Showing 18001 words to 21000 words out of 64149 words

Chapter 7 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

147

lallaSa Sardauna ya zo wajen Alhaji, cikin sanyin murya na ce dashi. 



 Ko zaka zo yau mu haWu.  



 So kike na zo ki haWani da shi?  



 A a magana zamu yi da kai.  



 Tam zan zo.  



Ya faWa tare da kashe wayar, haka na mayarwa da Hajiya a barta, ni dai gaba Waya wani sukuku haka nake, tunanin yadda zan fara fahimtar da Sardauna muhimmamcin zuwa wajen Alhaji kawai nake. 



Ra is ne ya buWe labulen Wakin. 



 Wai daman baki mutu ba?  



 Na watsa mai harara sannan na ce. 



 Sakar mini labule ka fita.  



 Na™iya, wai me kike yi a Waki kwana biyu?  



 Ra is ka sakar min labule ka fita kafin na yi ma rashin mutunci.  



 Karki fasa.  



Ya faWa yana shigowa ya zauna gefen gadon Wakin. 



 Wai na ji aure zaki yi?  



A razane na juyo na kalleshi sannan na ce. 



 Waya faWa maka?



 Duk abinda ake Soyewa ai mun sani, mun yi waya da Yaya Rumaisa ta faWan, sannan ta ce na zo na baki shawara.  



Shiru na yi ban ce komai ba, shi kuma ya Wora da cewa. 



 Wallahi indai saurayinki yana sonki, kin yarda da soyayyar da yake miki, to ki yi aurenki me zaki zauna ki yi a gidan? Ke mace fa, ba  yar zama ba ce, akwai lokacin da mace take samin samari cike har da na aure, da ta yi wasa ta ™ara girma shikenan zasu tsiyaye kamar hawaye su tafi.  



Kallon Ra is na yi a raina na ce. 



 Shi kuma kalal tashi shawarar kenan. A fili kuma na ce. 



 Alhaji yana so na yi karatu  



 To ai a gidan mijin ma zaki iya ci gaba da abinki, wannan fa a ganina ba matsala ba ce.  



Haka Ra is ya yi ta bani nasa shawarwarin, bayan ya tafi na zauna na haWe komai na cakuWa a kwalwalwata, na yi ta faman kwashewa da Webewa har zuwa yamma. 



Wajen ™arfe biyar na tashi na fito tsakar gida lokacin Hajiya na shara, kallona ta yi sannan ta ce. 



 Kwana biyu iskancin zaman Waki kika Waukarwa kanki ko Nana?  



 A a Hajiya, bani da lafiya ne fa.



 Baki da lafiya shine bazaki sanar ba.  



Yaya Ridwan ne ya le™o daga Wakinsa sannan ya ce. 



 Hajiya ™yaleta kawai.  



Ni a raina na rasa me yasa Yaya Ridwan baya sona da Sardauna, ina tuna lokacin bikin su Yaya Radiya duk da bai yi magana ba amma yanayinsa ya nuna yana farin ciki da hakan, amma ni ya fito ya nuna baya farin ciki da hakan, dan ko jiya da daddare sai da ya sake min magana akan Sardauna. 



Wayar Hajiya na Wauka na shiga Waki, ina shiga na kira wayar Sardauna, ya katse bai Waga ba can kuma ya yi min text. 



 Ki fito.



Abinda ya rubuta kenan, na rasa me yasa duk lokacin da Sardauna ya shigo unguwarmu sai na ji a jikina. 



 Ina zaki ke da ba lafiya?



Hajiya ta faWa ganin ina shirin fita.



 Abu zan amso a waje.  



 Wajen wa a waje?



 Šan ajinmu ne.  



Sai da ta kalleni sossi sannan ta ce.   Idan kinga dama ki zauna a wajen. Sannan ta ci gaba da abunda take, ni kuma na fice. 



Yau a barandarmu na sameshi, ya tsaya ya harWe hannunsa a ka faWa. Kamar ko yaushe dai cikin kyakyawar shiga yake. 



 Ke baki damu bama da kiran da Alhajin yake min ko?  



Abinda ya fara faWa kenan, bayan na ™araso inda yake. Na rasa me ya sa Sardauna yake ce min ni bandamu ba, ko so yake ya ga damuwar ™arara a fuskata? 



 Ba fa wani abu ba ne Allah.  



Na faWa bayan na ™araso inda yake. 



 Nana ajikina nake jin Abba bazai ban aurenki ba, ni dai idan kina da wata hanyar kawai ki faWan.



 Wace irim hanya?  



 Wacca zamu bi a fasa zuwa wajensa.  



 Maganar makaranta kawai zai yi ma fa, Alhaji ba zai janye maganar karatu ba fa, kuma Alhaji idan yana ce akan magana babu mai sauye sai Hajjansa ita kaWai.  



 Wace Hajja?  



 Kakarmu fa.  



 Aina take?  



 Dutse Gadawur.  



 Kina ganin ba zanje na gaishe ta ba yau, sai na ce mata nine saurayinki?  



TaSe baki na yi tare da cewa. 



 Ni ban wani cika shiga al amuranta ba, hasali ma ba ta son mu.  



Murmushi ya yi sannan ya ce. 



 Zata so ku, bani address kawai.  



Ba shi cikakken address na yi na gidan, bai wani jima ba ya tafi, na shiga gida. Ina kallon wani irin kallo da Yaya Ridwan yake min, ni narasa na mene haka?. 



Ko da dare da Alhaji ya dawo bai yi min maganar ba, sai ma sanar damu da ya yi ansa bikin Isah Nadabo sati biyu, ya sami mata a jihar kano. 



Na ji daWi sosai a raina tare da yi masa fatan alheri, nasan dai bikine zamu sha dan a gidanmu zaayi komai daga farko har ™arshe, dan iyayensa  ba anan suke ba  yan Gumel ne. 



Kwata kwata ba muyi magana da Sardauna ba har washe gari, sai da safe ya kirani muka sha soyayya kuma a yanayinssa babu wannan fargabar, nima kuma ban tambayeshi ba. 



Wajen ™arfe tara da rabi, ina zaune bakin rariya ina wanke wanke, Hajiya na Wakin Alhaji yana shiryawa, Ra is kuma na sharar tsakar gida muka jiyo balo™o™on Hajja. 



Gabana ya yanke ya faWi.  Me ya kawo matar nan gidan nan kuma?. Na faWa a raina, sabida daman a tsarin Hajja sai ta gama balo™o™o kafin take shigowa gidan. Hajiya da Alhaji duk sun fito tsakar gida suna jiran ta shigo, ita kuma tana can ta tagar Wakinsu Yaya Ridwan ta baranda tana faman yi masa sababi. 



 Ni dai kaf zuri a ta a kanku a gama tabbatattu, ga dai farin jini Allah Ya yi muku amma sai ba™ar zuciya, wacca nasan wajen uwarku kuka gado, yo daman fulanin jeji ina zuciyar arzi™i a tare da su, Allah Ya kyauta dai.  



Abinda ta shigo da shi cikin tsakar gidan kenan a bakinta, Alhaji ne ya fara tarar da faWin. 



 Hajja Barka da safiya, sannu da zuwa.  



 Yawwa sannu.  



Ta faWa tana kauda ido, Hajiya ma ta ce. 



 Hajja sannu da zuwa, ina kwana.  



 Lafiya.  



Ta amsa a da™ile, Ra is ma ya ce. 



 Sannu da zuwa.  



Banza ta yi da shi, nima na ce. 



 Sannu da zuwa.  



Aikuwa ta washe ha™ora tare da faWin. 



  yar arzi™i ke nake ta baza idanun ganin, kinsan idanun ba kowanne ke da kyau ba, gashi ke ba zuwa kike ba uwar mai mugun nufi ta hanaki.



 Ikon Allah sai kallo, yau rikicin tsufan nan ya kawo ta kenan.  



Ra is ya faWa yana daga inda yake, ni kaina nasan rikicin tsufa ne, dan ina ga ma Yaya Radiya take magana akai, tin da ita ce ta auri jikan da take so. 



 Kina ina ne, matso na shafiki, na shafi arzi™i.  



Ta sake faWa, kamar wacca ™wai ya fashewa a ciki haka na taka na je idan take. 



 Sannu mai ™ashin arzi™i! Sannu  yar nan.  



Ta faWa tana ri™e hannu, sannan ta juya ga Alhaji. 



 Sannu tabbatacce, kai yanzu ace yarinyar nan tana da wanda yake sonta daga gidan arzi™i irin haka kamar gidan Ta ambo, amma ka Soye min, sai yaron da kansa ya nemeni ya kawo min kayan arzi™i, ka ji tsoron Allah.



Legendspen

08129553971

971*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na tara

    (09)



Da ido kowa yake kallonta, dan babu wanda yasan ma suna saurayin nawa bare familinsa a tsakanin Alhaji da Ra is da suka san maganar, bare Hajiya da batasan komai a kai ba. 



 Hajja wane yaro kike magana a kai?  



Alhaji ya tambaya, dan shi tunaninsa ko Isah Nadabo zata ce, shine ta ce Ta ambo, dan dai dukkansu sunsan Familin Ta ambo ba ™aramin ahali ba ne.



 Ka ce haka mana, wallahi zama da wannan matar ta shafa maka mugun abu, shi ya sa na gwammaci na ™yale mata kai ka je ka ™arata daman ba wata tsiyar kake ban ba, to yanzu gashi Wan gidan arzi™i yana son yarinyar Gawasiya take kowa, mai dai sunan Mutanen can, jiya da daddare yazo gidana ya cika shi da abun arzi™i sannan ya cika mini ™ugu da sulalla. Dan haka abinda nazo na faWa ma shine, idan kana nan da wannan mummunan ra ayin naka na sai yara sunyi karatun yawudu da nasara ta ka sauke shi akan yarinyar nan, dan na yi mata miji na ce ya tura maka iyayensa ko sati yake so ka fito da kuWi, kema ki fito da kuWin shanu, aje a aurar da ita.  



Ta ™arashe maganar tana kallon Hajiya, ™asa Hajiya ta yi da kai ba tare da ta ce ko ™ala ba. 



 Magana nake da kai fa.  



Cike da ladabi da girmamawa Alhaji ya ce. 



 Hajja bangane kan zancen ba.  



 Baka gane ba, mene baka gane ba, ke yi masa bayani.  



Da sauri na kalle ta na ce. 



 Wane bayani kuma?  



 Yaron da yake son ki.  



Gaba Waya idanuna sun cika da ruwa na rasa me zance. 



 Ko kema bakya son sa?  yai mai ba™in hali.



Gaba Waya Hajja ta rikita gidan, kowa ya kasa gane inda ta nufa, kuma ta™i ta yi bayani yadda za a gane sai faman cewa take. 



 Ni dai na faWa ma zai tura iyayensa.  



Da ta gama banbamin ta tafi, Hajiya ta kalleni bayan Alhaji ya fita rakata ta ce. 



 Wane yake zuwa wajenki?  



Ra is ya yi saurin cewa.  Akwai saurayinta da yake zuwa wajenta wanda har Alhaji yasan maganar ya ce yana son ganinsa.  



 To shine Wan gidan da Hajja take faWa?  



Girgiza kai ya yi sannan ya ce. 



 Wannan ne kuma bansaniba.  



 Dake nake.  



Hajiya ta faWa tana kallona, na gyaWa kai kamar ™adangariya sannan na ce. 



 Eyh& eyh, a gidan Ta Ambo yake.  



 Aina ya san Hajja? Har yasan gidanta?  



 Ya tambayeni yana son ya je ya gaida  yan uwanmu ne na ce masa na Hajiya ba anan suke ba, na Alhaji ne anan.  



 Shi baki faWa masa halinta ba.  



 Bansan ma zai gane gidanta ba, kuma na ce mai ma bata son mu.  



Daidai lokacin Alhaji ya shigo, sai da ya ™are min kallo sannan ya ce. 



 Yaron da yake zuwa wajenki Wan gidan Ta 

Ambo ne?  



 Eyh Alhaji.  



 Shine kika ce masa ya je ya sami mahaifiyata, ya bata abun duniya?



Da sauri na girgiza kai sannan na ce. 



 Wallahi A a.  



 To Lallai kisa shi yazo.  



Daga haka ya juya ga fice, ni kuma na yi cikin Waki. 



A ranar na sake sanar da Sardauna sa™on Alhaji, cikin wayo da dabara ya dinga tambayata abubuwam da Alhaji yake so akaina, nan na sanar dashi zance karatu, kuma yana son nasami miji mai ilimi da tarbiya. 



Bayan Magariba Alhaji ya dawo, sabida zuwan Sardauna, wanda bai zo ba sai ™arfe takwas. A tsakar gida suka zauna mu kuma duka muna cikin Wakin gaba Wayanmu, amma hankalina gaba Waya yana kan su Sardauna da Alhaji. Yadda Sardauna yake magana da Alhaji cikin ladabi da nuna tsantsar tarbiya ya burge mu duka da muke cikin Wakin, Hajiya, Ra is da Ni. 



Yadda yake nunawa Alhaji zallar soyayyarsa ga karatu da burin na zama wani ya haifar da soyayyarsa mai girma a zuciyar Alhaji, haka kuma yadda yake magana da Alhaji kamar yana karSar Umarni wajen mahaifinsa ya nuna tsantsar tarbiyarsa.  



 Ma sha Allah, ubangiji Allah Ya sanya albarka a taraiyyarku, ya albarkace ku da zuri a ta gari.  



Alhaji ya faWa, daga cikin Wakin na ji wani daWi ya ratsani har cikin zuciyata. 



 Ka sanar da magabatan naka, sai su zo Allah Yasanya alheri.  



Maganar Alhaji ta ™arshe kenan, bayan Sardauna ya tafi Alhaji ya haWa mu gaba Waya har da Yaya Ridwan. 



 A gaskiyya na yaba da irin nutsuwa da tarbiyar yaron nan da Nana ta kawo, dan haka na bashi damar ya turu magabatan nasa.  



 Gaskiyya ne Alhaji, ni kaina daga cikin Waki na tsinci nitsuwa a cikin muryarsa, Allah Ubangiji yasanya alheri.  



 Amin Amin.  



Farin ciki ya cika rayuwata gaba Waya, bacci rabi da rabi na yi shi. Gari na wayewa ko takwas ban bari ta cika ba na je gidansu Amina na sanar da ita, ™awayena sai murna suke. 



Kwana biyu a tsakani  yan uwa Sardauna suka zo gidanmu aka tsayar da rana wata uku, lokacin na kammala jarabarwata. 



Lisaafi ya canja, abubuwa sun Wau harama, ni da ™awayena babu zama. Kowa ya ganni yasan wanda nake so zan aura, Su Yaya Rumaisa da Yaya Radiya da Ra is kowa farin ciki yake ta ya ni, idan ka cire Ridwan da na kasa gane kansa, ko sakarwa Sardauna fuska ba ya yi, idan muna tare zai zo ya wuce sau Wari bai isa ya kalleshi ba, Hajiya ta ce mu dinga taWi a cikin Wakinsu amma Yaya Ridwan ya ce ban isa ba, gaba Waya gani nake ya tsani Sardauna. 



A cikin wannan lokacin ne auren Isah Nadabo yazo da matarsa Adizatu  yar jihar kano, biki ne aka yi shi na alfarma daidai zamani, kuma mun halarci komai na bikin tun daga farko har ™arshe, kano ne kawai ba mu je ba, Amma Alhaji, Yaya Ridwan, da Ra is duk sun je. Tun da Sardauna ya ji na ce masa matar Isah Nadabo   yar kano ce Sardauna ya dame ni akan naje ta koyan girkin kano, yadda ake sarrafa fulawa ayi gurasa da su cincin. 



Ni ban fiya shigewa mutane ba, amma akan sardauna sai da na shigewa Anty Aadiza, daman ba ta da wata matsala tana son mu ta Wauke mu ™annen miji, ta Wauki Hajiya Uwar miji, dan ko da aka kawo ta daga kano hannun Hajiya aka mi™a ta. A hankali ta fara koyan sarrafa fulawa mussamman da na faWa mata wanda zan aura ne ya ce yana so. 



Hajja ba ta cika zuwa gidanmu ba, tun da Sardauna ya kan je ya kai mata kuWaWe da kayyaki har gida lokaci zuwa lokaci. Shi ya sa ta ™yalemu mu ci tsiyarmu. 



Kwance tashi ba wuya a wajen Allah, har muka kammala jarabarwamu, inda bayan sati biyu aka Waura mana aure da Sardauna, biki ne aka yi shi na garari, masu kuWine ke hada hada ta ko ina a wajen events Win da familin su Sardauna suka shirya. A cikin raina babu abinda nake ™auna da tsumaye irin a gama wannan kiWe kiWen akaini gidan Sarduna, inda zan samu soyayya mai daWi. 



Daga wajen taron aka wuce da ni gidana na Takur, tun ina cikin mota nake mamakin irin girman gidan, da aka fito da ni kuma sai na fara mamakin irin tsaruwar gidan. 



Haka aka shiga dani cikin gidan, kowanne Waki a tsare yake kuma sannan a cike yake da kaya. 



 Allah Sarki Alhaji da Hajiya, Allah Ya ™ara muku arzi™i, lafiya da nisan kwana.  



Na faWa a raina lokacin da aka shiga dani Wakin gadona, nan masu kawo ni suka zauna suna ta faman yi min nasiha, nikam gani nake kawai ™ari suke domin Abinda Alhaji da Hajiya suka faWa min, bana jin zan sake samun nasihar da ta wuce wannan, haka ma  yan uwana. Yaya Ridwan ma ganin dai dagaske za a kaini Wakin aure ya zo ya same ni da yau da safe, ya yi min nasiha mai ratsa jiki. Akwai kalma da ya faWan guda Waya wacca har yanzu tana nan daram a kunnuwana. 



 Nana ba tsanar saurayinki na yi ba, da ki kaga ina miki haka, Nana ina matu™ar kishin  yan uwana mata, bana son naga wani abu zai wahalal da su.  



Wannan kalmar kishin ta tsaya min sosai a zuciyata, nasa hannu na goge ™wallar da ta fito daga idona. 



Haka aka tafi aka barni da ™awayena, suma ba su wani daWe ba Sardauna da abokansa suka zo suka tafi da su, aka barni daga ni sai Sardauna. 



 Nana!  



Ya kira sunana a hankali, nima na amsa masa a hankali. 



 A yau sai mu gode Allah da ya cika mana burinmu, ya nuna mana wannan ranar ga ni ga ki a matsayin miji da mata, tabbas ina cikin farin ciki da hakan Nana, ina farin ciki marar misaltuwa.  



Ya ™arasa maganar tare da tasowa zuwa inda nake, yasa hannu ya yaye lulluSin fuskata, ya kalli fuskta da take she™i, ya sa hannu ya jawo ni jikinsa. 



 Nana kina jin sauti bugun zuciyata.  



Na Waga kai tare da cewa. 



 Ina ji.  



 Nana ki saurare abinda zan faWa daga zuciyata bawai bakina ba, ina matu™ar ™aunarki Nana, ™aunar da nima bansan irin ta ba, ina jinki cikin jini da tsokar jikina, ina son ganin walwalrki Nana, ina jin wani irin shau™i idan na ganni ga ki.



Kalaman Sardauna suka kashen jiki, suka haifar min da wani irin yanayi mai daWi, tabbas Nana na yi sa ar miji, na yi da ce da miji na gari. 



 Nana.  



Ya faWa yana matseni a jikinsa. 



 Kina jin yadda nake ji?  



 Uhm.  



 Kina jin kamar ki cinye ni, na koma jikinki gaba Waya?  



 Uhm.  



Haka Sardauna ya yi ta yi min kalamai masu nuna zallar soyayya da shau™in ™auna, mun kusa awa Waya a wannan yanayin sannan ya ce da ni. 



 Nana ta shi ki yi alwala mu yi sallah, mu mi™a godiyarmu ga Allah.  



A hankali na tashi daga jikinsa na nufi toilet na Waura alwala, bayan na idar na fito shima ya shiga ya Waura tashi alwala daga nan ya ja mu mu ka yi sallah, tare da addu o i na neman albarkar aure. 



Daga nan muka ci nama da lemo sannan ya kalli ni. 



 Kin gaji ko?  



 A a.  



 Ta shi ki canja kaya ki zo mu kwanta.  



Daga nan ya tashi ya fice, nima na tashi na sauya kaya zuwa na barci, bayan na sauya na zauna ina jiranshi.  Yan mintina kaWan shima ya shigo cikin shirinsa na bacci. 



 Wai baki kwanta ba? Sannu Nana.  



Ya faWa yana hawa kan gadon. 



 Matso kusa.  



Ya faWa tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login