Showing 6001 words to 9000 words out of 64149 words

Chapter 3 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

145

sakamini dashi? Mene abu Waya?"



Na yi shiru, gaba Waya jikina ya yi wani irin sanyi, wani sabon tausayin mijina ya lulluSe ni, a hankali na fara magana, idona cike da hawaye. 



"Ka yi hakuri dan girman Allah, wallahi bazan sake ba, sai da na ce mata kar ta zo amma ta™i." 

Sai yanzu na fara mamakin kaina, yadda aka yi na zama ma™aryaciya lokaci Waya, duk dan na faranta masa. 



"To bance duka kike goge lambobi su ba?." 



"Na goge fa, ai kana ganin wayar babu lambar kowa sai taka da ta 'yan gida, to idan suka kirani ne nake ganesu." 



"Bani wayar." 



Ya faWa yana takawo cikin falon, fuskarsa a haWe kamar zai dake ni, hannuna har karkarwa suke yayin da nake kokarin mika masa wayar, ya sa hannu ya fusgeta da ™arfinsa. Daidai lokacin sa™o ya shigo wayar ji kake. 'Wilim.' ™arar shigowarsa. 



"Waya turu miki sa™o?." 



Ya tambaye ni, cikin muryar kuka na ce. 



"Nima bansani ba." 



Wayar ya danna ya bude sa™on, ya ™ura ma wayar ido yana motsa baki, idanunsa na yawo akan sikirin Win wayar, wanda yake daidai da ™a™™arfan bugun da zuciyata ke yi. 



"Mitcheww." 



ya ja tsaki, ya danna maddanin gogewa ya goge sa™on. 



"Ina so ki ciro mini layin nan yanzun nan." 



Ya faWa yana mi™omini wayar, da rawar jiki na amsa na fara ™o™arin cire layin, yana kallona da idanunsa har na cire na mi™a masa, ya karSa ya sa a aljihu, kana ya zauna akan kujera, ya runtse idanunsa kusan mintina biyu sannan ya buWe su, ni dai ina tsugunne ina kallonsa, ™aunarsa da tausayinsa suna cika mini zuciya, ina son mijina,ina tausayinsa. 



"Hon! Matso ki zauna." 



Sassanayar muryarsa da tafi ruwan ™an™ara sanyi ta doki kunnunwana, ba shiri na mi™i na matso kusa da shi na zauna, ya sa hannuwansa ya kama nawa, a hankali ya fara matsa su. 



"Nana, kin san me ya sa nake yin haka?" 



Ya tambaya, muryarsa tana fitowa da wani irin sanyi mai ratsa zuciya. Ya kura mini ido, idanunsa da suke daidai da kwayar idona suka sanya na ji wani irin mugun tausayinsa.



"Domin ba na son kowa ya shiga tsakaninmu. Ke tawa ce ni kaWai, Nana. Idan kika bari waWancan kawayen naki da 'yan uwanki suka ci gaba da shigo miki da ra'ayoyinsu, za su lalata mana wannan kyakkyawar rayuwar da muke yi."



Na gyaWa kai, hawaye na wanke fuskata na ce.



 "Na gane Hon. Nagode da kake kare ni, nagode da kake nuna mini gaskiya."



"Yauwa Nana. Don haka, tunda yanzu babu layin a wayar, babu wani abu da zai dinga raba miki hankali. Ina so ki maida hankalinki gaba daya a kaina da kuma wannan gidan. Kuma ina so yau ki goge sauran kayan da suka rage."



Ya sumbaci tafin hannuna, wanda har yanzu yake zugi saboda kunar jiya da kuma takewar da ya yi mini Wazo. Amma kalaman sa sun sanya na manta da raWaWin.

Na gyada masa kai cikin sauri na ce. 



"Yanzu yanzu ma, kana fita zan ™arasa."



"Tashi ki je ki soma, ni kuma zan karya da kaina."

Na mi™e ina jin kamar an dora mini wani sabon nauyi, amma nauyin da nake ganinsa a matsayin Ladan Bautar Aure, da kuma tukwici ga soyayyar da ake nuna mini. Kai tsaye na shige Wakinsa na fito da ragowar kayan gaba Waya. 



Ina tsaka da guguwar bayan fitar sardauna naji ana sallama, gabana har faWuwa yake yayin da na tashi zuwa buWe kofar. Ra'is! 



"Ra'is lafiya?." 



Na faWa baki na yana rawa, ya kalleni cike da bacin rai, sannan ya ce. 



"Alhaji bashi da lafiya, ya ce yana son ganinki, yana son magana dake amma kin ™i, Yaya ta kira ki a waya kin ™i Wauka, anyi miki test message akan baba yana cikin halin jinya, amma kin gani baki ce komai ba, yanzu da safe an kiraki ma wayar akashe, sai kuma yanzu kika yi message a wayar mijinki kika wai ke ma baki da lafiya. Nana me yake damunki ne? Dan kinyi aure a gidan hali shine kika tsani 'yan uwanki?." 



Tun da Ra'is yake magana ™irjina yake bugawa, duk wata kalma da yake faWa guda daya tamkar ana doramin dutse a kirjina ne, fuskata cike da hawaye na ce. 



"Wallahi Ra'is ba haka ba ne, bansan Baba bashi da lafiya ba, kuma Sar...." 



"Ta ina zaki san ba shi da lafiya, kin zaSi miji mai abun duniya akan 'yan uwanki da iyayenki, wallahi Nana kin bawa kowa kunya ciki hardani, wahala da Alhaji da Hajiya suka sha akan aurenki basu sha ta akan kowa ba, Nana kinsan tunda kika ajiye karatun da Alhaji ya ci buri akanki bai ™ara lafiya ba. Wallahi Nana daba dan Baba ya takura ba babu abinda zai kawo ni gidanki babu shi, kuma idan kinga dama ki je ki ganshi idan baki ga dama ba kar ki zo, amma ki kwana da sanin duk wani abu da yasami mahaifinmu ba zamu taSa yafe miki ba." 



Yana faWin haka ya juya zai tafi, cikin muryar kuka na ce. 



"Ra'is! Dan Allah tsaya." 



Tsayawa ya yi ba tare da ya juyo ba, na tako inda yake sannan na ce. 



"Dan Allah kira mini Alhajin, na yi magana da shi dan Allah." 



Kallona ya yi sannan ya ce. 



"Ki yi magana dashi? Kina nufin bazaki zo ba?." 



"A'a Ra'is zan zo, amma dan Allah na fara jin muryarsa kafin nazo." 



Murmushin takaici Ra'is ya yi sannan ya sa hannu a aljihu ya zaro wayarsa, ya danna kiran sannan ya mi™o mini. Hannuna har rawa yake yayin da na amshi wayar, ana Wagawa na fara magana. 



"Ba..Baba!" 

Na fada, daga can bangaren Yaya Radiya ta ce. 



"Bara a mi™a masa." 



"Yaya ki yi hakuri, wallahi bansan komai ba akai, wayar ta hannun Mijina." 



"Mijinki kuma? Amma sa™on da kika turu dazu ai kece kika rubuta." 



Yaya Radiya ta fada, ban kai ga bata amsa ba ta sake cewa. 



"Ga Alhajin." 



"Alhaji ina kwana, Ya jikin naka?." 



Na faWa cikin rawar murya. 



"Rawasiya kina lafiya?." 



Ya tambaya muryarshi cike da alamun rashin lafiya, wani abu ya tsaya min a rai, yana cikin halin rashin lafiya amma tambaya ta yake ina lafiya?



Ina son Sardauna sosai, amma tabbas bai kai ko rabin soyayyar da nake yi wa Alhaji ba. 



"Alhaji lafiya kalau, ya jikin naka?" 



"Nana yaushe zaki zo?"



"Baba anjima zan zo, yana dawowa zan faWa masa ko da daddare ne sai nazo, ko gobe da safe." 



"Toh shikenan! Ubangiji Ya yi miki albarka." 



"Amin Baba, Allah Ya baka lafiya." 



"Amin amin Nana." 



Ya faWa yana mikawa Yaya Radiya wayar. 



"Nana ki samu ki shigo dan Allah." 



Yaya Radiya ta fada, duk jikina ya yi sanyi na ce. 



"In sha Allah Yaya." Daga nan na katse kiran na bawa Ra'is wayarsa, ya kaWa kai zai tafi. 



"Ra'is, baka shigo ba! Baka sha ko ruwa ba." 



Murmushi ya yi sannan ya ce. 



"A'a ba komai, zan wuce kawai sai kinzo." 



Yana faWin haka ya fice, ni kuma na koma Waki na zauna kan kujera, kamar wacca aka haskawa majigi haka rayuwata ta baya ta shiga tariyo wa a idanuna. 



******

Asalin labarina. 



Da farko sunana Rawasiya Alqasim Babuga wacca kowa ya sani da Nana, sunan da na zaSawa kaina kenan, tun ta sowa ta ni macece marar son hananiya ko kaWan, bana son abun da zai dame ni a rayuwa ko ya ne, abun da nasa a gabana shi nake yi, shi nake so. 



Mahaifina Alhaji Alqasim sannanne a anguwarmu dama gari gaba daya, kasancewarsa dan siyasa mai a™idar ri™au. Sannan Wan kwangila ne da yake da kamfaninsa wanda yake karbar ayyukan daga 'yan siyasa da ma sauran mutanen gari.



Mahafiyyata Sailuba haifaffiyar jihar Adamawa yola ce, irin kyawawan fulanin nan ne na Yola, a lokacin da mahaifina yake tashin aikin kwangila da kuma siyasarsa Allah Ya haWashi da ita, bayan shimfiWa kyakyawar soyayya kuma suka yi aure, inda mahaifina ya dawo da ita unguwar Federal Low-cost dake dutsen jihar jigawa. Unguwa mai kyau da daWin zama, unguwar da ta kasance ta masu matsakaicin hali, akwai manyan gidaje da kuma ™ananan, akwai hada™ar masu kuWi da talakawa. 



Zaman tsarkakkiyar soyayya ya ginu tsakanin Mammanmu da Abbanmu da muke kira da Alhaji da Hajiya, tun haihuwarsu ta farko Alhaji ya zo da wani tsari, babbar Yayarmu sunanta Radiya, bayan yan shekaru aka sake haifi wata aka saka mata Rumaisa, bayan ita kuma sai namiji da aka sa masa Ridwan, a lokacin Alhajinmu yana tsaka da siyasa da samun kudi ya dau™esu gaba Waya suka sauke farali, a lokacin ina ciki sai bayan sun dawo da aka haifeni inda aka samin Rawasiya, ban kai shekara ba dukkanmu Alhaji ya kwashe mu zuwa aikin Hajji, wanda bayan dawowarmu daga aikin Hajji karyar arziki ta sami mahaifina. 



A lokacin ina da wata goma sha Waya a duniya, wannan lamarin ya afku, inda mahaifina da alhalina suka shiga matsanancin tashin hankali na rayuwa, duk arzikin mahaifina ya kare a yadda nasamu labari wani lokacin gidanmu suna iya kwana ba tare da suncu abinci ba, ana haka mahaifiyata ta shawaraci Alhaji da ya sayar da gidansa na Federal low-cost ya nemi wani karamin mu koma can ragowar kudin ya sa su a kasuwa, haka kuwa aka yi mahaifina ya siyar da gidansa na Federal Low-cost ya nemi matsakaicin gida a unguwar Yelwawa, inda suka dawo nan, gida mai dauke da dakuna uku, Na Alhaji (Baba) daban, na Hajiya (Umma) daban, Yaya Radiya da Yaya Rumaisa daya, shi kuma Yaya Ridwan tun da shine karami yana kwana dakin Hajiya, ni kuma ina karama.  Daga Amana Academy makaranta mai zaman kanta aka dawo da yan gidanmu zuwa Government Day School Yelwawa, canji rayuwa ya yi wa gidanmu ™awanya, ni kam basan duk dadin da aka sha ba lokacin da Alhaji yake Alhaji bare nasan yadda aka shiga lokacin da ya dawo Hajijiya, wannan ya sanya Alhaji yake matukar so da tausayina, kasancewar gatan da yayuna suka samu a lokacin da suke kamar ni bansame shi ba, Alhaji ya fara zuwa kasuwar Laraba da take ci Mako Mako yana siyar da kayan abinci, sauran ranakun kuma yake zama a shagon da ya bude shima na awon kayan abinci a gida.



Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na huWu

    (04)



Shekarata uku a duniya, Hajiya ta sake samun ciki wanda shine cikin autanmu Ra is a zuwa wannan lokacin Alhaji ya fara samun rufin asiri, duk wani ci da suttura na masu rufin asiri baya gagararmu, haka karatu babu wanda bamayi, na zamani da na addini, bayan haihuwar Ra is sai Alhaji Yasa aka shigo da shagon waje zuwa cikin gida, bayan ya sami wani babban shago a bakin titi, tabbas ance haihuwar Ra is ta zo da alheri sosai domin akwai wasu cikin yaran da Alhaji yake biyawa kudin karatu da  yan bu™atun rayuwa lokacin da yake amsa sunan Alhaji, wani cikinsu mai suna Isah Nadabo da ya zama babban mutum shine ya siyawa Alhaji Shagon a bakin titi, bayan ya cika masa shi da kayan siyarwa, sannan wani kuma ya cika mana gida da kayan abinci. 



Tun daga lokacin haihuwar Ra is bamu sake zama da rashi ba a gidan, muna zaune cikin rufin asirin ubangiji, haka kuma muna samun tsayayyiyar tarbiya daga wajen mahaifiyarmu Hajiya, domin Hajiya macece mai tsayawa kan tarbiyar yara. A bangaren kyau, dukkanmu irin kyawunta mu ka yi mussaman mu matan da mu ka yi har farinta, Yaya Ridwan da Ra is da suka dan dakko duhun Alhaji, sai suka fi mu kyau ma, sabida ba suyi duhu dilik ba, sannan ba suyi haske fatau ba, sun yi black beauty ne, ko na ce Brown, ga sumarsu irin ta fulani, wacca duk muka Webo daga Hajiya, dan mu matan ma babu wacca gashinta bai kai gadon baya ba, kasancewar nafi su Yaya Rumaisa ™an™anta sai akafi ganin kyawuna akansu, kuma ni kaWai ce na yo dara dara idanu irin na Alhaji, shi ya sa aka fi ganin kyawuna akansu. Sai da fa duk gidan kowa ya kwana da sanin cewa Yaya Ridwan yafi kowa kyau dan shi kama yake da larabawan Dubai.



Yaya Radiya tana da matu™ar sau™in kai, hakuri da kawar da kai akan abu, saSanin Yaya Rumaisa Al-jarabatu, sunan da kowa ke kiranta dashi, bata neman sauki a rayuwatar ko kaWan, rigima bata ta ba sai ta shiga ta yi kane kane, sai ka rantse ta tace. Yaya Ridwan kam, Wan kurma dinfa kenan. Babu ruwanshi da abunda ba a sashi ba, wanda aka sa shi mai sai ya yi kamar bai ji ba, sai ya yini a gidan amma bai ce da kowa ™ala ba, ko abokai ba shi da su kullum yana cikin daki, sai ya yini a daki bai fito ba idan ba massallaci ba. Ni kuma ina cikin wasu nauyin mutane da ba agane kansu, idan naso zanyi surutu sai na addabi kowa, idan kuwa banso ba buWe baki ma wahala yake mini, duk da cewa inda hakuri da kawar da kai, surutun nawa ma sai da  yan gidanmu nake yi idan na ga damar, abun da ba asani ba dai bazan shiga ba, sannan kwata kwata ba na cikin nau in mutane marasa kunya, sannan duk abinda naga zai wahalal dani ina yi tattarashi gefe na watsar ko na tattara rayuwata na yi gaba. Haka ma Ra is bai da hayaniya shima ko kaWan duk cikinmu dai Yaya Rumaisa ce ta fita zakka, dan idan taso jarabarta kowa sai ya kula ta, Yaya Ridwan ne kawai ba ya kulata. 



Kasancewar sunana Rawasiya yasa  yan makarantar daren mu suke tsokanta, yau su ce Rawasiya, gobe Gabashiya, jibi har shami™antun sai su ce min, gaba daya na zama abar tsokana a unguwar, shi ya sa na tattara sunan na watsar na koma Nana, indai aka ce dani Rawasiya to a gidane ko  yan uwa. Lokacin da na shiga FUD STAFF SCHOOL J S 1, idan  yan ajinmu suka ji suna yayuna sai su yi ta tambayata me ya sa sunana bai fara daga Ra ba, amma na yayuna duka Ra, kasancewar dukkanmu muka shiga makatantar, Yaya Radiya da Rumaisa suna J s 3, Ridwan J s 2, ni kuma J s 1, Ra is ne kawai babu, sai na ce musu ni ba  yar gidan ba ce. Wata rana da Yaya Rumaisa ta zo ajinnu ta ce da ni Rawasiya nan  yan ajin suka Wauka Rawasiya shami™atin, amma da yake ban bada fuska ba akan sunan sai Nana yafi zama a bakin nasu. Sanda muka shiga Aji na biyu lokacin su Yaya Radiya sun shiga Siniya, a lokacin Yaya Ridwan ne kawai,  yan matan makaranta tin daga  yan ajinmu har na ajinsu kowacce sai ta zo ta ce dani tana son Yayana, kaf makarantar yafi kowa yawan masoya, ga halinshi na rashin son magana ya kara ja masa farin jini a makarantar. Lokacin da zan shiga Siniya ne lokacin da muka yi saukar Al-kur ani ni da Yaya Radiya, Yaya Rumaisa, Yaya Ridwan, ban da Ra is sabida mun yi masa nisa sosai a karatu mussaman na addini. 



Alhaji yana da burin mu yi karatu me zurfi, amma Allah bai nufi hakan ba, domin yaya Radiya tana shiga Aji 3 na babbar sakandire, Yaya Hadi dan gidan babbar yayarsu Alhaji ya ce yana son aurenta, babu yadda Alhaji ya iya haka ya sa ya aminta, sabida bai isa ya tunkari Hajjansa da maganar yana so ta yi karatu ba, ko da wani ne a waje ya ce yana sonta bare kuma Yaya Hadi jikan da tafi so a rayuwarta. 



Tabbas Hajjansu Alhaji macece mai mugun son zuciya da sabon abun duniya, an ce sanda Alhaji yana da arziki babu wanda take so sama da shi, amma tun da ya sami karayar arziki ta watsar dashi da iyalansa, ta kama wanda yake da shi, gashi ba ta wani cika son Hajiyarmu ba, har wani suna take kiranta dashi wai Fulanin tashi ko Fulanin jeji ne, ni ban wani sani ba, tun da ba cika shiga sha aninta na yi ba, domin nida Ra is ta tsanemu har ce mana take masu farar ™afa wai mune muka yi sanadiyar talaucewar Wanta, wani lokacin ma ta ce ubanmu idan tana jin tsiyarta. 



Shi ya sa ma mu a famili mu ka zama ware, muna gefe sai ayi abubuwa nawa ba muje ba, wani ma bamu sani ba, wani ko mun sani ba zama bu, da idan ba muje ba Hajiya na ta kura mana daga baya kuma ta kyalemu, tunda da zuwan da rashin zuwan ba tsira zamuyi da zagi ba, har gwanda bamu je ba ma zagin a bayan idanun mu ne. 



Allah Ya haWa jini Yaya Hadi Yaya Radiya tun da ita ma tana son abunta, ita ma Yaya Rumaisa ana haka saurayinta mai sunan Alhaji ya fito, ita ta turoshi ba ita ta turoshi ba Allah masani, dan da ya ce sai ta gama karatu amma rana tsaka ya sake maganar, hakan ya sa Alhaji ya amince zai aurar dasu tare da dora burinsa a kaina, ko ba komai ina da karancin shekaru a lokacin. 



Ba mu dade da yin biki sauka ba aka sanya ranar aurensu duka su biyun, dan Hajja ta ce babu amfanin karatun da zasu yi. Haka ya sa aka sanya auren nasu, sai dai duk wannan balo™o™on da ta yi da aka tashi bikin babu kobo da ta bayar duk Alhaji ne da kudinsa ya yi, sai kuma yaransa da yake tare da shi Isah Nadabo har wannan lokacin, wanda ya siya maa shago a bakin titi ya cika masa shi da kaya, shine ya dauki nauyin yin kayan daki na duka su biyun. 



Haka aka zo lokacin biki Alhaji da Hajiya sunyi hidima dai gwargwado, hidimar da babu wanda ya yi tunanin zasu iya irinta, dan bayan angama biki ma sai da Hajja ta kira Alhaji ta ce wai aina ya sami kudi, sai ya ce da ita  yan uwan Hajiya ne suka yi, maimakon ta gode musu ko ta yaba musu sai ta hau aibatasu, wai basu dauke ta da daraja ba da bazasu kawo gudumawa wajenta ba sai dai su ba wa  yarsu, abu kamar wasa sa ga Hajjan a gidanmu ta zo ta yi wa Hajiya tas, sannan kuma wai tafito da ragowar gudumawar sai dai Hajiya ta ce jiya ta haWe komai anyiwa Yaya da Radiya da Rumaisa gara an kai musu, abu kamar shafar iska sai ga Hajja a gidan Yaya Rumaisa ba ta je gidan Yaya Radiya ba sabida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login