Showing 27001 words to 30000 words out of 104042 words

Chapter 10 - MASARAUTAR JORDAN

CHN   

30 Oct 2025

3182

isa asibitin. Ya samu ita da Natashah a cike ban. Bai damu ba ya zauna yana tambayar Natashah nuna jikinta, sai kauda kanta tayi tare da ja mishi tsuka.

Jikin shine ya kama rawa sabida ɓacin rai, ya mike zuwa gabanta ya mari baƙinta sai da ya fashe zai kuma Nannah ta dakatar dashi ta hanyar gaya mishi magana.
"Idan ka kuma tab'ata sai na gaya maka Maganar da zai habaka sukuni a rayuwar ka. Ita SAFINAH da muka zo ance banga lokacin da tayi maka tsaki bane sai yarinyar da ba ruwanta. Kuma wallahi baka isa aurenta ba matukar Ni na haifeka."


Kura mata ido yayi al'amarin uwa alamarine mai girma da daraja, dan haka ba zai taba yin dalilin da Safinah zatayi bakin jini a gurin Mahaifiyarshi.

Cikin shagwaɓa yace.
"Shi kenan amma Ni dai sai na dawo da Uwar yarana kuma ai kin fi kowa sanin baiwata ce, na yantatta, toh yanzun na dawo da ita matsayinta, tunda bazan aureta ba.".

"Wallahi ba zai yiwu ba! A baiwa ma kasamu damar makale mata missing Ammih kece mu koma Oman." Inji Natashah,

"Eh ai dole can zamu koma, tunda na fahimci wannan munafukai ta fara kawo mishi kanta, dan haka kaje ka shirya muku kayan ku Oman zamu wuccin." Inji Nannah

"Yawwa Ammih gwara ki gaya mishi muyi komawar can, kuma zan rike yaranta da amana ko Ammyn"
Ta fada a shagwaɓe, tare da kwanciya a jikin Nannah.
Aikuwa inda Nannah ke shiga ba nan take fita ba, shiru yayi yana jinsu suna zagin hasken rayuwar shi, bai ce mata kome ba, haka suka gama masifar su, yana kallon su.
Kallon daya yayi musu ya sake murmushin mugunta.
Iska yaja tare da fesarwa yace.
"Toh Ni zan tafi."

"Ammyn ina zashi, baki ji dazun iyayen wancan yarinya sun kiraki wai bata dawo ba."

Gabanshi ne ya fad'i ya duba agogon hannunshi,. Tara saura dan ko sallah isha suna shigowa asibitin yayi suka je masalaci sallah Isha.

Tsare Natashah yayi da idonsa, tura mishi baki tayi, abinda ya fahimta zuwan Nannah ya kuma sata fallewa da rashin kunya, cizon lips dinshi nayi cikin ɓacin rai.
"Da fatan ka mai da musu da ita gida dan naga kana shishige mata."
Had'iye yawu yayi cikin b'oye abin yace.
"Baki yarda dani bane."
Ya juya ya fita daga d'akin ya fita da sauri abinda bai wani saba dashi ba sauri.

Duk yadda yaso ya zo da wuri abin yaci tura, haka dai yaja motar yadda ya saba, har ya iso gidan.
Ina zaune na zabga tagumi da hannu biyu, hankalina yana kan agogon falon.

Yana shigowa na kauda kaina bansan ya aka yi kwalla suka shiga bin fuskana ba,

Yana zuwa ya durkusa a gabana tare da zuba min hannuwan shi kan cinyata, kuka ne ya kwace min tare da ture hannunshi ina shasheka.

D'ago Ni yayi tare da rungume ni, yana shafa bayana, sai da yaji ina ajiyar zuciya sannan ya janye Ni daga jikinshi muka fita daga gidan.

Gabana sai Fad'uwa yake dan bansan me zan fad'awa Ummi ba, da girma da babu saurayi gidansa, wannan abin da kunya yaƙe, da wani fuska zan kalli iyayena.
(Kuskure da yan mata suke kenan dubi samarika gida ayita abin da bai dace ba, kuma karku ga laifin Iyaye dan wallahi suna bakin ƙoƙarin su amma haka zaku ga yaran suna ha'intarsu Allah ya kyauta)

Duk ya rasa yadda zai dani, dan ya lura bani cikin nutsuwa balle nasan me zance masa kuka nake sosai.
"Toh kiyi hakuri mana!!!"
Yadda yayi maganar sai da ya kashe min jiki, kallon shi nayi dan ban taɓa jin kalmar hakuri a bakin shi ba, sai yau nice Ashraf yake iya bawa hakuri.

Share kwalla nayi kaina a sunkuye yake.
Gabana bai tsananta Fad'uwa ba sai da muka nufi hanyar unguwar mu, nan naku cikina ya cire guri guda dan dare yayi kusan goma da rabi, bansan me zancewa Ummi ba, dama Abba baya gari.
"Sauke Ni anan zan shiga da kaina."
Kallona yayi cikin damuwa ranshi a jagule yace.
"Ummu Marhus!"
A hankali na d'ago kaina ina kallon shi.

"Kiyi hakuri kinji" gyada mishi kai nayi, zan fita riko hannuna yayi yana cewa.
"Ko zamu shiga ne, na gayawa Ummi na saki kiyi min girki ne."
Zaro ido nayi cike da mamaki Ashraf bai da sense inji bature Ni zai bakowa teku, ya gayawa Ummi ina gidan shi ta tsine min sauran albarka........
[24/02 1:24 PM] My 2nd Mtn: *number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah......

13.
       Wani mugun kallo na wurgata mishi da nasan nazo gida ba, na fito daga motar shi tare da shigewa gida da sauri, kifa kanshin yayi akan motar yana sauke ajiyar zuciya. Shi yanzun bai san yazai da Ammyn shi ba.
      .......
A hankali nake takawa, ina tafiya a nutse dan har tsoron karan takura nake ji, hango haske a falon Ummi ya tsinkar min zuciya tabbas duk D'ana gari dole ya kiyaye batawa iyayenshi, duk sai naji kunyar kaina da kaina lokacin da na isa falo babu kowa, cire takalmin kafana nayi na fara tafiya a hankali har na samu na shiga dakina, turss nayi ina sosai goshina dan wacce nake gudun fadar ta ce nasamu tana zaune tana jirana. Duk sai kunya da tsoro ya kamani. Diriri cewa nayi cikin inda inda na fara magana. Dakatar dani tayi ta hanyar d'aga min hannu.
    "Na yarda da tarbiyya da nassmu daga iyayena SAFINAH, kuma na yarda da tarbiyya da nake bawa yarana da na kishiyoyina, sannan kece babba a cikin yaran gidan nan, kuma akanki aka fara samun matsala a gidan nan, SAFINAH bansan me zan miki ki fahimci kuskure da kike aikatawa ba, ban san yadda kika dauki kanki ba, Safinah abinda kike aikatawa ya fara jure tunanina, yanzun dan Allah kin min adalci. Tun karfe nawa kika bar gidan nan keda Gimbiya Asma'u, sannan baki tashi dawo min gida ba sai sha daya, gidan Uban waye kika tsaya? Sam kina shirin mai da kanki bola mara daraja da kima, wai me kike nima a duniya. Allah Ubangijin ya kawo miki sauki ya kuma shirya min ke da sauran yaran Al'umma musulmai baki daya, amma ki bi a hankali dan duk rana da kika shiga hannuna zan gwada miki iyakar ki, wawuya shashesha kawai "
    
   Tana gama fadar haka ta raba gefena tabar dakin zubewa nayi a gurin na fashe da kuka. Me cin rai da zuciya.
  
           Ina zaune a gurin har karfe sha biyu ina kuka, sai da naji idanuna na zafi na tashi na shiga ban daki nayi alola sannan na fito na fara gabatar da nafilla, Najima ina gabatar da kuka na ga Ubangiji na. Kafin na juya na kwanta.

       ***
Washi gari kuwa Ashraf sammako zuwa asibiti. Yana shiga ya dame su zaune sai shiryawa Nannah tsiya Natasha take. Dake yau ya tashi a basaraken shi ne sam baya son magana asalima, zama yayi tare da mikar da kafanshi sosai ya samu balance da kujerar.
        
   Shiru suka yi dan sun fahimci yau maganar ce ba yaso kuma bayajin a ranshi yayi magana.
Ko me zasu yi abu ɗaya yasani kuma idan suka takurashi toh dole ya fada.

Ganin haka Natashah da gigin ciki ke dibanta ta kalle shi sannan tace.
"Ka shirya mana kayan mu ne!?"
Kamar bada shi take ba, asalima, hankalinsa yana kan wayar, yana niman Safinah.
Ganin wayar taki shiga dan bai san ya suka kare da Umminta ba jiya, kuma ya kira layinta user busy, wato dai ta manna shi a bakar jadawalin blacklist.

Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya mike zai fita.
"Baka ji bane ka shirya muku kayan ku dan zamu wucce Oman ne."
Cak ya tsaya shi bai gaba shi baiyi baya ba.
"Na shirya amma jordan zan koma."
Yana fadar haka yasa kai ya fita, ya barsu cikin tashin hankali da firgice, dan maganar shi ya girgiza su.

.... Yana fita bai zame ko ina ba sai gidan su SAFINAH, horn yayi me kula da get din gidan, ya fito da yaga Ashraf ne sai ya koma yayi zamanshi.
Sake danna mishi horn yayi amma yaki buɗewa.

Sai da ya fita da kanshi ya buga get din, ya buɗe masa ta ƙaramin kofa ya shiga.
Cikin harshen turanci mutumin yace.
"Yallabai zaka iya tafiya dan dan Dr yace kar na kuma barinka shigo gidan nan."
Mamaki ne ya kama shi toh meye matsalar shi da Abdullahi, yaga dai ba wani rashin jituwa suka ba. Amma ya fahimci sam Abdullahi baya kaunarshi.
Hannunshi ya mai da cikin aljuhun wandonshi ya fidda yan dubu ya mika mishi.

Jikinshi na rawa ya amsa har da godiya, sannan ya shige cikin, bai bi takan godiyar da ake mishi ba ya shigo gidan, Ummi tana zaune hankalinta na kan tv.
Ina zaune a kujeran gefenta, kaina a sunkuye sai share kwalla nake, sam bai lura da Ummi bane ko menene ganin ina kuka kawai tsintar kanshi yayi da daburcewa, da sauri ya iso inda nake.
"Ummu Marhus! Make faruwa? Innalillah! Kar dai wani abu ne ya same ki"

Tashi Ummi tayi tabar falon safe goshina nayi cikin jin sabon kuka nace.
"Don ALLAH ka rabu dani, kaje Ni bana son ganinka."

Duk yadda yaso yayi min Magana fir naki kuma na bar mishi falon, dan bansan me Nannah ta gayawa Ummi ba, da safe nan Dudu yazo yayi ta min rashin kunya, har da cewa idan Ashraf ya kuma zuwa gidan nan yan sanda ne zasu rabasu.

Jiki a mace ya fito daga gidan, ya rasa inda zai cusa kanshi yaji dad'i meye Ammyn shi ta gayawa Iyayen SAFINAH yayi musu zafi haka.

Zama nayi a bakin gado na fashe Da kuka, sosai domin ji nake kaman zuciyata zata fashe, kome Nannah ta gayawa Ummi ban sani ba.
..... Itama Ummi tana shiga d'akinta, kwanciya tayi rigingine kalaman Nannah na dawo mata a kanta.
"Mariamah ki shiga tsakani Ashraf da SAFINAH! In ba haka ba Ni zan ɗauki tawa matakin, banda rashin tsoron Allah, ta kaso aurenta ta makalewa yaro karami ta nemi miji dai dai da ita mana, koda ta lika mishi yara mun amsa toh wannan karon kar tayi tunanin idan ta dubi Datti zamu amsa dan mu ba sakarkaru bane, dan haka tun wuri kika mata kunne ta bar min yarima tunkan nasa a baddata."

Lumshe idanu Ummi tayi sabida zafin maganar da Nannah tayi mata, ko ba komai ai SAFINAH bata cancanci haƙa daga Nannah ba, yau tana tare da D'anta ne sabida SAFINAH, kuma tayi Imani da Allah bata gayawa D'anta ya rabu da SAFINAH ba, ita kuma bazata taba gaya mishi haka ba, kuma bazata sauya mishi fuska ba, balle yayi tunanin akwai wata magana a kasa, Allah ya gani ita bata taɓa zaluntar abokin zama ba, amma sai gashi Sabida SAFINAH tana biyar bashin da bata ci ba, abinda bai faru ba a shekarun baya ba shine yake faru da ita a wannan shekaru.

....
Asibiti ya koma yaje ya samu Nannah tafita Natashah na crush candy, fauce wayar yayi tare da shake wuyarta yace.
"Me kuka gaya musu!?"
Zaro ido tayi cikin kaduwa, take cewa.
"Wallahi Ammyn ce tace musu."
Rintsa idanunshi yayi tare da ture ta, jikinshi na rawa. Tabbas Ammyn bata kyauta mishi ba.
Saka yayi ya fita. Zuciyar shi kamar ta fado kasa, dan bakin ciki da ɓacin rai.


Wayarshi ya danna ya kuma kara a kunne yana cewar.
"Ka sama min gurin aikin."

Kome aka ce mishi kawai ya kashe kiran, ranshi na kara ɓaci.
.......

Koda Nannah ta dawo kuka Natasha tasa mata tana gaya mata, abinda Ashraf yayi mata hakuri ta bata, sannan tace zata gamu dashi.
🤔🙄 Ashraf ɗin....
***
Bayan barin shi asibiti sai ga Ghaniyu da Fahad, suka saka su Nannah a gaba har Airport, duk yadda taso ganin shi amma ba hali shi kuma yana airport ɗin kawai gurin sune yaki zuwa, yana zaune har jirgin Oman ya tashi,
Sannan suka koma tun da ya kwanta a jikin kujera bai kuma cewa kome ba.

Gurin aikin da aka nima mishi suka kai shi, gini ne na wata ma'aikata, fita yayi cikin motar da wasu kaya, yana zuwa suka gaisa da wanda yake lura da gurin sannan ya gabatar da kanshi a matsayin sabon lebura.
Nuna mishi aikin yayi yace.
"Yanzun dai ka dawo gobe sai mu fara da kai yau mutane sha biyar ake nima, sannan na gayawa yan uwanka kazo da wuri."
Mika hannunsa yayi sukayi musabaha, sannan ya koma mota.
***
Ina durkusa gaban Ummi ina kuka tare da mata alkawarin bazan kuma ba.
"Toh SAFINAH! Kefa ba yarinya bace! Sannan ban san meye haɗin ki da Yaron nan Ashraf ba, Mahaifiyar shi tace bata sonki, nima kuma naga dacewar haka don Allah ki bar sani Cikin damuwa kece zaki lakato karshe Ni ce zan biya laifinki don Allah ki min adalci nima nasamu yancin."

Gyada kai kawai nayi ina kuka dan gaskiya Ummi ta faɗa duk laifina ita ke dauka kuma nayi alkawarin bazan kuma yin abinda zai bata mata rai ba, tunda bai zama dole ba taya kenan!? Dole sai na rabu da Ashraf.
Wani irin bugawa kirjina yayi sai dana dafe kirjina. Sakamakon tuna ta yadda zan rabu da Ashraf.
Ba sauki! Toh me haka ke nufi.

★★★
Nannah sun sauka lafiya ita da Natashah, tunda suka koma ta shiga narkewa,ita tana da ciki karku manta ciki fa da ita, toh ba karamin bidiri akayi ba, dan Uwarta har da tambayar shin meye shene abin cikin.

(🙄🤔 Ni kuwa nace Katon baby boy 🤣😂)

Tun yana sati shida ake son sanin magajin jordan ko yaya.
Nan aka bazaka bin Asibiti dan a gano me take dauke dashi.

★★★
Yau kwanaki biyar da ya fara aikin gina, idan ka ganshi a cikin rana sai ya baka tausayi, ga rashin sabo da wahala. Duk yadda Fahad da Ghaniyu suka so hana shi fir yaki,gashi kuma baki buɗe shi.


Rayuwa ya cigaba da garamu, Ni ina ce ina fama da fushin da Ummi take dani shima yana can yana fama da daukar kasa da siminti.

Idan ya koma gida jikinshi yayi ta ciwo duk ya rasa inda zai kai gajiyar shi ya huta.

Dan ma yana cin abinci me kyau, amma ya dishe domin rana bata barshi haka ba, kullum sai yazo amma fir ake hana shi shiga, sosai ya shiga damuwa.

Koda yake ana biyansu kudi me kyau dan akala duk aiki na suka yi ana biyansu nera dubu uku da ɗari biyar.

Wani lokaci yakan hana su Ghaniyu zuwa daukar shi.
A sannu ya fara fahimtar yadda mutane suke rayuwar kunci da niman abinda zasu saka abakin salati.
Wani abin da ya kara bashi mamaki wasu a gurin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login