Showing 21001 words to 24000 words out of 87292 words

Chapter 8 - Duk Kyan Takalmi Complete Hausa Novel

Eeshat   

16 Jul 2026

283

baiwar Allah ai ba da sassafen nan
zaki zo ba, sai da rana in aiki ya lafa ko? Nayi
turus banji dadin amsar daya bani ba, ya wuce
abinsa ya barni a tsaye. Sai ga gogan nawa
yau kuma shigar hausa yayi, shadda ruwan
bula tazarce ya dora hular da ta dace da kalar
kayansa. Ya ratayo laptop dinsa a kafadarsa
sai naga ya kara yin kyau matuka babu wacce
zata kalle shi bata sake kallonsa ba. Ya tari dr
lukman sukayi magana, sannan kowa ya wuce.
Sai naji zuciyata na tafarfasa saboda shaukin
so, kai kace zakanya ce mai tsananin jin
yunwa ta ga nama haka zuciyata ta dinga zillo
tamkar ta ballo ta fito da taga abincinta. Sai
dai wannan abincin bana lasa bane, yafi
karfinta. Tamkar soyayyen nama ne aka soya
yana kamshi amma aka zazzaga masa guba
kaga duk kwadayin mutum doke ya kalla ya
wuce ko da kuwa marmarin naman zai kashe
shine. Na fara takawa a hankali na matsa daga
bakin kofar kafin ya karaso. Tun daga nesa na
amshi wata galleliyar harara daga gareshi.
Daya karaso bakin kofa kafin ya lalubo mukulli
ya bude kofar sai da ya waiwayo bayansa inda
nake a tsaye ya wurgo min wata hararar wacce
tafi ta dazu wulkilewa. Sai nayi sauri na juya
na fara tafiya ba tare da nasan inda zanje ba,
sai gani a bakin gadon marasa lafiya nayi wuki
wuki suna kallona ina kallonsu. Sannu likita,
zoki duba cikinsa ki gani ya kumbura. Inji wata
tsohuwa mai zaman jinyar danta. Na girgiza
kai nace ki kira likita ni ba likita bace. Nayi
saurin barin wajen na dawo bakin kofar ofis din
na tsaya, nayi kamar in tura kofar in shiga sai
na fasa. Na hakura na tafi ba don zuciyata
tana so ba. Ina zuwa ofishinmu na iske
kawayena suka hau min surutu. Wai aisha
farida ina kike shiga ne aka nemeki aka rasa
kullum har anyi test jiya ba kya nan? Nayi
shiru na koma gefe na zauna na rasa abun da
yake min dadi. Naci sa'a khadija sani tace inzo
in rakata ta siyo ruwa zata sha magani. Ashe
itama ta kunso labarai kala kala take so mu
kebe ta fatsar. Ta dube ni ta tabe baki tace
baki tambayeni dr shureim ba. Sai naji gabana
ya fadi, sai na zargi kaina ina ganin kamar
kowa yasan halin da nake ciki. Na zabura nace
kamar yaya ban tambaye ki dr shureim ba?
Tace kin manta inda muka kwana na nuna miki
sakonsa a wayata? To in fada miki an gasa
minshi da addua, ba adadi har sai da yaji ba
dadi. Ina kiransa ya amsa, yace dani wacece?
Sai na fada masa sunana khadija sani ismail.
Ni daliba ce a schl of nursing tanan aminu
kano, kuma ina attachment a nan cikin asibiti,
sai yace yayi kyau lafiya? Nace lafiya so nake
yayi saving lambata zan dinga kira muna
gaisawa. Na dafe kirji nace yayi saving lambar?
Tace kwarai kuwa, don da na sake kira sai da
ya ambaci sunana. Sai naji kwalla ta cika min
ido, kishi ya kamani, jikina yayi sanyi kalau.
Taci gaba da cewa da na sake kira sai yayi
tsiyar. Na tambaya a sanyaye meye tsiyar?
Tace wulkanci yayi min kamar zai zageni, wai
kada in sake kiransa. Kuka wiwi nayi da
hawaye na hakura dashi ma ni yanzu. Allah Ya
sa bai san fuskata ba, na goge lambarsa na
daina kiransa yanzu. Dadi ya rufeni, amma fa
na kara tausayawa kaina. Na bata shawarar
tayi hakuri taci gaba da addua, Allah Ya
musanya mata da abin da yafi alkhairi. Ta
amsa min da ameen. Da aka tashi daga
makaranta sai na kasa komawa gida, sai
nacewa khadiji sani ismali zanbi ta gidansu
somin 'yan gidanmu ba sa nan sun tafi unguwa
sai dare zasu dawo. Khadija tayi farinciki da jin
haka, sai muka dunguma muka tafi har yanzu
labarin dr takeyi min. Ban cika bata amsa ba,
tamkar tana min famin gyambon da yake
damuna da zugi ne. Kwakwalwata ta cunkushe
na rasa abin da yake min dadi, na kasa
tantance abin da zanyi. Abinci kala kala aka
jera min a gabana, amma na kasa ci da yawa
saboda damuwa. Khadija sani ta dube ni tace
wai don Allah aisha farida me yake damunki ne
kwana biyu kin susuce tamkar bake ba. Ba kya
son magana, ba kya son karatu gashi ba kya
son cin abinci tundazu dan abincin da kika
zuba kin kasa cinyewa, bakiga yadda kika rame
ba, kika kwanjale ba. Kin cika zurfin ciki, ba a
jin sirrinki daman. Wai me yake faruwa ne?
Nayi murmushi nace haka kowa yake ambata,
malaria ce ke cin jikina. Tace toh kisha magani
mana, yaya zaki zauna da ciwo kina malamar
asibiti, ko in saya miki babu kudi hannunki? Ta
soso min inda yake min kaikayi, na gyara zama
nace kamar kinsan satin nan cikin matsalar
kudi muke, kinga yanzu haka yayana ne aka
bashi ajiyar kudi, ya kawo gida aka shiga har
daki aka sace, ya rasa yadda zaiyi. Mai kudin
yana ta damunsa har da zai kai shi police
station yake ambato. Khadija tace a garin yaya
aka shiga har daki aka yi muku sata, babu
mukulli ne? Nace maso abinka ya fika dabara,
kinsan rayuwar cikin gari, gidan yawa aka shiga
aka dauke. Khadija tace babu dadi, Allah Ya
kiyaye gaba. Shi kuwa mai kudin bai san
kaddara bane? Yayi hakuri mana sai ya samu
ya biya shi. WaLlahi nima a cikin matsala nake,
domin na karbi kudi a wajen abba yayi dubu
hamsin kwanan nan haka ma a wajen mama.
Har sun gane ba'a makaranta nake kashewa ko
na tambaya basa bani. Sai tambayata suke me
nayi da kudi a cikin satin nan, naki fada, ai ban
isa ince malamai na kaiwa ba sai a kusa kashe
ni.
Tags :
Bansake magana ba dai har muka isa gidan
malam. Yana ganin mu ya fara washe baki,
fara'ar yau tafi ta jiya. Muka zazzage masa
kudaden jakarmu kakaf domin bayan dubu
ashirin da dayan da ya karba sai da ya sake
kwakwalo min wasu kudaden daban daban har
dubu biyar da dari biyar. Kuma na harhada na
bashi, a takaice dai har cikon dubu daya da
dari biyar nan gaba zan ciko masa. Ita ma
ummi ya kara mata wasu kudin, idan ta tashi
cikowa ba dubu goma zata ciko masa ba,
goma sha uku zata ciko. Yace ya bamu
kwanaki uku mu dawo, ranar laraba kenan kafin
komai zai daidai ta. Muka fito muna murna,
ummi tana tabbatar min komai zai daidaita in
kwantar da hankalina. Na tafi gida ita ma ta
koma gidanta, na sake shirgawa abida wata
karyar tunda ban taho da kayan walima ba,
naso in siyo musu lemo da biskit amma na
juyewa malam kudin dukka, da kyar ma na
karaso gida, sai da kudi ya kare. Ko kusa ban
damu da himilin bashin dake kaina ba, burina
aiki yaci in mallaki dr shureim shine a gabana.
Na yina ina hidindimuna da 'yan gidanmu cikin
walwala da farin ciki. Da dare yayi na shiga
barci sai na tsinci kaina na canza tunanina ba
irin na da bane. Yanzu tunani nake gani a
gidansa har mun zama ma'aurata, gani dare-
dare a cikin hadaddiyar motar nan tasa muna
tafe muna hirar soyayya. Na dade ina
tunaninsa sannan nayi bacci, na dora da
mafarkinsa mai dadin gaske. Na sa wa
zuciyata na sami dr shureim na gama kamar
yadda malam ya bani tabbaci. Naso in makara
saboda dadin mafarki, na tashi a gaggauce na
shirya na karbi kudin babur a wajen abida.
Yayana ya bata ta bani donshi yana riga ni fita
ma. Sai uwani ta biyo ni zaure da sauri ta
tsayar dani tace yanzu zaki karbo kudin daga
banki? Ko sai kin taso zaki taho dashi? Bilki ta
kawo zubinta jiya na wajenki kawai nake jira in
aikawa haj rabi na fada mata yau da rana zan
aiko mata. Sai zuciyata ta hau dukan uku uku
na fara zullumin inda zan nemo wadannan
makudan kudi. Na hau rawar murya ina kame
kame, nace sai an taso zan taho da kudin. Ina
kan babur ina tunanin yadda za'ayi idan na
dawo gida babu kudin? Ina shiga cikin asibiti
naji farin ciki ya lullunbe min zuciyata saboda
ko ba komai an fara aiki, zuciyarsa ta fara
bugowa gare ni. Sai kuwa naci sa'ar a ranar an
tura mu bangarensu dole zan ga ofishinsa ko
ba ma wajensa aka mu tura mu ba. Muna
shiga kuwa dakin darasin muka ci karo dashi
da dr lukman suna fitowa medical students
suna biye dasu zasu je zagayen marasa lafiya
(ward). Na tare su da sauri na gaishe su, sai
naji caraf ya amsa hadda kallon fuskata, ba
murmushi yake ba haka bai bata rai ba. Dr
lukman ne yake dariya, har yake yi min wasa
yace ke 'yar shagamu ina kika shiga kwana
biyu, rannan har yahaya umar yace in baki
waya ku gaisa, nace ba kya kusa. Nayi dariya
nace to yaushe zanzo ka kirawo min shi a
wayar muyi magana? Da yake yana tafiya ne
sanda yake magana, har yakai barandar waje
banji abin da yace ba. Sai wani dalibi ne yake
bayansu ya juyo yace min cewa yayi kizo gobe.
Na yini ina farin ciki saboda naga canji wajen
amsa gaisuwata da kuma kallon mutuncin da
dr shureim ya min. Ban fara fargaba ba sai da
aka tashi daga makaranta na tunkaro hanyar
gida. Na shiga zullumin karyar da zan gina
wacce ba za'a rutsoni ba, dakin uwani na nufa
kai tsaye sai ta fara murna tana gyara hannu
zata karbi kudi ta kidaya. Sai na zube a
gabanta ina marairaice murya ina bayani. Nace
wallahi tun safe ban huta ba muna ta kai kawo
a cikin asibitin saboda matar bata da jini, don
haka ba za'a yankata ba dole sai an kara mata
jini. 'Yan uwanta ne suka zo maza da mata
muna ta auna jinin har a sami wanda ya dace
da nata shi yasa ban samu fita daga asibitin
ba naje banki, amma gobe da sassafe zanje in
karbo. Uwani ta bata rai, yadda ta amsa min a
ciki ciki na san bata so haka ba, ta bini da kallo
har na fice daga dakin. Ina cin abincin rana na
fice wajen musbahu ban same shi ba, na bar
masa doguwar wasika. Nazo giftawa ya
makoftanmu nayi ido hudu dahare ta leko
kenan ta ganni, ita ma dari takwas ta ranta
min kudin dinkinta zata kai domin ta kusa
haihuwa, ita ma ranar litimin din nace zan
kawo mata. Dole na shiga gidan na tsara mata
karya iri iri na ce gobe zan kawo mata. Itama
ta nuna min bataji dadi ba, har mijinta yayi
fada da yaga kayan dinkin a ajiye bata kai ba.
Naji hankalina ya sake tashi na fito a gigice na
shiga gidan mu har sai da abida ta shiga
damuwa ganin yanayin da na shigo. Tayi ta
tambayata ko lafiya? Nace lafiya kalau. Idan
naji damuwa ta gallabeni sai in tuno menayi da
kudin, kuma nan gana me zan samu. Sai inji
sanyi a raina. Washe gari talata na fita zuwa
makaranta, kai tsaye ofishin dr lukman na
wuce. Ina shiga na iske shi zai fita. Yace dani
ke kuwa baiwar Allah ai ba da sassafen nan
zaki zo ba, sai da rana in aiki ya lafa ko? Nayi
turus banji dadin amsar daya bani ba, ya wuce
abinsa ya barni a tsaye. Sai ga gogan nawa
yau kuma shigar hausa yayi, shadda ruwan
bula tazarce ya dora hular da ta dace da kalar
kayansa. Ya ratayo laptop dinsa a kafadarsa
sai naga ya kara yin kyau matuka babu wacce
zata kalle shi bata sake kallonsa ba. Ya tari dr
lukman sukayi magana, sannan kowa ya wuce.
Sai naji zuciyata na tafarfasa saboda shaukin
so, kai kace zakanya ce mai tsananin jin
yunwa ta ga nama haka zuciyata ta dinga zillo
tamkar ta ballo ta fito da taga abincinta. Sai
dai wannan abincin bana lasa bane, yafi
karfinta. Tamkar soyayyen nama ne aka soya
yana kamshi amma aka zazzaga masa guba
kaga duk kwadayin mutum doke ya kalla ya
wuce ko da kuwa marmarin naman zai kashe
shine. Na fara takawa a hankali na matsa daga
bakin kofar kafin ya karaso. Tun daga nesa na
amshi wata galleliyar harara daga gareshi.
Daya karaso bakin kofa kafin ya lalubo mukulli
ya bude kofar sai da ya waiwayo bayansa inda
nake a tsaye ya wurgo min wata hararar wacce
tafi ta dazu wulkilewa. Sai nayi sauri na juya
na fara tafiya ba tare da nasan inda zanje ba,
sai gani a bakin gadon marasa lafiya nayi wuki
wuki suna kallona ina kallonsu. Sannu likita,
zoki duba cikinsa ki gani ya kumbura. Inji wata
tsohuwa mai zaman jinyar danta. Na girgiza
kai nace ki kira likita ni ba likita bace. Nayi
saurin barin wajen na dawo bakin kofar ofis din
na tsaya, nayi kamar in tura kofar in shiga sai
na fasa. Na hakura na tafi ba don zuciyata
tana so ba. Ina zuwa ofishinmu na iske
kawayena suka hau min surutu. Wai aisha
farida ina kike shiga ne aka nemeki aka rasa
kullum har anyi test jiya ba kya nan? Nayi
shiru na koma gefe na zauna na rasa abun da
yake min dadi. Naci sa'a khadija sani tace inzo
in rakata ta siyo ruwa zata sha magani. Ashe
itama ta kunso labarai kala kala take so mu
kebe ta fatsar. Ta dube ni ta tabe baki tace
baki tambayeni dr shureim ba. Sai naji gabana
ya fadi, sai na zargi kaina ina ganin kamar
kowa yasan halin da nake ciki. Na zabura nace
kamar yaya ban tambaye ki dr shureim ba?
Tace kin manta inda muka kwana na nuna miki
sakonsa a wayata? To in fada miki an gasa
minshi da addua, ba adadi har sai da yaji ba
dadi. Ina kiransa ya amsa, yace dani wacece?
Sai na fada masa sunana khadija sani ismail.
Ni daliba ce a schl of nursing tanan aminu
kano, kuma ina attachment a nan cikin asibiti,
sai yace yayi kyau lafiya? Nace lafiya so nake
yayi saving lambata zan dinga kira muna
gaisawa. Na dafe kirji nace yayi saving lambar?
Tace kwarai kuwa, don da na sake kira sai da
ya ambaci sunana. Sai naji kwalla ta cika min
ido, kishi ya kamani, jikina yayi sanyi kalau.
Taci gaba da cewa da na sake kira sai yayi
tsiyar. Na tambaya a sanyaye meye tsiyar?
Tace wulkanci yayi min kamar zai zageni, wai
kada in sake kiransa. Kuka wiwi nayi da
hawaye na hakura dashi ma ni yanzu. Allah Ya
sa bai san fuskata ba, na goge lambarsa na
daina kiransa yanzu. Dadi ya rufeni, amma fa
na kara tausayawa kaina. Na bata shawarar
tayi hakuri taci gaba da addua, Allah Ya
musanya mata da abin da yafi alkhairi. Ta
amsa min da ameen. Da aka tashi daga
makaranta sai na kasa komawa gida, sai
nacewa khadiji sani ismali zanbi ta gidansu
somin 'yan gidanmu ba sa nan sun tafi unguwa
sai dare zasu dawo. Khadija tayi farinciki da jin
haka, sai muka dunguma muka tafi har yanzu
labarin dr takeyi min. Ban cika bata amsa ba,
tamkar tana min famin gyambon da yake
damuna da zugi ne. Kwakwalwata ta cunkushe
na rasa abin da yake min dadi, na kasa
tantance abin da zanyi. Abinci kala kala aka
jera min a gabana, amma na kasa ci da yawa
saboda damuwa. Khadija sani ta dube ni tace
wai don Allah aisha farida me yake damunki ne
kwana biyu kin susuce tamkar bake ba. Ba kya
son magana, ba kya son karatu gashi ba kya
son cin abinci tundazu dan abincin da kika
zuba kin kasa cinyewa, bakiga yadda kika rame
ba, kika kwanjale ba. Kin cika zurfin ciki, ba a
jin sirrinki daman. Wai me yake faruwa ne?
Nayi murmushi nace haka kowa yake ambata,
malaria ce ke cin jikina. Tace toh kisha magani
mana, yaya zaki zauna da ciwo kina malamar
asibiti, ko in saya miki babu kudi hannunki? Ta
soso min inda yake min kaikayi, na gyara zama
nace kamar kinsan satin nan cikin matsalar
kudi muke, kinga yanzu haka yayana ne aka
bashi ajiyar kudi, ya kawo gida aka shiga har
daki aka sace, ya rasa yadda zaiyi. Mai kudin
yana ta damunsa har da zai kai shi police
station yake ambato. Khadija tace a garin yaya
aka shiga har daki aka yi muku sata, babu
mukulli ne? Nace maso abinka ya fika dabara,
kinsan rayuwar cikin gari, gidan yawa aka shiga
aka dauke. Khadija tace babu dadi, Allah Ya
kiyaye gaba. Shi kuwa mai kudin bai san
kaddara bane? Yayi hakuri mana sai ya samu
ya biya shi. WaLlahi nima a cikin matsala nake,
domin na karbi kudi a wajen abba yayi dubu
hamsin kwanan nan haka ma a wajen mama.
Har sun gane ba'a makaranta nake kashewa ko
na tambaya basa bani. Sai tambayata suke me
nayi da kudi a cikin satin nan, naki fada, ai ban
isa ince malamai na kaiwa ba sai a kusa kashe
ni. DUK KYAN TAKALMI 12 Sai naji hankalina
ya tashi, har na fara nadamar katobarar da na
tafka. Ta bude jakarta ta zaro dukka kudin da
yake jakarta, dubu daya da dari biyu ne kacal
sai 'yan canji. Ta miko min naira dubu daya, na
karba nayi ta godiya. Tayi ajiyar zuciya tace
wallahi dr ya cuce ni, na kashe kudina a banza
ko gezau baiyi ba. Na fada cikin marainiyar
murya nace karki damu kaddara ce Allah Ya
aiko mana. Sai nayi sauri na gyara zancen son
naga tayi sauri ta dubeni, sai nace ciwon 'ya
mace na 'ya mace ne, tunda ya shafe ki nima
ya shafe ni. Bakiji yadda zuciyata take tafasa
ba don takaici. To shi dr dame yafi sauran
likitoci su basa wulakanci sai shi? Khadija tace
yafi sauran mana ke kuwa, shifaa a london yayi
karatunsa, ke har pri sa secondary duk a can
yayi rabin rayuwarsa, sai da yazo nigeria fisha
ya tafi. Ance dai yayi aiki a asibitin nan
shekara 2 a lokacin yana karamin likita. Sai ya
koma ya sake shekaru hudu ya zama
consultant sannan ya dawo kwanan nan. A
bangaren ilimi addini kuwa a saudia yayi
karatun kurani, larabawa suka koyar dashi,
ance yafi kowanne likita sanin kurani. Don tun
yana yaro yaje saudia sai da ya sauke ya dawo
london, ya karasa primary kinga kuwa Allah Ya
yi masa baiwar da ba kowa yake da ita ba.
Gashi dan attajiri shima attajiri, ga ilimi dukkan
bangarorin biyu, ga wani kyau tamkar sai da
zaba aka bashi. Kowacce mace dole taso shi,
sai dai idan ta ga ba ta samu bata hakura
irina. Maryam ahmad ma na gano sonsa
takeyi, har wani kishi takeyi dani, nace kije na
bar miki in dai shureim ne zaki gaji ki kyale shi.
Amma ke aisha farida naga bai dadaki da kasa
ba, ko zancensa ma ba kya so. Kowa yana
yabon kyawunsa, ke ko ki kula. Baiyi miki
bane? Sai naji tamkar an saki bom a kahon
zuciyata, saboda faduwar gaba. Nayi firgigit
nace yanzu khadija ina ta kaina ina ni ina cusa
kaina wajen irin wannan halitta? Ai sai ku
kyawawa, masu mota 'ya'yan attajirai. Khadija
tace kin hutawa kanki wallahi kina burge ni
yadda kike tafiyar da rayuwa, ba kya jajubo wa
kanki abun da zai wahalar dake. Nima nayi
nadama ba zan sake shiga irin wannan hatsarin
ba. Yanzu mun bata da malaman nan
makaryata, wai yaga aurenmu har da haihuwar
'yan biyu. Shine ai na saki jiki nayi ta tura
musu kudi suna cemin zai zo da kafarsa
nemana ga mutum kamar zai yayyaga ni cikin
waya don masifa. Bani ba wani malami ai
yanzu na rufawa kaina asiri nace mohd ya aiko
da iyayensa muyi aure. Ina laifinsa yaro
matashi, yana da mota da gidan kansa da aikin
bankinsa, nima da aikina ya ishe mu rayuwar
duniya. Sai naji hankalina ya tashi, dana sani
ta afko min. Na gyara zama nayi tagumi ina
duban khadija na rasa in da zan saka raina, sai
yanzu na fara gane kuskuren da na tafka a
rayuwa. Ummi ta cuce ni. Na fada a cikin
zuciyata yayin da hawaye ya cika min ido.
Nace da khadija kina so kice

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login