Showing 9001 words to 12000 words out of 87292 words

Chapter 4 - Duk Kyan Takalmi Complete Hausa Novel

Eeshat   

16 Jul 2026

246

harhadawa in tafi duk da
kitso a unguwar bashi da tsada, kan manya
naira talatin ko arba'in, na yara kuwa naira
ashirin ko goma ne. Ban taba fadawawa
kawayena sirrina ba, duk da yawan kawayen da
nake dasu a ajinmu mata da maza, sai dai ayi
hayaniya wasa da dariya a watse, ina taka
tsantsan da harshena a koda yaushe. Babu
wanda a cikinus ya san yadda gidanmu yake,
basu taba zaton haka nake rayuwa ba, sai dai
sun fahimci wani abu akwai wasu matsaloli
wanda ba zasu boyu ba. Suyi ta zargi da sake
sakensu a ransu su kadai, ni dai bazasu ji daga
bakina ba kuma ba zasu iya tara ta su
tambaye ni ba. Ni daman bana zuwa gidan
kowa balle azo gidanmu, mu hadu a abakin
gate ne mu rabu idan an tashi. Bana jin dadin
rayuwata a wannan bangaren saboda bani da
wata takamaimiyar kawa ko masoyin da zan
amayar musu da radadin da zugin matsalolin
da suke addabata. Kawata guda daya, itace
aminiyata, yayata, masoyiyata wato matar
yayana abida. Muna zama ni da ita mu raba
dare ko mu yini muna tattauna matsalolinmu,
koda yaushe ina samun nutsuwa da kwarin
gwiwa idan abida ta bani hakuri akan talaucin
da na tsinci kaina da shawarwari, sai inji sanyi
a raina, tawakkali ya kama zuciyata sai inji ta
tuno min da nasihohin da mahaifina yayi min a
baya. Idan nayi haka sai in dawo da walwalata,
ni burina guda daya ne shine in gama karatuna
in fara aiki in taimaki kaina, in taimaki 'yan
gidanmu. Babbar matsalar ma da tafi damuna
shine zaman cakudi a gidanmu, cikin tsagoron
kazanta da cinkoso, babban burina ba wuce
inga mun bar gidan nan da umguwar mu canja
gida ko haya ce dai mu kama gidan da muke
mu kadai. Dakina daya da yara, ga dakin dan
karami mun cunkushe gashi su dukka yaran
abida fitsarin kwance sukeyi dan haka sun ruba
katifar sai zarni take dan haka na hakura da
katifar na bar musu. Na koma kwana akan
tabarma, idan na tashi da safe sai inyi salla
akai in nada in jingine a lungu sai zan sake yin
wani sallar sannan in shimfida. Har yanzu
kayana a jakar bagco yake a gefen shimfidata,
rayuwata ba irin na 'yan matan 'yan boko bace,
tamkar a kauye nake ba'a birni ba. Ko inyi
tunanin shiga hanyar banza, ban taba sha'awar
makalewa gidan kawaye ba ko arar kayan
kawa, na rike talaucina na kama kaina bana
sha''awar kayan wani. Daga makaranta sai
gida, a gidan ma nafi zama a daki kullum ina
karatu. Idan kaga na fito aiki nazo taya abida,
wankan 'ya'yanta , tsarkinsu ko aikin girki. Sai
'yan gidanmu da sauran 'yan unguwa suka
shiga yimin shaidar girman kai ne dani dan ni
'yar boko ce, basa ganin fara'ar da nake yi
musu. Kullum ina gaishe su ko basu ganni ba,
tabbas mutum ba'a iya iya masa, saboda dan
Adam ya kasance mai butulci ne. BABI NA UKU
Wata rana ranar litinin da misalin karfe daya na
rana muna cikin a sibiti, a bangaren marasa
lafiya muke wadanda aka kwantar dasu
sakamakon wasu kurajen da suka feso a
jikinsu. Muna biye da ma'aikaciyar jinya matron
maryam tana nunnana mana yadda ake aiki,
domin neman karin bayani sai tace bari ta
hada mu da kwararren likita wanda ya kware a
bangaren fata. Ta tura wani daki ta shiga
muma muka bita a baya da alama dakin
daukan darussa ne sabida naga kujeru ne zalla
da allo makale a jikin bangon. Kamar yadda
naji ta ambaci sunansa, dr shureim imran. Mun
iske shi tsaye a tsakiyar ajin tare da wasu
daliban likitoci guda 3 maza biyu, mace daya
da alama sunzo sunyi masa tambayoyi ne akan
wasu abubuwan da basu gane ba. Bayanai
yake yi musu cikin harshen turanci kai kace
baturen america ne, kalmomin kimiyyar
(botanical names) da yake ta ambato yana
jerowa layi layi da ka ba tare da yana duba
littafi ba, kai kace shine ya lakaba musu sunan
don ya haddace. Muna sake kutsawa cikin
ofishin yayin da zazzakar muryarsa, daddada
take sake shiga kunnuwanmu sai duk muka
kagu mu isa gabansa don mu kalli fuskar mai
muryan nan daddada. Kasancewar kofar ta
cushe muna shiga don muna da yawa, ga
dalibai likitoci nan suna kokarin fitowa sun
gama daukar darasin. Kowa ya kagu yayi ido
hudu da mai daddadar muryar nan, keyarsa
kawai na fara hangowa daga nesa sai na
tabbatar bakar fata ne dan uwana saboda ban
hango jan kunne ba da farin gashi irin na
turawa ba. Bakin gashi ne tattaura irin namu
na hausawa, sai dai gashin a gyare yake yana
shekin mai kuma ya kwanto lambar zuwa
karshen keyarsa. Kansu babu hula, yana sanye
da bakaken kaya riga da wando (suit), farar
riga mai dogon hannu daga ciki, ya daure
wuyansa da jan kyalle wato necktie. Dana
matso ciki sai na fara hango gefen fuskarsa,
wata lafiyayyiyar fata na fara hangowa mai
dauke da launi mai tsananin kyau. Irin kalar da
take tsada a duniya wato hasken duhu
(chocolate color). Ko dana sake samun daman
na matso kusa dashi sai ga gefen fuskarsa tar
ina gani wato idonsa daya da gefen hancinsa,
sai kawai naji wata mummunar fadywar gaba
ta far min ni ma bansan dalili ba har wadanda
ke kusa dani zasu iya jiyo karar ajiyar zuciya
danayi. Tunda nake a rayuwata ban ta ba ganin
irin wadannan dara daran idanuwan ba masu
tsananin haske daga ciki, da bakar kwayar ido
mai tsananin baki, aka zagaye idon da wasu
gashin ido da gashin gira masu yawa da
tsananin baki, ya gyara su sunyi kira mai kyau
suna sheki. A nutse ya waiwayo da kyakkyawar
fuskarsa gaba daya ya dube mu, bani kadai ba
duk wata 'ya mace da take wajen sai dataji a
ranta dama ace wannan kadarar mallakarta ce.
'Yan uwansa maza ma sai da suka raya a
ransu dama ace sune shi, ga kyau ga ilimi.
Ashe a da dana ke hango gefen fuskarshi ban
hango komai ba, kyau mai sunan kyau sai ka
kalle shi gaba dayansa daga kafarsa zuwa
kansa. Dogon mutum ne sosai ma kyawun
sura, bashi da kiba da yawa, haka bashi da
rama. Yayi kama da irin bakaken turawan nan
da ake kira african American, hukuncin da na
yanke masa kenan dan ko kusa baiyi kama da
'yan nigeria ba! Tabbas ruwa biyu ne suka
hadu suka same shi bakar fata da farar fata.
Duk da tashin hankalin da na shiga da naji
bayananta sai nayi murmushin karfin hali nace
subhanallah! Bai kamata kice zaki bi kowacce
hanya ba gara ma kice zaki bishi da addua in
da alkhairi Allah ya yi. Khadija tace bawai ina
nufin zan fita daga musulunci ba akansa ba,
amma fa dole saina saka malamaina sunyi min
addua. Na fahimci maryam ahmed da mansura
mahmud suna sonsa kin san su da bin
malamai, in ban dage ba sai sun janye
hankalinsa. Gaskiya tunda nake a duniya ban
taba ganin Kyakkyawan bakar fata irinsa ba, ko
kin taba gani? Na girgiza kai nace ban taba
gani ba, amma shima yana ji da kansa dan
yasan ya hadu kuma mata suna nuna masa
haka. Ba kya ganin 'yan matan nan medical
student suna ta kawo hare harens garshi?
Khadija tace tabbas na gani, shiyasa nace sai
nayi da gaske fa. Ai mu uku ne kadai muka
amayar da maitarmu a waje, nasan mata da
yawa sun dasa a ajin fada ne kawai basu yi ba.
Kin burge ni aisha umar, sai naga kwata kwata
ba ya gabanki, ko a bayan idonki muna yabonki
don kina kama kanki bakya shiga rigimar da
tafi karfinki. Sai kawai nayi murmushi nace a
raina kallon kitse kike yiwa rogo, aini zuciyata
tuni ta kunsa min abinda zuciyoyinku basu
kunsa muku ba. Tabbas nasan burina da fatana
akan dr shurain yafi nasu. Aisha umar kalli
motar can, inji khadija yayin da ta matse 'yan
yatsunna don gigicewa. Na juya da sauri, sai
naga wata dankareriyar mota baka mai farin
gilashi. A cikin motar kuma zankadeden mutum
ne, sanye da farar riga da bakin gilashi a
fuskarsa. Ya kalle mu, muma kallonsa mukayi
sai ya kawar da kai ya fisgi motarsa da gudu
ya nufi gate din fita. Na dubi motar har da
waiwaye sannan na juyo na dubi khadija nace
motar nan ta hadu, haka mutumin da yake
cikin motar ma ya hadu. Wanene shi? Tace au
baki gane shi bane? Dr shuraim ne likitan da
muke zancensa yanzu. Dan halak yaki ambato.
Sai nace kai bashi bane, ai shi bakar suit ya
saka. Tace bakar ta saman ya cire, ya bar
farar ta ciki. Baki shaida jan neck tie din bane?
Sai nayi shiru saboda haduwarsa tafi karfin
tunanina, sama ta yiwa yaro nusa ba zai iya
tabawa ba sai dai ya daga ido ya hango. Sai
na tuna ai Allah ne ya halicce shi wanda ya
halicce ni, babu wanda yafi wani a wajensa sai
wanda yafi bauta masa don haka na daina
raina kaina. Na kudira a raina zan sake rikar
addinina yadda zan sami babban rabo a lahira,
koda kuwa ban sami wanda nake so a duniya
ba. Zuciya ta fara warwarewa daga kuncin
daya damke ta na son maso wani. Tun ina
sauraron surutun da khadija takeyi har na
daina ganewa, burina kawai in ganni a gida na
shige lungun dakina. Ina hau yamutsattsiyar
tabarmata in kudindina inyi ta aiyano ni tare da
abin kauna ta shuraim. Ina daukar jakata sai
nayi musu sallama na nufi gate din fita a
sanyaye ina tafe ina tunani. Na fita waje na
tsayar da acaba kamar kullum na haye ya kai
ni kofar gidanmu. Tun daga zauren gidanmu
nake cin karo da matan gidan suna ta
hidindimunsu na saye da sayarwa da surutin da
suke yini suna yi, ayi gulmar wannan, a zagi
waccan, yau sai suka ganni ba kamar kullum
ba. Da bayan na gaishe su sai in dan zauna ayi
barkwanci sannan in wuce cikin gida, yau babu
kanta da kyar nake magana, sauri kawai nake
yi in shige ciki. Sunyi zaton yunwa nakeji, har
suke zolayata da cewa abida ba ta nan, ba'ayi
abinci ba. Na wuce abu na, na iske abida tana
dafa a binci a risho. Tana ganina tayi kasake
tana kallona, ta san akwai damuwa tunda bata
jiyo muryata ba, bata gano murmushina ba
saboda ina da yawan dariya. Ta dube ni tace
aisha farida kalau kuwa, ko allura zakiyi wata
mara lafiya ta kwace ta tsira miki? Nayi dariya
nace haba dai ayi haka kuwa? Bana jin dadi
dai. Tace Allah ya sawake, shiga daki kihuta
kafin abinci ya dahu ki ci zaki murmure. Ina
shiga daki na cire uniform dina sai na daura
tawul na dauki kwandon wanka zan je in watsa
ruwa dan inji dan sanyi a jikina saboda na
kwaso rana.sai na ga abida ta shigo tana
dariya tace da ni "af ashe wanka zaki yi da
labari zan baki mai dadi kuma marar dadi." Na
ajiye kwandon wanka na jawo hannunta muka
zauna.Na ce bani in sha ai na fasa wanakan,me
ya faru? Ta yi dariya tace labarin musbahu
tsohon saurayinki da matarsa lubabatu zan
baki daman,aure dai yaki dadi har ya yi mata
saki daya dazun nan aka yi rigimar. Lungun
nan ya cika da mutane mahaifiyarsa dai sai a
taya ta da addua don ta cika naci,ce masa tayi
idan ya sake furta kalmar saki sai ta tsine
masa dole sai ya zauna da lubabatu tasan
akan aisha farida yake yi mata wulaqanci kala-
kala. Tayi rantsuwa tace ko bayan ranta idan
ya saki lubabtu ya aure ki Allah ya isa. Kin ji
wata kiyayya sabuwa ko? Na yi murmushin
karfin hali nace,Allah ya kyauta,ta ma daina
kokarin tsinewa danta a kaina tuntuni na yi
masa sallama nace ya bi mahaifiyarsa don ya
sami rahama. Ya na aiko min da kudi tun ina
karba sai na daina karba daga baya idan ya
aiko sai in mayar da dan aiken in ce bana so
don zaman lafiya. Abida tace haka ya fi,ai gara
da kika yi. Masa haka kin taimake shi. Ni na
dauka ma zancen kika ji tun daga zaure da na
ga kin shigo ranki a bace. Amma fa ki godewa
Allah AF saboda kin samu kyakkyawon yabo a
ung nan. Ba kiji. Yadda kowa yake yabonki
ba,ake ta tsine mata ita kuma. Kowa ya dinga
cewa me ye laifin AF har da bata so danta ya
aura? Yarinya mai nutsuwa da hankali mai ilimi
da fara'a tana gaishe da mutane. Ta zo ta
tauyewa yaro rayuwarsa ta cusa masa
dakalkalalliyar macen da ba ta da tsari. Nace
au daman an sanni da yawa a ung nan haka?
Abida tace "ji ki da Allah da neman magana
waye bai sanki ba,musamman da kika shiga
skul of nursing kina karbar haihuwa kina allura
a cikin ung sai ki ji kowacce mata tana cewa
wajen aisha likita zan je ta rubuta min magani.
A nan dai muka tashi muka rufe hirar nan
zuciyata cike da tausayin musbahu ba don
mahaifiyarsa ba ta sona ba da na aure shi mun
zauna mun rufawa juna asiri,in huta fadawa
cikin hatsarin da nake shirin jefa kaina. Bayan
na yi wanka na ci abinci sai na wartsake na
shiga cikin matan gidan muna ta hira har ma
na ji na fara mantawa da abunda yake damuna
a zuciyata. Sai da kowa ya shiga barci dare ya
fara nisawa sai tunanin Dr shureim imran yace
da wa Allah ya hada ni in ba da ke ba,sai na ji
gaba daya daya zuciyata ta kasa sukuni. Da
zarar na rufe ido sai in ganshi tamkar a zahiri.
Sai na yi ta yaki da zuciyata ina ture shi daga
tunanina.kai in takaice maka a cikin satin nan
ban gane kaina da kaina saboda tsananin
tunaninsa. Idan na je asibiti bana walwala haka
idan na dawo gida ba na jin dadin zuciyata
kada ma dare ya ji labari sai ka ga idona ya
wartsake garau na burma tunanin DR shureim
imran. Da gaske sonsa nake,so ba da wasa
ba.tun ranar kuma ban sake ganinsa ba sai dai
kullum sai khadija ta yi min labarinsa.Albishir
din da ta yi min shi ne ta sami lambar wayarsa
amma tana tsoron kira don tana ganin zai yi
mata wulaqanci. Ta shaida min ta rabawa
malamai kudi ana ta ragargaza mata addu'a ta
koina,a kalla ta raba musu zunzurutun kudi ya
kai N25,000 so take sai an gama addua tas
sannan ta kira shi dolensa ya amince. Sai na
sake jin jikina ya yi sanyi na sake yi wa
zuciyata fada da ta yi ta- ka tsan- tsan ta
daina cusa abunda zai iya kasheta.idan da
khadija. Zata lura duk sanda ta fara yi min
zancen Dr shureim sai jikin yayi sanyi kuma na
kan rasa amsar da zan bata ko shwara.
Kallonta kawai nake tsayawa ina yi yayin da
zata iya ganin hawaye yana cika min ido sai
inyi sauri in mayar da shi ina tauisayinta na fi
tausayin kaina domin na san zuciyata ta fi tata
shiha hatsari kuma ta fini sanin yadda zata yi
da kanta. Ni ko wayar ma bani da ita babu
kudin saka kati balle in saka rai ko zan karbi
lambar in kira inji dadi. Na zama na rasa
walwala ta ko abincin kirki bana iya ci na
dukufa da adduar Allah ya yaye min don sonsa
ya zame min ciwo.naji duk na tsani kaina karfi
da yaji nake fisge tunaninsa daga cikin
zuciyata.amma abu ya ci tura sai ma karuwa
yake yi. Idan naki tunaninsa karfi da yaji a ido
biyu da zarar na kwanta sai nayi mafarkinsa,
sai gani cikin dare ina kuka wiwi ina sallah da
adduar Allah Ya yaye min, Allah Ya kawo abin
da zai sa inji na tsane shi ma. Duk satittikan
nan da nayi ina jinyar sonsa ko a hanya ban
hadu dashi ba balle ma in ji dan sanyi a raina,
ina so ina kara ganin suffarsa don in kawata
tunanina domin kamanninsa suna kokarin
disashe min. Ranar talata da sassafe ina
dirowa daga kan acaba a kofar shiga gate din
asibitin aminu kano sai na yi kicibus dashi a
cikin wannan tsaleliyar motar tasa. Na
waiwaya da sauri na dube shi yayin da shi ma
yake dubana har da rage tafiya amma fa duban
da yake yi min bana kauna bane, hararata yake
yi game da nuna tsana mai yawa a bayyane.
Sai yayi tsaki ya girgiza kai ya kada sitiyarin
motarsa yayi wucewarsa. Sai na dankare a
tsaye ni ban ciro kudin mai acaba na biya shi
ba, ni banyi gaba ba balle ace mantuwa nayi.
Bani kudin mana, inji zalamamman dan acba.
Na ciro kudin na mika masa ya karba yana
shirin ya miko min canjina naira ashirin sai na
girgiza kai nace kayi min sadaka, ku taya ni
addua don bani da lafiya. Sai ya tsaya yana
kallona cike da tausayi yace to ko gida za a
mayar dake idan ba zaki iya aikin ba? Ai komai
sai da lafiya akeyi. Nayi murmushin karfin hali
nace ciwona addua yake bukata ba hutu ba, ko
shan magani. Sannan maganin ciwon yana
cikin asibitin nan, idan na koma gida ai babu
maganin a can. Yace gaskiya ne duk wani
magani yana asibiti. Allah Ya yaye miki
kowanne irin ciwo ne wannan. Na amsa da
amin nagode. Na juya a sanyaye ina tafiya
kamar kwai ya fashe min a ciki. Ina mai
matukar mamaki da takaicin kallon wulakancin
da yayi min. Na kasa tantance ni kuwa laifin
me nayi masa a rayuwata da ya tsane ni,
yaushe ma ya taba ganina banda sau daya
shima a rubibi, yaushe zai ganeni? Aisha farida
umar, karaf naji an kira sunana daga gefena.
Nayi firgigit na juyo da sauri. Khadija sani
ismail na gani ta tsaya da motarta hience 2008
ta sauke gilashin wundonta kasa, na tsallako
inda take na bude gaban motar na shiga. Ina
kokarin gaishe ta sai ta katse ni cikin murna
take magana tace albishirinki? Na kira Dr
shuraim imran jiya ya dauka, sai dai mun fara
magana yace in bashi bane wanda nake newa
wrong number ce, ya katse wayar. Sai na tura
masa sako nace ni dalibarsa ce , na kira in
gaishe shi. Kinga amsar daya bani. Sai ta miko
min wayarta, sai hannuna ya hau kakkarwa,
har sai da ta tsaya tana kallona saboda gaba
daya jikina bari yake yi. Na duba na karanta
sai naga ya runuta "thanks". Sai na lumshe ido
don dadin ganin rubutunsa da lambarsa, naji
dama nice nake yi masa waya da tura sako da
ko amsar da ya bawa khadija na samu ya bani
kadai na gama jin dadin rayuwata, ta isheni
abin farin ciki. Na bude baki nayi magana da
kyar, nace lallai kinji dadi. Tace dadi ka-n jiya
ai jar da barci da munshari don samun
kwanciyar hankalin dana ji. Dole in karawa
malamaina kudi su sake dagewa da addua
sosai. Nayi ajiyar zuciya nace ya san sunanki?
Tace bai tambaye niba, ki kyale shi sai a
hankali, dan wulakanci ne fa wannan da kike
gani. Muka isa bangaren da muke,mun bar
bangaren masu kuraje mun koma bangaren
yara. Muna shiga ciki muka iske 'yan ajinmu a
tsaitsaye kowannensu da dan littafinsa a hannu
da biro, da alama matron ta fara bayani akan
wannan yaro mai ciwon amai da gudawa. A
tsaye nake ina kallon bakin yaron a hannun
mahaifiyarsa yana tsala kuka, amma ban
fahimci bayanan matron ba, ko kadan ban san
me take cewa ba. Tunanina kawai daman ace
dana ne wannan jaririn muka haifa tare da Dr
shureim imran. Sai da ta gama bayani ta juya,
naga an bi ta duuu a baya zuwa gadon wani
yaron marar lafiya, shi kuma mai ciwon
pneumonia ne, sai na ja birki na tsaya cak na
ki bin su saboda kafafuwana da kwakwalwata
sun gaji ba zasu iya daukar abubuwa guda biyu
ba, tunanin dr shuraim imran shi yafi matsa
min, gara in yi shi shi kadai, shi yafi
muhimmanci a gareni don haka na juya na nufi
ofishinmu inda muke zama mu huta da ajiye
jakunkunan mu. Ina shiga sai naga maryam
ahmad tayi kasake a zaune akan kujera tana
matsa wayarta, fuskarta babu walwala. Nayi
mata magana sai naji da kyar take amsa min.
Na tambaya cikin damuwa maryam lafiya?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login