Showing 9001 words to 12000 words out of 28895 words
Umma tace a a yakamata kibari masu aiki sudafa Miki
Yusrah tace umma aini nafuson indafa dakaina Dan masu aiki basusan irin yadda nake dafawaba barin dafa nakawo Mana muci
Keda kanki zakiji Dadi kice inrinka dafa Miki
Ummana kinsan miye inhar ina gidan Nan kindaina cin abincin Yan aiki hatta wanki da gyaran daki Ni zanmiki
Umma tace wane nidasa GEEMBIYA diyar sarki aiki
Yusrah tayi murmushi tace no umma ai hakkin kune akaina nima Kuma Lada nakeso
Umma tace shikenan Yar umma jeki dafa kikawo muci yusrah tace yawwa ummana
Tanashiga kitchen ta Soma aikinta cikin nutsuwa Indomie biyu tadafa da kwai biyu Sai rabun kaza tadauka tasa a oven tagasa tashirya komi
Direct dakin umma tawuce takaimusu Dan suci
Hartazauna saikuma tace sorry umma namanta da drinks barin dakko Mana
Wani makeken fridges tabude gari guda tadakko musu ziza domin yusrah ma abociyar son ziza ce
Takawo musu tace umma na muci ko
Umma kallon yusrah kawai takeyi tace to muci yusrah ta
Tare sukaci suka koshi umma tace waya koya Miki girki yusrah
Yusrah tace mummy mufa umma komi zatayi saita kirani Wai Danni macece gara na koyi girki
Maimuna tace da kyau.
**********
Yusrah ce zaune acikin dakinta takasa bacci Sai tunani maganar maimuna takeyi
Dan karamin agogon dake gefen gadon ta taduba taga karfe 1 da rabi na dare
Tatashi tashiga toilet tayo alwala tayi sallah raka.a Tara tare da addu.o I
Bayan ta idar tadauki qur Ani tasoma karantawa ahankali tuni tanemi damuwar dake zuciyar ta tarasa
Hirarsu da Yaya sabeer tatuna kwana buyu dayarage tafiyar sa yace karki Rama mugunta da mugunta karki dukwanda yacuceki kisaka mishi da alheri kizama Mai kyautata ma marasa karfi
Yusrah tayi murmushi tace miss u my bros gaskiya Dole muyi waya Dan nayi missing Dinka.
Ba yusrah takoma takwanta ba Sai da tagabatar da sallan asuba tayi azkhar dinta kafin takoma takwanta
Wani baccine Mai Dadi yadauketa tare da mafarkin Yaya sabeer Yana cemata yusrah neman tsokanarki yayi yawa fa kinsan halina ko
Yusrah tace haba Yaya na aikai Mai sanyi ne ko a bacci akace na defining Yaya sabeer zanyi define da cewa kaidin Mai sauki ne dakuma zuciya yayi dariya zaibita da gudu tafarka.
Koda tatashi zaita tsinci kanta cikin nishadi da annashuwa
Dinning tanufa taga anshirya komi na abunci saidai basuyi mataba
Kitchen tanufa tadafa Indomie tafito tahada tea Tasha dakin umma tanufa ta gaidata
Umma tace kintashi GEEMBIYA yusra
Yusrah tayi murmushi tace natashi umma me kikeso nayimiki yanzu abinci ko gyaran daki
Umma tace wanne kikeso kifara Yar umma
Yusrah tace zanfara gyara Miki daki
Umma tace bisimillah
Yusrah tahau gyaran daki umma saibinta da kallon mamaki takeyi
Karamar yarinya kamar yusrah ta iya aikin manyan Mata lallai yarinyar Nan Yar baiwa ce
Aha yusrah takammala aikin ta dakko turaren wuta takunna tare da feshe kowani sako da lungu da liquids room fresher masu kamshi
Tuni komi ya sauya
Dakinta tawuce ta gyara kamar yadda tasaba sannan tanufi kitchen
Cous cous yusrah tahada Mata Wanda yaji kayan lambu da kifi da nama tajuye a cikin cooler takawo ma umma hardakinta ta ajiye tace umma gashi kici inhar ina gidan Nan ki daina cin abincin Yan aiki
Umma tace nagide zauna muci tare yusrah tace to umma
Tare sukaci hmmm maimuna kenan naciki naciki
Saida suka Gama cin abinci yusrah takwashe komi takai kitchen tadawo
Agogo takalla taga karfe goma saura
Yusrah tace oh umma barinje nayi salla
Umma tace to tasallah
Tana fita umma tace zanyi maganinku uwar kini Bibi sainaga bayanku keda matsaiyatan tsoffin Nan da iyayen naki
Dukkanku atafin hannuna kuke
**********
Akwana atashi yau yusrah kwanata uku agidan
Umma maimuna tace yusrah meyasa bakiso kici abincin Yan aiki
Yusra tace sabida mummy batataba yadda ma aikata sunmata girki taciga bawai Kuma Dan batasoba tafison komai tanemi ladan dakanta
Shiyasa nima nakeson ladan agurin ku
Umma tace toshikenan idan nadafa nabaki zakici
Yusra tace umma na danayi farin ciki
Umma azuciyar ta tace Yar kinibibi zanyi magani ki
Umma tace to yau zanmiki girki Mai Dadi kici yusrah tace to umma na
Da misalin karfe biyu na Rana kuyanga tashigo tasami uwar gijiyar nata tabata maganin da boka yabata
Wannan maganin yace kizuba Mata a cikin abinci dashi za adafa Sai wannan kisamata aruwan juice
Idan kinyi Haka maganin zaisa tamanta kowa nata saike komai kikace tamiki zata Miki Dan Haka komi yakusa zuwa karshe
Maimuna takarba Tana murna tace zanyi maganin shegiyar yarinyar Nan da hanunta zata kashe iyayenta sannan daga karshe insa hukuma sukamata itama sukasheta
Kaji mugun alkaba.i hmmm Allah yamana tsari da sharrin masu sharri ameen.
Aikuwa maimuna dakanta tadafa spaghetti tare da zobo drink dayasha kayan kamshi
Dakanta takira yusrah tace zokici abincin ki my baby nasan kinajin yunwa
Yusrah Bata kawo komi arantaba Dan Haka tatashi da murna tace ummana gaskiya kinasona
Umma tace aidole insoki diyar sarki guda daya amiya .
Suna isowa dining umma tace zauna abaki zanbaki kinji Yar umma yusra tace to umma
Umma dakanta tasoma Bata abinci jitayi farinciki ya lullubeta Dan dama boka yace kartayadda taci abinci da BISMILLAH
Ganin batayi BISMILLAH ba yasa tajin cewa lallai magani zaiyi aiki.
Koda tagama Bata abincin umma tace yawwa Yar umma tashi kije ki kwanta ko yusrah ta tsaya kallon umman nata
Tafashe da kuka tace nidai umma tare dake zankwanta umma tayi murmushi tace Sam gara kije dakinki ki kwanta kinsan yau Abba. Ki anan yake so nizanje nakwana agurinshi
Yusrah tace to umma na takai Mata kiss agoshi tawuce dakinta takwanta Sai bacci.
Akwana tashi kwanaki sunja
. yuarah suna Shirin komawa gida
Dan tun kwana uku yarage sukoma Abban ta yadakkota umma maimuna harda kukan muna furci tace abarmara yusrah
Abban yusrah yace tayi hakuri dataga secondary school zata dawo Nan da Zama Kuma zaibata ita kyauta
Umma tayi murna hakanta yakusan cimma ruwa
Yusrah zaune gaban Abba da umman ta
Yusrah tace Abba umma kukula bazan Kara dawowa Nan gidan ba harsai na kammala karatuna na secondary da jami.a kusani acikin addu.ar ku akwai want babban aiki da zanzo nagabatar anan gidan Wanda nasan kudin bakusan meke tafiyaba
Saidai Koda nadawo karkusamin Ido akan abin da zanyi bazaku ganemin ba amma tahakan hakana zatacimma ruwa
Kuyimin addu.a Allah yabani nasara akan abinda NASA agaba
Abba da umma mamakin maganar diyarsu sukeji wannan want aiki takeso. Gabatarwa a gidan to koma miye
Kubiyoni abayan
Danjin komiye yusrah takeso. Aikatawa
Kuma wane irin aiki zata gabatar .
Taku ummu khaleel
More comment
More typing
Share to everyone body if you like
ummykhaleeel@gmail.comπ
[6/27, 10:23 AM] UMMY KHALEEL: BISMILLAH HIRRAHMANIR RAHIM
π·π·π·π·π·π·
π·π·π·π·π·
π·π·π·π·
π·π·π·
π·π·
π·
GEEMBIYA YUSRAH (PRENCESS YUSRAH)
WRITTEN BY UMMY KHALEEL
6
β FIRST CLASS WRITTERS ASSOCIATION β
FCWA
β Home of qualities and trusted writers of the nationβ
This page dedicated to all members of GEEMBIYA YUSRAH am very appreciate your comment you are making me glad cz you shown love and care for my short novel. I dont want it to long just to entertain you some manners. Luv you allπ
π·π·π·π·π·π·
Abba yace Allah yadafa Miki shirinki na alkhairi yusrah ina matukar alfahari dake amatsayin tilon Yar da Allah ya albarkaci Ni da ita
Yusra tace Nima ina alfahari daku amatsayin iyaye nagari.
Ranar da yusrah da abdul zasu koma har sashen umma maimuna sukaje sukai Mata sallama.
Driver ne yakaisu har garin kano
Abba Kam kewar diyartashi yakeyi sosai hakama umma Kai harma da sauran mutan gidan
Domin yusrah farin jininta daban ne agurin jama.a duk inda tazauna Sai ansota Dan Bata da girman Kai kokadan
Hatta umma maimuna bazatace batason yusrah ba saidai tace Taki jininta.
Misalin karfe biyu suka Isa garin kano
Mummy dama tariga tagama Shirin tarban yaran nata danhaka Tasha wankanta
Daddy Kam dariya yake Mata Wai basaban ba yau yaranta zasu dawo shine Tasha kwalliya Haka
Sallama su yakatse Daddy da tsokanar dayake Mata
Umma taware hanu akan yusrah tazo tamata oyoyo
Yusra tayi murmushi tace mummy nifa daddy na zanma oyoyo ainayi fushi dake
Daddy yayi murmushi yace kingani ko ai yusra tawace saiki Kama naki
Abdul yace lallai yusra kin iya sace GWIWA Amma mummy karki damu ai daddy yakusa tafiya kema saiki Rama
Yusrah tayima Abdul kwalo tace yaro ai wallahi umma bazata iya shareniba ko mummy
Mummy tayi murmushi tace da gaskiyarki yar mummy ammafa Nima zanrama duksukasa dariya
Mummy tace oya muje kuci abinci ina driver dayakawo ku
Abdul yace Yana tare da baba get man
Umma tace to oya kudauki nashi abincin kukai mishi inyagama Sai yashigo mugaisa
Yusrah tace mummy shima dai kawai yashigo muci abincin dashi
Daddy yace Abdul jeka kirashi yazo
Ba afi minti biyarba saigasu sunshigo da sallamanshi
Zaitsuguna harkasa yagaidasu daddy yace no kafi karfi Haka
Daddy yabashi hanu suka gaisa yanuna mishi gurin zama kusa dashi
Tare suci suka Sha
Sai bayan la asar driver yatafi daddy yacikashi da kayan alfarma.
***********
Zaune suke dukansu afalo suna kallon tashan aljazira yusra tace daddy please call my sabeer Mana wallahi nayi missing nashi
Dady yace to baby barin kirashi shima yayi missing finku
Abdul yace yawwa dady nimafa kace zaka sayamin waya Amma kaki kasayamin
Daddy yace saikagama secondary zakafara rike waya
Kira daya dady yayi yadauka
Yamkia ma yusrah
Hello bros muryarta yabigi dodon kunnenshi yace wow Mai kanwa nayi fushi gaskiya tunda saiyau Kika gadaman kirana
Yusrah takama kunnenta kamar tana gabansbi tace tuba nake my big bros nayi laifi sabeer yace kinsaba ai sukayi dariya.
Hira sukayi Mai Dadi da yayan nata harma sunmata da suna nesa da juna
Yusrah ce tagaji tace nikam yaro wallahi bacci nakeji sabeer yace nine yaronko yusrah tace oh sorry mantuwa nayi
Sabeer yace duk ina taraki yarinya idan nadawo Zaki gane wakike Kira yaro
Yusrah tace kafin kadawo kamanta
Sabeer yace shikenan bama daddy waya Tamika mishi
Sabeer yace daddy gaskiya nayi missing dinku gashi bayanzu zandawoba
Daddy yace karkadamu zamu kawo maka ziyara
Sabeer yaji Dadi sosai yace yawwa dady na nagode yaushe zakuzo
Daddy yace Sai su yusrah sunyi command entrance tukunna yace Allah yakaimu
*******
Akwana atashi jariri ango yusrah ce cikin uniform dinta Mai cike da daukar Ido riga da wando rigar fari daidai gwiwa Sai karamin hijab Wanda yazauna Mata a iya kafada Sai wando baki Mai ratsin farin layi tayi matukar yin kyau
Daddy dakanshi yashirya kaita school domin rubuta jarabawar command entrance.
Yusrah Yusuf itace acan baya sabida la akari da akayi da sunanta yazo a last alphabet Dan Haka itace a karshen baya
Wani copper ne Dake supervision nasu tsaye akanta yaga yusrah saifaman shading takeyi Bata jira azo abata amsa ba
Jikawai yayi yarinyar ta birgeshi matuka lallai yarinyar she's very brilliant girl Haka kawai ya tsinci kanshi da Kiran sunanta yusrah Yusuf tadago Kai takalleshi tace sir murmushi yayi Mata itakuwa tacigaba da shading dinta dan Yan miskilancin sunanan yau Kam
Saida tagama tas har alokacin time din tashi baiyiba
Haka yakarajij yarinyar tabirgeshi
Tabbas da babbace da yanemi auren ta karamar yarinya Sai kyau kamar ita ta halicci kanta.
Koda lokacin essay yayi Haka tadinka rubutu batare da Bata lokaciba ba ko mistake din words batayi
Copper dinnan tamatukar Kara birgeshi haka kawai ya tsinci kanshi da son sanin unguwar su
Koda ya tambayeta cewa tayi batasan unguwar su ba Dan haushina yabata
Lokacin tashi yayi daddy yazo daukanta copper din hargurin daddy yazo yagaidashi sannan yayi sallama da yusrah
Bayan tafiyarshi daddy yace yusrah wannan Cooper dinfa
Yusrah tace wallahi Ni daddy haushi yake bani yafaye kallo dayswa aibanso ka amsa gaisuwanshi ba daddy yayi murmushi.
Suna dawowa mummy tataresu da oyoyo yusrah tafada jikinta tace mummy tace mummy alhamdulillah yau nagama primary
Mummy tace saura walima kenan Kinga yazo daidai da saukar karatunki Dan Haka Sai ahada gaba daya
Yusrah murna takeyi tace yawwa mummy na saidai fa zanso Yaya yazo walimar Nan daddy yace ana yin walima da kwana biyu zaku kaimushu ziyara yusrah tace yawwa daddy we are proud of you as our house leader
********
Aranar walima idan kaga jama.a zakayi tsammanin bikin Yar shugaban kasane
Ba abinda yafi daukar hankali irin tsarin gurin da aka Kama Dan gabatar da walima saidai
Abinda zaikara burgeka shine shigar da yusrah tayi tiga da skirts ne tasa Sai dogon hijabi fari har kasa Sai nikab da tadaura dukda shigar datayi yanbala.in yimata kyau
Haka hafizan qur Ani sunyaba da tarbiyar da yusrah tasamu
Iyayen yusrah Kama daga former Mai martaba har kanana mutanen gidan dogarawa sunzo hakama gomnoni da yayansu sunzo
Koni UMMY KHALEEL tsayawa nayi nagani shin dagaskene wannan tsadaddiyar walimar da ake Hama yusrah Yusuf wacce batati shekara goma da dannwatanniba walima Kaya tacce hadda gayyatar manyan kasa
Lallai gata ba abinda bayasawa ayi
Anfara gabatar da walima babu Wanda yaga fuskar yusrah sabida lullubr yake da nikab
Babban malamin islmiyyan wato shugabar makarantar ya umurci yusrah datazo tayi karatun Al qur Ani Mai girma
Yusrah cikin taking mulkinta dayau takeni tataso dukda katon hijabi dake jikinta baihana agane tafiyar nata akwai kasaita aciki ba
Tana isowa tazauna a inda aka umurceta
Cikin zazzakan muryarta tasoma karatu da bisimillah
Inda takaranta suratul ma Ida tundaga farko harzuwa tsakiya babu Bata bare gargada
Gurin yadauki kabbara
Mahaifinta sarki Yusuf tsabar murna Saida yayi hawaye
Waiyau gudan jininshi ce da haddar Al qur Ani Mai girma
Lallai ya gode Allah dayabashi yusrah amatsayin.diya
Itakuwa maimuna babu abinda kedamunta Banda bakin ciki da bacin Rai
Amma azuciyarta tace sainaga bayanku
Umma firdausi kam addu.ar alkhairi tarinkayi ma diyar nata dama Al ummar musulmai Baki daya.
Tanagama karantawar Tamike
Jitayi wani jiri yakwasheta nantake tazube aharabar hall din cikin tashin hankali jama a suka yiyo kanta
Maimartaba dakanshi ya dauketa yanufi want karamin guri wato privaypart nacikin hall din
Dakanshi yabude fridge yadakko ruwan sanyi ya zuba Mata saidai dukda Haka ba alamun numfashi atare da ita
Hankalin Mai martaba yatashi kwarai dagaske Dan Haka yashiga karanto Mata addu.a oi
Sambatu tafara magana da yare tasomayi hankalin jama.ar dake waje yatashi
Umman yusrah da mummy saikuka sukeyi
Mummy tace yusrah karki mutu Dan Allah kitashi kinada matukar amfani arayuwar mu
Tana cikin wannan sambatun ne Fulani firdausi itama tafadi agurin
Subhanallah aikuwa tuni maigidan ta yadauketa yasata amota mummy tarufa musu baya
Malamin islamiyya su yusrah shima yatake musu baya
Suna Isa gidan mummy's malam muhd yasoma karanto Mata karatun qur Ani
Umma firdausi saifaman turje turkey takeyi
Malam muhd yace jinnu ne Amma zamuyi maganinsu yanzu kubani ruwa nayi alwala
Aikuwa Yana alwala yazo yasoma karatu akanta
Cikin ikon Allah suka fita batare da sunyi magana ba
Bacci Mai nauyi yadauketa
********
Acankuwa Mai martaba da kyar yashawo kan yusrah saidai itakam alhamdulillah ba jinnu bane Basu riga sunshiga jikin nataba
Sundaiso su shafetane saisuka kasa Dan Wanda yashafi jikintama Saida yakone
Acewar Wanda yashafi jikinta din
Tofa yatakene
**********
Dukwanda yazo walimar yatafi danalhinin abinda yafaru
Wasu suce Anya wannan abunda yafaru ba makirci bane kuwa wasu Kuma suce tsabar murnace kawai kowa dai da abinda yake Fadi
Awash gari su umma sukabi jirgu suka koma bauchi yusrah ma tasami sauki kamar ba itaba .
Aranar dazasu wuce Saudi yusrah murna zataje taga yayanta sabeer 2 years kenan rabonsu da juna saidai tawaya ko idan yaturo hotonshi ta WhatsApp.
Wani tashin hankalin tunda su Mai martaba suka koma gida Sai firdausi takamu da wani ciwo Wanda akarasa gane kanshi saidai anki afada ma yusrah khaleel Kam kullum yanakan ummanshu Yana Mata addu.a Dan tuni ya riga yasaba da addu.oin datake koya mishi Dan Haka kullum idan yadawo makaranta suna tare gaba daya umma firdausi tacanza kwata kwata acikin kwana uku
Abin kamar dawasa Amma Kuma yazarce tunani.
*******
Saudiya
Sabeer dakanshi yazo daukan iyayen nashi
Yusrah tana ganinshi ta Isa wajen da gudu harzata rungumeshi saikuma tafasa komai tatuna oho
Sabeer yamata murmushi yace daddy mummy welcome
Abdul yace Ni aibaka ganniba sabeer yace nidakai waye babba yusrah tace to baban son girma aikoda Kaine babba tunda gurinka mukazo zaka gaishemu
Sabeer yakalli yusrah dakyau yaga takara girma tayi kyau yace kekuma Yar rainin wayo ko mummy tace kudai duk inda kuka hadu saikunyi Yar Hali daddy yace barsu sunfi kusa.
Dakanshi yayi driving zuwa masaukin su dama gida suka Kama mishi 3 bedroom flat
Suna shigowa gidan yusrah tace my bros Wai akwai mata agidan Nan ne sabeer yace mekika gani
Yusra tace naganine komai nagidan yayi kamar Mai Mata
Sabeer yace bakowa nikadaine
Sabeer yace kuzo muje kudakko abincin danayi muku
Abdul da yusrah sukabishi suka dakko abinci
Dama yunwa sukeji danhaka yafara serving dinsu
Yusrah tace Yaya Anya kaikayi abincin Nan kafada gaskiya kidai sawa kayo akayi maka
Sabeer yace yarinya ci abinci dai kinji girki ba irin jagwal gwalankuba
Yusrah tabata Rai tace nidonce yarinya daddy ince tunda nagama primary na girmako
Daddy yace dagaskiyan ki Kam kingirma
Sabeer yace yarinya da sauranki agirma
Yusrah rakalli mummy cike da kuru ciya tace mummy Dan Allah ranar Dana kwanta akan gadonki ina nakusa tsayin gadonko mummy tace eh
Yusrah tace to bagashi ba mummy tace eh
Duksuka tuntsure da dariya sabeer haryana hawaye
Yace todama kedin ai tsayine kawai yamiki yawa
Abdul yace kaji Wai kura zaice dakare maye kaida yusrah waye zaizagi wani gurin tsayi
Yusrah tamike tsaye tace wallahi mummy Yaya yarainani kijifa Wai tsayi kawai nakedashi baiyadda nagirmava ince yanzu shekarata shadaya ko mummy tace hakane yusray
Daddy Kam yaran dariya suke bashi.
Saida sukaci sukasha sannan sukagabatar da sallar la asar.
Gidan cike yake da JINDADIN rayuwa yanayin dasuke gudanar da rayuwar su gwanun Sha awa
Dukda dukiyar da Allah yamallaka musu basa was da addinin su
Yusrah ce kwance kan kujera tana wasa da wayar mummy sabeer yashigo yasameta yace my yusee inasu mummy
Yusrah tace sunfita Amma yanzu zasu dawo yace ok mekikeyi yusrah tace investigation
Yace na miye yusrah tace kainifa wasa nakemata number umma nakeson Kira yace barinkira Miki umma
Yana Kira yabata takarba suka gaisa tare damata fatan alkhairi.
Su mummy sundawo yusrah tamusu oyoyo
Yusrah tace mummy nakira umma na munyi way saidai bangane muryartaba Dan kamar Bata da lafiya
Mummy tace lafiyarta Lau infada Miki may be tatashi bacci ne ahakaidai mummy tashawo kanta dantasan yusrah da binbini.
Kwanasu uku suka shirya komawa gida sabeer yaji kamar yabisu kodashike yakusa gama karatunshi Dan a gida Nigeria zaiyi service dinshi saidai yanason yayi masters nashi anan saudiya.
Ranar dazasutafi sunji badadi especially YUSRAH.
*********
Rayuwa tanesa yusrah anfara Zama yanmata yanzu ana jss 1 a IQRA model school
Makarantar both Islamic and boko new danhaka basa tashi dawuri wani lokacin Sai shida saura na yamma take tashi.
Yanzu Abdul ana ss3 ankusa karabawar ssce
Yusrah anzama yanmata duk inda zataje da nikab