Showing 24001 words to 27000 words out of 64149 words

Chapter 9 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

149

masa sannu da zuwa, sai da ya kallani sannan ya ce. 



"Aini yanzu dole na kama kaina, nasan matsayina tun da kin raina ni bakya so na." 



Bakina har rawa yake na fara magana. 



"Wallahi ba haka ba ne, shi da kan shi ya yi min magana kuma ni bansan shi ba." 



"Waye? Kar dai ki ce min yaron can, bana so! karki sake maganarsa a gidana, ni ba akan shi nake magana ba, akan ™yale ni da kika yi."



"Ba ™yaleka na yi ba wallahi Allah.." 



"To me kika yi?" 



"Bakomai, kawai bana so ma cika takura ma a yadda kake ranka babu daWi." 



Jawoni ya yi kusa da shi, sannan ya ce. 



"Ni na taSa ce miki kina takura min?" 



"A'a ba ka ce ba." 



"To me ya sa kika yi wannan tunanin?" 



Na yi shiru na rasa amsar da zan bashi. "Uhm? Magana nake." 



"Kawai." 



Kawai me?" 



Ya faWa yana mi™ewa tare da ni zuwa Waki, ya ajiye ni kan gado ya hawo. 



"Ina tambayarki?" 



"Ba kowa." 



"Tom." 



Ya faWa yana matseni a jikinsa, tun zamana a gidansa kusan wata huWu yau ce rana ta farko da wani abu na aure ya shiga tsakanina da shi. sardauna ya zauna da nine kaiwa yana kallona kuma yana ba ni kula, sai a wannan ranar nagane aure da wata wahalal shi da ake faWa. 



Tun daga wannan lokacin zamanmu da Sardauna ya canja taku, da ba ya nuna sha'awarsa a kaina, amm yanzu kullum ne, WaiWaikon rana kune yake fashi. Tun ina jin wahala da azaba har komai ya wuce. Irin azabar da na sha a ranar ta mantar da ni zance jarabawa ta sai da aka kwana biyu sannan na tuna, shima sakamakon wayar da muka yi da Ra'is yake ce min na ba shi number exam card Wina zai duba min, Jamb kuma na yi wa mijina magana ya yi min Regostration. 



Da dadare bayan ya dawo na faWa masa amma dai ya yi banza da ni kamar bai ji ba, haka aka kwana Waya aka kwana biyu shiru bai sake min maganar ba, a kwana na uku na yanke shawarar ™ara tun kararsa da maganar, sai dai a lokacin ma banza ya yi da ni. 



Washe gari Ra'is ya zo mun da sakamakona na WAEC da NECO na yi ta murna ganin result Win, ya ce da ni wai Abba ya fara tambaya akan wai na yi rijistar JAMB ko banyi ba, kar su rufe. 



Lokaci na farko da na fara yi wa wani na gidanmu ™arya akan al'amuran gidan aure. 



"Ra'is ban masa maganar ba, kwana biyu suna aiki a kamfaninsu ne, bai ma cika dawowa da wuri ba, amma in sha Allah zan faWa masa." 



"Tom yakamata dai gaskiyya, kinsan su Jamb ba wani dogon lokaci suke badawa ba fa." 



"Nasani sosai, ina Yaya Ridwan?" 



"Yana nan." 



"Baice ka gaisheni ba? Shi fa bai taSa zuwa ba. Kuma ya je duk  gidansu Yaya Radiya." 



"To ai su yayunsa ne, ke kuma ™anwarsa ce. Yaya Radiya ma tana gida." 



"Zuwa ta yi?"



"Eyh, ta kwana biyu ma." 



"Tafiya mijin na ta ya yi?" 



"A'a saSani suka samu da shi, wai yana da wata matar a waje." 



"Mata a waje? Yau she ya yi auren ba mu sani ba?" 



"Bawai matar aure ba, abokiyar iskanci." 



Kama baki na yi sannan na ce. "Lallai chaS."



"Jiya kuma Hajja ta zo ta sauke kwandon rashin mutuncinta tsaf a gidan." 



"Da aka yi mata me? Ita kuma."



"Wai ai Yaya ce ba tasan mene darajar miji ba shi ya sa ya fita ya nemi wata." 



Na yi matu™ar mamakin jin wannan abun, ko da yake a son zuciya irin na Hajja inda za a bata kuWi ta bata™i ko kisa aka yi ba ta ce, wanda ya mutum shi ya taso ya kashe wanda ya yi kisan.



"Ita ta sani, yanzu mai Alhaji ya ce?" 



"Ita Yaya ta ce ba zata koma ba, haka kawai ya kwaso wata cutar ya goga mata." 



"Wallahi Allah da gaskiyyarta, kuma ko ya ce zai daina ba lallai ya daina ba tun da daman ba mutunci ne da shi ba." 



Na faWa daman ni tun da ba gaisawa ma muke da shi ba. 



"Haka Yaya Ridwan ya faWa, ya ce ko kotu ne sai anje an raba auren." 



"Uhm, ni kaWai ce Yaya Ridwan ba ya so." 



Kallona Ra'is ya yi sannan ya ce. 



"Waya faWa miki haka?" 



"Ra'is alamunsa na gani, kana ganin ko Allah Ya sanya alheri bai yi min ba, kai ko gidana bai taSa zuwa ba, farkon aure na da na kirashi da ya Waga ya ji ni ce sai ya katse." 



"Kinsan halinsa dai." 



Ra'is ya faWa yana mi™ewa. "Ni zan tafi." 



"Tsaya na baka abu ka kaiwa Hajiya."



Na faWa ina shigewa Waki, na Wauko wata leda da daman na ajiyeya na ba shi ya tafi sannan shima na bashi dubu bakwai, wanda shine kuWina gaba Waya. 



Ko da Sardauna ya dawo sai da ya tambayeni waye ya zo? Na yi mamaki sosai na yadda akayi ya sani, shi ba camera ce da shi ba amma ya sani, ko da na ce masa Ra'is ne bai wani saki fuska ba. Bayan ya ci abinci na Wauko masa takardar da Ra'is Win ya ciro ya kawo min, buWar bakinsa sai cewa ya yi. 



"Kun dage dai sai kin yi karatun ko?" 



"Alhaji yana so kasani kaima." 



"Uhm." 



Ya faWa ya ci gaba da danna wayarsa, ni kuma na zauna ina wasa da ™afarsa. Sai da aka kwana biyar da maganar sannan Sardauna ya kai ni wajen Rijsitar jamb, shima sai da na sake masa magana sannan ya kai ni. 



Masu kuWi basu da al'adar zuwa gidan mutane, amma kuma suna da kirki idan anje musu, duk ranar da mukaje gidan Hajiyarsu kamar zata cinye ni sabida kulawa ita da ™annensa, haka idan na kiranta a waya shima kamar zata goyani, duk mutan gidansu suna sona sosai idan na je musu, sau Waya ™anwarsa Lubna ta zo shima daga lectures ta dawo shine ta biyo. 



Haka lokacin zana jarabarwar Jamb ya zo Sardauna ya kai ni na yi, idan na sami maki 189 na ji daWi sosai domin zan sami Addmission a FUD, haka a gida kowa ya ji daWi ya yi murna. 



A lamarin Yaya Radiya kam, ta dage ba zata koma ba, haka Yaya Ridwan ma domin sun binciko asali ba iya wannan abun ba ne ya baro ta gidan, bayan neman mata harda shaye shaye yake yi, shima dalilin da ya sa su ka gano wata rana ne yazo gidan namu a buge ya yi wa musu tijara da hau na ™arshe, ya ci musu mutunci sai da Ra'is da Yaya Ridwan suka fita dashi. Amma da Hajja ta zo yin ta ta tijirar sai cewa ta yi an dake shi an ji masa rauni. A yanzu Alhaji ya daina damuwa da abubuwan Hajja tsakanin shi da ita sai dai tom, amma ya faWa mata a wannan maganar ba yadda ya iya tun da yarinya da 'yan uwanta sun dage akan ba zata koma ba. Sardauna ya Wan san maganar tsilli tsilli ban saki jiki na faWa mai komai ba, tun da naga kamar bai son maganar. Da kan sa ya kaini gidan Anty Adiza har sau biyu a cewarsa duk ranar da na je ina samu sabon ilimin sarrafa fulawa. 



Kwance ta shi ba wuya a wajen Allah har aka zo lokacin da jami'a ta fara raba Addmission, kuma ina cikin mutanen da suka samu a lokacin farko. Alhaji bai taSa zuwa gidana ba sai a lokacin ya zo ya yi wa Sardauna godiya akai, daga nan na fara shirye shiryen makaranta sai dai har zuwa wannan lokacin babu ciki a jikina, tun ina Soyewa har abim ya fara damuna, har na fara sanar da Sardauna amma sai ya ce shi haka yake so, da ya ga dai na fara damuwa da al'amarin bisa ga auren Malaika da akayi bayan namu, ta tafi jihar kano kuma a yanzu ta sanar da ni cikinta ya shiga watan haihuwa. Hakan ya sa na sake damuwa, sai shima ya fara nuna damuwarsa, yake kuma kwantar min da hankali. Da dai ya ga abun namu ba ™arami ba ne sai ya ce na shirya zai kai ni naga likita. Rasheed shekoni special hospital ya kaini, asibiti da na yi ma sa gani na biyu a rayuwata, lokacin da mai mashin ya tsaya gyara. Kai tsahe wajem likitan muka je wanda daga yanayinsu kasan abokinsa sa ne, bayan ya yi masa bayani likitan ya sa na kwanta akan wani gado anan ya yi dube duben da zai yi sannan ya ce na koma na zauna. 



Kusan mintina goma sha biyar, sannan ya fara bayani. "Madam mahaifar ta yi ™an™anta ne da Waukan ciki, amma kuma yau da gobe ya sa ta fara girma, idan kika yi ha™uri kuma kin zuwa ganin likita in sha Allah za ta buWe." 



"To wane magani za'a ba ni." 



"A'a babu magani fa." 



"A'a a bata wannan pils din mana." 



Sardauna ya faWa, wani kallo na ga Dr ya yi masa sannan ya ce. 



"Ai zai yi mata ™arfi, sai dai a dinga ba ta sha sau daya ko biyu a wata." 



"Eyh hakan ma ya yi." 



Sardauna ya faWa, sannan ya dafa ni yana faWin. 



"Nana ki daina damuwa kin ji ko, rashim haihuwar ba matsala ba ne." 



Na gyaWa masa kai, sannan ya ce. 



"Ki jirani a mota." 



Na mi™e na fice na barsu a cikin ofis Win, ina fitowa waya ta ta hau ruri, ina dubawa na ga sunan Ra'is na Waga da faWin. 



"Ra'is ya aka yi?" 



"An raba auren Yaya Radiya fa." 



Gaba Waya sai na ji wani iri, Allah ya gani ina matu™ar tsoron mutuwar aure a rayuwata. 



"Yaushe?" 



"Shekaran jiya Hajiyarsa ta zo ta yi wa Hajiya rashin arzi™i. Yaya Ridwan ya sa 'yan sanda suka kamata, amma a ranar aka sake ta shine Wazu ya aiko da takardar." 



"Ka ce tashin hankali aka yi kenan? Allah Ya tsare gaba zan shigo in sha Allah." 



"Amin amin, ya shirin makaranta?" 



"Ranar monday zamu fara lectures." 



"Allah Ya sa albarka." 



"Amin amin." 



Daga haka na katse wayar na shiga mota na jira Sardauna, sai da ya Wau wajen mintina ashirin sannan ya fito, a hanya nake sanar da shi mutuwar auren Yaya Radiya, ya tausaya har muka koma gida. 





Ranar Monday ranar da zan fara lectures Sardauna ya tashi baya jindaWi kwata kwata, ta dole na ha™ura da makarantar ban je, sabida bai samu kansa ba sai wajen sha biyu na rana. Haka washe gari ma ya tashi da irin ciwon, gaba Waya na ruWe kamar shafar aljanu, duk asuba idan ya fara juye juye bai nutsuwa sai rana ta fito, kusan sati biyu a haka, ta dole na ha™ura da makarantar sabida lafiyar mijina tafi min komai a duniya, har da ni kaina. 



Legendspen

08129553971.

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na sha biyu.

    (12)



Abu kamar wasa ciwon Sardauna yana ta tsananta har lectures Win mu ta yi nisa, tun da ina bibiyar al amarin makarantar ta waya har wasu malaman suna shirn fara yin test. 



Tun ban damu da lamarin makarantar ba har na fara damuwa, mussaman da Baba ya kan kirani ya ce min ya karatu, gashi har Ra is ya aiko ya kawo min dubu ashirin wai na ™ara kuWin makaranata kar a bar mijina da wahala, ranar har da ™wallata, da Sardauna ya dawo na yi masa maganar sai ya ce da ni, lafiyarsa zan sa a gaba sama da komai, daga ba ya na ce masa ai har lectures Win 12 muna yi har 2 wata ma 4 ce dan haka idan ya fita zan iya zuwa, ya daWe yana kallona kafin ya ce ya amince. 



Daga nan na fara zuwa, amma duk wata lectures ta ™arfe takwas ko goma babu ni a ciki, cikin ikon Allah kuma ciwon na shi ya fara baya daga nan na samo damar hallartar ta ™arfe goma amma dai banda ta takwas. Tabbas yanayin makarantar ta burgeni, kuma ina jindaWin zuwa makarantar sannan na mayar da hankali akan karatun sosai, dan dana ta shi cikin masu ™o™arin ajin na shiga ana damawa da ni. 



Kwance ta shi babu wuya a wajen Allah, mu ka cinye zangon karatu na farko, bayan munyi jarrabawa muka sami hutu na sati biyu, a lokacin ne naje gida Alhaji yana ta farin ciki da alfahari da ni da karatun, Sardauna kam ya sha albarka kamar Alhaji zai ari baki, ita ma Yaya Radiya Addmission za a sama ta a makarantar lafiya, washe gari na je gidansu, Hajiyarsa da Lubna gwanin sha awa sai kuma na tarar da babbar yayarsa ta England ta zo jiya Sister Noor suke ce da ita, dake su lamarinsu kamar  yan chochi kowa Sister ce, kamar baki!  Sardauna na fita TURAKI ya shigo, wanda rabona da shi tun ranar Family meeting Win da suka yi wanda ba asake wani ba sai bayan wata shida kuma da dukkan alamu wata shidan ya kusa dan na ji Sister Noor tana cewa tana nan za ayi.  Yana ganina ya washe min baki tare da faWin. 



 Matar ™ani.  



Kaina a ™asa na ce. 



 Ina kwana?  



 Lafiya ™alau ya kike ya gida?  



 Alhamdulillah.  



Daga nan ya shige wajen Hajiya, ita ma bai daWe ba ya fito ya yi wajen Sister Noor, ita ce suka daWe suna hira kusan awa Waya, har ya tafi Sardauna bai dawo ba. Bayan Sardauna ya Waukeni da yamma daga nam ya kai ni gidan Anty Adiza sai wajen tara ya dawo ya Wauke ni. 



A kwana a tashi ba wuya a wajen Allah har muka cinye hutunmu muka koma makaranta, abubuwa suka ci gaba da gudana ba mu daWe da komawa ba sakamakon jarabawar mu ya fito idan na sami 3.67cgp, na yi murna sosai kowa ma ya yi murna banda Sardauna, kuma na yi al™warin ™ara dagewa na sami sama da haka a wannan zagon, inda zan sami CGPA mai kyau. 



Zancen ciki dai har yanzu shiru kamar an shuka dusa, magani dai ina sha sau biyu a wata wani lokacin ma Sardauna ya kan ce min na sha sau uku a wata ko zan samu cikin ya zo da wuri. 



Wannan karon bansami zuwa Family meeting Winsu Sardauna ba sabida ina da test har biyu a ranar, dan mun kusa fara jarrabawar zango na biyu, daman haka karatun yake da zarar zangon ya fara zaka ga yazo ™arshe. Lokacin jarrabawa da ya zo Sardauna ya tsiromin da wani abu, baya bari na na yi karatu kwata kwata, ya ta takuramin ayi ta abu Waya ba gajiya, gashi kuma ya ce dani yana so a rage amfani da kayan wuta sabida jan kuWi, ya ce a daina amfani da dutsen guga da abin girki, na ce to daga baya ya ce adaina kumna ac sai dai fanka, duk da yanayin zafi na amince sabida tausayin da na ke yi masa. Wata rana bayan ya dawo ya ce wai na daina amfani da firinji kuma iya nawa, anan ne na so na ce wani abu sabida yanayin zafin da ake yi na gari amma ya ce da ni.



"Nana! A gidanku babu firinji, baki sa ba shan sanyi ba, sabida yanayin unguwar ku ma zafi ake yi, dan haka anan ma ba zai zama wani abu ba dan na ce ba zaki dinga kunna firinji ba, sabida yanayin jan wutarsa."



Tun daga wannan lokaci bansake gigin kunna firji ba da duk wani abu mai jan wuta, haka na yi ta fam da karatu ga wasu ™arin wahalhalu da Sardauna ya fito da su, duk da ni ban taSa ganin su da idon wahala ba, sai na bautar aure. 



Cikin ikon Allah muka kammala jarrabawarmu, mu ka sami hoto na wata biyu, a wannna lokacin komai ya dawo daidai tsa™ani da Sardauna duk da bai janye wasu dokokin na sa ba, amma yanzu mun kan zauna mu yi hira, mu kan yi  yan wasannin mu da muka saba yi a baya. 



Kwancw ta shi ba wuya a wajen Allah muka cinye wata biyu na hutu a kafara shirye shiryen komawa makaranta sai dai Sardauna ya fito min ™arara ya ce da ni bazan koma makaranta ba, na yi tunanin a wannan lokacin ne ba zan koma ba shi ya sa ban damu da hakan ba. Amma ganin har an kusa cin tsakiyar zango na sake yi masa magana sai ya ce da ni gaba Waya karatun ne ba zan ci gaba, wata ™ara na ™walla tare da zubewa a ™asa, abun mamaki sai ga jini yana zuba bayan faWuwar da na yi, ko da muka je asibiti sai aka ce Sari na yi. Na yi danasanin faWuwar amma kuma na ji WaWin cewar yanzu mahaifata ta yi ™wari zata iya Waukan ciki. 



Bayan na dawo gida na yi ™aramar jinya na warke, mu ka ci gaba da Sardauna inda ya ce shi fa a a Boko Haram, ba zam ci gaba. Na yi kuka sosai na nuna masa damuwata amma Sardauna ya ce a a, ranar da abun ya yi ™amari sardauna ya zaunar dani ya yi ta yi min bayani amma na nuna masa ni a a Abbana yana son karatun nan gashi na fara har na cinye shekarar farko ga shi course mai kyau ma aka bani. Amma sardauna ya fara yi mini magiya yana haWani da Allah. 



 Dan Allah ka barni, tun da na fara kamar yau ne zan kammala.  



Na faWa ina goge ™wallar da ta fito daga idona, ya kama hannun tare da faWin. 



 Sakko nan.  



Na sakko na zauna, hannunsa yana cikin nawa ya fara magana. 



"Nana, ina da arzi™in da zan ri™e ki bake kaWai ba har da gidanku, muna da arzi™in da bazamu taSa talauci ba, Nana a cikin gidan nan zaki zama kamar sarauniya ne, Nana bana son karatun boko nan, Nana bana son cuWanya da maza, ina miki so mai tsanani, ina miki kishi mai zafi Nana dan Allah dan Annabi ki ha™ura da karatun."



Gaba Waya jikina ya yi sanyi, maganganunsa gaskiyya ne dole akwai kishi a hakan, kuma ni ina son sa bana son abinda zai dameshi amma Alhaji fa?. 



 Sardauna Alhaji fa? Na yi Yaya da shi?  



Wani murmushi ya sakar min, ganin ya fara nasara a kaina tin da har na fara tunanin yadda zaayi da Alhaji. 



 Honey! Idan kin amince Alhaji ma zai amince ba zai zama mai wahala ba.  



Shiru na yi, ta Sari Waya ina jin son mijina yana rura zuciyata, ta Sari Waya kuma ina tausayin Abbana na yadda yake jindaWin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login