Showing 69001 words to 72000 words out of 104042 words

Chapter 24 - MASARAUTAR JORDAN

CHN   

30 Oct 2025

3197

zagaye masarautar, kafin ya zana wani d'an abu haka

Bilal
|
/ \
Ukshe Malika
| |
Raziyana=Alexander
Abeel^ ^Zoya

Mannah^Hinduh
|
Azrah
*SAFINAH*
<>
|
Natashah^Rania
[ASHRAF]
"Dukkan su, zasu yiwa Bilal aikine!?"
"Ta yake nan Sultan!?" Inji,
Fahad,

"Kuma haka ne!? Nima dai zanyi mamaki taya zasu yi mishi aiki." Cewar Ghaniyu,

Tafi yayi sannan yace.
"Bari na koma daga sama, na ciro muku yadda aikin zai kasance,"
Ajiye alli ya kuma a karo na biyu, sannan ya sake murmushin jin dad'i yace.
"Sannan idan aka fara wasan yan wasansu kaina zata kare, sai dai zuwa kaina ne wasan zata zama wasan mutuwa ko rayuwa, a wannan gabbar zasu iya amfani da kowa dan cimma nasara, a cikin kuwa har da mutanen da bana fatar wani abu ya shafe su.(SAFINAH-Ammyna)"

Gyara zama Ghaniyu yayi cikin nutsuwa sannan yace.
"Sultan! Taya kasan haka!?"
Zuba musu ido yayi cikin nazarin abinda zai gaya mishi sannan yace.
"Yanzun dai kaje ka nima min menene raunin Bilal."

Dariya Fahad yayi, ganin irin kallon da suke mishi yace.
"Afuwa! Ranka shi dad'e! Ai a cikin kwana biyu da shigowar mu na gudanar da wannan bincike, abinda na samu me sauki ne, ga sha-sha-sha irinsa, rauninsa na farko mashayi ne!? Sai na biyu bai yarda da kowa ba sai Mahaifiyarshi!? Bayan haka bai da damuwa a kan mace."

Gyad'a kai yayi sannan yace.
" Ku koma dai! Zaka samu dan sun san yadda zasu nimo rauninsa, toh nima ina son na sami nasu raunin kafin lokaci ya kure."
"Sultan! Amma naga shan giya ai yana cikin Abinda yake, kuma."

"Bazamu iya ritsa shi ta giya ba!? Ku dai duba meye raunin sa"
Yace musu,

"Idan muka kirkiro matsala da Mahaifiyarshi fa, muka jefa mishi rashin yarda da ita fa."

Murmushi yayi wanda ya bayyana hakorinshi.

"Bayahudiya ce! Tana da fikra da ilimi."

Shiru suka yi duk suka rasa tacewa.
Shigowar wata budurwa da yake musu girki me suna Sanda, yarinyar! Ruwa biyu ce. Mahaifiyarta yar kasan islamabad ce ta yanki Pakistan, mahaifinta, balarabe nan yanki jordan. Sandia tana da wani irin kyau irin kyau me sanyin wanda sai ka nutsu zaka fahimci haka, kalar fatarta ja ne, sannan gashinta nakine har gadon baya, Yarinyar tashin kasar Hungry ce, wayayya ce, sannan tana jin Yaren latin american, wato Argentina. Sannan tana jin English sosai. Karfin zuwanta gurin Fahad dan tana masifar don shi, kamar tayi hauka.

Binta Ashraf yayi da ido har ta wucce kitchen, zuwa yayi gaban allon ya dauki Chuck ya rubuta a kasa.
My Mission
Sandia.......

Kuyi hakuri don Allah.... Wallahi abubuwan sun min yawa sosai, Insha Allah gobe zan goge laifina, nima kaina page d'aya damuna yake balle ku da lalataku da pages biyu 😹🤫🤭🤗
[16/03 10:43 PM] My 2nd Mtn: number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah

3️⃣2️⃣

Mik'ewa Fahad yayi jikinshi na rawa.
"Sultan! Sandia kuma!?"
     
Kallon shi Ashraf yayi cikin rashin damuwa, sannan yace.
"Abinda nace za a yi ko wanda kace?"

          Shiru yayi kanshi a sunkuye, ya rasa ta yadda zai kare kanshi, takowa Ashraf yayi gaban shi. Ya hannun hard'e a kirjinshi,  cire hannun yayi. Tare da kallon yadda ya diririce.
     Jan kujera yayi ya zauna, tare da Crossing leg.
"Idan taka ko Safinah zata iya rasa rayuwarta! Ammyna ma haka! Dan haka karka kuskura kace zaka shiga wancan zanen Kaddara dan ko Mahaifiyata da Mata ta suka shiga ciki wallahi bazan fasa."

Mik'ewa yayi cikin kasaita ya isa gaban Fahad, ya cigaba da cewa.
"Idan nace ayi abu, baya nufin ban san me nake yi bane, idan na dubi abu nasan dalilin yin haka, wannan ya zama kuskure na farko daka aikata Cikin manta waye Ni!"

    Sunkuyar da kaina yayi cikin kaskantar da kai yace.
"Afuwa"
     
    Share shi yayi bai kuma bin takanshi ba, ya shiga d'akin shi. Ya saka wasu kaya irinta larabawan kauye, sannan ya rufe fuskarshi da hirami. Ya rage idanunshi kadai zaka iya hangowa, sannan ya fito daga d'akin. Yana kallonsu sannan yace.
"Ghaniyu zan shiga cikin garin Amaan. Ku tabbatar da kunemo min abinda nake buƙata."

     "Amma Sultan da kanka"
Kunce d'aurin fuskar shi yayi, ya tsare su da ido. Murmushi ya sake wanda ya bayyana dimple point d'in shi.
"Kowa da aikinsa, nima da nawa aikin, karku manta Ghaniyu ka tsaya da Sandia Fahad."

...... Fita yayi daga gidan yana me rufe fuskarshi, bayan fitar shi ne Fahad ya juya ga Ghaniyu cikin damuwa yace.
"Ina tsoro kar Y'ar mutane ta shiga damuwa sabida ni, ya zanyi Sultan ya fahimce ni.!"

Dafashi Ghaniyu yayi cikin rarrashi yace.
"Babu abinda zai faru da Ita, ban san dalilin da yasa zai amfani da Sandia ba, amma nasan bazai tab'a bari a cutar da ita ba."

Ture hannun Ghaniyu yayi ran shi a b'ace yace.
"Baka san ciwon akan abinda ranka keso ba! Shi yasa."

Duk yadda Ghaniyu yaso fahimtar dashi yak'i bashi hadin kai karshe haka ya fita, shi kuma Ghaniyu ya tsaya sai da ta gama girkin sannan ya rakata gida, yaso mata bayani amma ya Kyaleta.
........ Cikin masarautar Fahad ya shiga, da shigar shi Irin tsofi, tare da sandar shi yana dogarawa.

Duk yadda yaso shiga cikin gidan sarautar hana shi akayi dole ya hakura.

......
"Mu'awiyah! Kana tsammani inda mulkin adalci ake a cikin masarautar a kara mana haraji, sannan kana tirjewa kashe ka zasu yi, shi yasa ana zuwa amsar kud'in nake saurin bayarwa kodan tsira da rayuwata da ta Iyalina."

Wanda aka kira da Mu'awiya ya kalli, mutumin da yake maganar ya mik'e tare da nufar cikin shafin sa, ya ɗauki abinda zai ɗauka ya fito ya cigaba da cewa.
"Tun bayan shugabanci Sultan Abdullahi, da aka rage mana kashi sittin na harajin"

Yana jin su, yasa kai ya wuce, ba tare da yace komai ba. Bai zame ko ina ba sai, Ofishin yan kasuwa.
Juyawa yayi ya fita. Daga nan gida ya komo, computer ya d'auko ya fara tura e-mail.

Kara wayar shi tayi, a hankali shi nakan computer, ya swipe wayar.
"Ka manta damu! Yau baka kiramu ba, Ni da yara muna kewar ka. Yaushe zaka zo?"
A sanyayye na tambaye shi,
"Beb! Ina wani aiki ne, idan na gama zan zo da kaina kinji."

"A'ah Ashu! Nikam sai kagan mu kawai."
"Karki fara zuwa."
"Allah kasa ido zaka ganmu."

Kafin yace wani abu na datse kiran. Dukar table d'in yayi da karfi, sai da komai na table d'in ha watse. Hucci yake kamar yaci babu.
Kiran Ummi yayi wayar tana cikin user busy, layin Abba ya kira. Yana ɗauka sai ya kasa cewa komai.
"Hmm! Dama nakiraka ne mugaisa."

"Toh! Madalla, nazata."
"A'ah! Abba su zauna har sai nazo."
"Toh shi kenan."

Murmushi yayi tare da cewa.
"Sai naga ta yadda zaki zo, me shegen jin magana."

★★★
Nigeria....
Ajiye wayar nayi ina kwafa nace.
"Dole ma ina gama wanka nazo gareka, ko wata uwar yake a can, ina cewa idan ya ganni kamar ya cinye ni d'anye yanzun ina ce masa zan zo ya hau masifa zuwa zan yi, naga abinda yake yi a can."
Haka nayita mita, Ni d'aya ta, har Ummi tashigo ta same Ni ina cika ina batsewa, tace.
"Lafiya irin wannan fushin!?"
Kamar wacce aka min abin arziki na shiga hura hancina,(🤣 kai kace Saniyar hud'a,)
Sake hura hancina nayi kamar wacce take ganin Ashraf d'in, nace.
"Ummi waye banda Babansu Ablah."
Na karshe maganar ina tura bakina gaba.
Murmushi tayi cikin jin dad'i sannan tace.
"SAFINAH! Hanyar da kika dauka ba me bullewa bane, sam bazai kai ku ga yin nasara ba sai Fad'uwa, kuma ba komai yaja haka ba, sai bayyanawa soyayyarku a idanun duniya. Ban ce karki kula da mijinki ba, amma maganar gaskiya ki koyi b'oye son shi, dan kodan soyayyarku za a cutar dake."

Kallonta nayi ina mamakin ta nace.
"Ummi! Amma naga bawani abu muke yi ba! Kawai kulawa ce."

"Safinah! Duk yadda kuke son juna, dole ki dinga sakaya shi, lallai kuwa baki san inda zaki bane, ko kin manta cikin larabawa zaki shiga, idan kin manta ki tuna. Zasu iya amfani da wannan soyayyar su cutar dake, ba iyake ba hatta shi da yake Shugaban, ki nutsu da hankalinki guri guda, domin kuwa akan haka zaki iya shiga tsaka me wuya, ina gaya miki gaskiya a matsayin abokiyar shawarar kice ba a matsayin Uwa ba, idan baki koyi b'oye so ba. Tabbas zasu raunana zuciyarki, daga haka sai tsana da fushi, daga karshe ya gaji yace ki dawo gida."
Da sauri na d'ago kaina, dukda ban fad'i.
"Eh mana! Safinah idan ASHRAF! Yarone kefa? Tun lokacin bai kure miki ba, yaki soyayyarku domin zata iya zame muku guba, wacce zata iya haifar muku da tashin hankali."

Hmm idan nace na fahimci bayanin Ummina wallahi nayi karya, dan abinda zuciyata ke hararo min taya Ashraf zai juya min baya, mutumin da muke kaunar juna kamar mu dafa kanmu mucinye, tsabar so. Dan haka tana magana ta kunne dama Allah yana fita ta kunne hagu, tana gama fad'arta tafi.

Bawai banji fad'arta bane abinda ta faɗa ne bana tunanin zai tab'a faruwa, taya mutumin da muke masifar son juna za ace, zai juya min baya. Taya haka zai faru? Ni ban hango haka a tunani na ba, dan haka zai dai rage abinda nake tunanin zan iya amma ban da So, wallahi bazan Iya daina son Ashraf ba, dan shine mahad'in rayuwata, wato ina kafa hujja ne akan ya zauna dani, tunda Mahaifiyarshi bata kaunata. Dan haka bana jin akwai wadda ya isa had'a mana husuma.

A sannu kwanakinmu suka yi ta, karewa burinmu nakara hauhawa! Kalubale na kuma Kunno mana kai, dan yau kwana biyar da Iyayena Anim suka zo, ana nimanshi kusan sheka uku kenan babu shi babu labarin shi.

Anan ne naji abinda yasani kuka, domin anje inda gawarshi take, an samu lafiya kalau, sabida karfin tsafin da suka mishi. Karshe Malam baban Shabhan, shi aka nimo yazo ya fidda shi.

Aka tafi da gawar aka sallace Bayan anyi mishi sutura.

Na tausayawa Matar shi, sabida shiga damuwa na dogon lokaci, kwalbar da wancan fatalwar take ciki an jefata a ruwa, shikenan babin Anim ya shafe kenan.

★★★
Oman....
Alhamdulillah..
Jikin Natashah yayi sauki, sai ma wani sabon alwashin tsige SAFINAH da take shirin yi, idan suka haɗu. Dan ta rantse sai taga bayan SAFINAH, ita a yanzun bata ta Nannah, tafi mai da hankalinta akan SAFINAH.

Sun gama kula tsiyar su, ta fito daga d'akin Mamanta ta nufi bangaren Nannah. Tana zuwa ta sameta a falo zama tayi a kujeran kusada ita. Sannan ta narkewa Nannah, kamar zata shige mata jiki, ita kuwa Nannah a tsorace take da Natashah dan bata manta shaƙar da ta mata ba.
"Ammyn! Ki kira Ashraf ki tambaye shi yaushe zan koma tunda na warke sumul."

Cikin tsoron da take ƙoƙarin b'oyewa tace.
"Ai... Nima toh kije zan nimo shi"
Tana gaya mata tare da barin falon, sabida tsaro(😎🤣😂Saura naji magana ya biyo baya dan nasan sarai sai kuce Nannah ta ji tsoron ta gudu.)

Kafin Natashah ta kuma wurgo mata tambaya tuni rawa kofar d'akinta, key (🤣) ajiyar zuciya ta sauke cikin muzurai, hannunta dafe da kirjinta tace.
"Muguwa tazo sake min wani muguntar shine zata dake da Ashraf ta cuce ni ai tsakaninmu zira'i saba'in, yar banza me kama da aljanun."(🙆🏽‍♀️Na shiga uku Ni Uwar Mutane 😂🤣) tabbas Nannah taga Idi a hannun Natashah, shi yasa har da kwashe mata albashi me lawashi banda haka.

Kwafa tayi ƙamar zata iya zane Natashah, amma ba hali ta gama bala'inta ita kad'ai. Buga kofar Natashah tayi, ai da gudu Nannah ta shige ban d'aki tsabar tsoro ma hayewa kan abin bayan gidan tayi, tana me Makurewa a jikin wall din ban d'akin.
Kuma buga kofar Natashah tayi amma fir Nannah taki fitowa,(😂🤣🙆🏽‍♀️🤭 Yau Nannah takai karshe)

Duk yadda Natasha taso Nannah ta buɗe kofar taki, karshe haka ta bar part tana mamakin sauyin Nannah.

Nannah kuwa bata fito ba sai da tabbatar Natashah tabar part din sannan tafito tare da rufe gidan.

★★★
Jordan.....

"Sultan! Yanzun wata biyu kenan da zuwan mu jordan har yanzun babu nasara!"inji Fahad,

Kanshi na nutsuwar shi yana ga Computer gabanshi, gabaki d'aya ya sallama ruhin shi ga abinda yake yi.

"Ghani! Please coffee"
Mikewa Ghaniyu yayi zuwa kitchen can sai gashi da mug me dauke da ruwan coffee, ya ajiye mishi sannan ya koma inda yake, kurb'a yayi, tare da lumshe idanunshi. Sannan ya bud'e a hankali yace.
"Ina aikin da na baka na nima min raunin shi!?"
Shiru Fahad yayi kanshi a sunkuye sannan, ya d'ago kanshi ya kalle shi a karo na biyu yace.
"Baka bani amsa ba!?"

D'ago kanshi cikin damuwa yace.
"Sultan ban same rauninsa ba"

"Babu ne ko baka samu ne!?"
Ya datse masa tunanin da ya fad'a.
"Sultan! Ni ban san taya zan samu bane, sunki barina shiga masarautar."

Ya fad'a a sanyayye, murmushi Ashraf yayi sannan ya mik'e tare da isa gurin allon nan ya ɗauki, alli ya rubuta *Fahad kaji kunya,*
Sunkuyar da kai sukayi sannan Ashraf ya jingina da kujeran, shafa kanshi yayi cikin matsanancin damuwa ya cigaba da yatsuna gashin kanshi, yana damkewa. Sannan yace....


*Kuyi hakuri Wallahi Muwaddah ce ba lafiya*
[16/03 10:44 PM] My 2nd Mtn: number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah

3️⃣3️⃣

     "Ina binku dan ku nima mana mafita, amma kun gaza fahimtar haka. Idan nayi magana kuga kamar nafison kaina da ku, idan ta nine bazan damu na dawo k'asa ba, kune kuke da wutar fansa a ranki."
  
    "Afuwa Sultan."
   Bai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login