Showing 9001 words to 12000 words out of 28895 words

Chapter 4 - GIMBIYA YUSRAH

12 Jul 2025

1652




Umma tace a a yakamata kibari masu aiki sudafa Miki


Yusrah tace umma aini nafuson indafa dakaina Dan masu aiki basusan irin yadda nake dafawaba barin dafa nakawo Mana muci

Keda kanki zakiji Dadi kice inrinka dafa Miki


Ummana kinsan miye inhar ina gidan Nan kindaina cin abincin Yan aiki hatta wanki da gyaran daki Ni zanmiki


Umma tace wane nidasa GEEMBIYA diyar sarki aiki


Yusrah tayi murmushi tace no umma ai hakkin kune akaina nima Kuma Lada nakeso


Umma tace shikenan Yar umma jeki dafa kikawo muci yusrah tace yawwa ummana


Tanashiga kitchen ta Soma aikinta cikin nutsuwa Indomie biyu tadafa da kwai biyu Sai rabun kaza tadauka tasa a oven tagasa tashirya komi


Direct dakin umma tawuce takaimusu Dan suci


Hartazauna saikuma tace sorry umma namanta da drinks barin dakko Mana


Wani makeken fridges tabude gari guda tadakko musu ziza domin yusrah ma abociyar son ziza ce


Takawo musu tace umma na muci ko


Umma kallon yusrah kawai takeyi tace to muci yusrah ta


Tare sukaci suka koshi umma tace waya koya Miki girki yusrah


Yusrah tace mummy mufa umma komi zatayi saita kirani Wai Danni macece gara na koyi girki


Maimuna tace da kyau.

**********

Yusrah ce zaune acikin dakinta takasa bacci Sai tunani maganar maimuna takeyi

Dan karamin agogon dake gefen gadon ta taduba taga karfe 1 da rabi na dare


Tatashi tashiga toilet tayo alwala tayi sallah raka.a Tara tare da addu.o I


Bayan ta idar tadauki qur Ani tasoma karantawa ahankali tuni tanemi damuwar dake zuciyar ta tarasa


Hirarsu da Yaya sabeer tatuna kwana buyu dayarage tafiyar sa yace karki Rama mugunta da mugunta karki dukwanda yacuceki kisaka mishi da alheri kizama Mai kyautata ma marasa karfi


Yusrah tayi murmushi tace miss u my bros gaskiya Dole muyi waya Dan nayi missing Dinka.


Ba yusrah takoma takwanta ba Sai da tagabatar da sallan asuba tayi azkhar dinta kafin takoma takwanta



Wani baccine Mai Dadi yadauketa tare da mafarkin Yaya sabeer Yana cemata yusrah neman tsokanarki yayi yawa fa kinsan halina ko


Yusrah tace haba Yaya na aikai Mai sanyi ne ko a bacci akace na defining Yaya sabeer zanyi define da cewa kaidin Mai sauki ne dakuma zuciya yayi dariya zaibita da gudu tafarka.



Koda tatashi zaita tsinci kanta cikin nishadi da annashuwa



Dinning tanufa taga anshirya komi na abunci saidai basuyi mataba


Kitchen tanufa tadafa Indomie tafito tahada tea Tasha dakin umma tanufa ta gaidata


Umma tace kintashi GEEMBIYA yusra


Yusrah tayi murmushi tace natashi umma me kikeso nayimiki yanzu abinci ko gyaran daki


Umma tace wanne kikeso kifara Yar umma


Yusrah tace zanfara gyara Miki daki


Umma tace bisimillah

Yusrah tahau gyaran daki umma saibinta da kallon mamaki takeyi


Karamar yarinya kamar yusrah ta iya aikin manyan Mata lallai yarinyar Nan Yar baiwa ce


Aha yusrah takammala aikin ta dakko turaren wuta takunna tare da feshe kowani sako da lungu da liquids room fresher masu kamshi


Tuni komi ya sauya

Dakinta tawuce ta gyara kamar yadda tasaba sannan tanufi kitchen


Cous cous yusrah tahada Mata Wanda yaji kayan lambu da kifi da nama tajuye a cikin cooler takawo ma umma hardakinta ta ajiye tace umma gashi kici inhar ina gidan Nan ki daina cin abincin Yan aiki


Umma tace nagide zauna muci tare yusrah tace to umma


Tare sukaci hmmm maimuna kenan naciki naciki

Saida suka Gama cin abinci yusrah takwashe komi takai kitchen tadawo



Agogo takalla taga karfe goma saura


Yusrah tace oh umma barinje nayi salla


Umma tace to tasallah


Tana fita umma tace zanyi maganinku uwar kini Bibi sainaga bayanku keda matsaiyatan tsoffin Nan da iyayen naki


Dukkanku atafin hannuna kuke

**********

Akwana atashi yau yusrah kwanata uku agidan

Umma maimuna tace yusrah meyasa bakiso kici abincin Yan aiki


Yusra tace sabida mummy batataba yadda ma aikata sunmata girki taciga bawai Kuma Dan batasoba tafison komai tanemi ladan dakanta


Shiyasa nima nakeson ladan agurin ku


Umma tace toshikenan idan nadafa nabaki zakici


Yusra tace umma na danayi farin ciki


Umma azuciyar ta tace Yar kinibibi zanyi magani ki


Umma tace to yau zanmiki girki Mai Dadi kici yusrah tace to umma na



Da misalin karfe biyu na Rana kuyanga tashigo tasami uwar gijiyar nata tabata maganin da boka yabata


Wannan maganin yace kizuba Mata a cikin abinci dashi za adafa Sai wannan kisamata aruwan juice


Idan kinyi Haka maganin zaisa tamanta kowa nata saike komai kikace tamiki zata Miki Dan Haka komi yakusa zuwa karshe



Maimuna takarba Tana murna tace zanyi maganin shegiyar yarinyar Nan da hanunta zata kashe iyayenta sannan daga karshe insa hukuma sukamata itama sukasheta


Kaji mugun alkaba.i hmmm Allah yamana tsari da sharrin masu sharri ameen.


Aikuwa maimuna dakanta tadafa spaghetti tare da zobo drink dayasha kayan kamshi


Dakanta takira yusrah tace zokici abincin ki my baby nasan kinajin yunwa


Yusrah Bata kawo komi arantaba Dan Haka tatashi da murna tace ummana gaskiya kinasona


Umma tace aidole insoki diyar sarki guda daya amiya .

Suna isowa dining umma tace zauna abaki zanbaki kinji Yar umma yusra tace to umma



Umma dakanta tasoma Bata abinci jitayi farinciki ya lullubeta Dan dama boka yace kartayadda taci abinci da BISMILLAH


Ganin batayi BISMILLAH ba yasa tajin cewa lallai magani zaiyi aiki.



Koda tagama Bata abincin umma tace yawwa Yar umma tashi kije ki kwanta ko yusrah ta tsaya kallon umman nata


Tafashe da kuka tace nidai umma tare dake zankwanta umma tayi murmushi tace Sam gara kije dakinki ki kwanta kinsan yau Abba. Ki anan yake so nizanje nakwana agurinshi


Yusrah tace to umma na takai Mata kiss agoshi tawuce dakinta takwanta Sai bacci.


Akwana tashi kwanaki sunja
. yuarah suna Shirin komawa gida


Dan tun kwana uku yarage sukoma Abban ta yadakkota umma maimuna harda kukan muna furci tace abarmara yusrah


Abban yusrah yace tayi hakuri dataga secondary school zata dawo Nan da Zama Kuma zaibata ita kyauta


Umma tayi murna hakanta yakusan cimma ruwa



Yusrah zaune gaban Abba da umman ta


Yusrah tace Abba umma kukula bazan Kara dawowa Nan gidan ba harsai na kammala karatuna na secondary da jami.a kusani acikin addu.ar ku akwai want babban aiki da zanzo nagabatar anan gidan Wanda nasan kudin bakusan meke tafiyaba


Saidai Koda nadawo karkusamin Ido akan abin da zanyi bazaku ganemin ba amma tahakan hakana zatacimma ruwa


Kuyimin addu.a Allah yabani nasara akan abinda NASA agaba



Abba da umma mamakin maganar diyarsu sukeji wannan want aiki takeso. Gabatarwa a gidan to koma miye


Kubiyoni abayan


Danjin komiye yusrah takeso. Aikatawa



Kuma wane irin aiki zata gabatar .


Taku ummu khaleel

More comment

More typing


Share to everyone body if you like


ummykhaleeel@gmail.com😘
[6/27, 10:23 AM] UMMY KHALEEL: BISMILLAH HIRRAHMANIR RAHIM
πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·
πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·
πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·
πŸ”·πŸ”·πŸ”·
πŸ”·πŸ”·
πŸ”·
GEEMBIYA YUSRAH (PRENCESS YUSRAH)

WRITTEN BY UMMY KHALEEL

6

β˜€ FIRST CLASS WRITTERS ASSOCIATION β˜€

FCWA

β˜€ Home of qualities and trusted writers of the nationβ˜€

This page dedicated to all members of GEEMBIYA YUSRAH am very appreciate your comment you are making me glad cz you shown love and care for my short novel. I dont want it to long just to entertain you some manners. Luv you all😘
πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·πŸ”·

Abba yace Allah yadafa Miki shirinki na alkhairi yusrah ina matukar alfahari dake amatsayin tilon Yar da Allah ya albarkaci Ni da ita


Yusra tace Nima ina alfahari daku amatsayin iyaye nagari.


Ranar da yusrah da abdul zasu koma har sashen umma maimuna sukaje sukai Mata sallama.


Driver ne yakaisu har garin kano


Abba Kam kewar diyartashi yakeyi sosai hakama umma Kai harma da sauran mutan gidan


Domin yusrah farin jininta daban ne agurin jama.a duk inda tazauna Sai ansota Dan Bata da girman Kai kokadan


Hatta umma maimuna bazatace batason yusrah ba saidai tace Taki jininta.



Misalin karfe biyu suka Isa garin kano


Mummy dama tariga tagama Shirin tarban yaran nata danhaka Tasha wankanta


Daddy Kam dariya yake Mata Wai basaban ba yau yaranta zasu dawo shine Tasha kwalliya Haka


Sallama su yakatse Daddy da tsokanar dayake Mata


Umma taware hanu akan yusrah tazo tamata oyoyo


Yusra tayi murmushi tace mummy nifa daddy na zanma oyoyo ainayi fushi dake


Daddy yayi murmushi yace kingani ko ai yusra tawace saiki Kama naki


Abdul yace lallai yusra kin iya sace GWIWA Amma mummy karki damu ai daddy yakusa tafiya kema saiki Rama


Yusrah tayima Abdul kwalo tace yaro ai wallahi umma bazata iya shareniba ko mummy


Mummy tayi murmushi tace da gaskiyarki yar mummy ammafa Nima zanrama duksukasa dariya


Mummy tace oya muje kuci abinci ina driver dayakawo ku


Abdul yace Yana tare da baba get man


Umma tace to oya kudauki nashi abincin kukai mishi inyagama Sai yashigo mugaisa



Yusrah tace mummy shima dai kawai yashigo muci abincin dashi


Daddy yace Abdul jeka kirashi yazo


Ba afi minti biyarba saigasu sunshigo da sallamanshi


Zaitsuguna harkasa yagaidasu daddy yace no kafi karfi Haka


Daddy yabashi hanu suka gaisa yanuna mishi gurin zama kusa dashi


Tare suci suka Sha


Sai bayan la asar driver yatafi daddy yacikashi da kayan alfarma.


***********

Zaune suke dukansu afalo suna kallon tashan aljazira yusra tace daddy please call my sabeer Mana wallahi nayi missing nashi


Dady yace to baby barin kirashi shima yayi missing finku

Abdul yace yawwa dady nimafa kace zaka sayamin waya Amma kaki kasayamin



Daddy yace saikagama secondary zakafara rike waya


Kira daya dady yayi yadauka


Yamkia ma yusrah


Hello bros muryarta yabigi dodon kunnenshi yace wow Mai kanwa nayi fushi gaskiya tunda saiyau Kika gadaman kirana


Yusrah takama kunnenta kamar tana gabansbi tace tuba nake my big bros nayi laifi sabeer yace kinsaba ai sukayi dariya.


Hira sukayi Mai Dadi da yayan nata harma sunmata da suna nesa da juna


Yusrah ce tagaji tace nikam yaro wallahi bacci nakeji sabeer yace nine yaronko yusrah tace oh sorry mantuwa nayi


Sabeer yace duk ina taraki yarinya idan nadawo Zaki gane wakike Kira yaro


Yusrah tace kafin kadawo kamanta


Sabeer yace shikenan bama daddy waya Tamika mishi



Sabeer yace daddy gaskiya nayi missing dinku gashi bayanzu zandawoba


Daddy yace karkadamu zamu kawo maka ziyara


Sabeer yaji Dadi sosai yace yawwa dady na nagode yaushe zakuzo


Daddy yace Sai su yusrah sunyi command entrance tukunna yace Allah yakaimu


*******

Akwana atashi jariri ango yusrah ce cikin uniform dinta Mai cike da daukar Ido riga da wando rigar fari daidai gwiwa Sai karamin hijab Wanda yazauna Mata a iya kafada Sai wando baki Mai ratsin farin layi tayi matukar yin kyau


Daddy dakanshi yashirya kaita school domin rubuta jarabawar command entrance.


Yusrah Yusuf itace acan baya sabida la akari da akayi da sunanta yazo a last alphabet Dan Haka itace a karshen baya


Wani copper ne Dake supervision nasu tsaye akanta yaga yusrah saifaman shading takeyi Bata jira azo abata amsa ba

Jikawai yayi yarinyar ta birgeshi matuka lallai yarinyar she's very brilliant girl Haka kawai ya tsinci kanshi da Kiran sunanta yusrah Yusuf tadago Kai takalleshi tace sir murmushi yayi Mata itakuwa tacigaba da shading dinta dan Yan miskilancin sunanan yau Kam


Saida tagama tas har alokacin time din tashi baiyiba


Haka yakarajij yarinyar tabirgeshi

Tabbas da babbace da yanemi auren ta karamar yarinya Sai kyau kamar ita ta halicci kanta.


Koda lokacin essay yayi Haka tadinka rubutu batare da Bata lokaciba ba ko mistake din words batayi


Copper dinnan tamatukar Kara birgeshi haka kawai ya tsinci kanshi da son sanin unguwar su



Koda ya tambayeta cewa tayi batasan unguwar su ba Dan haushina yabata


Lokacin tashi yayi daddy yazo daukanta copper din hargurin daddy yazo yagaidashi sannan yayi sallama da yusrah



Bayan tafiyarshi daddy yace yusrah wannan Cooper dinfa

Yusrah tace wallahi Ni daddy haushi yake bani yafaye kallo dayswa aibanso ka amsa gaisuwanshi ba daddy yayi murmushi.


Suna dawowa mummy tataresu da oyoyo yusrah tafada jikinta tace mummy tace mummy alhamdulillah yau nagama primary



Mummy tace saura walima kenan Kinga yazo daidai da saukar karatunki Dan Haka Sai ahada gaba daya


Yusrah murna takeyi tace yawwa mummy na saidai fa zanso Yaya yazo walimar Nan daddy yace ana yin walima da kwana biyu zaku kaimushu ziyara yusrah tace yawwa daddy we are proud of you as our house leader

********


Aranar walima idan kaga jama.a zakayi tsammanin bikin Yar shugaban kasane


Ba abinda yafi daukar hankali irin tsarin gurin da aka Kama Dan gabatar da walima saidai


Abinda zaikara burgeka shine shigar da yusrah tayi tiga da skirts ne tasa Sai dogon hijabi fari har kasa Sai nikab da tadaura dukda shigar datayi yanbala.in yimata kyau

Haka hafizan qur Ani sunyaba da tarbiyar da yusrah tasamu



Iyayen yusrah Kama daga former Mai martaba har kanana mutanen gidan dogarawa sunzo hakama gomnoni da yayansu sunzo


Koni UMMY KHALEEL tsayawa nayi nagani shin dagaskene wannan tsadaddiyar walimar da ake Hama yusrah Yusuf wacce batati shekara goma da dannwatanniba walima Kaya tacce hadda gayyatar manyan kasa


Lallai gata ba abinda bayasawa ayi



Anfara gabatar da walima babu Wanda yaga fuskar yusrah sabida lullubr yake da nikab


Babban malamin islmiyyan wato shugabar makarantar ya umurci yusrah datazo tayi karatun Al qur Ani Mai girma


Yusrah cikin taking mulkinta dayau takeni tataso dukda katon hijabi dake jikinta baihana agane tafiyar nata akwai kasaita aciki ba



Tana isowa tazauna a inda aka umurceta


Cikin zazzakan muryarta tasoma karatu da bisimillah


Inda takaranta suratul ma Ida tundaga farko harzuwa tsakiya babu Bata bare gargada


Gurin yadauki kabbara


Mahaifinta sarki Yusuf tsabar murna Saida yayi hawaye


Waiyau gudan jininshi ce da haddar Al qur Ani Mai girma



Lallai ya gode Allah dayabashi yusrah amatsayin.diya



Itakuwa maimuna babu abinda kedamunta Banda bakin ciki da bacin Rai



Amma azuciyarta tace sainaga bayanku



Umma firdausi kam addu.ar alkhairi tarinkayi ma diyar nata dama Al ummar musulmai Baki daya.


Tanagama karantawar Tamike



Jitayi wani jiri yakwasheta nantake tazube aharabar hall din cikin tashin hankali jama a suka yiyo kanta


Maimartaba dakanshi ya dauketa yanufi want karamin guri wato privaypart nacikin hall din



Dakanshi yabude fridge yadakko ruwan sanyi ya zuba Mata saidai dukda Haka ba alamun numfashi atare da ita


Hankalin Mai martaba yatashi kwarai dagaske Dan Haka yashiga karanto Mata addu.a oi


Sambatu tafara magana da yare tasomayi hankalin jama.ar dake waje yatashi



Umman yusrah da mummy saikuka sukeyi


Mummy tace yusrah karki mutu Dan Allah kitashi kinada matukar amfani arayuwar mu


Tana cikin wannan sambatun ne Fulani firdausi itama tafadi agurin


Subhanallah aikuwa tuni maigidan ta yadauketa yasata amota mummy tarufa musu baya



Malamin islamiyya su yusrah shima yatake musu baya


Suna Isa gidan mummy's malam muhd yasoma karanto Mata karatun qur Ani


Umma firdausi saifaman turje turkey takeyi


Malam muhd yace jinnu ne Amma zamuyi maganinsu yanzu kubani ruwa nayi alwala


Aikuwa Yana alwala yazo yasoma karatu akanta


Cikin ikon Allah suka fita batare da sunyi magana ba

Bacci Mai nauyi yadauketa

********

Acankuwa Mai martaba da kyar yashawo kan yusrah saidai itakam alhamdulillah ba jinnu bane Basu riga sunshiga jikin nataba


Sundaiso su shafetane saisuka kasa Dan Wanda yashafi jikintama Saida yakone


Acewar Wanda yashafi jikinta din


Tofa yatakene


**********


Dukwanda yazo walimar yatafi danalhinin abinda yafaru


Wasu suce Anya wannan abunda yafaru ba makirci bane kuwa wasu Kuma suce tsabar murnace kawai kowa dai da abinda yake Fadi



Awash gari su umma sukabi jirgu suka koma bauchi yusrah ma tasami sauki kamar ba itaba .



Aranar dazasu wuce Saudi yusrah murna zataje taga yayanta sabeer 2 years kenan rabonsu da juna saidai tawaya ko idan yaturo hotonshi ta WhatsApp.


Wani tashin hankalin tunda su Mai martaba suka koma gida Sai firdausi takamu da wani ciwo Wanda akarasa gane kanshi saidai anki afada ma yusrah khaleel Kam kullum yanakan ummanshu Yana Mata addu.a Dan tuni ya riga yasaba da addu.oin datake koya mishi Dan Haka kullum idan yadawo makaranta suna tare gaba daya umma firdausi tacanza kwata kwata acikin kwana uku


Abin kamar dawasa Amma Kuma yazarce tunani.

*******

Saudiya



Sabeer dakanshi yazo daukan iyayen nashi


Yusrah tana ganinshi ta Isa wajen da gudu harzata rungumeshi saikuma tafasa komai tatuna oho


Sabeer yamata murmushi yace daddy mummy welcome


Abdul yace Ni aibaka ganniba sabeer yace nidakai waye babba yusrah tace to baban son girma aikoda Kaine babba tunda gurinka mukazo zaka gaishemu


Sabeer yakalli yusrah dakyau yaga takara girma tayi kyau yace kekuma Yar rainin wayo ko mummy tace kudai duk inda kuka hadu saikunyi Yar Hali daddy yace barsu sunfi kusa.


Dakanshi yayi driving zuwa masaukin su dama gida suka Kama mishi 3 bedroom flat


Suna shigowa gidan yusrah tace my bros Wai akwai mata agidan Nan ne sabeer yace mekika gani


Yusra tace naganine komai nagidan yayi kamar Mai Mata


Sabeer yace bakowa nikadaine


Sabeer yace kuzo muje kudakko abincin danayi muku


Abdul da yusrah sukabishi suka dakko abinci


Dama yunwa sukeji danhaka yafara serving dinsu


Yusrah tace Yaya Anya kaikayi abincin Nan kafada gaskiya kidai sawa kayo akayi maka


Sabeer yace yarinya ci abinci dai kinji girki ba irin jagwal gwalankuba


Yusrah tabata Rai tace nidonce yarinya daddy ince tunda nagama primary na girmako


Daddy yace dagaskiyan ki Kam kingirma


Sabeer yace yarinya da sauranki agirma


Yusrah rakalli mummy cike da kuru ciya tace mummy Dan Allah ranar Dana kwanta akan gadonki ina nakusa tsayin gadonko mummy tace eh


Yusrah tace to bagashi ba mummy tace eh


Duksuka tuntsure da dariya sabeer haryana hawaye


Yace todama kedin ai tsayine kawai yamiki yawa


Abdul yace kaji Wai kura zaice dakare maye kaida yusrah waye zaizagi wani gurin tsayi


Yusrah tamike tsaye tace wallahi mummy Yaya yarainani kijifa Wai tsayi kawai nakedashi baiyadda nagirmava ince yanzu shekarata shadaya ko mummy tace hakane yusray


Daddy Kam yaran dariya suke bashi.


Saida sukaci sukasha sannan sukagabatar da sallar la asar.


Gidan cike yake da JINDADIN rayuwa yanayin dasuke gudanar da rayuwar su gwanun Sha awa


Dukda dukiyar da Allah yamallaka musu basa was da addinin su


Yusrah ce kwance kan kujera tana wasa da wayar mummy sabeer yashigo yasameta yace my yusee inasu mummy


Yusrah tace sunfita Amma yanzu zasu dawo yace ok mekikeyi yusrah tace investigation



Yace na miye yusrah tace kainifa wasa nakemata number umma nakeson Kira yace barinkira Miki umma


Yana Kira yabata takarba suka gaisa tare damata fatan alkhairi.


Su mummy sundawo yusrah tamusu oyoyo


Yusrah tace mummy nakira umma na munyi way saidai bangane muryartaba Dan kamar Bata da lafiya


Mummy tace lafiyarta Lau infada Miki may be tatashi bacci ne ahakaidai mummy tashawo kanta dantasan yusrah da binbini.



Kwanasu uku suka shirya komawa gida sabeer yaji kamar yabisu kodashike yakusa gama karatunshi Dan a gida Nigeria zaiyi service dinshi saidai yanason yayi masters nashi anan saudiya.


Ranar dazasutafi sunji badadi especially YUSRAH.



*********
Rayuwa tanesa yusrah anfara Zama yanmata yanzu ana jss 1 a IQRA model school


Makarantar both Islamic and boko new danhaka basa tashi dawuri wani lokacin Sai shida saura na yamma take tashi.


Yanzu Abdul ana ss3 ankusa karabawar ssce


Yusrah anzama yanmata duk inda zataje da nikab

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login