Showing 3001 words to 6000 words out of 28895 words
mahaifinta yaki amincewa da aure sabida zigar amaryar shi wai sayansu za ayi ina firdausi ina manyan mutane haka
Limamin garin ne yayi ruwa yayi tsaki yabasu auren firdausi Dan yasan irin halin da yarinyar tashiga agurin matar ubanta kande.
Yusuf Kam tunda aka daura aure yake tatamar murna saifaman kyauta yakeyi limankam yasha kyauta kala kala hadda jujerar haji da gida da mota hakama Yan gari sunsha kyaututtuka
Aranar bayan sunkoma aka Kai firdausi gidan mijinta inda akafara kaita gurin uwarmijin tunda bawasu mutane bane suka kawota sadeeya ce dakanta takawota Sai makota
Firdausi Kam Banda kuka ba abin da takeyi ace ranar auren ta babu ko mutum daya nata shinma wai ina maman ta ne
Bayan biki da sati daya yahadasu a dakinshi yamusu nasiha maimuna tace haba ai firdausi kanwace agareni zamu sauna lafiya
Jiyayi yafara sonta da wannan kalma datayi
Firdausi tace nagode anty maimuna Allah yabamu zaman lafiya
Watan firdausi daya agidan tasoma laulayi karkaso kaga murna agurin Yusuf da mahaifiyar shi da Mai martaba kanshi
Itakuwa maimuna hankalinta yatashi matuka Dan Haka tashi sake sake da murde murde
Ana Haka Kuma Mai martaba yace yanason zaiyi murabus yadaura yaronshi akan karagar mulki
Yusuf baisoba Amma Haka Dole ya amince Dan baison jayayya da iyayenshi kokadan .
Tofa alhamdulillah anyi bikin nadin sarauta inda Mai martaba yasanar dasu zaije saudiya Karin karatu Sai Nan da shekara uku zaidawo idan firdausi ta aihu asa ma diyar suna HAJARA sannan amata lakabi da YUSRAH inkuma namiji ne asamishi suna Abdul azeez akirashi da sultan Yusuf yace angama ranka shidade Haka ma mahaifiyar Yusuf tanajin dadin KULAWAR da mijinta kemata
Maimartaba yabar Nigeria Dan Haka mulki yakoma hanun Yusuf
Watarana Yusuf na kwance Kiran babanshi yashigo jikawai nayi yace insha Allah zanyi. Ydda kakeso yace Allah yabaka nasara
Wannan shine dalilin dayasa Yusuf baya yadda ya bar diyarshi ga kowa Sai amintattunshi dukda dai banji meye Mai martaba yafada mishi ba
Wannan shine TAKAITACCEN TARIHI
Muje zuwa
More comment
More typing
Luv u allππ
ummykhaleee@gmail.com
[6/23, 1:31 PM] UMMY KHALEEL: [6/22, 7:30 AM] UMMY KHALEEL: BISMILLAH HIRRAHMANIR
π·π·π·π·π·π·
π·π·π·π·π·
π·π·π·π·
π·π·π·
π·π·
π·
GEEMBIYA YUSRAH
(PRENCESS YUSRAH)
WRITTEN BY UMMY KHALEEL
3
β FIRST CLASS WRITTERS ASSOCIATIONβ
FCWA
β home of qualities and trusted writers of the nationβ
I dedicated this page to my luvly sist jidda baiwar Allah. Allah yabar zumuncin kauna kina matukar nuna kulawarki gareni Allah yabarmu tare 2gather 4rever ameen
π·π·π·π·π·π·
CIGABAN LABARIN
Sarki Yusuf Abdul azeez shike rike dankaragan mulki saidai wannan karon mulkin ta canza salo Dan Yana gudar da mulki ne akan tsarin musulunci ba bisa Al adaba.
Umman yusrah ce zaune ita da yuarah sun idar da sallah kuyanga tashigo da sallamanta
Umman yusrah ta amsa wa alaikassalam barkanki da shigowa Cikin sakin fuska kuyangar hajiya mahaifiyar Yusuf tace ranki shidade uwar gidana tana bukatar ganinki yanzu umman yusrah tace haba mama saunawa zance Miki banson wannan karramawar keta uwace agurina banson wannan rissinawar da kikeyi
Kuyangar tace tuba nake me za ace Mata
Umman yusrah tace mutafi tare tadauki diyar tata tarungume ajikinta suka nufi inda sashen umma yake
Ana tasameta a kishin gide ta shiga da sallama ta amsa Mata da fara.a
Tanemi gefe guda tazauna kusa da umma ta saddakai kasa tace gani umma
Umma tayi ma kuyangar alamar taje kawai
Bayan fitar ta umma tace firdausi nakira kine sabida wasu dalilai saidai bansan irin naki ra ayinba Sai da Amin cewarki kafin muzartar da hukunci
Firdausi kanta akasa Dan tana matukar Jin kunyar surukar tata
Tace umma dukwani hukunci da zaku zartar akaina karku bukaci shawarata kuzartar kawai
Umma tace Dole mubaki hakkinki amatsayin na diyarmu
Anan umma tace firdausi idan kin amince former Mai martaba wato mijinta kenan Yana so kiba sadeeya kyautar yusrah sabida wasu dalilai Wanda koni Bai fadama ba
Firdausi tadago Kai tace umma wanna aiba wani Abu bane aunty sadiya tamkar uwace agareni Allah yasa hakan shine mafi alheri
Saidai umma zanso akawomin KHALEEL abani shi Dan ina kaunar yaron araina umma tayi murmushi tace karki damu Allah yamiki ALBARKA
Yusrah dama yau Yan shagwabar nakusa ba yadda umma batayi tazoba Amma taki zuwa tace kizamanki dama banson kizo kamar yusrah taji abin da tace taimata gwalo tana dariya
Sarki Yusuf yaji hukunci Mai martaba wato mahaifin shi Yakuma amince Dan haka aka ranar Kai yusrah kano gurin Yar mahaifin ta
Khaleel Kam dayaji za akawoshi bauchi murna yakeyi Dan dama jinin su yahadu da umma firdausi
Gashi Kuma shine auta agirin iyayenshi saidai ya girmi yusrah da shekara biyar.
********
Bayan shekara biyar yusrah ce kwance kafar mummy sadiya tana kuka itafa bazataje makarantaba tagaji mummy saifaman lallashin ta takeyi Abdul Rashid yafito cikin shirinshi wato Mai bin sabeer Wanda khaleel kebinshi yace ato ke kullum bakison zuwa school ko Zaki Zama Yar kauye
Yusrah tafashe da kukan shagwaba tace mummy kinjishi ko
Mummy tasaba da shagwaba irin ta yusrah Dan Haka tasamu ta lallabata tatashi sutafi
Abdul Rashid ya zabga Mata harara yace Mai riikicin banza kawai yusrah tafashe da wani ihu
Arazane mummy tajuyo tace lafiya yusrah tace ba bros Abdul vane yake.... Bata karaba ya Dalla mata harara tayi shiru
Mummy daitakara lallashin kafin tayi shiru suka tafi
Bayan fitansu sabeer yafito yasami mummy zaune akan kujera tanacin apple daddyn shima lokacin yafito Dan zuwa office
Sabeer yace mummy wannan Yar rigimar ta tafi ko daddy yayi murmushi yace babana kenan yusrah kake cema Yar rigima idan tajikafa kasan aranar za awuni gidan da rikici shima sabeer murmushi yayi yace gaskiya daddy bantaba ganin shagwaba irin na yusrah ba yarinya kamar akanta aka halicci shagwaba
Mummy murmushi tayi tace kunfi kusa nidai nawa Ido
Tashi tayi takarbi jakar mijinta dama tasaba tamishi rakiya har gurin mota
Body guard suka takomusu baya suka bude mishi kofar baya yashiga
Har kunnen shi takai bakinta tamishi addu.ar da tasaba ya kashe Mata Ido sabeer yayi murmushi yace mummy always funny
Suna mishi bye bye
Suna dawowa gida mummy tace sabeer yakamata kakula da yusrah fa inason kakula da ita game da karatun addini sosai
Sabeer yace insha Allah mummy na zanyi yadda kikace saidai fa mummy kinsan halin doter dinki
Mummy ta fahimci me yake nufi Dan shi sabeer Bai daukan raini shiyasa Basu cika Shiri da khaleel ba
Sabeer yanzu Yana zaman jiran jarabawar shi dayayi na jsce ne shiyasa yanzu yake zaman gida baya zuwa ko ina daga islamiyya Sai computer training.
Bayan suntaso daga makaranta suna isowa falo yusrah ta jefar da school bag din nata adakin tanufi dakin mummy da gudu tana kuka
Ganinya yasa mummy tambayar lafiya batama San sabeer na gurinba
Yusrah tana nuna Mata kofa da yatsa Dan batajin magana saifaman kuka takeyi
Sabeer yace ke kimana shiru shagwababbiya kawai yusrah takalleshi da manyan idonta takomar da kallonta ga mummy takara nuna Mata saveer da hanu mummy tace sorry my picking meke damunki
Abdul Rashid ne yashigo dakin yasamesu yace mummy Allah zan babballa yarinyar Nan Bata da kunya yusrah tace mummy kinjishi ko
Mummy tace metayi maka
Abdul Rashid yace mummy tunfa da muka tashi taki fitowa a class muna ta jiranta kowa yatafi yabarmu Saida naje class dinsu nasameta tana zaune akan sitter tana karatu
Mummy tayi murmushi tace mulkin yatashi kenan ko yusrah
Abdul Rashid yace mummy kimata magana Dan intasake Haka saina mammauje ta sabeer yace ya Isa Haka jeka parrot
Abdul Rashid yajuya ya barfalon
Mummy tace doter idan antashi kidaiba zama kekadai a class kinji yusrah tace to mummy zansha ice cream.
Sabeer yace bazakishaba basan ko abincin ki bakici ba
Yusrah kamar zatayi kuka tace please yaya yace inkibaso Kisha ice cream Sai kinci abinci da murnar ta tace to zanci
Abdul dakanshi yakawo musu abinci duk fadansu basa yadda su raba plate din abinci
Sabeer dakanshi yabata taci takoshi mummy tamata wanka
Da yamma suka fita wani Dan karamin super market yasai nata ice cream Dan ya gommace yarinak Saya Mata at any time da tabukata da yasa ya ajiye
Dan Bata da wani abinci danyawuce ice cream.
Akwana atashi asarar Mai Rai yusrah angirma shekararta 9 saidai Basu cika zuwa bauchi ba Dan Abba yace karsu takura kansu da Dole Sai sunkawo ta nanma gidane
Dan tunda maiartaba yadawo yaga yusrah angirma yasan tabbas yarinyar tana da bukatar tsaro Dan Haka Bai amince arinka yawan kawotaba
Fulani maimuna zaune gaba want kasurgumin boka shirgege dashi
Yadaka Mata tsawa meke tafe dake cikin dakewa dashike tasaba tace boka sonake akashe yarinyar Nan ko atura Mata aljanu
Boka ya sheke da dariya yace kinmakaro jahilar banza
Yusrah tana da tsari saidai akwai abubuwan da zamuyi Wanda zai kautar da hankalin ta
Ya labarin uwar yarinyar maimuna tace gaskiya tana yawan fama da laulayi saidai banso Haka ba nafison itama akasheta kawai kowa ya huta
Boka yace itama kishiyar taki akwai tsari atare da ita saidai zamu tatauta Mata abubuwan tsoro Wanda zai haifar Mata da hawan jini da ciwon zuciya Wanda zata shagala da addu.oin da takeyi Sai musami Daman turamata aljanu da zasu kashe Mana ita
Maimuna tayi murmushi tace
[6/22, 8:09 AM] UMMY KHALEEL: Shikanshi Mai martaba inason a maida soyayyar shi gareni yazama yadaina kula kishiyar tawa
Boka yace kaji jahila angama barinyi bincike
Wasu surutai marasa kan gado yaytayi
Sannan yafashe d la dariya yace sa ar kadan ce
Maimuna tace ina sauraranka
Boka yace ga wannan maganin kiyi amfani dashi a gaban ki dazarar ya kusanceki bazai sake iya kusantar wataba
Saidai soyayyar kishiyarki tadabance kozai wulakanta ta bazai daureba
Saidai zantura mishi aljanu Wanda zasu dinga mantarwa dashi agareta
Maimuna tace hakan ma yayi
Kudi taciro a Jakarta ta ajiye mishi
Tana dawowa tarsaya agidan su tasanar da mahaifin ta abinda ake ciki
Shima Rai bace yace zansan yadda za ayi Dole sainayi mulkin garin bauchi
Sai magriba takona gida
Ankuwa yi say yau kwanar tane Dan Haka tai kokarin yin amfani da maganin da boka yabata
Cikin Sa a kuwa ya kusanceta saidai shi dakanshi yaji wani canji Dan Haka yarasa gane kanshi
Jiyayi kan najuya mishi tuni yasoma karanto ayatul kursuyu da alqunut hakan kuwa bakaramin daga mata hankali yayi ba Dan tasan shikenan aikinta ya lalace
Lokaci guda yadawo hankalinshi
Dan muna furci yace yadai meke faruwa ya kalleta yace bakomi shikenan tafada yamike yanufi toilet yayi wanka ya dauro alwala yazo yagabatar da nafila
Hmm mutum Mai ibada irin wannan tayaya asiri zata kamashi
Allah kabamu.ikon rike addinin mu da gsky ameen
Bayan kwana biyu ko canji maimuna Bata ganiba asalima kaunar firdausi kamar karawa akeyi acikin zuciyar shi
Firdausi ce zaune kan sallaya na alfarma gabanta ancikasu da kayan marmari
Sarki Yusuf yashigo yasameta tanacin banana yazauna kusa da ita Yana Mata barkwanci
Fulani Mai ran karfe nima abani abin naci Mana
Firdausi tayi murmushi tace mijina bakaina adalin shugaba barka da shigowa ya jama.a
Alhamdulillah yafada Yana daukar Apple dasauri tasa hanu takarba tace wannan ba aikin ka bane nawane
Da bisimillah ta yanka Apple din da Dan karamin wuka Mai masifar kyau tayanka daidai bakinshi tasamishi da BISMILLAH
Yabude baki ahaka sukacu sukasha
Khaleel yashigo da gudu Yana kuka firdausi hankali atashe tace meke damunka khaleel
Yace umma mekikayi ma umma maimuna wai zata kasheki yanzu naji suna fada da ita da.mai aikinta
Firdausi tayi murmushi tace lafiyanka kuwa kodai bani kaji anceba
Shikuwa sarki hankalinshi yadan tashi yace a ina kaji khaleel yace Hira sukeyi nazo wucewa naji su
Umma firdausi tace no bani suke maganaba Mai martaba yace Anya maganar yaron Nan abin bincikene
Khaleel Yana kuka yace ummana Dan Allah karki bari sukasheki inasonki umma ta lallashe shi tace karka damu komai yafaru da bawa daga Allah ne
Mai martaba acikin ranshi yasa Dole ya tsananta bincike Dan ance yaro baya karya.
Ahaka suka tashi sukavar gurin
Tundaga ranar Khaleel ya tsani maimuna
Mai martaba zaune akan sallaya maimuna tashigo da sallama ya amsa mata fuska ba yabo ba fallasa
Tunda taga Haka tasan akwai matsala Dan Haka tanemi gefe guda tazauna
Saida ya Gama laziminshi yashafa aranta tace sainayi maganin ku
Afili Kuma tace barka da Ibada ranka shidade
Yakalleta yace meke tafe dake
Maimuna tace Dan Allah inbazaka damuba inason nadakko yaron yayan babana yadawo gurina da Zama
Yace shikenan nabaki izini yaron kamar wayake
Tace sa oi suke da khaleel kaga khaleel yasami abokin wasa yace gakane kokuma abokin karatu ba tace godiya nake tatashi tafice
Allah sarki firdausi akwai kokari dukran kwanarta Bata yadda mijinta yaci abincin Yan aikin gidan dakanta take mishi komai shiyasa tasaye zuciyar Mai martaba gaba daya
Misalin karfe ukun dare firdausi tatashi tashiga toilet yin alwala cikin bacci yajiyo ihunta Mai dauke da addu.a irin a fitaccen hankali
Yatashi yaje yabude toilet yaganta sumammiya hankalinshi yatashi yadakkota yafito da ita yadaurata agado yasoma tofa Mata addu.a Amma ina babu alamar numfashi
Hankalinshi yatashi yacigaba da addu.a ahankali har Allah yasa ta farfado
Cikin ihu take magana Dan Allah kabarni zanfice daga jikin matarka Dan Allah kabarni kana konani zanfita inbarta har abada
Shikuwa addu.a yaci gaba dayi tana ihu Wanda yasa mutanen gidan dawowa gefensu hadda umma da Mai martaba
Mai martaba ne yace kowa ya dakata awaje shida matarshi suka shiga
Yanayin dasuka samesu yadaga musu hankali firdausi hauka fujajan danka shima Yusuf din jarumi ne
Maimartaba yadafa shi yace Allah uamaka albarka Miko ruwa yatashi yakawo ruwa
Mai martaba yatofa addu.oi acikin ruwan yabude bakinta yazuba mata
Aikuwa amai tasoma yi Wanda akarasa gane Aman meye ne
Murmushi kawai Mai martaba yayi ya kalli Yusuf yace akwai sammu akan yarinyar Nan Dole Sai muntsaya da gaske
Yusuf cikin tashin hankali yace Abba wayayi sammun
Abban yayi murmushi yace zanyi bincike naduba nagani Allah yabata lafuya kakara kulawa agareta
Yusuf yace to abban nagode
Wani baccine yadauketa ba ita ta farkaba Sai Kiran sallah asubah
Hmm idankaganta bazakace wani Abu yasameta ba saidai tadan rame
Tana tashi da salatin annabi abakinta mijin nata yakalleta cikin tausayawa yace kintashi tace yaukam.na makara shine ko karasheni gaskiya nayi fushi
Murmushi yasakar Mata itakam batasan meyafaru da itaba
Zata Mike taji duk jikinta yamata nauyi ahaka ta daure tamike zata shiga toilet kenan taji kamar anbuga Mata dundu tadawo tazauna a hargitse ganin. Hakan yasashi saurin ajiye qur an din dake hanunshi yazo gareta
Lafiya yatambayeta tace lafiya banking Dadi ne yace muje namiki wanka bamusu Dan jikinta ba karfi da addu.a ya shafata yadauketa cak Sai toilet wani abin tsoron shine idan ta runtse ido saitarinka ganin wasu irin halittu masu ban tsoro
Tofa meke Shirin faruwa da Fulani firdausi
Kubiyoni a next page
More comment
More typing
Luv u All
ummykhaleeel@gmail.com
[6/23, 1:31 PM] UMMY KHALEEL: BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
π·π·π·π·π·π·
π·π·π·π·π·
π·π·π·π·
π·π·π·
π·π·
π·
GEEMBIYA YUSRAH
(PRENCESS YUSRAH)
WRITTEN BY UMMY KHALEEL
4
β FIRST CLASS WRITTERS ASSOCIATIONβ
βFCWAβ
Home of qualities and trusted writters of the nation
π·π·π·π·π·π·
My sweet sist jidda wannan page din nakine ina alfahari da ke da irin kauna da kulawarki gareni Allah yabar zumunci ameen
Ina fatan zakici gaba da rubutun makociyata
Muna jiranki
π·π·π·π·π·π·
Yanayin yadda ta dibirbice yasashi fahimtar wani Abu Dan gaba daya tafita hayyacin ta former Mai martaba yakira tawaya
Ba afi minti biyar ba saigashi ya iso cikin rashin kwarin jiki ya fiddota daga toilet din saiga firdausi lafiya Tama rasa meya gudana Adan kankanin lokaci
Mai martaba yace lafiya da asuban Nan ko jikin natane yatashi sarki Yusuf yace abban jikintane wai meke damun firdausi ne
Yana magana a kasalance
Mai martaba yace karka damu komai zaiwuce yanzu kawai addu.a za atsaya Mata dashi itama takara kokari yafi nada
Yusuf yace to Abba yanzu meye abinyi ?
Mai martaba yace zansan yadda za ayi insha Allah
Yakira sunanta firdausi
Ta amsa na am abban yace meke damunki tace Nika bansaniba kawai bangane ma jikina kwanan Nan
Mai martaba yace kina addu.a kuwa Sai alokacin tatuna kwanan biyun Nan takan yawaita Jin kasala game da ibadan da takeyi
Mai martaba yace to kifarga da wuri kikama ibada ko ince kikara akan Wanda kikeyi tahakan ne kawai zamu samu mafita Mai sauki
Firdausi tace to abban nagode yatambayeta ko tayi sallah tagyada Kai tace a a yace tashi kije kiyi alwala Amma Kita hailaalla acikin zuciyarki
Cikin ikon Allah tashiga toilet tayo wanka tare da alwala tafito tasamesu agurin
Anan tagabatar da nafil fili tare da farillah.
Abu kamar wasa ciwo yadauke daga gareta yanzu Bata da matsalar komi
Ganin haka yadaga ma maimuna hankali Dan Haka tashi sake sake
********
Yusrah ce zaune agaban sabeer Yana koya Mata karatun qur Ani da sauran littattafai Masha Allah tana fahimta sosai
Dukda rashin jituwar su karatun yusrah Yana birge sabeer Dan tana da sharp brain baya wahala gurin koyar da ita
Dan Haka yake yawan yimata wa azi dukda karancin shekarun ta tana fahimtar wasu Abu especially dayasa Mata tauhid acikin zuciyarta
Yusrah akwai mulki da Jin kasaita saidai Inka fahinceta tana da saukin Hali raini da wulakan cine kawai bataso
Tofa hakan bazaiyuwu musuba atsakanin su da sabeer ba
Danshi sabeer akwai son girma itakuma Sai tana ganin kamar raini ne yamishi yawa Dan Haka Basu cika wani shiriva hargara Abdul Rashid
Khaleel ne kawai Basu yazo days sosai Dan suna yawan waya.
Akwana atashi bawuya yanzu sabeer Yana zana jarabawar shi na ssce inda Abdul Rashid ya zana Junior waec khaleel Yana jss1 itakuma yusrah tana primary 4
Alhamdulillah rayuwar take tafiya yusrah anyi nisa acikin Al qur Ani dukda karancin shekarunta idan Tana maka kira.a saikaji rsigar jikina ka natashi tsaban zakin muryarta
Saidai yanzu yusrah wani mulki ne keson shiga jikinta kokuma ince yanayintane hakan tacika shiru shiru dayawa Bata cika son hargitsiba
Shikuwa sabeer ya fahimci yusrah kamar Mai girman Kai Dan ko magana yamata Sai taga dama take amsa mishi inkuwa Bata gadama ba tabarshi Yara surutu ba abinda yadameta hakan Yana Bata mishi Rai kwarai da gaske Dan sabeer akwai zuciya
Yauma kamar kullum yagama biya Mata karatu da asuba tatashi zata tafi harta Isa bakin kofa yace yusse kibiya dakin Abdul Rashid kice yazo yayi nashi karatun Bata amsa mishiba tafice
Aranshi Yana mamakin halin yusrah Mai kamar hawainiya idan Yan miskilancin suka motsa wane sarauniya Koda shike jinin mulkice
Amma idan Yan barkwanci suka juyo saikasha mamaki
Koda tafita bataje ko inaba dakinta tawuce tayi kwanciyar ta abinta
Sabeer yagama zaman jira ba Abdul Dan Haka yanufi dakin Abdul dakanshi yasamu Yana bacci
Yadauki filo ya buga mishi Abdul yatashi yace haba Yaya menayi maka kuma
Yace baka da kunya tun yaushe nake jira kazo kabiya karatu