Showing 39001 words to 42000 words out of 64149 words

Chapter 14 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

156

bai fito ba sai da ta tafi. Sai da aka yi sati biyu sannan ta sake zuwa, ranar na yi murna kamar na cinye ta, haka itama ta dinga biya min mun hira sosai kuma na ji daWin zama da ita sosai da sosai, tun daga wannan lokacin ta fara zuwa duk da ba ko yaushe ba,  babban abin daWin Sardauna bai taSa yi min ™orafi akan zuwa na ta ba, duk da wani lokacin su kan haWu. 



Na yi mata maganar rashin haihuwata, ta ™ara ™arfafamim gwiwa tare da ba nj hakuri akan hakan, da cewa na dage da addu'a, babban abinda ya burgeni da Bilkisu shine karatunta ta ti degree a yanzu ma ta Waura masters sannan tana yin aiki, mace mai ilimi daban ce, komai na ta gwanin ban sha'awa akwai tsari, ban taSa zuwa gidansu ba, amma ina yawan  ce mata zanje idan na fita. 



A Sangaren Turaki har yanzu auren shiru, sai dai kawai na ji mostintsa idan ina falo amma bai taSa shigowa ba kuma ko a waje bamu taSa haWuwa ba, da muka yi magana da Ra'is ta wayar Hajiya ya ce da ni wai Turakin nema yake nemansa a waya lokaci zuwa lokaci ya ji lafiyarsa da ta mutanen gidan. 



A tsakanina da Sardauna abubuwa suna tafiya yadda suke, kawai dai kwana biyu ya ™ulla sabuwar abota da wayarsa da kuma zuwa majalisa, wanda a yanzu ya Wan rage bai cika fita kullum ba. 



Yau tum safe na kammala aikina, dan mu yi da Bilkisu zan koya ma ta yadda ake Samosa wrap, ta ce tana so kuma ta ga ina yi yawan yi tasan dole maza suna so. 



Ina tsaka da aikin gida ta shigo, daman ta ce yau gudun wajen aiki za ta yi, murmushi na sake sannan na ce. 



"Har kin ta so?" 



"Na dai gudu, ai yau sai na koyi abin Samosar nan, har da wasu kayan fulawar tunda nima na kusa aure." 



Murmushi na sakar mata sannan na ce. 



"Ke ce muna da shan biki." 



"Ke ba wanda nake kulawa, kawai ma faWa ne." 



"Wai damam ina ta so na tambayeki me ya sa bakya kula maza ne, ba ayi miki zancen aure a gida?" 



"To Nana ai aurw lokacine, bazan iya biyewa namiji ba inda ba na aure ba, dan ba duka ba ne suke da kirki, yanzu zai yi miki SARTSE a rayuwarki indai namiji ne." 



"Amma nikam Alhamdulillah wallahi, miji dai na yi da ce." 



Na faWa ina shiga cikin kicin, bayana ta biyo tana faWin. 



"Ga alamu nan dai, muma idan mun sami irin nakun sai mu aura, amma wa'yanan samarin shawon ba dani ba." 



Na tuntsire da dariya sannan na ce. 



"Lallai fa Samarin Shawo." 



Haka muka shiga ina yi tana kallo tana 'yan tamnayoyinta har muka kammala. Daga nan muka dawo falo muka shiga hira tana nan har yamma sannan ta tafi. 



Haka rayuwata ta yi ta tafiya, yau daWi gobe akasin haka, abubuwa suna tafiya wasu yadda aka tsara wasu kuma ba yadda aka tsara ba, tsakanina da Sardauna kullum sabuwar soyayya, sabuwar biyayya, a kullum Sardauna yana farin ciki tare da yin alfahari da ni. Yana yawan ce min. 



"Nana kin yi min komai a rayuwa, Allah Ya bani ikon faranta miki rai." 



Ni kuma a kullum duk wata sabuwar na'uin biyayya yi wa Sardauna nake, wani abu ni a kaina na kan ji kamar ya zarci hankali, dan a yanzu takai idan Sardauna yana kan kujera ni a ™asa nake zama, sai ya dage min nake zama akan kujerar ko na ga ya sauko ™asa. 



08:30pm. 



Zauna nake a falo, hankalina yana kan wayata dan nasan Sardauna yanzu ba lokacin dawowarsa ba ne. 



"Hon!" 



Kamar daga sama na ji muryarsa. 



"Kawo min abinci." 



Ya faWa yana nufar kan gadon, a tsorace na tashi gabana ya na faWuwa, me ya sami Sardaunana haka? 



A yanayinsa ma kamar cusa abincin yake dan kamar baya jindaWi. 



"Me ya faru dan Allah." 



"Bakomai." 



Ya faWa yana ci gaba da abincin, yana cikin ci ya tashi ya shige Wakinsa, ba shiri nima na bishi ciki amma kafin na je ya kulle Wakinsa. 



"Innullahi wa'inna illahir raji'un, me ya faru dan Allah, Ya Allah Ka kawo wa Sardauna na sau™i." 



Na faWa ina komawa falon, sai dai gaba Waya na rasa abinda zan yi tunaninma na kasa, halin da Sardauna yake ciki ya dameni, Whatsapp na duba naga Bilkisu na online, na tura mata message



" 'yar uwa da matsala." Na haWa mata da emoji na kuka, cikin ™asa da minti ta dawo min sa amsa. 



"Sisi me ya faru?" 



"Sardauna ne ya dawo gida da damuwa." 



"Me yake damunshi?" 



"Bai faWan ba wallahi."



"To me kike da baki tambayeshi ba, Nana kije ki tambayeshi mana, a shawarar da nake baki a kullum ina faWa miki ki mayar da damuwar mijinki taki." 



"Ya kulle Wakin." 



"Toopa, gaskiyya wannan babbar matsala ce, ko dai zuwan da na yi Wazu ne?" 



"Anya kuwa, Sardauna baya son mutane su zo amma ke bai taSa min magana akanki ba." 



"Ikon Allah." 



Ta haWo da emoji na mamaki. 



"Yanzu mene abin yi?" 



"Abin yi kije ki tambayeshi mene, ki yi amfani da duk wani ikon da ™arfinki wajen ganin kin magana ce mai damuwar tasa." 



"Na gode 'yar uwa." 



Daga nan na kashe data ta na kwanta, ina ta faman sa™e sa™e har bacci ya Waukeni, washe gari da safe bayan na yi duk wani abu da nasaba, amma Sardauna har wajen ™arfe tara bai fito ba, ina nan zaune akan a falo ya fito da shirinsa, da sauri na tashi tare da faWin. 



"Ina kwana?" 



"Lafiya, ya kike?" 



"Alhamdu Lillah, ga abin breakfast nan." 



"Nana bazan iya cin abinci ba, ina cikin damuwa ki yi ha™uri." 



"Me yake damunka dan Allah, ka faWa min ka ji." 



"Nana ina cikin damuwa kawai, ki yi ha™uri." 



"Yanzu akwai damuwar da bazaka faWan ba a matsayina na matarka dan Allah?" 



"Ba haka ba ne Nana, ki yi ha™uri zuwa na dawo kinji."



Yana faWin haka ya fice, ya barni tsaye kamar wacca aka dasa, na kusa minti goma sannan na sami waje na zauna, haka na shiga damuwa gaba Waya ko breakfast Win nima ban iya ba, sai wajen sha biyu na rana na iya sa abu a bakina, daga nan na dawo kan kujera na ci gaba da zaman damuwa, sai ™arfe biyu Bilkisu tazo bayan ta dawo daga ofis, ta yi mamakin ganin yadda na rame ma fige duk a iya rana Waya. 



"Nana haka kika damu da Sardauna? Duk akansa kin wani canja hala ji fa?" 



"Bazaki gane ba Bilkisu, wallahi ina son mutumin nan sama da kowa, sama da komai a wannan rayuwar, bana so na ga wani abu guda Waya da zai dami Sardauna a duniya, bana son shi wallahi." 



"Lallai Nana, to yanzu me ya ce miki yana damunsa?" 



"Ya ce sai ya dawo." 



"Allah Ya sa alheri ne, Allah Ya sau™a™a al'amuran." 



"Amin amin." 



Haka tai ta yi bani shwarwrin hamyoyin da zan bi na yi maganin damuwar tasa da yanda zan kwantar mai da hankali, na nuna komai zai zo da sau™i, sai yamma ta tafi kamar ko yaushe. 



Tana tafiya na yi wanka na gyara gidan, bayan na yi sau™a™™en abinci na dawo na zauna, ina nan zaune na ji hayaniyar mutane. Labule na Waga na buWe Turaki na gani yau ma kaya ake shigo masa da shi, da alama yau ya dawo dan dama na ji alamun baya gidan, komawa na yi na zauna akan kujera na ci gaba da tunanin yadda zanyi kwantarwa da Sardauna hankali yana dawowa. 



Sai wajen tara sannan ya shigo gidan, babu damuwar a fuskarsa kamar jiya, amma bayan na shiga Waki na fito na ganshi ya haWa lai da gwiwa, da sauri na ™araso inda yake tare da cewa.



"Sardaunana, jarumina, Honey me ya faru?" 



"Nana! Bansan ta inda zan fara yi miki bayani ba, amma tabbas akwai matsala." 



"Wace irin matsala ce haka dan Allah?"



"Nana su Big Daddy da Hajiya ta sun matsamin wai suna ganin jikokinsu na wajena, wai shirun ya yi yawa, Nana duk bayanin da yakamata na yi musu, amma su kasa fahimta, faWi kawai suke duk inda matsalal take na nemo to na yi maganinta, Nana na shiga damuwa matu™a na rasa abinda zan yi shi ya sa kika ga na damu kwana." 



Shiru na yi nima kaina na rasa abinda zan faWa, matsalal daga ina take, me ya kawo duka wannan zancen? 



"Kinji abun wani kala ko?" 



Na gyaWa kai, sannan na ce. 



"Yanzu mene abun da za ayi?" 



"Ni kaina bansaniba, ina ta faman tunani." 



"Allah Ya sau™a™a mana." 



"Amin Honey nah." 



Haka muka zauna jigun jigun gaba Waya na rasa abinda ke mun daWi, me ya kai 'yan uwan Sardauna wannan zancen? Su da suke wayayyu, 'yan boko masu ilimi, amma zasu zo da wannan zancen? 



"Kar ki sakawa ranki damuwa kinji Hon, komai zai zo da sau™i." 



"Nasani." Na faWa tare da yi masa murmushin ya™e, sai yanzu na ji ina ma ina da halin kiran su Hajiya na faWa musu, gaba Waya rabona da su an kusa wata guda, Sardauna duk ya hanani. 



Ko da muka je bacci ma haka kowa ya kwanta, ransa babu daWi, ni barcin ma rabi da rabi na yi, Sardauna ne daman shi duk girman damuwa ba ta hanashi bacci, ni kuwa ko ya damuwa take mussamman ta al'amarin Sardauna to ba ni da wata nutsuwa akai. 



*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na sha tara.

    (19)





Gaba Waya Sardauna ba walwala ya yi komai har ya fice, a yanzu ba ni da kowa na kusa sai Bilkisu ita kaWai nake magana da ita, itama sabida mijina ya zaSe ta, kiranta na yi a waya duk da nasan tana wajen aiki, har ta ™araci ringing Winta ba ta Wauka ba, sai da na kira sau uku sannan ta Wauka. 



"Hello Nana, ya aka yi ina ofis ne." 



"Bilkisu akwai matsala ne babba ba ™arama ba." 



"Ta mece? Me yake damun Sardaunan?" 



"Matsalal daga gidansu take, akan zancen haihuwa ne." 



"To ai Nana ba ke ce me matsalal ba ko? Kamar kince min kin taSa Sari ko?" 



"Eyh na taSa, nice me matsalal, wai mahaifata ™arama ce, shi ya sa jariran basu fiya zama ba." 



"Innullahi yanzu Nana mene abun yi?" 



"Wallahi Bilkisu bansaniba, duk na shiga damuwa, mussamman ganin Sardauna da na yi a yanayin damuwa." 



"Ai ba daWi irin haka, ki lallaSashi ki ji ko akwai wafa mafita da yake gani, yau bazan shigo ba sabida zani unguwa amma zan zo a satinan." 



Daga haka ta kashe wayarta ta barni cike da damuwa. Ina nan zaune na rasa abinda ke min daWi, kawai na kira Ra'is bayan mun gaisa na ce da shi. 



"Ra'is akwai matsala a gidana." 



"Ta mece ba dai mijinki ba." 



"Shine Ra'is."



"Lallai Nana, ke kenan bamu da amfani sai matsala ta taso tsakaninki da mijinki shine mule da rana, ba kyajin kunya sai ki tunkare mu idan kuma kuna cikin soyayya babu 'yan iska sama damu ko? To wallahi kisani babu wanda zai ™ara shiga al'amuranki tsakaninki da mijinki tun da kin zaSi mutumin da ya haWu dake ta ha™waranki talatin da uku, kin bar wacca ta raini ki a cikinta har kika fito duniya, ta yi Wawainiya dake, kin bar wayanda suka raine ki, su ka so ki, su ka bakk farin ciki, su ka tsoraci kukanki Nana, duk akan wani mutumi guda Waya, ki je rayuwar duniya ce." 



Yana gama magana ya kashe wayarsa, kuka na fashe da shi, tabbas nasan maganarsa gaskiyya ce, kuma ya faWa min abinea nake bu™atar a tinasar da ni, amma ya zanyi da Sardauna Allan da ya hallice ni shi ya sanya mini soyayyarsa. 



Daga wannan lokacin na ™udiri aniyar bazan sake kiran kowa a gidanmu akan damuwa ba sai dak gaisuwa kawai. 



Bayan sati biyu. 



Tun lokacin da maganar nan ta fito gidanmu ya canja daga gidan farin ciki zuwa damuwa, daga gidan walwala zuwa na ™unci, babu wani abu Sai daWi a gidan, kullum muna neman mafita amna ta™i samuwa, ta Sangaren gida kullum Sardauna matsanta masa ake yi, an hana shi sakat. A yanzu Sardauna har baya son zuwa gidan Hajiyarsu ko Family House, kullum daga gida sai Majalisa yanzu ma da mota yake fita majalisar, ni kam bana iya komai banda tunanin mafita. A ko yaushe cikin sa™e sa™e nake, na yi ba™i na rame gaba Waya na fita hayyacina. 



Gashi Bilkisu ba ta sake zuwa ba, tun ranar da na faWa mata matsalal ta ce zata zo a cikin satin, idan ma na kira ta sai ta ce ba ta gari ma baki Waya.  Jiya da muka haWu da Turaki sai da ya tsareni da tambayar me yake damuna, me ya faru tsakanina da Sardauna, amma na ce da shi komai lafiya. Daga ™arshe ma ya fara yi min nasihohi masu ratsa zuciya akam ha™uri da rayuwar aure, sannan ya dinga jaddadamin na dinga yi wa mijina biyayya, har sai da na yi mamakin me ya sa ya yi haka.



Da na dawo Waki ma na yi ta faman tunani maganganun Turaki me suke nufi, yanayin maganar kaman faWa da nasiha yake min daga baya kuma ya dawo shawara. 



"Allah Ya sa alheri ne." 



Na faWa, sai kuma can na yi tunanin ko akan maganar da ta Sullo ne ta haihuwa shi ya sa. 



"Innullahi wa'inna illahir raji'un, ya zan yi ni Nana?"



Na tambaye kaina tare da fashewa da kuka, sai da na yi mai isata na ta shi na shiga Waki, zaman gidanma ya isheni tun da na zo gidan ban taSa fita ba ko sau Waya, a yanzu an kai wata uku zuwa huWu amma ban taSa fita ba ko gida ban je ba. 



Kwanciya na yi akan gadon na shiga tunanin rayuwa, da irin abubuwan da Sardauna ya saukar akaina, gashi kuma yana ™ara fuskantar wasu. 



"Lallai Sardauna ya cika sadauki, Allah Ka ™ara mai lafiya da arzi™i, Allah Ka ™arawa Sardaunana ha™uri da juriya akan abubuwanda suke tun karoshi, Allah Ka sani ina son bawan nan naka, Allah Ka so shi, ka yarda da shi, ka amince masa akan duk abinda ya sa gaba." 



Cikin ikon Allah wani bacci ya Waukeni, wanda kiran sallar magariba ne ya tayar da ni, ina tashi na Waura alwala na yi sallah, dan yanzu Sarduna a waje yake magariba, idan aka yi isha kuma ya fita, tara da rabi zuwa goma yake dawowa. 



Ina idar da sallah na shiga haWa masa abinci akan dinning, ina cikin haWawa ya shigo, fuskarsa kamar kullum amma yau ma tafi raunana, ajiye abinda nake na yi tare da tawowa inda yake. 



"Sannu da zuwa Mijina." 



"Yawwa Nana." 



"Ya ofis?"



"Nana rayuwa babu daWi, abubuwa duk sun kacame." 



"Innullahi wa inna illahir raji'un, me aka sake cewa kuma?" 



"Mene ma ba a ce ba Nana, mene ba a ce ba? Kinsan yau kwanakin da Big Daddy yaban zasu ™are gashi babu wata mafita da muka samu." 



"Ya baka kwanaki ne?" 



Na tambaya cike da mamaki, ya gyaWa kai kusan minti biyar sannan ya ce. 



"Big Daddy ya ban 10days akan na fitar da mafita, na ce ya ™ara min zuwa sati biyu to kinga yau anyi sati biyun." 



Hawaye na ji suna gangaromin a fuskata, da sauri na gogesu sabida kar Sardauna ya gani, ni da zan ™arfafa masa gwiwa bai kamata na raunana ba. 



"Nana bansan abinda Big Daddy zai ce ba." 



"Ni kaina kwana biyu na dage da addu'a sosai da sosai, abinda nake gudu kenan tun farko akan rashin haihuwar nan ka ce kai ba komai, yanzu ga shi komai ya juye." 



"Nana ni kaina matsamin aka yi a gida, shi ya sa kuma wallahi nauyinki nake ji Nana, ina jin kunyar yi miki magana akan haihuwa Nana." 



"Nasani, duk wannan matsi da takurar da muka shiga akan haihuwa ba ra ayinka ba ne, na kasance me yi maka uziri a ko yaushe Sardauna, ina sonka son da na yarda da kai fiye da kowa fiye da komai, na yi imanin har abada ba zaka taSa cutar da zuciyata ba Sardauna." 



Na kama hannunsa, ya Wago ya kalle ni. Idanuwansa fal da damuwar da ta dame ni. 



"A ko da yaushe ina mi™awa ubangiji Amanarka Sardauna, ina mi™awa Allah ragamar kula da kai, nasani Allah zai amss addu'a ta, ba zai taSa Woramin abinda zaifi ™arfinka ba, a ko da yaushe ina sonka zan kasance mai sonka Sardauna har numfashi na ™arshe."



Ji na yi ya jawo ni jikinsa ya rugumeni tare da faWin. 



"Nana, bani da wata kalma guda Waya da zan iya godewa kan alherin soyayyarki agareni, Nana nasami damarmaki masu yawa sanadiyar soyayyarki, na gode Nana, nima ina sonki."



Haka mu ka yi ta lallaSar juna, ina ™ara nunawa Sardauna girman soyayyarsa a zuciyata, har na samu ya ci abinci ya shirya ya fita Majalisa.  Sai goma ya dawo gida, ina nan inda ya barni ina ta faman sa™e sa™e dan yanzu babu abinda na ™ware da shi kamar damuwa, ina sa™a wancan na since wancan. 



"Honey baki yi bacci ba?" 



Ya faWa yana zama. 



"Ban yi ba tukunna, har ka dawo?"



"Eyh na dawo Honey, kin ga."



Ya faWa yana buWe ledar da ya shigo ita, kwalin wayar iphone, ya mi™omin. 



"Nana take." 



Na sa hannu na amsa ina mai jindaWi. 



"BuWe mana." 



Na fara kici kicin buWewa, iphone 16normal ce pink kala mai kyau. 



"Na gode sosai mijina, Allah Ya ™ara arzi™i lafiya da wadata." 



"Amin My love." 



Ya faWa tare da Waukana zuwa Waki. 



Washe gari Sardauna bai fita ko ina ba, muna gida gashi ba weekend ba, da na tambayeshi sai ya ce. 



"Bana som fita ofis, zan haWu da Big Daddy. Kuma kinga yau kwana goma sha huWu ta cika." 



Kamo hannunsa na yi, sannan na ce. 



"Wane irim hukunci kake tunani kake tunanin zai yanke?" 



"Nima bansani ba, amma bana son ya bani hukunci mai tsauri Nana." 



"Duk tsaurinsa bai zai yanke ma hukuncin da zaka rasa rayuwarka ba, Sardauna nasan ba zai yanke ma hukuncin da zai cutar da lafiyarka ba, to ina ganin duk wani hukunci da ya biyo bayan wannan mao sau™i ne a wajena da kai, ni zan ta ya ka karSar kowanne irim hukunci ne Mijina." 



"Na gode Nana, Na gode amma bana son wani hukunci da zai cutar da rayuwarmu, ko wani hukunci da zai sa mu yi abinda ba zamu ji daWi ba, Nana ke nake so ke kaWai a duniya, ban damu da 'ya'ya ko rashin su ba Nana, amma tabbas ina jin ba daWi idan na ga Hajiya ta a cikin halin damuwa, na kan ji zafi idan na ga Alhajina a cikin damuwa, duk akan yara." 



"A kullum kaine mai cemin haihuwa da rashinta duk na Allah ne, akan wannan na tashi, akan shi na Waura yarda ta, kuma nasan suma sun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login