Showing 78001 words to 81000 words out of 87292 words
ji da wannan angon naki,
ance mai kudi ne shi ya tsaya miki, ance
yana sonki tamkar ransa. Auwal dan ajinmu
yace min a likita zaki aura , rannan na hadu
dashi auwal din a ministry of health yace
min tare kuke aiki. Wai meye gaskiyar
maganar? Aisha farida dai har yanzu dariya
take yi, tace khadija don Allah ki ajiye
tambayoyin nan naki sai mun nutsu zan
amsa miki su. Daidai lokacin khadija ta tura
kofar gate din suna kokarin fitowa, ta daga
kai ta dubi dankareriyar motar da aka kawo
aisha farida a ciki, sai tayi ajiyar zuciya kafin
tayi magana. Sai ta daga kai ta hango
santalelen saurayin da yake tsaye a jikin
motar. Ya kalle ta, ta kalle shi, ta daka
tsalle ta koma cikin gida da gudu, ta labe a
jikin gate din tana salati. Aisha farida ta
firgita itama tabi bayanta da sauri ta rike ta
tana tambayarta lafiya? Khadija ta rike kirji
tace aisha umar kamar dr shuraim nake
gani a kofar gidana? Lafiya ya biyoni? Ba dai
asirin da nayi masa bane yanzu ya fara
cinsa ya biyo ni har gidan mijina? Yaya zanyi
yau?
Aisha farida tayi dariya tace ta yaya dr
shuraim zai san gidanki har ya biyo ki? Wa
ya fada miki asiri yana ci? Tabbas sihiri
gaskiya ne amma bai cika kama wanda yayi
imani da Allah ba. Dr shuraim ni ya kawo,
don ni yazo gidannnan, shine angona.
Khadija ta bude ido da baki gaba daya tana
duban aisha farida, mamaki marar
misaltuwa zaka gani a idanuwanta. Tace
aisha umar yanzu dr shuraim zaki aura
shine baki fadawa kowa ba? Ashe daman
kema kina sonsa a lokacin da muke sonsa
kika boyewa kowa? Ta ya kika same shi? Ke
kuwa wane irin asiri kikayi masa haka?
Aisha farida ta girgiza kai tace babu asiri
acikin lamurana, sai dai addua. Addua na
rike, ita ta kaini ga matsayin da ban taba
zato ba. Khadija nayi alkwawri idan na
samu nutsuwa zan fada miki dalla dalla
yadda muka hadu da dr shuraim har ya
zama mallakina. Sai anjima, sai kinzo bikina,
adireshin wuraren duk suna jikin katin.
Aisha farida ta juya ta tafi, yayin da ta bar
khadija a sankare a tsaye, baki a bude don
gigicewa da mamaki. Daga gidan khadija,
gidan maryam ahmad suka wuce dake
unguwar sallari. Irin wannnan mamaki da
figici da ya samu khadija sani shi ya fadawa
maryam ahmad. A lokacin da ta fito har
mota don su gaisa da angon kawarta, ta
iske dr shuraim ne. Sai da aisha farida ta
tare ta don ta kusa faduwa don tsorata. Ta
shiga yiwa farida rada tana cewa ke dr
shuraim ne wannan ko kaninsa? Aisha umar
ina kika same shi har zakuyi aure? Labarin
yana da tsawo! Amsar da ta bata kenan ta
shige mota suka ja suka tafi ta bar maryam
a sankare a kofar gida.
Aisha farida ta sake kyalkyalewa da dariya
tace tunda kace Allah ai ka gama daure min
jijiyoyin jikina. A lokacin tabbas nima
mutum ce kamar kowa, kuma mace yadda
suke mata. Naji abinda suka ji a raina,
amma sai na fisu hakuri da tawakkali. Na
sama raina har abada ba zan same ka ba
gara ma kada in jefa kaina cikin wahala.
Don haka ban cusa kaina ba, ina gefe ina
addua, Allah masanin komai, sai Ya bani kai
a lokacin da ban taba zata ba. Dr shuraim
yayi murmushi ya lumshe ido yace na
fahimce ki, kuma na gamsu da bayananki.
Amma maiyasa kika tsorata baki zo kin
gwada sa'arki ba? Kika sani ko kici nasara ki
same ni? Ta girgiza kai tace karfina ko
wayona da kwarkwasata ba zasu amfana
min komai ba. Saboda naga 'yan mata da
suka fini komai basu same ka ba. Yayi
dariya yace kin taba sanin kina da kyau
kuwa? Kyawun da tunda nake ban taba
ganin wacce ta yi min kyau kamar ke ba.
Tun ranar da na fara ganinki a duniya na
tabbatar kina da kyau , da zan iya samunki
da naji dadi. Sai aisha farida ta dafe haba ta
bude baki tayi ajiyar zuciya ta langwabar da
kai gefe. Tace shikenan my dear tunda har
abin ya zama ba'a. Dr shuraim ya juyo a
hankali ya dubi kwayar idon abin kaunarsa
yace na taba yi miki karya ne? Toh ki yadda
da magana ta, kina da kyaun da ba a ko ina
ake samunsa ba, babu kantin da za'a iya
samunsa a saya.
DUK KYAN TAKALMI 3* 12
Yace,na taba miki karya? toh ki yarda da
maganata,kina da kyan da ba a koina ake
samunsa ba,babu kantin da za a iya samun
irinsa a saya saboda dalilaina masu zuwa.na
daya kina da kyakkyawar fata irin ta 'yan
kasar itiofiya,mai hasken duhu(chocolate
color).na biyu,kina da gashi mai kyau,irin
na asalin Africa mai gazar-gazar da baki,irin
wannan gashin shine a girarki da fatan
idonki.na uku,kina da kyawun kwayar ido
dara dara,farare sol!idan kina kallon mutum
sai yaji wani yarr a jikinsa saboda kina da
idanuwan nan da ake kira sexy eyes.na
hudu,hancinki bashi da tsayi sosai,haka
bashi da fadi ya dace da fuskarki.na
biyar,bakinki dan karami,kina da hakora
farare sol,ga 'yar siririyar wushirya a
tsakiya.ga ki da fara'a idan kika yi dariya sai
gefen kuncinki su loba dukka biyun,na
shida,Allah yayi miki wata irin murya mai
dadin gaske,wacce ko yar uwarki mace taji
muryarki sai ta waiwayo balle da na
miji.dadadan lafuzzanki su suke karawa
muryarki dadi.na bakwai,Allah ya miki kirar
jiki mai kyau,a dire kike,baki da kiba,ba ki
da rama.sannan bakiyi gajarta ba,ba kiyi
tsawo zalolo ba.amma duk wannan bai jaa
hankali na na fara sonki ba,sai da na gama
karantar halayenki na tabbatar kina da
hankali,kirki,t awakkali,sannan kina da aji.
Abubuwa biyu ne suke tafiya da tunanina a
wajen mace,shine,idan mace tana da aji da
kuma kamun kai wacce ba yar iska ba.kin yi
sa'a kina da duk wadannan.aisha farida tayi
hamdala a zuciyarta,tayi murmushi a
sarari,ta dube shi tayi fari da ido.ta ce,nayi
sa'a da nayi dace na sameka.Dr shuraim
hakika kana da kyau babu inda Allah ya
rage ka tun daga halittarka,ilimi da
dukiya.duk wadannan basu dameni ba,sai
na dinga lura da halayyarka.na shiga halin
damuwa alokacin da ka gwada ni cewar
zaka tafi da ni gidanka ko ba kayi bayani ba
na fahimci abun da kake nufi,sai na kudiri
niyyar rabuwa da kai har abada,kyawunka,
dukiyar baza su taba burgeni ba,tunda kake
sabawa Allah.sai daga baya na tabbatar ba
haka kake ba,kai mutum ne mai tsoron
Allah da tausayi shine na saki jikina na
tabbatar nayi dace da miji nagari.su dukka
sukayi dariya a lokaci guda.
Dr shuraim yace kin cika mai hankali mai
zurfin yunani,kuma ba zakiyi da na sani ba
tunda kika farga kika san kyau da kudi ba
komai bane in dai mutum bashi da hali na
gari.matsalar da ke damun yanmatan
zamanin nan ke nan,shi yasa ake samun
matsala a zaman aure,sakin aure ya yawaita
a kasar hausa.hirar so da kauna da fahimtar
juna suka yi tayi,har suka isa kofar
gidansu.yayin da yaran suke baya suna ta
hidima da kayan dadi,sai ci suke tayi,ya ki
ya kare saboda ledoji da yawa ya ciko
musu.aisha farida tayi godiya suka fito daga
motar suka shiga gida,dr shuraim yana daga
muau hannu,su ma suna daga masa har ya
tafi.su dukka suka ji kamar kada su rabu da
juna,sai kuma gobe idan Allah yaa kaimu zai
dawo don yanzu ba ya fashin zuwa wajen
farida.ASUBA TA GARI LIKITAN AISHA!!!
BABI NA ASHIRIN BIKI!BUDIRI! BIREDEDE!
Rana bata karya sai da uwar diya taji
kunya.tun ranar laraba aka fara gudanar da
shagalin bikin farida da angonta dr
shuraim.akayi kamu laraba,alhamis akayi
kunshi,jumaa akayi sisters eve da
yamma.ranar asabar aka daura aure da
misalain karfe goma sha daya na safe abisa
sadaki mafi kankanta don neman albarkar
aure,kuima a ranar akayi yinin biki.dangin
farida sunzo da yawa maza da mata daga
shagamu,tun sanda biki ya rage sati guda
suka fara zuwa don su taya ta murnar biki.a
ranar asabar da daddare akayi hadadden
party a hotel din tahir guest palace,wanda
mutane da dama suka halacci wajen.
Manyan likitoci abokan ango da kawayen
amarya,da yanuwaansu da abokan arziki
kowa yazo.makada kala kala sunzo kamar
mai dawayya,dan asharalle,yaron saadu
bori,fati niger,rabi mustapha,kowannensu
an bashi fili ya cashe.wannan yayi sai ya
matsa ya baiwa wani fili.babu abun da ake
kira sai likita shuraim angon sista
farida.barista muazzam da amaryarsa
janan,barista nuradin da uwargidansa
baraka su ma sun hallara.yan unguwansu ta
da duk sun zo babu wanda yasan adadin
wadanda suka zo,saboda yawansu.taro yayi
taro har amarya da ango basu iya gane
wadanda suka zo da wadanda basu zo
ba.kallo daya zaka yi wa ango da amarya ka
tabbatar suna tsananin murna.idan ka kalle
su zaka san maauratan nan suna tsananin
son junansu.sun ba wa kowa shaawa sosai
saboda sunyi kyau matuka,shigarsu ta
burge kowa,kowacce rana akwai kalar
kayan da zasu saka kala daya.
Kawayen amarya su ma sunyi nasu
ankon,dangin ango da irin nasu ankon
daban.'yan shagamu ma da irin nasu ankon
daban.masu daukar hotuna da bidiyo suna
ta aikin dauka,sai yau mutane da yawa suka
gasgata shuraim yayi saar mace mai
kyau,don kyawunta ya fito kamar ba ita
ba.ana daf da za a tashi sai ga uwar gidan
shuraim faiza ta shigo fili,ta yi wa kowa ba
zata ita da kawayenta guda biyu hafsat da
halima su ma mazauna london ne,tare suka
zo daga can.don da shuraim yayi yayi tazo
bikin tace baza ta zo ba,toh ashe ta taho
bai sani ba.ta danne kishinta tayi ta musu
kari da daloli sai a lokacin aisha farida ta
fara ganinta,ita ma haka,don ko a hoto ma
bai taba nunawa ko wacce ba.kyawunta bai
tsorata aisha farida ba ko kadan,don bata
fita kyau ba.fari kawai zata nuna
mata,tsayinsu daya,har farida ta fita tsawo
da yawan gashi.faiza ce ma ta tsorata da
ganina aisha farida saboda tayi mata ba
zata,ba ta zaci ta hadu haka ba,don 'yan
gulma sun tsegunta mata yar talakawa
ce,baka mummuna,ashe abun ba haka yake
ba.
Faiza ta kudiri aniyar zama na kishi,ba
kishin dokedoke da zage zage ba sai dai
zata nuna mata ruwa ba saan kwando
bane.wayewa da gogewa a cikin wayayyun
duniya tabbas abun da ta sani farida bata
sani ba,kuma ba zata taba sani ba.zata san
tayi garajen aure mata mili,don mai karbar
shuraim ahannunta sai yayi shirin yaki sosai
DUK KYAN TAKALMI 3* 13
Sai dr shuraim yaji dadi da ganin faiza ta
saki ranta,suka gaisa da farida sosai,har da
baby yarsa mai kama da uban kamar an
tsaga kara.babu wacce ta fi jin mamaki da
ganin aisha farida ita ce amarya sai
kanwarsa da suka hadu da ita a asibiti.suna
ganin juna suka shaida kansu,suka gaisa
cike da farin ciki.
Washegari ranar lahadi da yamma akayi
walima da yamma a farfajiyar gidansu
farida,aka zuba kujeru da yawa da manyan
dardumai.mata ne zalla da kananan yara sai
amarya da ta sha alkyabba,kawaye nta suka
zagayeta tana kan darduma a zaune daga
gabagaba.
mata guda uku ne suka yi waazi a wannan
waje,dukkaninsu akan falalar bin miji suke
magana.saboda yadda aazin ya ratsa
zuciyoyin mata,sai kowacce jikinta yayi
sanyi har da masu zubar da hawayen
imani.daga karshe abida ce ta karbi
lasifikata hau kujerar malamai ta dubi
dandazon matan da suka taru a
wajen,yawansu ya kai yadda baza su kirgu
ba,yara,manya,yanmata da tsofaffi.sai tayi
murmushi tayi musu sallama,sannan tayi
bismillah,ta dubi aisha farida. Like · 2 · 9
April 2013 Hajara Haruna Mahmud Ta
ce,nasiha zanyi miki ya ke kanwata farida
game da zaman aure.na farko iani miki
nasiha da ki bi mijinki domin aljannar mace
tana karkashin tafin kafar mijinta.yake
kanwata,ki fi shi farin ciki idan yana farin
ciki,sannan idan yana bakin ciki ki fishi
bakin ciki.ki kwantar masa da hankali.ya ke
kanwata aisha,ki lura da lokacin cin
abincinsa,domin mayunwaci mafadaci
ne.duk lokacin da kika lura lokacin cin
abincinsa yayi toh ki tanadar masa kafin ma
ya iso.idan ya shigo gida bayan kinyi masa
tara irin ta darajawa,toh ki gabatar masa da
abinci ba sai yace ina abincina ba?don idan
bari ma ya tambayi abinci to ransa ya baci
ma kafina a kawo masa abincin.wani ma sai
yaji baya shaawar abincin,sai yaji gara ya
tafi hotel ya ci mai dadi,duk ranar girkinki
sai yaki dawowa yaje yaci awaje.
Ya ke kanwata ki lura da lokacin da mijinki
yake jin bacci,ki bar shi ya kwanta ya huta
saboda wadansu matan sai sanda mijinsu
yake jin barci zasu tayar da shi su ce suna
da magana,yayi-yayi ta bar maganar sai da
safe tace wlh sai ka saurareni.daga lokacin
da kike hana mijinki yayi bacci a lokacin da
yake jin barcin to kina haddasa kakkaurar
gaba ce wacce ba zata gushe a tsakaninki
da shi ba. ya ke kanwata ki zauna a shirye
ki nunawa mijinki koda yaushe kina
bukatarsa.duk wani yanayi na kwarkwasa ki
dinga nuna masa.duk lokacin. Da kike
zaune da shi. Ki dinga shafar dukkanin
sassan jikinsa yadda zai yi farin ciki. Ya ke
kanwata ina horarki da yin ado ki lura da
ina yake fara kallo a jikinki da zarar ya shigo
cikin gida. Wani mijin fuskar matarsa yake
fara kallo,wani mijin da ya shigo kirjin
matarsa yake fara kallo,wani bayanta yake
fara kallo. To ki nutsu ki gane inda naki yaje
fara kallo. Idan fuska ce ki kula da lokacin
dawowarsa kafin ya shigo sai ki gyara fuskar
ki wanke ki saka hoda ki saka jagira,jan
baki,eye shadow da dai sauransu yadda
fuskar zata yi kyau sosai. Da ya zo sai ki yi
kokarin nuna masa fuskar kina murmushi.
Idan kirjin yake fara kallo to ki tanadi bra
mai kyau,irin mai karfen nan mai gyara
kirji. Tunda kin san kirjin yake fara kallo to
ba zai so kirjin ya ragwargwabe ba. Ko
bayan kin haihu sai ki bi duk hanyar da za ki
bi kada ki bari ya tamule,don wasu matan
su suke kwararraba kansu da zarar kin
haihu sau daya yaga kin tsufa sai ya fara
sha'awar ya auro wata budurwar mai kirji a
cike. To amma idan kika iya kula da
kanki,ba ki lalace ba ba zai tunanin neman
wata ba
In a gargajiyance ne akwai abunda larabawa
suke yi kirjinsu ba ya tamulewa,alkamadin
nan da kuka sani tana da amfani. Da zarar
kin sa rananr da zaki yaye danki kamar sati
uku kafin ranar da zaki yaye shi sai ki dinga
yin kunun alkama da nono ko
madara,madarar fulani ba yar kanti ba. Ki
sha kofi daya da safe kofi daya da yamma.
Bayan kin yaye yaron ma sai ki sake yin sati
uku kina sha,sati 6 kenan. Sannan randa
kika yaye yaron kuma sai ki saka bra wacce
ta matse ki sosai to wannan zai hana shi ya
zube duk da gyara ba zai yi kamar kari ba.
Ya ke kanwata ki lura da wuraren da mijinki
yake sa ido a jikinki in bayanki yake fara
kallo to akwai bukatar ki koyi tafiya idan
yace miko min buta sai ki juya kina
jujjuyawa ki wuce gaba yana biye da ke kice
za ki kai masa har bandaki. Ya ke kanwata
kada ki yarda mijinki yaga abun ki a jikinki,
ki kiyaye hancin mijinki kada ki yarda hancin
sa yaji wani karni,doyi ko bashi a jikinki to
duk lokacin da ya shigo dakin ki ko baby
warin sai yaji kamar da warin ba zaki taba
yin farashi a wajensa ba,kin zubar da ajinki
a wurinsa.saboda dauda ta dade tana kashe
aure sai a dauka wata aljana ce take zuwa
ta raba aure nan kuwa alnakiya ce kawai.
Ya ke kanwata ki kyaye kunnen mnki kada
ki yarda ya ji mummunar magana daga
bakinki. Ya zamanto duk abinda zai fito
daga bakinki zuwa kunnen mijinki to
magana ce ta girmamawa,jan hankali ko ta
tayar da sha'awa. Misali da na ganka sai
naji jikina ya yi wani zim don dadi (haha)
yake kanwata a lokacin da mijinki yake
kwance dake ki nuna tunda kike a duniya
ba a taba dadada miki ba irin a wannan
lokacin domin wannan zai sa kullum ya yi
sha'awar kasancewa tare dake. Ya ke
kanwata magana ta karshe da zan fada miki
ki guji bakin kishi,kishin da zai sa ki kasa
zaman lafiya da mutanen gida. To wannan
kishin zai saka tsana a zuciyar mijinki,kishin
da mace za ta yi shine wanda na fada a
baya,ya zamanto ba ya ganin wata mace a
duniya sai ke.duk abunda zaki yi ya
zamanto idan yana rumfar kasuwarsa ko
office ke yake tunawa.amma kishin da zaki
sa mijinki,abokiyar zamanki ko makotanki
cikin fitina to wannan kishi ne na lalatar
zamantakewa na aure. Allah ya nuna mana
ladubba na aure babu laifi mace taci abinci
tare da mijinta.ta bangaren maza kuma
addini ya nuna kada ango yaje dakin
amaryarsa haka hannu ba komai ya nemi
dan wani abu da zasu lasa kamar dan
nama,lemo ko dan cincin ya tafi da shi
dakin amarya.
Da farko yayi mata sallama ita kuma wajibi
ne ta amsa ba wai ta dinga noke-noke ba
wai sai an sayi baki. To bakin dukka ya biya
tunda ya biya sadaki. Bayan nan sai ya
shiga dakin da farko ya kama gashin
madigarta ya rike sai yayi addua yana tsaye
a kanta. "Allahumma inni as'aluka min
khaira ha wa khaira ma fiha wa khaira ma
jabaltaha alaihi wa'auzubikha min sharriha
wa sharri ma fiha wa sharri ma jabaltaha
alaihi. Ma'ana "ya Allah ina rokonka
alkhairin wannan amaryar tawa da alkhairin
da ka halicce ta akai kuma Ya Allah ina
neman tsarinka daga sharrinta da sharrin da
yake tare da ita da sharrin da ka halicee ta
akai" saboda wata ballagazar daga ya kai
hannunsa kanta sai ta buge hannun ta ce zai
murde mata kai. To iyayenta basu taba
fada mata ba ko malamanta. Ko da ya
manta to ki cire dankwalinki ki mika masa
kai,ki tuna masa idan ma bai sani ba ki fada
masa yadda zai yi idan ke kin sani. Kuma ba
amrya kawai ba ko da wani abu kika siya
kamar gida,mota ko dabba kafin ka fara
amfani da abin ka yi wannan addua. Idan
dabba ce an ce ka dafa bindin kamar kaza
sai ka kama bindinta ka yi wannan addua to
ba za ki ga wani abun bakin ciki game da
wannan dabbar ba. Haka idan sabon gida ne
ya dafa saman gidan yayi wannan addu'ar in
mota ya siya ya daga saman motar yayi
wannan adduar. Bayan ya yi wannan adduar
to sai ya zauna a kusa da ita su rungumi
juna su yi godiya ga Allah da yasa suka
zama halal ga junansu sannan ya gabatar da
wannan dan kayan makulashen da ya shigo
da shi su ci,ana ci ana hira ta sha'awa da
bege.
Amma an fi so kafin ciye- ciyen su fara
gabatar da sallah raka'a biyu nafila,kai ne
daman liman sai ka daga hannu ka yi muku
addua,Allah ya raba ku da sharrace-sharac
cen makiya,ya baku zuria ta gari,amarya
tana cewa amin.in duk sun kammala
wannan suka shiga kwanciya miji ya kusanto
matarsa sai yayi wannan addu'ar yace
bismillahi Allahumma jamnibnashaidan a wa
jannabul shaidana ma razaktana. Ma'ana,da
sunan Allah,ya Allah ka nisantar da shaidan
daga garemu,kuma ka nisantar da shaidan
daga abunda ka azurtamu da shi. Manzon
Allah (S.A.W) ya ce idan Allah Ya azurta su
da da a wannan saduwar da suka yi to babu
rabon shaidan a jikin wannan dan. Ba zai
iya cutar da shi a jikinsa ba ko a zuciyarsa
ba. Ba ranar angonci kadai ba duk randa
zaku sadu miji yayi wannan addua idan ya
manta ki tuna masa. Ba amarya kawai
ba,babu wacce bata karu da nasihohin
abida ba. Kuka yayi mata face-face a ido
kafin ta gama kamar yadda ya yiwa aisha
farida. Ta tabbatar yau abida ta cika amanar
da ta dauka ta rike ta tun tana karama har
zuwa wannan ranar data aurar da ita,ranar
da za ta damkata a hannun mijinta. Aisha
farida ta taso da sauri tana kuka ta
rungume abida suna ta kuka.kanwar
amarya manauwara ita ma ta taso ta zo ta
rungume su suna kuka.yayin da yan'uwa da
sauran jama'ar dake zaune a wajen suka
dinga fashewa da kuka don tausayinsu.
Aisha farida ta dago ta dubi jama'ar dake
wajen ta sharce hawaye. Tace" aunty abida
ta yi min komai wanda uwa da uba suke yi
wa yarsu. Tun ina karamata har izuwa ranar
da zata raka ni gidan mijina. Alllah shi ne
gatana abida ita ce jigo kuma jagorar data
kaini ga samun nasarar komai da na samu a
rayuwata.karatuna,zama da jama'a,farin
cikina da mijin da na aura. Abida ta hana
dan cikinta abu ta bani dan uwana yana
hana ni abu ita ta ba ni.anti abida bata son
taga damuwata,balle ta ga kukana. Ina yi
mata fatn Allah ubangiji Ya saka mata da
gidan aljanna,Ya raya mata