma alhamdulillah tamin yadda nakeso Dan Haka komai namu take tafiya



Haka Yaya sabeer dayasa fuskan abokinshi shiya taimaka gurin wasu abubuwa da dama Haka abokin nashi yajiyo Mana surruka da dama Wanda takai ga yanzu muncinma burinmu



Alhamdulillah Abba komi yayi daidai komi yatafi yadda akeso



Abba dakaina nahau bishiyar dalbejiya Dan ganin iyayenmu sunsamu lafiya



Anan yusrah tasanar dashi yadda tasami bishiya da irin hadarin da tafada



Yusrah tace Abba Koda nayi nisa da Fara hawa bishiyar harnakai tsakiyar wani aljani yace tabbas kincika sadau kakkiya akan iyayenki Dan Haka zan taimakeki


Banganshi ba kawai alokacin naji komi nawa yacanza SAINAJI kamar baniba


Adaidai lokacin da zan karyi itacen Sai naji anbugi hanuna ansake bugu naji zafi natuna cewa iyayena suna wahala Basu mutuba Amma suna Jin jiki Dan Haka nakara Kai hanu sainaji abun laushi aikuwa ina sakkowa bansan yadda hankalinta yayiba



Sai alokacin sabeer wato Fahad alokacin yace gaskiya ne kamanninki suncanza yusrah alokacin da Kika dumfari bishiyar hakama dakika sakko kinyi doguwar Suma kamanninki alokacin suncanza nida wannan bawan Allah wato hakimi mukaitamiki addu.a cikin ikon Allah Kika samu sauki Kika dawo normal yusrah



Hakimi tunda akafara maganar saifaman hawaye yakeyi Dan Wanda aka rasa hawayen meye


Yayi gyaran murya yace tabbas yusrah kinhadu da maciji Haka saber macijin da ya nade maka hanu tabbas ba asalin maciji bane turosu akayi gareku



Yusrah tun alokacin dakuka zo gidana na ji kaunarku araina Dan Haka nakuduri aniyar taimaka muku



Hakimi ya kalli sabeer yace tabbas sabeer kacika Dan halak Dan uwa ga yusrah Dan kayi jarumta kwarai



Hakimi yaci gaba dacewa macijin da kuka gani anturoshi ne Akan yakasheku Amma tafiyata daku bazasu tana iya cutar dakuba domin tun ina yaro mutanen boye kefamn bina tun suna wahalar Dani har suka Fara sani bada magani basa taba barin acuci Wanda nake da niyyar taimaka mishi Dan Haka suka kasa cutar daku




Sannan inason firdausi ki gafarceni kiyafemin tabbas Baki ganeniba Amma ni naganeki dukyadda Kika canza Dole zanganeki domin ke gudan jini nane



Firdausi nine mahaifin ki



Umma firdausi tamike zumbur ta Isa gareshi tabbas tumfitowasu take kallon shi saidai tarasa gane inda tasanshi ashe mahaifin tane Wanda suka rabu tun tana shekara bakwai tunda yasaki mahaifiyar ta


Cikin kuka umma firdausi baba Kaine dama baba ashe zansake ganinka baba ina mama na



Hakimi yayi kuka Mai cin rai yace mahaifiyar ki Allah yayi Mata rasuwa da jimawa


Ainan sabuwar kuka takaru sarki suna tabata hakuri Dole tahakura dama tunda mahaifiyar ta tabar gidan akabarta agurin matar uba muguwa shikenan karshen rabuwarsu da mahaifiyar ta Allah sarki umma firdausi Allah yajikan ta




Anan ka jakanta



Yusrah tace Abba kasan yadda akayi na yanki gashin wa innan azzaluma



Alokacin danake acting amtsayin ameena dakaina NASA musu maganin bacci a ruwa nabasu suka Sha Basu saniba



Aikuwa bacci yadaukesu agurin Dan Haka na yanki gashinsu Haka buhari yaso yaudarata naki amincewa Koda yaje shagon askin nace musu gashin shi nakeso nabasu kudi Mai yawa sukabani


Haka watarana waziri zaitafi gurin bokanshi nayi saurin rigashi tafiya muka hadu ahanya alokacin nacanza duffata


Wani fuskan robber tafitardashi tasaka tace waziri katuna wannan fuskar



Waziri yimike Yana nunata da yatsa Yace kece



Yusrah tayi.murmushi tace kwarai kuwa akan iyayena zan iya sadaukar da Raina Dan Haka Koda naji abinda boka yafada maka nace tosaina Zama maka ciwon Ido



Anan yamusu bayanin komi



Duk matanen dakin sun jinjina ma yusra da kaifin basirar ta


Yusrah tace Abba yanzu wuka da nama agurinki


*******


Mata biyun nan.dasuke gurin tunda akafara magana Basu tofa uffan Sai yanzu wata tsihuwar Mata tace tabbas waziri mugune Haka diyarshi da ya Haifa



Tabbas yaso kasheni Amma Allah baibashi sa.a ba Allah yasa inada Nissan kwana



Yakasheni ban mutuba har ansani akabari nasoma motsi da rabon zan rayu



Wasu mutane sukaga motsina suka dawo suka tononi



Wani kauye suka nufa Dani anan suka kula dani harnasamu lafiya


Koda naji abinda ke faruwa agarin bauchi nace lokaci yayi danza tona mishi asiri Ashe asirin shi yariga ya tonu



Aikuwa guri yadauki salati


Waziri ya kece da dariya yace munafukan banza da wofi kunason kuci mutuncinmu ko to munfi karfinku yakara fashewa da dariya abu kamar wasa hauka fujajan



Maimuna kuwa ai tuni tasoma barkewa da zawo akayi waje da ita


Former Mai martaba yayi addu.a yace ko Haka akabarku kunshiga uku



Bazamu dauki wani matakiba zakuje kuhadu da Allah



Anan maimartaba yamusu ardu.a yass musu albarka
[7/5, 9:17 AM] UMMY KHALEEL: *******


Mai martaba dakanshi yasa aka gyara ma hakimi wajen Zama da matar waziri


Hakama Aisha yanemi iyayenta yayi musu godiya tare da Fahad abokin Yaya sabeer


Khaleel yace gaskiya Aisha Kinsha Mari duk aka tuntsure da dariya


Sarki Yusuf farin ciki ba a misaltawa agurinshi Haka Mai martaba



Yau ranace tafarin ciki Dan Haka yashirya walima Yan uwa da abokan arzi


Bayan anwatse daga walima Mai martaba hada family meeting


Meeting din akan hada auren yusrah da sabeer saikuma


Aisha da Fahad dama already sun hada kansu suna son junansu


Koda Mai martaba yanemi hakan aikuwa iyayen Aisha Dana Fahad sun amince Dan Haka akasa biki Nan da sati biyu



Mai martaba shiyayi komai Kama daga gidan da zasu zauna har kayan da akasa adaki tabbas komi saidai muce alhamdulillah


Aranar da aka daura aure aka hada kayatacciyar walima wanda yatara dumbin jama.a nagida Dana waje



Gida daya suke saidai kowa dansashin sa Amma komai nagidan iri dayane


Karkaso kaga umman sarki Yusuf Baki harkunne bama ita kadaiba duk Wanda yake kaunar su yusrah to aranar suna Taya su farin ciki


Anyi biki anwatse angwaye anrakasu dakin amaren su


Kowanne ya umurci amarya datatsh sugabatar da sallah nafila


Nidai daganan nafita nabarsu Dan banson shiga dakin amarya lol


Da safe yusrah ce na hango kwance jiki. Saber Sai faman shagwaba takeyi shikuwa Sai biye Mata yake



Rayuwarsu gwanin Sha awa


Bayan wata shida sabeer yafito daga dakinshi yusrah ma binshi take tana faman zumbura Baki yace waike lafiya kike ta zumburo Baki Haka



Yusrah tafashe da kuka tace ninace bazanje karatu wajeba anan gida zanyi karatuna



Sabeer yayi murmushi yakara manneta jikinshi yace is okey zanmema miki admission anan ko yusra da murna tace yawwa nawan ta kwace daga jikinshi taruga shima yabi bayanta



Hakama Aisha da sabeer soyayya sukeyo Mai tsafta Mai cike da so da kaunar juna



Bayan shekara wasu Yara na hango mace Dana miji akalla zasu Kai shekara biyar kansu daya suna wasa


Jiyayi namijin yace sister bazakizo kibani ball dinaba yace bros saidai kazo ka kwace da gudu suka kwasa zuwa inda iyayen nasu suke wato Hassan da Hussaina kenan yaran yusrah


Daga kan da zanyi Naga wata beautiful baby itama tazo tatada jikin yusrah ta tana gwaranci yarinyar batafi shekara dayaba cikin nabiyu wato firdausi kenan diyar Aisha Wanda taci sunan umma firdausi ana kiranta danyasmi



Duka da Hassan da Hussaina sukazo suka dauketa suna murna Dan suna matukar kaunar kanwar tasu


*********



Akwana atashi yusrah burinta yacika tazama babbar lawyer Wanda ake alfahari da ita Nan gida da waje



Aisha da Fahad ne suka jero suna takawa cikin so da kaunar juna yusrah da sabeer ganinsu yasa suma suka tashi Dan taryar su yaransu biyu da Yasmin suka zo dagudu suka rungume iyayen nasu




Tammat bihamdul lah



Anan nakawo karsnen wannan short story Mai dauke da wasu darusa Wanda Mai karatu ya fahimta


Nagode masouana da bani lokacinku da kukayi Allah yaba kauna


My besty ummu afan inamiki fatan alheri keda mummy jidda baiwar Allah tare da ummu haneef Allah yabaki lafiya



Sai kinji Ni dauke da sabon novel Dina Mai zuwa




Taku har kullum UMMY KHALEEL



ummykhaleeel@gmail.com

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login