Showing 96001 words to 99000 words out of 104042 words

Chapter 33 - MASARAUTAR JORDAN

CHN   

30 Oct 2025

3164

tana jiranka."

"Maryam Zo kije can shashin ki buga kofar karki shiga, sai an baki izni, sannan Kiyi musu sallama, ki kaiwa Appanku kice ya duba kan wayar inji Ni."

Gyad'a min kai tayi tafita da sauri. Ihun ta naji tana kara kamar ranta zai fita. Natashah da take can tana shiryawa ta rigani fitowa. Ina isa na sameta ta saki fitsari a jikinta, sai rawa yaƙe, ta kasa cigaba da kuka.

"Ashraf!!!"
Na kira sunan shi a haukace, tare da dukar kofar, buɗe kofar da yayi da sauri ya fito jikinshi duk kumfa, daga shi sai towel. Yasa yarinyar zub'ewa na gabanshi ragwab, Natashah zata kai hannun na riƙe ta, sai lokacin Zoyah ta fito rike da wayar shi a hannunta, bansan me yasa duk abinda zaka min zan iya jurewa amma banda tab'a min Yarana. Mai dashi gefe nayi, bayan ya dauki Yarinyar, naje gaban Zoyah na tsinke mata mari, sai da wayar ya kwace, na kuma tsinke mata wani marin, sannan na riko gashinta, nace.
"Wallahi kika kuskura aka ce min ta Karye, Allah sai na shayar dake mamaki dan karyaki zanyi, muguwar banza kawai."

Juyawa nayi na kalle shi, sannan na amshi yar, na sakata a kafad'ana, riko shi nayi har shashin Natashah na kai shi, sannan na fito.

Tana tsaye rike da kumatun ta, harara na watsa mata, sannan na wucce da y'ata, ina sauya kayana ya shigo.

Bai ce min komai ba ya fita da yarinyar, nima dake ina jin haushinsa ban ko kalle shi ba.

_Na fahimci wasun ku basu san yakana ba, Pages biyu nake baku idan na bada d'aya Uzuri ne ya riƙe Ni, amma baki fahimci haka ba🤦🏾‍♀️ jiya da na baku Page 44 sai da na baku hakuri amma hallau wasu na tambayata 45 da dare fa, wallahi abin bani mamaki karfe goman zan muku typing? Ko yaushe?! Ki ji a ranki ke Marubuciya ce, kina da miji da yara, ki kalle abin a kanki mana kiji, wallahi a duk lokacin da zan saka buk din kudi abinda nake fara karo dashi shine na sauke nauyin ku dake kaina, na huta, da yawanku sunan ban tab'a jan labari haka ba, sabida bana dogon labari idan naja labari 56, yar yadiko 46' da ciwon a rsyuwata 58, matar malam 59 toh da sauran books dina bans rike labari duka duka labarin MJ pages 105 ne. A cikin kwana arba'in da uku, Ni bana son haka, duk wacce ta gaji ko take sauri tayi min magana na mai da mata kuɗin ta marubuta yan kasuwa suna dayawa, sabida ranki ke ɗaya bazan batawa Nawa Iyalin ba Please muyiwa juna Adalci. Idan nayi kuskure kuyi hakuri_🙏🏻👏🏼





[20/03 2:30 PM] My 2nd Mtn: number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Masha Allah*

4️⃣6️⃣
Tun da suka dawo da yarinyar, naga yadda aka daure shi da bandaji, naji zuciyata na ta fasa mik'ewa nayi zan fita dawo dani yayi tare da zaunar dani cikin b'acin rai yace.
"Wallahi kika kuma dukar musu Y'a har gidan nan zasu zo su miki mugun duka, kuma babu abinda ya dame ni, dan su ƙabilar su suna da had'in kai."
Yadda ya gama maganar cikin zolaya, na kwace hannuna na fita zuwa gurin Natashah. Har na fita na kuma dawowa.
    "Wallahi sai na rama mata abinda tayi mata ka ajiye maganar, matukar ina gidan nan sai itama an daurata."

        Gyada kai yake kamar kadangare, bowl d'in da na yanka kankana da Grape, mutumin ku, ya shanye tass dake na zuba madara da zuma, sai da ya gama shanyewa sannan ya ce min.
"Hmm dazun kina magana me kika ce ma?!"

   Abinda Ya faru lokacin da Aamih ta kaiwa Baban su Waya, koda ta isa kofar buga kofar tayi tare da sallama, tana kiran Babanta, dake ya shiga wanka. Zoyah ce taji buga kofar, tana fitowa ta kalleta bayan ta zaro mata ido tace.
"Me ya kawo ki?! Da zaki dame mutane da buga kofa."

Dake tana tsoronta jikinta na rawa ta mika mata wayar tace.
"Appa na kawo mishi jin Ummuna wai ya duba."

  Nuna mata ciki tayi ita kuma ta rab'a ta shige, bata gan shi ba shine ta ajiye tazo fita, har ta fita da ta kuma kiranta, ta kamo hannunta ta tare da rufe mata kofa akan yatsunta, ta kuma tayi maza ta shige d'akinta kamar bata san komai ba.

       Shigewa nayi na barshi a gurin, amma naji ciwon abinda Zoyah tawa Mariamah koda nayi magana cewa yayi zan fara taurin kaina kenan, shi yasa nayi shiru ban ce mata komai ba, sai dai na hana Aanih fita gabaki d'aya saboda itama na lura bata kaunar Mariamah, abin ya bani mamaki yadda ko zama muci abinci yarinyar bata yarda ya zauna kusa damu. Dan haka ban dauki alamarin da wani muhimmin ba, tunda nasan basa shiri da juna.

            ...
     Kwanan mu biyar da dawowa su Nah suka dawo, ita da Ablah da Zakiya. Yarinyar tayi wayo abinta, dake itama bata da hasken fata, amma bata kai Aamih ba. Toh har ita Ablah bata bari ta tab'ata idan kuwa tab'a ta, zata shiga bayi tayita wanke gurin, kamar wacce ciwo ya tab'a ta, a hankali ta fara tsantsar yan uwan, da zaran ina kitchen zata hanasu tab'a komai na falo ko daki tana gani na zata koma kamar ba ita ba.

       Ban a sannu sai Ablah ta shiga jin tsoron ta, da zaran ta ga Aanih zata shiga niman b'oya. A nan na fara lura da takurawa da Aamih take na yawan zama ita d'aya ko kuma ta biyo NI kitchen,  Husnah itace amma lokaci d'aya na shiga tambayar kaina a ina ta dauko mugun hali, dan nasan daga Ni har Ashraf bamu da wannan dabi'ar, sai da na fahimci baya nan, na kama kamar zaneta nace.
"Maza gaya min meye yan uwanki suka miki haka da baki son su."
  
Ruwa idanunta ya kawo cikin tsoro tace.
"Ummuna! Su basu da kyau Ni nafi su kyau shine, Ummu Zoyah tace kar na zauna dasu zasu goga min baƙi, ni ki mai dani gurin Ummu Zoyah, tana sona."

"Wallahi sai dai ki mutu baki zuwa gurin wata banza naga kafarki a gurin kafin Ummunku ta dake ki nice zan fara miki duka, da manyan idanunta nan kamar na Habibi."

       Wato da manyan idanu kamar na Ashraf,(😂🙄 keda shi)

          ★★★
Tun daga ranar da Nannah ta dawo, gidan mu ya rikid'e, a hankali Nannah ta shiga jin haushin mu, da zaran yana dakin Natashah tayita nishi da tari, dasu haki dasu wani irinsa na numfashi, kamar me cutar Asthma, kar kuce Natasha ka dai ce a'a har dani ai nawa yafi muni, domin da zaran ya shigo gurina ajima kad'an ta turo a kirashi, idan yaje sai yafi awa biyu sannan ya dawo, bayan kamar minti arba'in zata kuma kiran shi, idan yaje sai yafi kusan awa uku, wasa gaske sai kiran asalatu ke fidda shi, daga shashinta, abin tausayi ya fito yayita hamma, dake kwana d'aya d'aya yake mana.

        Dan haka girki ya dira kan Zoyah.

      Na fito ina karkad'a jina nayi tsifar kitso hud'u da nakewa kaina, kallon gashin tayi yadda ya sauka kamar yadda nata yake, har yafi nata ma da cika.

     Wucce Ni tayi abinta bata ce min kala ba, nima kuma ban d'ago nasan tana gurin ba, dan Ni banda Natashah da Yarana Ni bana surutu, idan kaji surutuna da dariyana, Ashraf ya sani a gaba da wasan, banza nan kan ko kana daga waje zaka ji dariyata.

      Falon Nannah ta shiga ta zauna, tashi zaune Nannah tayi. Sannan Zoyah tace mata.
"Ni ban damu dake kin nan ki baki nan! Ni abinda nasani kin haifi d'an kuma ina auren shi, naga abinda kikawa Yar d'an uwanki balle kuma wacce ta sadaukar da Rayuwarta domin ki, wallahi kika kuskura mijina yazo d'akina kika min wannan tsiyar da kika musu, wallahi."

    Mik'ewa tayi tazo dai dai fuskar Nannah sannan tayi mata magana kasa kasa.
"Tabbas zan baki kyauta na musamman."

Murmushi Nannah tayi sannan tace.
"Ban haifawa kowacce a cikin ku d'an ba, dan haka kome zaki yi ki yi bazan fasa ba."

"Lallai zaki sha mamaki, daga kaina baki kuma tab'a wata."

       Sam abin ba dad'i tsakanin Nannah da Zoyah, dan kowanne su  ya tsaya akan maganar shi, ina muka san budirin da suke,har akaci aka cinye

    ..,.......  Yau da ya dawo dama yanka tsaya a gurinta su fara gaisawa, sannan yabi kanmu sannan ya wucce d'akin me girki, sai gashi ta rike shi, aka shiga bashi labarin Bara taci wanke, gashi yau a matsa yake da lalura. Wasa wasa, Nannah bata bar Ashraf ba. Sai karfe biyu saura shima zuwa Zoyah yasa ta hakura ta bar shi, cikin idanunta Zoyah ta kalla sannan ta nuna mata wani alama da hannun.

Nah bata bu takanta ba, ita ba dai ta kuntattawa Zoyah ba, burinta ya cika,

Suna shiga zoyah ta sha gaban shi dan a gajiye yake zai kwantar.
"Sultan meye Mahaifiyarka take nufi ne damu?! Taci lokacin ta akan me take shiga hakkinmu, don Allah duba karfe nawa ka shigo biyun dare wannan wata irin Uwa ce mata adalci?! Toh wallahi an gama idan ta kuma zan kai ta kara gurin iyayena."

Mika mata hannu yayi sannan sannan yace..
"Kiyi hakuri?! Zo mu kwanta,"
Fir taki yarda karshe ma, kunna wutar rikici suka yi sosai, abinda ya masifar daga mishi hankali kenan, duk rigimar SAFINAH bata tab'a hanashi barci yau gashi Sabida Ammyn yau Zoyah ta hana shi barci, dake yasan tafishi gaskiya bai ja al'amarin ba, sai ma Kyaleta da yayi tayita masifa har goshin Asuba.

Mu dai muna cikin damuwa dan wallahi Nah ta hanamu mijinmu, shi kuma ya ki fahimtar abinda Mahaifiyarshi take aikata mana, sai na kudiri aniya a raina zan mishi tsiya, dan ma Allah ya taimaka cikin jikina babu laulayi shi yasa babu wanda yasan ina da ajiyar shi, a cikin yan tsakanin ya saka Yaran shi makarantar, nafi tunani sabida halin da yake ciki na bukatar kebewa damu, ga Mahaifiyarshi ta hana shi kwana bamu, sai ya saka yaran a makaranta.

Toh a haka da ya samu yara na makaranta shi kuma sai ya baro pada yazo ya turmushe wacce take da girki, da wannan hikimar aka same zaman lafiya, Amma saboda bin diddigin matar nan sai da yasan yadda ta kamashi a dakin Natashah. Bayan fitar shine ta kira Natashah wacce cikinta ko yau ko gobe, sannan tasata ta kiramu, duk muka hadu a falonta.

"Toh munafukai na tarakune na gaya muku cewa duk wacce na kuma ganin Ashraf ya fito d'akinta sai na sashi ya rabu da ita." Inda take shiga ba nan take fita ba cin mutuncin kamar me, tana gamawa nace.
"Nannah! Iya girmamawa muna baki muna mutuntaki, muna kuma miki biyayya, Nah Ashraf d'anki ne mu kuma matan shine, Nah abu daya zuwa biyu, Ashraf dai ba sauran shi zaki yi ba!? Sannan babu abinda zaki iya mishi, mu matan shine sabida nutsuwar shi da jin daɗin shi yana gare mu, iya biyayya yana miki amma tunda kin nuna ke din surukar zamani ce tabbas zamu nuna miki zamanci."

"Toh mara kunya! Kuma nace kar na kuma ganin Ashraf a dakunarku."

"Wallahi bakin isa ba, Dole ya dawo mana." Inji Natashah

Abin Nannah yayi yawa, ta addabi rayuwarmu akan wata shirmenta na daban, shi.

★★★
Ina kwance a falo, sai gashi ya shigo yana hucci tunda naga haka nasan itace ta gaya mishi abinda muka mata.
"SAFINAH! Har rashin kunyar ki takai keda Natashah ki zagar min dan baki da tarbiya."

Wani kallon banza na mishi sannan na kauda kaina nace.
"Toh su tarbiya manya! Ai matukar tace bazata fita harkan mu da kai, wallahi abinda muka mata baya ga komai ba"

"Mahaifiyar tawa?! Safinah kike gayawa Maganar banza."

D'aga hannun shi yayi da niyyar zai mare Ni, sai ga Zoyah tashigo tare da rike mishi hannu.
"Haba Sultan , taya zaka d'aga hannunka akan fuskar mace, nida nasan gaya maka abinda suka yi zai kara tun zuraka da ban fara ba, na zata bazaka ji ciwon abinda suka aikata bane."

Riko hannunshi tayi suka fita ina zaune a gurin ashe kuka rahama ce, domin kuwa ban tab'a daukar al'amarin an ci ba, Amma ba komai.
Kiran Ummina a waya, kuka nasaka mata, sosai ina bata labarin abinda Nannah takei mana. Murmushi tayi sannan tace..
"Ina SAFINAH take, ajiye miji a gefe kiji da kanki in cikin wannan karon babu matsala."

Gaya mata abinda mukayi nayi ta min fad'a sosai, sannan ta kuma ce na bashi hakuri, sannan tace.
"Ki kwantar da hankalinki"
Wayyo na dakyar na gama wannan pagen nayi gyangyadi yafi sau biyar😂🙄
[20/03 2:30 PM] My 2nd Mtn: number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Masha Allah*

4️⃣7️⃣

"Ummina! Ya dauki zafi fa sosai."

" Eh mana ai dole ya dauki zafi Mahaifiyarshi ce fa! Kuma duk d'a nagari dole yayi kishin Mahaifiyarshi, dan haka ki bashi hakuri sai a wucce gurin"

Ciki sanyin jiki nace mata.
"Toh shi kenan zan yi yadda kika ce Ummina"

"Yawwa yar albarka! Wancan watan abokin mijinki da wasu mutane sun zo niman auren Batul."

"Toh wa kenan a cikin su?!"
     "Fahad?!"
"Laa! Aukuwa ta more miji, dan bai da matsala, Allah ya nuna mana lokacin da rai da lafiya."
"Amin Ya Allah"
Munyi hira da ita sannan na kashe wayar.

          Ina ta zuba ido naga shigowar shi ko Natashah babu su babu labarin su.

      Can wajen maraici sai gashi ya shigo, ko takaina bai bi ba. Ya shiga dakin yarana ya fara diban kayan Aanih zai fita dashi.
"Wallahi ka kaiwa wata mace Y'ata sai naci mutuncinta sannan na tattara yarana mu bar maka gidan, idan kuma kana ganin bazan iya bane bismillah"

   Na cigaba da abinda nake a falon,  zuwa yayi gaba kamar zai rufe Ni da duka, d'ago kaina na kalle shi a tsanake sannan nace.
"Wallahi duk ranar da zuciyarka ta baka shawara ka tab'a Ni da sunan duka."

   Gyara zama nayi ina rike kofin zumar da nake sha. Cikin isa da na koya daga gare shi, hannunshi naga ya kawo dai dai wuyata.
"Lallai Ashraf! Toh ka tab'a Ni ka gani idan baka da hankali! Wallahi Ni ba Natashah nace da zaka daketa tayi hakuri dan tana sonka. Idan ka tab'a Ni sai kayi dana sanin yin haka har karshen rayuwarka, dan kaga ina kyale ka ba tsoronka nake ji ba, igiyar auren tsakaninmu nake girmamawa, sannan inda akan abinda nayiwa Nah ne kaje Ni na yafe mata kai Ni ka sallame Ni dan ko baka sake Ni ba zan fita na bar maka gidanka."

         Ina gama fad'ar haka nabi gefenshi na wucce, hakurin da Ummi tace na bashi ma na fasa, dani dasu shege ka fasa.

           ....... Ashe a lokacin da ya shigo ya Same Zoyah a falon Nah, tana bata hakuri tare da cewa.
"Kiyi hakuri Ammyn wallahi sai yanzun na fahimci abinda yasa kike rike shi, Ashe ba lafiya ce dake ba, kuma daga yau bazan kuma niman shi ba ya cigaba da kula dake Ni farin cikiki shine nawa."

Zama yayi kusada Nah cikin gajiya kwantar da kan shi yayi jikin kujera, zuciyarshi tana cikin kewar SAFINAH, yasan da itace da tuni ta cire mishi takalmin kafar shi da Safar ta shiga matsa mishi, mik'ewa yayi zai bar falon. Zoyah tace,

"Tunda ka shigo kaga yadda muke ai ka tambayi lafiya, amma baka yi ba. Sai ma tashi da kayi zaka Duba wata kaskantaciyar matar ka wacce bata san daraja kanta ba balle na iyayenta, dan duk wanda zai bud'e baki ya zagi Uwar wani toh bai san darajar tasa uwar ce ba."

Ware idanunshi yayi akanta mamaki na kama shi, ince itace ranar ta hana shi barci akan ya zo gurin Ammyn shi yau itace ke ihun.

Nad'e hannunshi yayi a kirji sannan yace.
"Ina jin ki!"
"Toh wancan bakar da lafiya al'amarin ta akan na kowa ce ita da Natashah suka zagi Ammyn."

Kuka tasaka tare da girgiza kanta sannan ta gaya min shi komai bayan ta gama sannan ta kara da cewa..
"Banga amfanin zama da su ba, amma kayi hakuri idan na maka shishigi, sai dai Ammyn ba Mahaifiyarka bace kai d'aya nima Uwata ce."

Ko gama jinta bai yi ba, ya shige dakin Natashah ya sameta tana kwance, shine ya maka mata duka a cinya, ya karta mata rashin mutunci sannan yace.
"Kar na kuma ganinki a shashin SAFINAH, tunda kina da komai na buƙatarki kar na ganki ko a waje."

Dake tana tsoron shi hakuri ta bashi, Ni kuwa yar tawaye shine da yazo wai zai mare ni, na gama lura

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login