Showing 48001 words to 51000 words out of 87292 words
ni kadai na amsa, dr
shuraim ne ya share ta. Dr lukman yayi
dariya yace kai ka fara iskantarta kake cewa
wai ko kanwar zamani ce, alhali lallabata
nakeyi, don kada ta zata mun mayar da ita
baiwar mu. Ko kudin na bata ba ta karba,
duk kyauta muke ci in dai ba dubara ba zata
karba ba. Gashi daga dukkan alamu ba su
da hali sosai, dole ce ma yake sawa ta hau
acabar ba zata iya biyan shatar adaidaita
sahu ba, inajin kuma gidansu ba hanyar bus
bane. *nxt page din is damaged, bana
ganin rubutun sosai*
Dr shuraim ya ja doguwar ajiyar zuciya yace
Lukman don Allah da gaske kake ita ce ke
dafa ma dambun nan da kanta?dan iska
kace kakarka ce ko kakarku daya ne? Dr L
yayi dariya yace ka taba ganin dangina a
kano balle in yi kaka? wallahi itace ta ke
kawo min da farko ma ajiya ta kawo ta
dahowa kawarta an kwantar da ita anan
asibitin to bata san an sallameta ba nace
mata za mu dandana tace mu cinye dukka"
dr Sh yace to me yasa ka boye mana kace
kakarka ce take dahowa? Lukma yace kawai
don inji dadin bakina ni ma kun koya min
shakiyanci ne ai? Dr sh yayi shiru can yace
kuma yarinyar ta tabbatar maka da
hannunta take dafawa ko dai mamanta?
Lukman yace eai kai me ye abun mamaki ta
tabbatar min ita take dafawa zata min
karya ne?Shuraim yace ashe alkawarinmu
ya tashi ke nan da muka saka ran zuwa
gaishe da tsohuwa mai dambu,ashe
karyarka ce? Lukman yace ga yarinya mai
dambu ta gaishe ka ka ki ka amsa ka yiwa
kanka"shuraim yayi murmushi yace Daman
ai don kai take yi ba don ni ba idan ka yi
mana bakin ciki don kada mu ci to ai shi ke
nan don ta ni mai sauki ne don kada mu ci
to ai shi ke nan don ta ni mai sauki
ne .kada yake Abbana fa ya kamu da son
dambun nan jiya ma ya tambaye ni yaushe
zan kawo masa dambun nan mai dadi inda
ya sake son dambbun ma da nace ba na
gidan sayarwa bane a gida ake yinsa na
musamman ga tsafta"
Lukman yace ka ci albarkacin abba bari in
kirata ta zo in ce ta yi mana"dr shuraim
yace kada ka bari ta san mune muke ci
kasan abun da zaka fada mata"Dr L yace
ban iya karya ba ko karyar kuma zaka koya
mani? Ya dauko wayarsa ya lalubo sunan
Aisha farida ba ta ankara ba ta ji wayarta
tana kokarin daukar kara alhali ga ta a
jingine a jikin kofarsu sai ta falla da gudu ta
fita daga farfajiyar ofisoshin sannan ta
matsa dr Lukmn ya ce kanwata kina kusa
ne ki zo mana ina da magana dake"Aisha ta
amsa masa na da yi nisa yayana sai nan da
minti 30 zan karaso"yace babu komai sai
kin zo tana ganin Dr Shuraim da Dr Mohd
suka fita daga ofishin Dr Lukmn don kada ta
zo ta same su ita ma saboda su din ne ta ki
zuwa da farko da suka fice sai ta yi wuf ta
fada ofishin.Dr L yayi murmushi da ganinta
yace a'a ai ko minti 5 baki yi ba kika zo?ta
ce Ashe zamu gama da wuri na dauka zamu
dade kasan tafiya shi ne muka dan harhada
kayayyakinmu"yayi dariya yace mata dai
duk inda kuka je sai an barbaza shirgi wato
dan zaman da kukayi asibitinmu har kun
baza mana shirgi kenan? Aisha Farida ta yi
dariya tace Wallahi kuwa don wasu jaka
guda cika a nan suke cire kayan
makarantasu wata ma jakar kayan
siyarwarta a nan take bari duk a ofishin
metron Maryam.
Doctor ina so inyi muk dambu da danwake
gobe, ina fatan kana gari ko? Yayi dariyar
farinciki yace kai haba! Kina wahala da
kanki, ki bari kawai. Aisha farida tace a'a ai
nayi niyya ba a mayar da hannun kyauta
baya. Dr lukman yayi dariya yace koda yake
na bankwana ne ko? Gashi zaki tafi ba
ganinki zamu dinga yi ba. Aisha farida tace
haba yayana ko kasar ka bari inda hali ai
zan ziyarce ka balle nan da nan. Ai duk
sanda kake da bukatar dambu ko ba kai
bane, ko abokanka ne kada kaji komai, kayi
min waya kawai. Dr lukman yayi godiya
yace to amma abin da yasa zaki sage min
gwiwa idan na baki kudi ba kya karba, ni
kuwa banga dalilin da tika tika damu mun
daukar albashi mai tskoka zamu zauna
muna tsotse dan alawus din dalibarmu. In
kina so mu shirya to duk abin da na baki ki
karba, idan da ciko na yadda ki cika mana
idan babu yawa, idan kudin sunyi yawa ki
rike canjin. Haka ake rayuwa, sai muma mu
sami kwarin gwiwar cewa a kawo mana
gobe. Aisha farida tace to yayana amma
banji dadin kudin da zan dinga karba ba,
adduarku manyanmu muke nema. Dr
lukman yace kaji uwar iya magana, kin cika
wayo kanwata. Baki tambaye ni laifin da
abokina yake zarginki dashi ba. Kin fita kina
kuka, na dauka kina shigowa abin da zaki
fara tambaya ta kenan.
Aisha farida tayi murmushi ta langabar da
kai kasa tace bana son in cika tambayar
manya, amma tambayar tana raina. Dr
lukman yace uhmm aisha tsiri kenan, ko ba
haka bane sunanki, don naji haka yahaya
yake kiranki. Kina da hankali sabanin 'yan
matan zamanin nan. Dr shuraim yace kina
da hankali amma da zaki daina dane bayan
acaba da sai kinfi hankali. Suka tuntsire da
dariya su dukka. Dr lukman yace ai baya
son yaga mutum akan acaba, musamman
ma mace. Aisha farida tace a zuciyatya ni
da acaba kuwa har abada, tunda yin haka
zai jawo min samun kaunar wanda nake
kauna. Kudin da dr lukman ya miko mata
ne jimus dashi ya firgita ta, ta dafe kirji tace
na meye wannan kudin? Karbi mana. Ya
fada cikin tsawa a lokacin da yake zunguro
mata kudin gabanta. Ta girgiza kai tace dr
kudin yayi yawa fa. Yace nawa ne kike
tunani? Naira dubu uke ne fa kawai, ba
yawa don dai 'yan dari bibbiyu ne shiyasa
kika gansu da yawa. Nifa bana son mu
dinga irin wannan abun, ke fa ni yayanki
ne. Bana son ina baki abu kina kin karba.
Aisha farida tasa hannu biyu ta durkusa ta
karba sannan tayi masa godiya tayi masa
sallamaa ta tafi. Yau farin cikin da yake
lullube a cikin zuciyarta Allah ne kadai Ya
sani, saboda ta sami canji da yawa daga
wajen masoyinta.
Ba ta da wani buri wanda ya wuce ta ganta
a wajen abida ta bata labarin abubuwan da
suka faru tsakaninta da dr shuraim a yau. Ai
kuwa tana isa gida ta iske abida a zaune ita
da matan gida dankar suna hira, suna ta
soya awarar siyarwa. Aisha farida ta kasa
daurewa ta bari har sanda abida zata gama
ta shiga daki sannan suyi hira don haka sai
ta damko hannunta. Tace maman farouk zo
muje ciki in baki sakonki daga shagamu.
Abida na biye da aisha farida har cikin daki.
Suna shiga aisha farida ta jefar da jaka. Tace
Allah Shine Allah, Allah Shi ne mamallakin
duniya da lahira, Shine mai yawan kyuta ba
Ya gajiyawa. Tsarki da yabo sun tabbata ga
Ubangijina, sarkin sarakuna. Bai haifa ba, ba
a haife shi ba. Abida ta runguma aisha
farida yayin da ita ma farin ciki ya lullube
zuciyarta tun kafin taji abin alherin da ya
sami aisha farida, ko ba a fada ba tasan
akan dr shuraim ne. Tace alhmdl farida me
ya faru? Dr shuraim ko? Aisha farida ta jawo
hannun abida suka zauna ta jawo jakarta ta
zaro kudin da dr lukman ya bata ta mika
mata. Tace inji dr lukman suna son dambu
da danwake gobe. Abida ta karba cike da
murna, ta kirga ta daga ido ta dubi aisha
farida ta harare ta. Tace na dauka dr
shuraim ne ya baki kudin da kansa yace a yi
masa?
See Translation
DUK KYAN TAKALMI 2* 10
Aisha farida tace antina kin cika gaggawa,
karkade kunnenki kiji labari. Aisha farida ta
zazzagewa abida labarin abin da ya faru yau
a asibiti tsakaninta da dr shuraim babu dadi
babu kari. Daga karshe ta zurawa abida ido.
Tace kinji abin da ya faru, meye shawararki
kuma meye abinyi nan gaba? Abida tayi
dariya tace Ikon Allah kenan, farida kinga
faidar addua ko? Kinga banbancin
madanfaran bokaye ko? To duk abin da kike
so ki nema a wajen Allah Shi kadai, kuma ki
yarda Zai baki. Aisha farida ta gyada kai
tace na yadda da haka na dade da yin imani
da wannan. Abida tace a yanzu da Allah Ya
sa shuraim ya sanki, yasan kina raye, yasan
sunanki, yasan kina da amfani a wajensa, ya
fara damuwa da rayuwarki, ya fara gane
halayyarki, ya yabe ki da bakinsa. To anzo
gangara, lokaci yayi da zan fada miki mataki
na hudu da zaki taka. Aisha farida ta gyara
zama ta dafe kirji da hannayenta biyu taja
doguwar ajiyar zuciya tace Allah Ya sa zan
iya. Abida tayi dariya ta dafa kafadar aisha
farida tace kada ki damu, ba abu ne mai
wuya ba, guda ukun na farko sun fishi
wahala. Ai abin bi da bi ne, na daya yafi na
biyu wahala, na biyu zai fi na uku wahala,
na uku zai fi na hudu wahala, na biyar duk
yafi su sauki.
Har yanzu dai ajiyar zuciya aisha farida take
yi, zuciyarta sai dukan uku uku takeyi don
fargabar abin da abida zata fada, so take
taji mai yiwuwa ne ko ba mai yiwuwa bane?
Abida tayi shiru kamar mai tunani, can
dagao ta kalli aisha farida tace idan na fada
miki wannan mataki na hudu, ba wai ina
nufin ki zubar da matakai uku na baya ba,
a'a duk zaki hada kici gaba. Kici gaba da
addua sosai ki ma kara wata akan ta da.
Haka hakuri sai kin sake ci gaba sannan ki
hada da na ukun ki rike mutuncinki sai na
hudun da zan fada....saboda kaguwa aisha
farida ta katse ta tace fadi na hudun
wannene? Abida tayi murmushi ta gyada
kai tace ki zamo mai yawan biyayya da
ladabi a gare shi. Jikin aisha farida sai ya
dauki rawa ta rike abida cike da rudani tace
antina ban fahimce ki ba, ta yaya zanyi
masa biyayya ni da ba ganina zai dinga yi
ba, musamman ma mu da zamu bar asibiti?
Abida ta mike ta dube aisha farida tayi
murmushi tace haba farida bafa na son
rikicewa, kina tsoron shuraim kamar wani
malaikan da zai dauki ranki alhali
TAKALMIN da zaki sura ne ki saka a kafarki.
Ki dauki wannan ruguntsumin da ake ciki
tamkar wasan 'yar tsana ne da yara suke yi,
ki dauka tamkar wasan kwaikwayo ne don
nishadi, ki dauka tamkar cartoon din tom
and jerry ne da yara suke kallo a talabijin,
sai ki daina fargaba. Ko kin manta DUK
KYAN TAKALMI KAFA CE MAI TAKA SHI?
Nace ki saka a ranki daurin dan kwalin da
kike yi a kanki yafi wahala akan samun dr
shuraim. Abu ne sassauka dalilina kuwa
shine kince yana da ilimi, yana da wayewa,
yana da tausayi uwa uba yana da riko
addini, ma'ana tsoron Allah ne. To sai kibi
duk hanyoyin nan da kika san yana so kiyi
kane kane. Abin nufi ki zama mai amfani da
iliminki duk abinda zakiyia agabansa, ki
zama mai wayyayyen kai, idan yana wajen.
Ki zama abar tausayi don ya tausaya miki,
sannan ki nuna masa kinfi shi rikon addini,
sai kiga hankalinsa ya karkato gare ki. Aisha
farida ta dora hannu biyu aka tace anti kin
sake rudani, don Allah yi min misalin yadda
zanyi. Abida ta girgiza kai tace bazan fada
miki yadda zakiyi ba, saboda ke mace ce,
kuma nayi imani kowacce mace an haife ta
da irin tata kissar a jikinta. Musamman ke
aisha tun kina yarinya kin kware da iya
zama da mutane da lafazai dadada. Haba
kin manta zamanki a cikin tsofaffi ne? Kin
manta halinki na kissa wanda ko zaginki
akayi sai kiyi dariya ki ba wa mai zaginki
hakuri? To shine wannan. Kije Allah Ya baki
sa'a, sai mun hadu a mataki na biyar in kinci
nasarar cinye wannan jarabawar. Abida ta
juya zata fita, aisha farida ta lngwabe kai
tace anti mataki na hudu yafi na daya dana
biyu dana uku wahala. Abida tace hakuri
yafi komai wahala, tunda kikayi hakuri zaki
iya wannan. Idan baki gane biyayya ba, to
bansan yadda kike so nace miki ba. To bari
dai in baki misalain abin da nake nufi, ki
durkusa har kasa ki gaishe dashi a duk inda
kika ganshi, zaki fita daban daga cikin 'yan
mata a idanuwansa, don 'yan matan yanzu
basu da wannan tarbiyar. Ki rabu da hawan
acaba tunda baya so, sauran kuma kinfini
sani. Aisha farida tayi ajiyar zuciya tace sai
yanzu na fahimce ki, godiya nake. Abida ta
fice yayin da aisha farida ta daka tsalle ta
rungume pillow gami da cewa waYyo
shuraim dina. Da tazo kwanciya ta jima
tana juyi, don tunanin shuraim yayi mata
katutu a rai, ta rasa dalilin da yasa ta tsinci
kanta tana cikin farin ciki yau. Ta kagu gari
ya waye ta dauki dambu ta kai masa da
alama hadin da sukayi wa dambun nan zaiyi
dadi. Daga barci ya soma wartarta sai tayi
firgigit ta bude ido ta jawo wayarta ta duba
agogo tana gudun kada asuba ta shude su
makara ba ta tashi ta dora dambu ba. Karfe
uku saura ta mike taje tayi alwala tazo ta
fara sallah. Rakaoi ba adadi, doguwar
sujjada take yi tana zayyanowa Allah yadda
take so ta kasance a cikin zuciyar shuraim.
Karfe hudu da rabi ta fita ta fara kokarin
dora dambu don ya turara sosai, bayan ta
dora da jimawa sannan taji motsin fitowar
abida daga daki. Abida ta shigo dakin ta
dube ta tayi dariya. Tace kaji mai himma,
wato kin daura dambun tun kafin assalatu
tayi, koda yake aikin shuraim ne babu bata
lokaci. Aisha farida tayi murmushi ba tare
da ta bata amsa ba, saboda tana wuridi.
Karfe 8 saura kwata a babur din a daidaita
sahu ta yi wa aisha Farida ita da kwandunan
abincinta har guda 2.ba ya ga kayataccen
food flask guda 2 manya,daya a shake da
hadadden dambu daya a shake da danwake
sai farantunan tangaran 3 sai cokulla sai
wasu robobi 3 yan kanana masu murfi daya
yaji ne mai dadi gaske ya sha maggi daya
man gyada zaryan aka soya da albasa sai
kamshi yake dayar kuwa salad ne aka yanka
shi kanana da tumatir da albasa da
kokunba.ta isa ofishi kanta tsaye babu
shajja ba tsoro,don ba ta ga motar gogan
nata ba tasan bai iso ba don bai saba zuwa
da wuri ba.
Karfe 8 saura kwata a babur din a daidaita
sahu ta yi wa aisha Farida ita da kwandunan
abincinta har guda 2.ba ya ga kayataccen
food flask guda 2 manya,daya a shake da
hadadden dambu daya a shake da danwake
sai farantunan tangaran 3 sai cokulla sai
wasu robobi 3 yan kanana masu murfi daya
yaji ne mai dadi gaske ya sha maggi daya
man gyada zaryan aka soya da albasa sai
kamshi yake dayar kuwa salad ne aka yanka
shi kanana da tumatir da albasa da
kokunba.ta isa ofishi kanta tsaye babu
shajja ba tsoro,don ba ta ga motar gogan
nata ba tasan bai iso ba don bai saba zuwa
da wuri ba.
Ta kwankwasa kofa sai ta murda ta tura kai
dauke da kwandunan abinci riki-riki a
hannunta ta yi sallama ta shiga sai ta ga
wayam babu kowa a ofishin.babu tantama
ko ya shiga bandaki ne don haka sai ta daiki
gwandunan ta tura lungun da take ganin
yana ajiyewa dan ta kawo masa.tana tsaye
a gaban teburin tana jiran ya fiti amman
shiru kuma abun da ya bata tsoro ba ta jin
motsin komai a bandakin. Motsi ta ji an
turo kofa da karfi yayin da ta waiwaya da
sauri fuskarta cike da fara'a tana murna da
ganin yayanta.tace a ranta ashe ba'a
bandaki yake ba yana waje"sai dai kash da
ta hada ido da mai shigowar ba fuskar Dr
Lkman ta gani ba tayi matukar firgita gami
da razana a bayyane wanda shi kansa
wanda aka yi razanar dominsa ya gane.
Kallonta yake yi a nutse har sai da ya shigo
cikin ofishin ya mayar da kofar ya rufe ya
fara tafiya a hankali zuwa gaban teburin
kusa da inda take a tsaye. Numfashinta ne
yake kokarin daukewa, idanuwanta kuwa
sai suka kasa tsayawa a waje guda suka
dauki farfari yayin da ta nemi yawun
bakinta ta rasa, balle ta samu damar fitar
da lafaxi guda daya. Ya dauke kansa daga
kanta ya zagaya ya jawo kujera ya zauna
yaci gaba da bincike wani file. Da taimakon
addoui aisha farida taji numfashinta ya
daidaita, ta sami nutsuwa a cikin zuciyarta.
Ta dube shi cikin kunya hade da ladabi ta
sunkuyar da kai kasa, sannan ta kaskantar
da muryarta kasa ta zakaka makoshinta, ta
duka har kasa ta gaishe shi. Dr shuraim ya
daga ido ya dube kasa kasa da alama yaji
dadin yadda ta gaishe shi, sai ya amsa cikin
sakin fuska. Ya kara da cewa kina neman
lukman ne ko? Ta gyada kai ba tare da ta
iya hada ido dashi ba, tace eh. Ya dube ta
da gefen ido yace ai bai karaso ba, sai
anjima nine na bude ofishin. Aisha farida ta
duka tace nagode. Sannan ta juya zata fita.
Kamar a mafarki taji yayi mata magana.
Babu abinda za'a ce masa? Ta juyo a nutse
ta dube shi sannan tayi masa wani
dandasheshen murmushi, wanda ta
tabbatar an sha tabbatar mata idan tayi shi
yana kara mata kyau. Siririyar wushiryarta
ta bayyana yayin da kumatunta gefen dama
ya lotsa, fararen hakoranta sai su sake
haske. Tace dama sakonsa ne na kawo
masa, gashi can na ajiye masa. Sai ta nuna
lungun data ajiye kwandunan. Ya wurga
dara dara idanuwansa ya kalli wajen sannan
yaci gaba da dube duben file dinsa. Har
yanzu aisha farida tana tsaye a jikin kofa ta
rike kofa ita bata fita ba, ita bata dawo ciki
ba. Ya dago da kai a hankali ya dube ta,
yayin da ita kuma ta sunkuyar da kanta
kasa a hankali. Yace okay zan fada masa.
Tace kace masa kanwarsa ce aisha farida
umar. Ya dago da kai ya dube ta da alama
yaso yayi mata wata tambaya ya fasa, sai ya
gyda kai yace idan nace masa kanwarsa mai
hawan acaba ai ya sani. Sai ta ya danyi
murmushi lokacin da yake karshen
maganar. Ta langwabe kai ta marairaice ido
kamar mai shirin fasa kuka. Tace yaya
lukman ya fada min laifina jiya, nayi
kuskure bazan sake ba, nima nayi tunanin
naga ban kyauta ba. Sai ya kalle ta kawai ya
ci gaba da rubutu, can yayi magana ba tare
da ya sake dubanta ba. Yace hakan dai zaifi,
ki yiwa kanki fada, don ke mace ce, a
addinance ma bai dace ba. Dan wasu 'yan
acaba ba su da hankali. Ta duka tayi masa
godiya ta murda kofa ta fita. Ta jawo kofar a
hankali ta tafi. Taji kamar ta fasa ihu, ko ta
daka tsalle ta dire don murna. Ta shaki iska
ta lumshe ido ta daga ido sama tayi wa
Allah godiya gami da yiwa alkawarin zata yi
ma Sa azumi gobe don godiya, da Ya fara
karkato da hankalin dr shuraim kanta.
ALLAH ABIN GODIYA!!
BABI NA GOMA Nan da nan aisha farida ta
ajiye aikin ta take yi ta jawo gyalenta da
sauri ta biyo dan aike ta fito don taga mai
sallama da ita da yammacin nan. Tana
fitowa sai taga muazzam ne. Sai ta ji farin
ciki ya rufe ta, tayi sauri ta durkusa har kasa
ta gaishe shi, yayin da ta nemi izini a
wajensa zata shiga ta dauko sallaya ta
shimfida masa akan dakali. Sai ya dakatar
da ita, yace ta bari kawai daman daga wajen
aiki yake hanya ta bullo dashi tanan, shine
yace bari ya karaso su gaisa. Aisha farida
tayi murmushi ta lngawabar da kai tace sai
in rasa harshen da zanyi amfani dashi wajen
gode maka yayana. Allah Ya saka maka da
alkhairi da wannan zumuncin da kake
gudanwarwa a tsakanin mu, nagode. Ai na
sayi waya da wannan kudin da ka bani,
ashe ban karbi lambarka ba, na rasa inda
zan nemo ka, dole