Showing 9001 words to 12000 words out of 64149 words

Chapter 4 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

146

tasan jikanta ne zai ci komai, sa ta je gidan Yaya Rumaisa, haka ta dinga jidar kayan garar abun haushi a gaban dangin mijin Yaya Rumaisa, har da kukanta sai sune suka rarrashe ta bayan Hajjan ta tafi. 



A da Alhaji baya Soyewa Hajja komai amma yau da gobe tafi karfin wasa, a hankali ya gane Hajja ba ta yi dashi dan ba zai ce ba ta kaunarsa ba tun da babu uwar da zata haifi Wa ta ce ba ta son shi, shi ya sa ya boye mata Isah Nadabo, mutumin da ya taimaka masa wanda ya rike amana ya dawo yana sakawa Alhaji da fin abinda ya yi masa, dan tsaf Hajja zata sa shi a gaba yakirashi ta kuma sa shi ya bata ma™udan kudaden da ba lallai gobe ya sake tun karar Alhaji, kuma ta dinga i™irarin tsine masa idan ya™i, a haka ma duk sati sai ta aika an amsar mata shinkafa da wake har dasu mai da maggi da kudi a shagon nasa, wani lokacin ma sai ta zo da kanta tai ta jidar indomi da madara, wani abun ma bata san shi ba kawai mugun hali ne, dan akwai lokacin da ta dauki Izel na wanke bandaki ta tafi dashi ta dauka abun sha ne ta sha, dakyar ta mi™e dan ta yi jinyar wajem wata biyu, maimakon ta yi hankali sai ta ce ita yanzu ta fara. Haka take rufe ido ta yi ta jidar kaya duk sanda tazo, akwai ma lokacin da ta fado daga kan kanta, dake shagon akewaye yake anyi gini tsakanin inda  kayan suke da inda mutane zasu tsaya, sai da fridge da kayan ruwa sune daga waje, shagon yana da girma da fadi, to garin haurowa ta tsallaka ciki ne ta dawo kasa ta fadi, nan ma sai da ta yi jinya, amma dake matar nan babu Allah a ranta sai ta ci gaba da zuwa. A kullum burina shine na yi karatu mai zurfi, na zama wata ko da a iya Dutse ne, na taimaki iyayena da  yan uwana, ina son ganin na yi wa Alhaji wani abu da zai ji dadinshi a rayuwa, mahaifina da mahaifiyata suna da buri akaina na ganin cewa na yi karatun boko mai zurfi, kuma ni kaina haka sabida na fahimci idan banyi karatu mai zurfi ba, babu inda zani. 



Haka rayuwa take ta tafiya, yau fari gobe ba™i. Yayuna suna gidan aurensu kuma kowacce babu abinda zamu ce da Allah sai godiya, dan kowacce da ka ganta zaka san tana cikin rufin asiri, a hankali rayuwa tana gangarawa inan da burin na karatu mai zurfi, sai dai bansan me kaddara ta tsara mini ba.



09:30pm. 



Zaune muke a tsakar gida ana dan taSa hira, ni da Hajiya da Ra is, ko na ce Hajiya da Ra is da ni da ido kawai nake binsu, bansan me ke damauna ba amma gaba Waya tun yamma banajin daWi, gaba Waya ji na nake wata sukuku. Yaya Ridwan kam yana can daki yana faman game, dan yanzu game ya siya da ake yi a tv da wani abu na rikewa a hannu wai shi Handle, in ji Ra is. 



Alhaji ya shigo bakinsa dauke da sallama, da sauri na mi™e ina faWin.



  Sannu da zuwa, babanmu.  



Ya sakar mini murmushi sannan ya ce. 



 Yawwa.  



Bayan ya zauna ne Ra is da Hajiya suka yi masa sannu da zuwa, Hajiya ta mi™e Wakko masa abinci, Ra is da Hajiya Aminan juna ne, ko da yaushe tare zaki gansu, dan Ra is ina ga ko a waje baida wasu abokan kirki, kullum suna zaune da Hajiyya hirar su ba ta ™arewa, karasa me suke cewa, yanzun ma tare suka nufi kitchen din Wauko ma Alhaji abinci. 



Bayan Alhaji ya gama cin abincine ya ce. 



 Rawasiya ga sa™onki.  



Ya faWa yana mi™amin leda, nasan sa™on bai wuce maset da kalkuketa ba, dan su na ce masa ina so Wazu da safe, sai kuma biskit na makarantar gobe, kafin na gama buWewa Ra is ya ce. 



 Hajiya nima ina so littafi nawa sun cika, sannan rulata ta karye.  



Dariya na yi masa sannan na ce. 



 Ai Hajiya ba ta da shago.  



 Barshi dai ya faWa mata, ina ga kantin zata bini ta karSa masa.  



Alhaji ya faWa, Hajiya kuma ta ce. 



 Ina ni ina binka kanti, kawai dai a kawo masa.  



 Wannan ya yi bacci ne?  



Alhaji ya faWa yana nuna Wakinsu Ya Ridwan. 



 Yana ciki yana faman sana ar.  



Hajiya ta faWa, sannan ta ™ara da cewa. 



 Wai ni kuwa Alhaji yaushe yaron nan zai fara zaman kantin nan ne? Ya kamata ya fara rage ma wasu abubuwan da wannan zaman asarar da yake.



Murmushi Alhaji ya yi sannan ya ce. 



 Yaron da yake shirin shiga jami a, ina yake da lokacin zaman kanti?



 Ni kuwa ansama masa Addmision din ne? Bai ma faWan yadda suka yi da bawan Allah nan ba.  



Hajiya ta faWa sai da Ahaji ya sha ruwa sannan ya ce. 



 Ai Isah Nadabon ma ya zo waje na Wazu, har yake yi mini maganar ita Rawasiya.  



Da sauri na katseshi da cewa.



 Alhaji Nana dai.  



Banza ya yi dani ya ci gaba da cewa. 



 Yana tambaya wai aure zata yi itama ko sai ta yi karatu, na ce dashi sai ta yi karatu, to wai da ya nuna sha awar shi ne akan yana son aurenta, sabida ya na son ya yi tafiya ta shekara biyu kuma shi kanshi zaifi son ace ya tafi tare da iyali ne.



Legendspen

08129553971

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na biyar

    (05)





Tunda Alhaji ya fara magana gabana yake faduwa, aure kuma? Ni ba auren ba ma wallahi kwata kwata bana son mutum ya girmeni sosai, gaba daya shekara ta sha bakwai, Isah Nadabo a yanzu ya kai wajen talatin, ni nafi son yaro dan shawalwali, wanda baifi 26 ba haka, maganar Hajiya ce ta katse min tunanin da na shiga da na tana cewa. 



"To Alhaji kamar Isah Nadabo ai yafi ™arfin haka a wajenmu ko, da an bashi." 



"Kai Hajiya!" 



Na faWa a raina, Alhaji ne ya ce da ita.



"A'a dai, ai bama za ayi haka ba ita yarinyar ba ta da zaSi ne?" 



"Ai shikenan dai, Allah Ya bata na gari." 



Alhaji ya ce.



"Amin."



Ni dai nan zaune bance ko ™ala ba, amma naji dadi gaskiyya, na auri Isah Nadabo na ce na auri wa, ™anin babane ko me? Babba dashi da ace ya yi aure a shekara goma sha wani abun da yanzu yana da yarinya kamar ni, kowacce ta girmi ni ma. Gashi wani baki ma, ni Allah Ya gani ina son dan gayu dan zamani, shi kam kallo daya zaki yi ma Isah Nadabo kinsan mutum ne mara walwala, kansa a kulle yake. 



Daga wannan rana ba a sake wata magana da ta shafi Isah Nadabo ba, kuma nima na ji daWin haka, haka na ci gaba da rayuwa ina 'yan matancina a gida har zuwa ranar da ™addarar YallaSaina ta faWa mini. 



Ranar wata lahadi bayan sallar magariba na fito daga gida ina shirin tafiya makarantar dare da nake zuwa, wacca gaba daya banfi a sati biyu da fara zuwanta ba. Tafiya nake kamar ko yaushe cikin nutsuwa,kamar ance Waga idonki. 

Kyakyawan matashin saurayi, mai kyakyawan yanayi da kyakyawar shiga, fuskarsa fara ce sosai yana da tarin kwantacciyar suma. Gaba Waya kammaninsa ba sa yanayi da na 'yan nigeria sabida yanayin idonsa har wani wal™iya suke mai daukan ido, hancinshi mai matsakaicin tsini haka bakinsa, wani kyakyawan gashin baki ya yi masa ™awayan ya gangaro gefe da gefe ya haWe da Wan ™aramin gemunsa. 



"Ya Hayyu Ya Qayyum!" 



Abinda na faWa a raina, sannan na ce.

"Wasu kamar sune suka hallicci kansu, sabida tsabar tsagwaran kyau, ina ganin Yaya Ridwan yafi kowa kyau ashe mummunane a gaban wannan." 



A hankali ya fara ta kawo yana tun karo ni, wani irin "Dif! Dif!" Na ji ™irjina yana bugawa, ™afafuna suka fara karkarwa, ™walla ta taro a idona sakamakon matsanancin bugun da zuciyata take mai ™arfi. A lokacin da ya matso gab da ni, sai da na ji numfashina ya Wauke na da™i™a.



"Salamu alaikum." 



Wata sassanyar murya mai yanayi da busar sarewa ta shiga kunnena, bayan sassanya ™amshin turarensa ya cika min rayuwa gaba Waya.  



"Ina wuni?." 



Na tsinci kaina da faWa har da dur™usawa, ya yi murmushi sannan ya ce.  



"Gidan can zan aiki ki." 



Ya faWa yana nuna min gida dake kallon namu, na juya na kalli gidan sannaan na ce. 



"Toh!" 



"Nan ne gidan Alhaji Hadi ko?"



Ya tambaya, ni kuwa jikina har Sari yake amsa tare da gyaWa kai. 



"Eyh! Nan ne." 



"Ki shiga ki ji yana nan? Idan yana nan ki ce masa Fahad Ta'ambo ne, wanda su ka zauna tare a jirgi daga Dubai zuwa Nigeriya, ya yi mantuwar ne a cikin jakata shine na zo kawo masa." 



Tun da ya fara magana gabana yake faWuwa har ya ™arashe. Yana gamawa kamar wacca aka umarta na fara tafiya, ban tsaya ba sai da na shiga gidan, bayan na isar da sa™on Alhaji Hadi ya ce dani yana zuwa, na dawo na faWa masa ya yi min godiya, amma maimakon na kama hanyar makarantar sai na dawo gida, gaba daya ji na nake wani sukuku, unguwar ta yi min faWi, ™amshi turarensa ne ka dai yake yawo a kwanyar kaina, sai kuma maganarsa tun daga farko hat karshe, ban manta ko kalma daya ba. 





"Ki shiga ki ji yana nan? Idan yana nan ki ce masa Fahad Ta'ambo ne, wanda su ka zauna tare a jirgi daga Dubai zuwa Nigeriya, ya yi mantuwar ne a cikin jakata shine na zo kawo masa." 





Abinda na fada kenan da safe bayan na buWe idona, da sauri na daki kaina tare da faWin. 



"Rawasiya wake-up, me yake damunki ne haka?" 



Mi™ewa na yi tare da nufar banWaki na wanke baki na na fito zuwa tsakar gida, sai da ™amshin turarensa har yanzu yana yawo a hancin na, 

yanayin da na ji jiya yana nan kamar yanzu yazo unguwar. 



Haka kwana daya ya wuce ina jin wannan yanayin a tare da ni, kwana na biyu ya wuce, sai da na yi sati sannan na ji yanayin ya fara raguwa, sai da na Wau tsawon wata guda ina fama, kafin manta amma kuma har lokacin kammaninsa da sunan sa suna nan a kwakwalwata, domin a kallo daya kwakwalwata ta dau™i hoton sa, wanda ya tsaya a a zuciya.



Ranar da Allah Ya nufa zan sake ganinsa ranar wata laraba da yamma, lokacin Hajiya ta aiki ni gidan wata ™awarta a fagoji, banson zuwa fagoji kwata kwata, ni ba ma fagoji ba gaba daya ban fiya son zuwa wani waje nesa ko kusa ba. Daidai bakin titin Rasheed shekoni special hospital mashin din da nake kai  ya tsaya, me mashin Win ya tsaya yana duba mashin Win ni kuma na sauka ina jiranshi.  



A jiki na naji ido na yawo a kaina baya ga matsananciyar faduwar gaba da naji. Ina kai idona bakin asibitin na ganshi tsaye ya harWe hannusa a ka faWa yana kallona. Da sauri na sunkuyar da kaina ™asa ina faWin. 



"Wayyo Allah." 



Dan wani irin ™arfaffan bugu zuciyata ta yi lokacin da muka haWa ido dashi. 



"Sannunki." 



Na ji muryarsa dab da ni sai dai na kasa Wagowa, idanuna suka kai kan ™afarsa, takalminsa ma kaWai abun tsayawa a kalla ne. 



"Kamar ke ce ta unguwarsu Alhaji Hadi ko?" 

Da sauri na gyaWa kai, tare da faWin. 



"Eyh! Ni ce." 



"Lol, me kike yi anan?" 



"Mashin ne ya sami matsala, amma gashinan ya gama dubawa." 



Ya kalli mashin din sannan ya kalli ni. 



"Kuma a wancan unguwar kike?" 



Ya faWa yana baya da hannu alamun can. Na gyaWa kai tare da cewa. 



"Eyh! Yalwawa." 



"Uhm! I see." 



Ya faWa yana shafa gashin bakinsa daga tsakiya zuwa gefe sannan ya ja shi zuwa ™asa. 



"Mu tafi ko?" 



Mai mashin Win ya faWa, na juya zan hau mashin Win sai na ji ya ce. 



"Na ce ki tafi?" 



Ba shiri na tsaya kaina a ™asa. 



"You're eager to go, kin gaji ko?"



Ya faWa cikin wani irin yanayi na fushi, da sauri na girgiza kai sannan na ce. 



"A'a, bangaji ba.... Me mashin Win." 



Kallon me masahin Win ya yi sannan ya ce. 



"Malam ka jira." 



"Alhaji sana'a fa nake, idan na ajiyeta wasu zan Wauka." 



Hannu Ya sa a aljihu ya zari kuWi 'yan dubu dubu da a ™alla sun kai guda goma ko sha, ya mi™a masa. Ba shiri me mashin Win ya amsa tare da matsawa gefe ya zauna, a raina na ce. 



'Yanzu mu dai babu yaren da muke ganewa sai na kuWi." 



"So ba zaki tambayi sunana ba?." 



Ya faWa yana kafe ni da idanun da nake jin su tamkar na zaki sabida kaifi. 



"Ka yi hakuri ai naga ranan ka faWa min." 



"Ni... when?" 



"Da ka ce na cewa Alhaji Hadi Fahad Ta'ambo ne." 



Shiru ya yi yana kallona na kusan minti biyar sannan ya ce. 



"So kin ma ri™e sunana, shine da kika ganni kika yi kamar baki sanni ba ko? Na gode." 



"Ba haka ba ne, ban kula da kai ba." 



Na faWa murya ™asa ™asa. 



"Amma ni na kula da ke?" 



"Ka yi ha™uri." 



"It's fine, you can go. Na gode." 



Shiru kamar an shuka ni a wajen na kasa matsawa. 



"You can go fa." 



"Ka yi ha™uri." 



"Kije kawai." 



Ya faWa yana barin wajen, sai da ya shiga cikin motarsa sannan na iya matsawa zuwa ga mai mashin Win, ya Wauke ni muka ci gaba da tafiya. 



Gaba Waya hankali na ba yaga hanya, na tafi tunanin wannan mutumin, komai na shi burgeni yake, ya iya magana. Amma abinda ya bani mamaki shine kwata kwata banji ya tambaye ni sunana ba, ko da yake mene ala™arshi da sunana da zai tambaya, kamar daga sama na ji ana cewa. 



"Mun kusa wuce jakshon Win fa." 



Na kalli me mashin Win na kalli hanya, sannan na ce. 



"Wannan layin zaka shiga." 



********



08:30pm



Kamar wancan lokacin na farko da na haWu da Fahad Ta'ambo na kasa mantawa da komai na shi, to yau ma haka. Tun dawowa ta na ™ure a Waki ina zaune ni kaWai ina maimaita duk wata kalma guda Waya da ya faWa a cikin zuciyata. 

Hajiya ce ta le™o tare da faWin. 



"Rawasiya me kike yi a Waki ne, bazaki ci abinci ba ne?" 



"A'a Hajiya na ci acan, duk gjiya ce wallahi ke ci na." 



"Mene abin gajiya a zuwa Fagoji? Sai ka ce yau kika fara?" 



"Bazaki gane ba Hajiya." 



Na faWa ina juya baya. 



"Eyh, bazan gane wannan karatun sangartarba." 



Ta faWa tare da ficewa, ni dai daren nan haka na ™arar dashi a Waki ina ta hango kammanin kyakyawan matashi Fahad Ta'ambo. 



Washe gari ma dai da mafarkin kyakyawar fuskarsa na tashi, ni dai ban taSa soyayya ba, amma nasan yanayin da nake ji game da Fahad na san yanayi ne na soyayya. A gurguje na yi shirin makaranta na fito tsakar gida na Wauki abin kari na na yi, bayan na karya na amshi kuWin makaranta wajen Alhaji na nufi makaranta. 



FUD STAFF SCHOOL

11:30am. 



Tun da aka fita break ban matsa ko ina ba daga kan bencina, duk ™awayena su Fauziya Tasi'u su Malaika sun fita sun dawo amma sun tarar dani anan zaune. Malika safwan ce ta zauna kusa dani tana faWin. 



"Nana meke dumunki ne haka? Tun Wazu kina zaune sai faman murmushi kike?" 



"Murmushi?"



Na faWa da alamun tambaya. 



"Au baki ma san kina murnushin ba, sai dake malamar soyayya." 



Ta faWa tana dariya, na kalleta na ga yanayin ta ko a jikinta, daman Malika irin wayayyun 'ya'yan nan ne, dan a yanzu haka ma tana da saurayi abunta, idan anyi magana sai ta ce 'idan basu yi min aure ba, ji™ani zasu yi su sha?.' A yanzu haka har cikin Malamai tana da saurayi, sabida wayewarta ma Malaika Arora ake ce ma ta. 



"Ni Malaika ban faWa wata soyayya ba." 



Na faWa bakina yana rawa, kallona ta yi sannan ta ce. 



"Mai da karuwa 'yar iska." 



Tana faWin haka ta juya ta shiga sabgoginta ta barni da faman tunani. 



"Ya zaayi ace na faWa soyayya, faWawar da har wani zai iya ganewa, ko da yake a wayewa da gogewa irinta Malika ba abun mamaki ba ne dan tasan haka, amma ta ya zaayi na fara soyayya da mutumin da ko sunana bai ta Sa tambaya." 



Haka na yini sukuku, har washe gari ma hakan, sai da aka sake Waukan sati ina cikin wannan yanayin kafin na ji na dawo daidai, sai dai a cikin wannan satin fa duk ™awaye na sun yarda da maganar Malaika kan na faWa soyayya. Ni kam tsakanina dasu sai da ido, daga baya ne ma na fara biye musu har wata rana suka ce wai sai na zayyane musu kammanin mutumin, da na rufe idona kawai sai na ganshi ya harWe hannu yana kallona. 



Duk yadda na kai ga gaya musu cewar yadda na fasalta musu shi, haka yake a gaske sun ™i yarda, dan daga masu cewa jaruman indiya nake fasaltawa, sai mai cewa larabawan Dubai ne, ni kam daga ranar ban sake biye musu ba. 



A lissafina ranar da na cika kwana goma da haWuwa da Fahad Ta'ambo na sake ganinsa, sai dai abun da ya yi matu™ar bani mamaki shine inda na gansa, daga can gaban gate Win makarantarmu, da sauri na juya baya sai dai naga idanun ™awaye na akansa. Fauziya ta yi saurin matsowa kusa dani sannan ta ce. 



"Ke Rawasiya! Wannan ai shine sak mutumin da kika fasalta mana, ko shine?" 



Na gyaWa mata kai, gaba Waya na rasa nutsuwa ta, kamar ko da yaushe. Da zarar ya Wor ™awayar idonsa a kaina, shikenan na rasa nutsuwata. 



"Gaskiyya ™arya kike Rawasiya." 



Mailaka ta faWa a saitin kunnena. 



"Kina ganin yadda yake kollonta, zaki ce ™arya ne." 



Amina Aminu ta faWa.. 



"Wannan ai yafi ™arfinki Rawasiya, bama haWi wallahi."



Na ji muryar Malika ta faWa, a take Amina Aminu ta cafe da cewa. 



"Ni ban ma yarda ba, gashi dai gani nake da idona, amma na kasa gasgatawa." 



"Kinsan kuwa wane ne Fahad Ta'ambo?" 



Malaika ta faWa, daidai kuma lokacin ya fara takawo kusa da mu, ni kam gaba Waya sai na ji maganganunsu sun tsayan a raina, ni kaina nasan tabbas wannan saurayin yafi ™arfina, bazan taSa samun wannan saurayin ba domin kuwa duk wani abu da ake nema ya haWa. Kyau, kuWi, Nasaba, gayu, ilimi da duk wani abu da 'ya mace ke nema wajen datattacen Namiji. 

Gaba Waya daskarewa na yi na kasa motsi, kar na yaudari kaina Fahad ba tsarar aure na ba ne. 



"Yau ba magana ne, kin wane tsari ni da ido kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login