Showing 48001 words to 51000 words out of 64149 words

Chapter 17 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

155

na ji ta ce yadda kike son mijinki ba za ta iya shiga tsakaninku ba.  



 Hhhm, idan ba ta shiga ba rasa ka zanyi gaba Waya.



 Nana ki daina wannan tunanin ba zaki taSa rasani ba, Nana a yadda nake jin ki a rayuwata idan babu ke nima ai babu ni.  



 Nima nasan ba zan rasa ka ba, amma biyayya ga iyaye dole ce idan muna neman albarka a rayuwa.  



 Nana bari na je gidan Hajiya na gara kiranta yanzu.  



 Tom Allah Ya tsare hanya.  



 Amin Ya Allah.  



Ya faWa yana tashi, yana fita na sake kiranta a waya amma bata Wauka ba, message na hau rubuta mata. 



 Salam, Bilkisu dan Allah ki fahimceni, ina so ki aure mijina Sardauna sabida ki tsira daga auren dole da zaayi miki, shima ya tsira daga auren dolen da za ayi masa ki fahimta dan Allah.  



Na tura mata amma har Sardauna ya dawo ba ta yi min reply ba, washe gari da safe ma na sake tura mata wani amma shima ba ta ce dani komai ba. 



 Honey ya kuka yi da yarinyar?  



Kallonsa na yi sannan na ci gaba da haWa mai tea Win, sai da na gama sannan na ce. 



 Ba ta sake cewa komai ba, amma dai zan ™o™arta zan sake magana da ita.  



 Shikenan Nana, nasan zaki iya, Allah Ya yi miki albarka.  



 Amin Amin.  



Bayan mun kammala breakfast ya tafi, na dawo na ci gaba da kiran wayar Bilkisu amma bata Wauka ba, ganin ba zata Wauka ba na shiga fito da wankin kayan Sardauna na hau yi, da ™arfi nake dirza kayan sabida ina son su fita su yi haske yanda zai ji daWi, sai wajen la asar na gama wankin na shanya su s abun shanyar mun na bayan kitchen, ina dawo na ga missed call Win Bilkisu, jikina har Sari yake na Wau wayar na kira ta, ina kira ta Wauka, cikin rawar baki na fara magana. 



 Bilkisu!  



 Na am Nana.  



 Bilkisu kinga messages Wina?  



 Nagani Nana, ni bansan abinda zance miki ba shi ya sa ma ban miki reply ba, kina magana kamar wata  yar ™waya.  



 Hhm Bilkisu ba zaki gane ba ne, amma dan Allah ki taimaka, ki taimakeni ki taimaki mijina.  



 Nana babu wata hanyar taimako da zan ia yi miki bayan wannan? Gaskiyya wannan abun yafi ™arfina, ki barni da matsalal Abbana kawai.  



 Bilkisu dan Allah ki biyo ta gidana mu yi magana.



 Nana bana jin zan sake zuwa gidanki, tun abinda kike son ™ullamin kenan? Ace na zo gidanki na aure miki miji, duniya ta yi ta zagina.



 Haba Bilkisu ya zaki ce haka? Dan Allah kizo ko ba zaki aureshi ba nasan akwai shawarar da zaki ban.  



Shiru ta Wanyi na  yan mintina sannan ta ce. 



 Shikenan, bari na zo yanzu.  



 Tom Bilkisu na gode sosai.



 Sai na zo.



Ta faWa tana kashe wayar, na koma na zauna.  A halin da Bilkisu take ciki na yi tunanin zata amshi wannan tayin hannu biyu biyu? Ko dan mafita da take nema, amma ta™i! Lallai Bilkisu ta cika mutuniyar arzi™i.  



Ta shi na yi na duba kayan Sardauna dana wanke, na fara kawahe waWanda suka bushe na shiga dasu ciki, ina fitowa itama ta shigo Wakin, ban bari ta zauna ba na fara mata magana. 



 Haba Bilkisu, ahalin da kike ciki na yi tunanin wannan mafita ce a garemu duka?  



 Nana mafita ce mana, amma da ace wani ne ba mijinki ba, Nana da wane ido zan kalli duniya? Da wani ido zan kalli mutane zan kalli makwafta, zan kalli  yan uwanki, ace ina ™awarki na zo na auri mijinki, zagin da zan sha Nana ba ™arami ba ne, Nana tsinuwa zan sha a bakin jama a, ta yanda babu yadda zaayi na kare kaina, tun da gani a gidan naki, Nana a dinga duba ana saran gatari.  



 Bilkisu mu zauna. Na faWa ina kama mata hannu, zaman ta yi sannan na ce. 



 Ina ruwanmu da surutun wani? Waye zai sani? Waye zai san mi dake ™awayene, Bilkisu ko sun sani mene a ciki? Ba dai mu muna zaune ba, nasani Bilkisu zaki zauna tare dani cikin aminci, mu kula da mijinmu, to ina ruwanmu da zancen mutane? Su yi ta yi kar su daina.  



 Idan ke kunnenki zai iya jurewa, to ni nawa ba zai ya jurewa ba. Nana bakisan mene bakin mutane ba, idan suka sa ka agaba wallahi duk wata albarka dai ka nemeta ka rasa, Nana idan ke kin fahimta ina  yan uwanki zasu fahimta?  



 Kishiya ce fa Bilkisu! Kuma ba Kaina farau ba ko karau? Mijina ne kaWai ya taSa ™ara aure?  



Hannuna ta kama sannan ta ce. 



 Nana, ki yi ha™uri abar wannan maganar, kamar zata fi amfani Nana, idan duk na ce na ji nagani shi mijin naki fa? Yana sona? Zai soni? Zaman alfama Nana bazan iya ba dan Allah.  



 Salamu alaikun.  



Muyar Sarauna ta ratsa Wakin, ban maji ko warn Winsa ba, kawai sallamarsa na ji.  



 Sannu da zuwa.  



 Yawwa sannu.  



 Sannu da zuwa.  



Bilkisu ta faWa kanta yana ™asa. 



 Yawwa sannu. Yana amsawa ya shige cikin Wakin, bai ™ara sa shigewa ba Bilkisu ta mi™e tare da faWin. 



 Nana, zan tafi.  



 Bilkisu bamu gama magana ba.  



 Nana ni dai nagama yanke hukuncina.  



Tana faWin haka ta fice, hannuna na Wora a goshine tare da faWin. 



 Hhhm, Ya Allah.  



Šakin da ya shiga na bi shi, ina zuwa na tarar da shi zauna a kan gado, idanunsa sunyi jawur alamun ya ci kuka ya gode Allah. 



Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na ashirin da uku.

    (23)



 Ya salam! Me ya faru Sardauna?  



Wasu hawayen ne suka fara fitowa daga idanunsa, waWanda suka ™ara Wagamin hankali, ya ri™e hannu. 



 Nana nagaji, ina danne zuciyata ina sonki, bana son abinda zai cuceki, amma Hajiya ta dage wai tana son ganin jikokinta, Nana ko zuwa gidan Hajiya bana son yi, bana so na ji an soke ki ko anci mutunciki, Nana bana son zaluntarki, bana son cutar da zuciyarki, bazan iya ™ara aure ba kwata kwata, karki ga yadda ake zancen nan a family house kamar akaina aka fara shekara uku da aure ba haihuwa. Hon haihuwar nan dole ne?.



Wani irim tausayinsa neya ratsamin zuciyata, sai na ji dama ni ce nake shiga wannan matsin ba Sardauna ba, dama nice nake wannan kukan ba Sardauna ba, bazan iya jure ganin hawayen Sardauna ba, suma azabatar da rayuwata. 



 Ka yi ha™uri, haihuwa ba dole ba ce, amma tabbas a idon iyayenmu gani suke dole ne, Sardauna a yanzu ma da ka zo maganar muke da Bilkisu amma ta™i fahimta ta duk da nasan zata fahimta in sha Allah. Ina tunanin idan ka yarda zanje gidansu gobe mu sake magana da ita. 



 Hon ina cikin damuwa, ina cikin tashin hankali, rayuwa ta yi min ba™i mutuncina yana watangarirya. Na yarda ki je da kanki, kisan yadda zaki yi da ita ta amince, Hon ki dur™usa mata a ™afa, ko ni naje na dur™usa mata kawai Hon, da mutuncina ya zube a idon duniya, gwanda na yi haka, ko menene zan iya yi mata wallahi indai zata aureni.  



 Ya zaayi kaje ka dur™usa mata? Haba dai. Ka barni da kaina zanje gobe, zan yi magana da ita ta yadda dole zata amince, ka sa ha™uri a ranka dan Allah.



 Nana idan ba ta amince ba ina cikin tashin hankali, ni dake Nana bamu da wata mafita.  



Ji na yi kamar na tashi a cikin daren na je gidansu Bilkisu amma ba hali, da™yar na lallaSa Sardauna ya nutsu amma bai iya cin abinci ba, haka muka kwanta duk ranmu ba daWi. Washe gari lokaci Waya muka fita dashi, ya yi ofis ni kuma na yi gidansu Bilkisu ta hanyar kwantancen da ta yi min tun kwanaki. A bakin gate Win na tarar da wata mata mai kama da Bilkisu na shirin fita, ™asa na tsugunna tare da faWin. 



 Ina kwana?  



 Lafiya.  



Ta amsamin a da™ile, sannan ta ce. 



 Wa kike nema.



 Bilkisu.



 Tana ciki.



Ta faWa tare da hucewa, na kusa minti biyar a tsaye ina faman tunanin ta yadda zan fara da Bilkisu, bana son ta tirjemin kamar yadda ta yi jiya. A hankali na tura ™ofar falon na shiga, zaune na tarar da su 'yan mata ne sun kai su biyar da alamu ma wasu ™awayenta dan ba 'yan gidansu ba ne, duk da nima wannan ne zuwa na na farko gidansu. cikin wani irin yanayi kamar na isgili haka ta tarbeni. 



"A'a Nana kina ™araso." 



Na yi mata murmushi sannan na ce. 



"Eyh wlhi, ya gida?" 



"Muna lafiya." 



Zama na yi sannan na kalli sauran matan dake Wakin, sannan na ce. 



"Sannunku." 



Bansaniba ko sun amsa ko basu amsa ba, nidai abinda ke gabana shine kaWai ke damuna. 

Gaba Waya tunanin maganganun da muka yi da  Sardauna ya cika min ™wakwalwa, bana iya tuna komai sai muryarsa. 



'Nana nagaji, ina danne zuciyata ina sonki, bana son abinda zai cuceki, amma Hajiya ta dage wai tana son ganin jikokinta, Nana ko zuwa gidan Hajiya bana son yi, bana so na ji an soke ki ko anci mutunciki, Nana bana son zaluntarki, bana son cutar sa zuciyarki, bazan iya ™ara aure ba kwata kwata, karki ga yadda ake zancen nan a family house kamar akaina aka fara shekara uku da aure ba haihuwa. Hon haihuwar nan dole ne?.'



"Allah Sarki Mijina." 



Na faWa a zuciyata, a fili sai kuma na kalli Bilkisu na ce. 



"Dan Allah magana nake so mu yi dake, ina son mu shiga daga ciki." 



Dariya ta yi ita da mutanen nan nata sannan ta ce. 



"Haba Nana kamar ba wise ba." 



Šaya cikin ™awayen ta ce. 



"Baiwar Allah kizo ki ganmu tare sannan ki ce wai ta tashi ku shiga ciki a wane dalili?" 



Baki sake nake kallon ikon Allah. 



"Nana waWannan ™awayena ne duk wani sirri zan iya yi dasu, dan haka ki faWi abinda zaki faWa." 

Ji nai na yi wani irin muzanta, kamar bata san maganar da zamuyi ba, to ma wai '™awayenta ™awayena ne?, ko da ™awaye na ne kowacce magana yakamata na yi a gabansu?.



"Hon ina cikin damuwa, ina cikin tashin hankali, rayuwa ta yi min ba™i mutuncina yana tangarirya Hon, na yarda amma ki je da kanki kisan yadda zaki yi da ita ta amince, Hon ki dur™usa mata a ™afa, ko ni naje na dur™usa mata kawai Hon, da mutuncina ya zube a idon duniya, gwanda na yi haka." 



Kalaman Sardauna suka dawo kunnuwa kamar yanzu yake faWinsu. 



"Bazan taSa bari ka hula™anta ba in sha Allah Mijina." 



Na faWa, sannan na kalleta tare da tasowa zuwa inda take, na sanya gwiwoyina a ™asa sannan na ce. 



"Maganar mu ta jiya, ki taimaka ki auri mijina." 

Wata shegiyar dariya na ji ™awayen na ta sun kice da ita, kamar daman jira suke na yi magana.



 Bilkisu wannan mahaukaciya ce?



Šaya cikin ™awayenta ta faWa, tana wata irin dariya. 



 Bana ce ba, ni yadda nasanta lafiya ™alau take, amma daga jiya zuwa yau gaba Waya ta canja.  



 Bilkisu kinsan komai, wannan abun mafita ce gani da ke.  



 Nana ki saurareni, na gama magana fa wai ma idan aure ne macece zata nema masa aure? Ke awa da zaki nema masa aure, ba zai zo da kansa ba? Kinga kenan kece kika aureni bashi ba.  



 Ba haka ba ne Bilkisu, kusancin dake tsakanina dake ne yaja haka, amma da kin bashi dama zai zo da kansa Bilkisu.



 Ke amma kin rako mata wallahi, bantaSa ganin ballagaza marar kishin kai ba irinki, mijin naki kike yawo da shi a haka? Kina neman a aure shi? Sannu Saratu ba ki yi wa kanki tanadi ba wallahi, bama alfahari dake.  



Wani irin Waci na ji ya tsayamin a ma™ogwaro zuciyata ta fara wani irin raWaWi.  Ko Bilkisu ta kawo waWannan ™awayen na ta suci mutunci na ne?. Na tambayi kaina, ban kai ga samun amsa ba na ji wata ta ce. 



 Ni yau na fara ganin asara irin wannan ba, amma dai duk da yadda aka yi mijinne baya sonta, shine ya bata dama ta kawo mai wata ko ya rabu da ita.  



Suka tuntsire da dariya, Bilkisu ta ce. 



 Ba fa haka ba ne, ni bansan mene asalin matsalal ba kamar haihuwa ne ba ta yi.



Wani zafi na ji a zuciyata, wai Bilkisu ke hula™antani, tana shela da ni haka, kamar ba ta san komai ba. 



 Ai kuwa babbar matsala ce, dole ta fito ta nema masa aure kafin ya kaWata, dan ba kowa zai iya jurar mace daga ci sai kashi ba.  



˜walla na ji tana zirara daga idona, a fili na furta. 



 Ya Allah Ka na ji ka na gani.  



 Nana idan zaki tashi ki tashi, babu abinda zai sa na auri mijinki, gwanda ma ke nemi wata mafitar.  



 Ji ta ballagaza. Wannan ita ce maganar da tafi ™onamin rai, ba shiri na mi™e a raina na ™udiri cewar zan nemawa Sardauna wata ba dole sai Bilkisu ba, tun da daman ba sonta yake ba. 



 Na gode Bilkisu.  



 To Nanan Sardauna, ki gaida gida sannan ki canja shawara. Bilkisu ta faWa, wata cikin ™awayen ta ce. 



 Ki canja tunani kam, kuma a dage a rage ci tun da ba haihuwa za ayi ba.  



Ban kai ga ™arasa fita ba, na ji sun kece da wata irin dariya, haka na tawo ina haWa hanya sakamakon matsanancin jirin da nake ji, fuskata ta ji™e shargab da hawaye, wannan cin mutuncin har ina? Lallai Bilkisu. 



A haka na shigo cikin gidan, daidai lokacin da Turaki ya fito daga Sangarensa, da sauri na yi ™asa da kaina sabida kar ya ga fuskata. Ba ni da damar yin sauri sabida jirin da nake ji, hakan yasa na tafi a hankali. 



 Nana!  



Ya kira sunana, ta dole na tsaya ba tare da na juyo ba. 



 Kuna waya da Hajiyarki?  



Na gyaWa kai, ba tare da na yi magana ba. 



 Good. Ya faWa tare da fara tafiya, jan hanci na yi tare da wata shashe™a da ta ™wacemin ba tare da na shirya ma ta ba ya sa shi dawowa. 



 Nana! Meke damunki? Kuka kike?



 A a.  



 ˜arya zaki yi min, Sardauna ne ba lafiya?  



 A a.  



 To me ya sa ki Kuka?  



Ya faWa yana matsowa inda nake, girgiza kai na yi bance komai ba. 



 Me ya saki Kuka!  



Ya faWa a tsawace.



 Ba komai, ka yi ha™uri, zan faWa ma.  



 Ha™urin me Nana? Me ya ta Sa ki haka?  



 Ka yi ha™uri, zan faWa ma.  



Na sake maimaitawa gaba Waya na ruWe.



 Nana kina da damuwa ne? Duk kin ruWe kin fita hayyacinki, are you okay?  



 Yes! I m okay.  



 Hhhm.  



Kawai ya faWa tare da sa kai ya fice, ni kuwa har da harWe ™afa sabida sauri na shige ciki, ina shiga na faWa kan kujera na fashe da kuka, mai tsuma zuciya. Kuka nake yi mai ™arfi har sai da na fara jin Waci a ma™wogarona. Kukan da ya haifarmin da wani ciwon kan wanda ya haWe da jirin da nake ji gaba Waya na ji duniyar ta fara yi min zafi, abubuwan sun har gitsemin sama ta juye ™asa. 



Da™yar wani wahalallen bacci ya Waukeni marar daWi, ina yi ina firgita, ina zabura kamar wacca za a taSa, cikin barci na fara jin hayaniya sama sama. A hankali na buWe idanuna sa suke jawur, wani irin sarawa na ji kaina ya yi, amma a haka na dafe kan na mi™e sabida jin kamar cacar baki. A hankali na le™a ta window Sardauna da Turaki ne. 



 Turaki ina so ka sani, ni Sardauna na yi maka nisan da har abada ba zaka taSa kamoni ba, Turaki duk abinda zaka yi tsakaninka da ni sai da ido. Kasani abinda Sardauna ya taSa har abada ya yi maka nisa.  



Turaki ya saki wani murmushi, sannan ya dafa kafaWar Sardauna ya ce. 



 Alfahari da fariya na ™arya kake yaro, ni lokacin da zan zauna na yi wannan maganar marar amfani ma ban da shi, sannan ina tunasar da kai cewar Ajuri zuwa rafi, wata rana tulu zai fashi. Shashasha.  



Yana faWin haka ya wuce yabar Sardaunar a wajen, da sauri na koma kan kujera na kwanta, na rasa mene asalin wannam faWan dake tsakanin Sardauna da Turaki. Da ™arfi ya saki ™ofar bayan ya shigo, na runtse idona sabida wani irin bugu da na ji zuciyata ta yi. 



 Nana! Nana! Nana!  



Na buWe idanuna na kalleshi. 



 Me kike yi a kwance.



 Bakomai.  



Na faWa ina mi™ewa zaune. 



 Me ya shigo da wannan Wan iskan bangarena?



 Waye?  



 Karki rainan hankali mana, waye banda Turaki.  



 Bai shigo ba.  



 To aina ya ganki?  



 A parking space ne, bayan na dawo daga gidansu Bilkisu.  



 Hhm, har ni zai cewa wai na dinga yin adalci, me kika ce masa?  



 Babu abinda na ce masa, to me kake yi min da zan faWa masa?  



 Nasan mike, nasani ko kin yi min wani sharri.  



 Uhm.  



Kawai na faWa tare da sake komawa na kwanta, kallona ya yi sai kuma ya sha jinin jikinsa. 



 To kawai yana ganina ya wani hau yi min magana, ni da ba shiga sha aninsa nake ba, tun muna yara Turaki yake son shiga rayuwata, yana ba™in ciki da ni a rayuwarsa, ni kuma ko magana ma bana son naga ta haWani da shi, ina kishin naga nasan abu Turaki ya san shi, shi ya sa ma duk family na bar masa, na ja rayuwa ta na yi gefe, ranar da na ga ya yi miki magana a family meeting wallahi Nana ji na yi kamar an watsamin tafasheshen ruwan zafi a zuciyata, na ji zafi fiye da yadda kike tsamanni.



 Hhhm, to yanzu ni me zai haWani da shi da har zan hau yi masa magana akanka.  



 Ki yi ha™uri to.  



Ya faWa yana kama hannuna. 



 Bakomai.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login