Showing 45001 words to 48000 words out of 64149 words

Chapter 16 - Sartse Part 1 Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

152

daga cikin damuwar da nake ciki, yamma lis sai ga Bilkisu ta zo itama a kiWime, al'amarin mahaifinta ya ta azzara akan auren da ya ce  zai yi mata. 



Itama gaba Waya ta yi wani sukuku, ta fita hayyacinta. 



"Bilkisu to ke ki duba cikin masu zuwa wajenki mana."



Na faWa dan dai nasan Bilkisu ba zata taSa rasa masu zuwa wajenta ba, domin dai tana da kyanta yadda yakamata, ga ilimi kuma yar gayu ce sosai da sosai. 



"Nana bazaki gane ba kwata kwata, duk masu zuwa wajena ba na aure ba ne, burinsu na basu haWin kai su Sarar mun da mutunci su cuceni."



"Ya salam, Allah Ya tsare ki."



"Amin amin, ku yanzu kun sami matsaya?" 



"Eyh mun samu, aure kawai Sardauna zai ™ara kamar yadda suka umarta."



"Allah Sarki Nana gaskiyya kinyi namijin ™o™ari Allah Ya baki haihuwar nan." 



"Amin Bilkisu, Allah Ya kawo miki mafita." 



Itama ta ce Amin, nan muka zauna kowa na jajantawa kowa har Sardauna ya dawo ya sameta, sai bayan ya dawo ta tafi. 



A yanayin Sardauna na yau dai babu wata sabuwar matsalal, kuma na ji daWin hakan sosai da sosai, haka washe gari ma babu wata matsalal. Al'amuran kamar sun sau™a™a wajen kwana biyar, sai ranar kwana na huWu Sardauna ya dawo cikin tashin hankali, Hajiyarsa ta ce lallai lallai ya sake ni idan har bai fito da mata ba cikin kwana biyu, a kiWime na ce. 



"To baka ce musu kana dubawa ba ne?" 



"Nana wa zan duba, har yanzu fa ban ga wata da na ji zan iya haWa ta dake ba, Nana mata basu da kama ko kaWan, bazan iya auren wacca zata hula™anta ki ba ko kaWan Nana." 



"Kar ka damu Sardauna, ni zan iya zama da kowace muddin kana nan kuma kana ganina a matsayin da kake ganina yanzu, Sardauna ka auri duk wacca ta yi maka." 



"Nana anya kuwa kina kishi na?" 



Kallonshi na yi, sannan na kalli ™asa. 



"Tayar maka da hankali shine kishi? Sardauna indai sai na Waga maka hankali na saka a damuwa bayan wacca kake ciki shine kishi to ni bana kishi, hasali ma babu zuciya a tare da ni, ina sonka a kowanne irin hali, zan ci gaba da sonka a kowanne irin yanayi Sardauna." 



"Nana bana jin zan iya neman wacca zan aura, ina neman alfarma a wajenki guda Waya dan Allah." 



Ya faWa yan goge ™wallar da take idonsa, bai bari na yi magana ba ya tsugguna a gabana, tare da ri™e min hannuna. 



"Nana! Dan Allah, dan girman ma'aiki ki ta ya ni duba wacca zan aura, Nana kowa kika kawo indai kin aminta da ita to zan aura Nana, dan ke zan yi auren kuma ina so ki nema min waccan zan aura da kanki da hannunki Nana." 



Wani irin nauyi na ji ya danne ni kamar an Wauramin gungumen dutse. Tabbas wannan alfarmar da Sardauna ya nema a wajena da girma take, ta ina zan fara? 



"Nana dan Allah, mutuncina da darajata duk suna hannunki a yanzu ki tallafa min Nana." 



"Ka tashi zaune dan Allah." 



"Nana ki yi min wannan alfarmar dan Allah." 



"Tom na yi ka tashi zaune ka ji."



"Na gode Nana."



Ya faWa tare da zama kan kujerar, ya ™ureni da ido sannan ya ce. 



"Nana!" 



"Na'am." 



"Na ga kin rame kamar bakya cin abinci?" 



Kallon jikina na yi, ni banga wata rama ba amma tabbas nasan a jikina ina jina falai falai kamar wata takarda. 



"Nana kamar ba kya cikin ni'imar aure, matar Ta Ambo ce a haka Nana?"



"Ba wata rama da na yi fa, kawai strees ne."



"Name?" 



"Abubuwan da suka dagule mana, komai ya rincaSe." 



"Nana ai komai yazo ™arshe ko? Komai zai yu sau™i tunda a yanzu za ayi auren kuma ai shikenan ko?" 



"Eyh shikenan in sha Allah." 



"Yawwa Nanaty, zan ci abinci." 



Tashi na yi ma nufi wajen dinnig Win, shi kuma yana biye da ni a baya, alkubus da miyar taushe ne na yi, ya zauna ya ci sosai nima kuma ya matsamin sai na ce, yadda ya ci haka na ce. Ko majalisar ma baije ba ya kwashe ne muka yi Waki, duk ranar da Sardauna ya Waukeni da kansa ina shan wahala har nagane, shi ya sa bana so ya Waukeni nafi son mu tafi ™afa da ™afa. 



Tun daga wannan lokaci Sardauna ya sani a wata duniyar ta daban, kullum aikina tunanin wace za ta da ce da Sardauna, dan ya zama dole na nema masa a ™asa da kwana ukun da ya ambata. ˜awayena Malaika ta yi aure tana kano, Fauziya ta yi aure, Amina Aminu ma ta yi aurenta daman su kenan, Yaya Radiya kuma Yayata ce babu aure a tsakaninsu, Anty Adiza kuma matar aure ce, ni kuma su kaWai ne mutanen da nasani, sai dai ko Bilkisu ita kuma aure ne ba ta so a yanzu. 



"Ni fa ina ganin can yaje danginsu ya nema, zai fi mana sau™i." 



Na faWa a fili kamar ina magana da wani ko wata, ko da ya dawo ma baiyi min maganar ba kuma nima bance komai ba, washe gari ma haka na yi ta faman tunani, sai gab da yamma na shirya naje gidan kitso wanda daman na tambayeshi, tun zuwana unguwar gidan kitson kawai nake zuwa shima sai na yi wata nawa banje ba. A hanya na yi ya kallon 'yan mata ko akwai wacce za ta da ce da Sardauna, amma bansamu ba. Haka a gidan kitson ina zaune ina kallon mutane sai hira suke, a Wauko gulmar waccan a sauke a Wauki ta waccan har layi yazo kaina ni dai ban tanka musu ba. 



"Baiwar Allah a wane gida kike?" 



Wata mata ta tambayeni. 



"Nan baya." 



"Ina ne baya ko ba anan kike ba?"



Wata daban ta yi tambayar.



"Eyh ina Takur Site C ne." 



"Eyh kam da dan nisa gaskiyya, amarya ce?" 



"A'a na shekara biyu." 



"Allah Sarki Allah Ya sanya alheri." 



"Amin." 



Na faWa daga nan ban sake ce musu komai ba har aka gama yi min na tashi na tafi, a raina na ce. 



"Ina fita zaku hau yi dani." 



Illai kuwa ko ™arasa fita ban yi ba na ji muryar wata ta ce. 



"Wai ita matan Takur sai wani shan ™amshi ake." 



Murmushi na yi na ™arasa ficewa ta, ba su san Wimbin damuwar dake damuna ba ne shi ya sa ma suke wannan zancen. 



Har na ™araso gidana ina kallon 'yan mata hanya sai dai Allah bai sa na ga wadda zata da ce da mijina ba, haka na dawo gida shiru. Nan dai na yanke shawarar tamnbayarshi na ji ko akwai wata yarinya da yake burgeshi haka, ko yake yawan ganinta. 



Banyi masa maganar adawowarsa ta farko ba, sai da ya dawo daga Majalisa sannan na ce. 



"Na yi tunani a iya matan da nasani, amma kafin nan kai babu wata yarinya da ka sani ko kake ganin tana da hankali." 



"Nana bayan ke bansan kowa ba."



"Ko a wajen aikinku, ko a family?"



"Nana bayan ke bansan kowa ba." 



"Ka na ji, ko a unguwarku da kuna ™anana?" 



"Nana unguwar da na taso ba irin Yalwawa ba ce, Unguwa ce da ba ruwan kowa da kowa, unguwa ce ta masu arzi™i babu talaka ko Waya a unguwar dan haka babu 'yar wanda nasani Nana, ba kamar ku ba cike da yara wani gidan na cin wani gidan, yara su shiga wancan gidan su fita wancan, mu duk ba haka muke ba."



A maganar sai na ji kamar gori, na yi mishi murmushin ya™e sannan na ce. 



"Ba haka nake nufi ba ranka ya daWe, irin ko a makaranta haka?" 



"Nana, zaki yi min ko bazaki yi ba? Idan bazaki yi ba just tell me, ba sai kina haWani da ™azamar rayuwa marar daraja ba, rayuwata ba irin wannan ba ce Nana. Ina ga har yanzu bakisan su waye Familyn mu ba Nana."



"Ka yi ha™uri, baka fahimce ni ba." 



"A'a ba wani ban fahimce ki ba Nana." 



"Ka yi ha™uri." 



Ta shi ya yi ya shige Waki ba tare da ya ce dani ko ™ala ba. 'Oh ni yau me yake damun Sardauna ne?.' Na tambayi kaina a zuci. 



Washe gari ma haka ya tashi yana faman cicin magani ko breakfast ma cewa ya yi wai ba zai ci ba. 



"Dan Allah me ya faru?" 



"Nana kinfi kowa sanin duk abinda ya faru."



"Bansan sani ba, bansan wani abu da ya faru wanda yasa ka canja baki Waya."



"Hhm! Nana sai na fito fili na faWa miki cewar ki nemo min aure?"



"Ai akan wannan maganar muke kai kuma ina kan dubawa." 



"Su wa kika duba?" 



"Duk cikin ™awayena kowacca ta yi aure." 



"Duka babu marar aure kenan?" 



"A na kusa dai babu, shi ya sa nake so kara faWa tunanina don bincikawa." 



"Nana yau ne fa ranar ta ™arshe da Hajiya ta bani." 



"Nasani kuma in sha Allah yau komai ™are." 



"Nana ki yi duk abinda kike tunanin zaki iya, dan Allah." 



"In sha Allah, to muje ka yi breakfast Win." 



Muka nufi dinning Win, muna cikin breakfast Win Sardauna ya ce. 



"Nana! Ko zan samu ki wanken kayana ko guda biyu ne, na ji daWin wancan da kika yi min." 



'Ashe Sardauna ya kula na yi masa wanki? Amma ko a ido bai taSa nuna min ba, ko da yake gashi yanzu ya faWa.' Murmushi na yi masa sannan na ce. 



"Babu damuwa, ko ban yi yau zanyi gobe."



"Me ya sa sai gobe."



"Idan ba mafita na samu akan wannan maganar ba bani da nutsuwar da zan iya yin wankin da zai burgeka ya yi maka kyau." 



"To shikenan, Allah Ya yi miki albarka Nanaty." 



"Amin amin." 



Tin fitar Sardauna nake tunanin inda za a sami mafitar ™arshe, kwatsam Bilkisu ta kirani a waya, bayan na Waga muka gaisa na ce da ita. 



"Ya Abban naku?" 



"Nana ya ™aramin one week Wazu, na ji daWi sosai wallahi Nana zan duba yanzu duk wanda yazo zan bashi fuska." 



"Ma sha Allah Bilkisu, Allah Ya kawo na gari."



"Amin Nana, na gode miki da nuna kulawa, zan je ofis mu yi magana anjima." 



Bayan ta kashe wayar kawai tunanin haWa ta da Sardauna ya faWomin. 



"Zaman Sardauna da Bilkisu zai yi Waya kuwa? Tsakanina da Bilkisu akwai fahimtar juna, akwai soyayya to amma Sardauna fa?" 



Legendspen

08129553971.

*SARTSE*

-Amanar-Janafty-

*Sayyid Legendspen*

MAH/2026/001



Sadaukarwa.



RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA

(Mai Dambu) 



Shafi na ashirin da biyu.

    (22)



 Sardauna baya son karatu? Bilkisu har aiki take yi, shin Bilkisu za ta iya barin aikinta sabida Sardauna, ko kuwa Sardauna zai iya ha™ura ta yi aiki, ya ce kuma yana da kishi ba zai iya jurar matan shi na yawo a titi ba suna cakuWuwa da maza, amma tabbas Bilkisu za ta dace da zamanmu a wannan ™adamin, tun da itama mahaifinta ya bata lokaci kamar yadda Hajiyar Sardauna da Big Daddy suka ba shi?  



 To Nana hakan ba matsala? Na ji wani Sari na zuciyata ya faWa a fili kamar wani daga wajene ya faWa.  Sardauna yana sona, kuma Bilkisu tana sa ilimi zata zauna da ni da Sardauna lafiya, ni bani da wata matsala indai Sardauna na nan kuma yana kallona a matsayin mata ina ™ar™ashen inuwar aurensa.  



Waya ta na Wauka na kira Bilkisu amma ba ta Wauka ba, ™ila bata ™arasa ofis ba sai kawai na tura mata text. 



 Bilkisu dan Allah ki kirani, akwai mafitar da nake tunani wacca za ta kawo ™arshen komai in sha Allah.  



Na tura mata tare da emoji na kuka da na ro™o, ina turawa na nemi lambar Yaya Rumaisa dan tabbas sai na sanar da wani nawa. Bugu Waya ta Wauka tare da faWin. 



 Manya yau a gari?



 Ina wuni Yaya?  



 Lafiya ™alau Nana, ya gidan?



 Alhamdullah Yaya, dan Allah wata magana zan faWa miki amma bana son Hajiya ko wani ya sani.  



 Wace magana ce haka Nana?  



 Ki yi min al™wari dan Allah.



 Nana ya za ayi na yi al™wari akan abinda bansani ba?



 Dan Allah ki yi min, ba wani abu ba ne na cutarwa kawai labari zan baki.



 Shikenan Nana na yi miki.  



Na sauke ajiyar zuciya sannan na ce. 



 Zan ™arawa Sardauna aure.  



 Bangane abinda kike nufi ba.  



 Yaya a gidansu aka bashi zaSi guda biyu, tun da ni bana haihuwa mahaifata ba ta gama ™wari ba ko ya sake ni su aura masa wata ko kuma ya ™ara aure.  



 Ke bana son rashin hankali, uban waye ya ce miki ba kya haihuwa?  



Ta faWa cikin jarababbiyar muryarta.



 Munje asibiti sabida na yi Sari har sau biyu, shine aka ce ba ta yi ™wari ba.  



 To da zai sake auren shine ke zaki ™ara masa?  



 Yaya ya bani zaSi ne akan na nema masa matar.  



 Wannan shine kuskure na biyu da zaki yi a rayuwarki da Sardauna, na farko kin zaSi miji sama da kowa, sai da ya raba ki da  yan uwanki da duk wasu mutane a kusa dake shine zai ™ara aure? Nana wai uban me kike sha?  



 Yaya Umarni ne daga gida, shi ya sa ma ya bani damar zaSa masa wadda zai aura.  



 Lallai Nana mahaukaciya ce ke? Dan mun yi al™warin bazamu sake shiga al amuran gidanki ba, amma dai sai na zo har gidan na ci ubanki na ci uban mijin, banza marar hankali wace yarinyar kika zaSa masa?  



 Wata ma™wafciyar mu ce.



 Jaka! Nana bansan ki lalace ba sai yanzu.  



Tana faWin haka ta katse kiranta, ni nama manta da halin faWa irin na ta har na kira ta, gashi ta zageni ta zage mijin nawa gaba Waya, ita daman bata da ha™uri ba abinda ta iya sai faWa a rayuwarta. 



 Mitcheww.  



Na ja tsaki na kwanta akan kujera, banda rainin hankali irin Yaya Rumaisa mutumin da baya son auren ™arshe ma yaban zaSi shine za ta ce wai ya rabani da kowa shine zai ™ara aure. Duk sai da na yi danasanin kiranta, daman ita ba a fiya yin abun arzi™i a kwashe duka da ita ba, haka na yi ta faman Sacin rai har yamma, yau indomie na yi wa Sardauna dan ba abinda zan iya sabida wani irin ciwon kai da na tashi dashi bayan na kwanta da yamma. 



Fuskarsa babu yabo babu fallasa haka ya shigo cikin gidan. 



 Sannu da zuwa. Bai amsa ba ya ajiye jakarsa, yanayin da nake ji ma bazan iya tashi na bishi ba, yanda ya shiga Wakin haka ya fito. 



 Baki da lafiya ne?  



 Jiri nake ji.



 Sannu, bama ki yi girki ba kenan?



 Na yi.



 Bari na ci.  



 Tom, akwai magana.  



 An samu?



Na gyaWa masa kai.



 FaWamin to.  



 Ka fara cin abincin.  



 A a faWan.  



Sai da na tashi zaune na ri™e hannunsa. 



 Kasan dai bazan zaSa ma abinda zai cutar da ka ba, dan Allah ina son ka amshi zaSin da na yi maka da hannu biyu biyu, kuma kasa a ranka alheri ce a garemu duka.



 Nana duk jikina ya yi sanyi, wace ki faWamin dan Allah.  



 Bilkisu! Wannan ™awar ta wa ta kake Wan ganinta.  



Shiru ya yi sai kuma can ya ce. 



 Wata fara haka?  



 Eyh ita.  



 Anya Nana?  



 Dan Allah karka ce a a.  



 Nana zan yi shawara.



 Tom, amma da matsala guda fa?  



 Kinji ko? Wace matsalal?  



 Tana aiki.  



 Wane kalal aiki kuma?  



 Aikin Ofis, kuma ka ce ba zaka iya jure ganin matarka na cakuWuwa da maza ba, shine nake so dan Allah ka yi ha™uri ka barta.  



 Nana sai na yi tunani gaskiyya, bari na ci abincin.  



Yana faWin haka ya tashi ya nufi dinning Win, da kanshi ya zuba ya ce kuma bai yi magana akan indomie Win ba, ko da yaga ban jindaWi ne? 



*********



Yau Sardauna bai fita majalisa ba, da na tambayeshi sai ya ce bani da lafiya dole ya yi jinyata kuma gashi yana son ya yi tunanin akan al amarin nan. Haka dai na yi bacci na barshi yana faman tunane tunane. 



Washe gari bayan munyi breakfast zai fita ya ce da ni.



 Nana na yi tunani duba da yanayin da muke ciki na matsi Hajiya da Big Daddy na amince zan barta ta yi aikin na ta, amma gaskiyya bana so.  



Har cikin raina na ji daWi. 



 Alhamdulillah, Allah Ya sa albarka, yanzu sai na yi mata magana nasan zata amince itama.  



 Wannan ya rage naki.  



Ya faWa yana ficewa, ni kuma na koma kan kujera na zauna, na Wau wayata na fara kiran lambar Bilkisu, amma bata Wauka ba, gashi message Win na jiya ma ba ta dawo da amsa ba. Sake kiranta na yi har ta gama ™arar ta ba ta Wauka ba, haka na ajiye wayar da tunanin an jima zan sake kiranta idan ba ta kirani ba. Har yamma ba ta kirani ba kuma nasake kira ba ta Wauka ba, na yi ta addu ar Allah Ya sa lafiya dai. Da ddaddare na faWawa Sardauna na ce ya bani wayarsa na kira ta sai ya ce na sake kiranta dai. Ina kira kuwa ta Wauka. 



 Nana ki yi ha™uri, yau na yi busy da yawa wallahi, ina ta ganin kiranki ban sami zama ba.



 Ayyah ba komai Bilkisu, ya gida ya aikin?  



 Alhamdullilah, ya mai gidan?



 Lafiya ™alau, na ce ya ake ciki da maganar Abban naku an da ce kuwa?  



 Tun da ya ™aramin sati Waya bamu sake maganar ba, kuma kamar naga sa™onki ko? Kince kin sami mafita?  



 Eyh Bilkisu na samu wacca nake ganin za ta yi amfani wa ni dake.  



 Nana ai matsalal mu ba ta da ala™a da juna.  



 Eyh Bilkisu sai dai kamanceceniya, Abbanku ya matsa miki, nima Hajiyar Sardauna ta matsa me zai hana Bilkisu mu haWu a rufawa juna asiri, ki auri Mijina.  



 Nana kina da hankali? Kinsan abinda kike faWa kuwa? Na auri mijinki Sardauna?  



 Is for the best Bilkisu Please.



 Nana bazan iya ba, a yadda kike son mijinki na shiga ciki? Ki rufan asiri Nana.  



 Bilkisu ke ce last hope Wina, aure na ma tangarWa yake ki taimaka.  



 Lallai Nana, dan Allah ina so ki a ranki bamu taSa wannan maganar ba dan Allah.  



Tana gama faWin haka ta kashe wayar, na kalli Sardauna da yake zaune yana sauroro. 



 Nana akawai wata bayan ita?  



Na girgiza kai sannan na ce. 



 Ita kaWai ce.  



 Nana to ya za ayi?  



 Ita Win dai, nasan za ta fahimta in sha Allah.  



 Nana banga alama ba, ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login