Showing 12001 words to 15000 words out of 104042 words

Chapter 5 - MASARAUTAR JORDAN

CHN   

30 Oct 2025

3200

D'ago kai yayi cikin izza hadi da mugun mulki, jinin sarauta na yawo a jikinshi, chafko wuyata yayi ya matseni a bango, kafin yayi kokarin haɗa jikina da nashi na kuma zuba mishi wani mari, na kuma marin shi.
Zare hannunshi yana kallona, zuba gwiwarshi muryanshi na rawa, yace.
"Ki min kome SAFINAH! Kawai ki dawo garemu"

"Kai jahili ina ne? Da aurena kake bina, Muh'd ka gaya min meye nayi maka da zafi haka ka rabu dani mana, don Allah ka barni nayi Rayuwata da mijina."
Tunda muka fara rigimar Dr yake tsaye, bai iya motsawa ba, sai da yaga zan fito ya juya da sauri ya koma inda ya muke, ina zuwa gurinshi na zube a jikinshi ina kuka nace.
"Baby! Mu bar garin nan."
Rintsa idanunshi yayi zuciyarshi na zafi, ji yake kaman ya an cimma mishi wuta, ji yaƙe kamar ya rufe Ashraf da ya fito jikinshi ba laka, yaƙe ya zauna yana goge hanci sa da jini yake.

Kukan da nake sosai nake ganin kamar hankali mutanen zai dawo gare mu ya mike dani muka koma masauki sa, muna shiga cikin d'akin na ajiye Ni. Ya juya abinshi.

Wannan shine karon farko da ya fara jin ciwon akan aurenta, bai ga dalilin da zai bar Ashraf yana tun kara matarsa. Dole yau zasu bar garin dan.

....... Nayi kuka har na godewa Allah, banga Dr ba, har kusan Asuba, da nafito na hango shi zauna a kan kujerar, takawa nayi gabanshi, tare da saka hannuna akan gwiwarshi nace..
"Hameed! Nasan kaga abinda ya faru tunda kaki zama kusa da ni Hameed do.."

"Don Allah karka juya min baya ko? Safinah da tun farko kin nuna min Uban yaranki SAFINAH da ban shiga rayuwarki ba, Safinah abinda kika min baƙi kyauta min ba, amma banga laifinki ba, nine me laif.."
Rufe mishi baki bayi da hannuna, a hankali na shige jikinshi, ina kuka.
"Don Allah ka yafe min wallahi kai nake so, Hameed daka rabudani gwara ace bana numfashi. Don Allah kabar Mutuwa ta rabamu, karka.".

Haɗe bakinmu yayi, nima na riƙe kanshi. Shi kuka Ni kuka dan mun fahimci rabuwa da juna ba abu me sauƙin bane, tun daga wannan kiss din abubuwa suka sauya, sosai ban taba jin dadin kasancewa da Dr ƙamar yau, shima ya fahimci haka, kwantar da kaina nayi a kirjinshi, ina sauke ajiyar zuciya, a hankali yake shafa bayana, a Sannu har barci yayi gaba dani. Leka fuskana yayi a hankali yaga yadda yanake barci, shafa fuskana yayi a hankali don da tausayi, ji yayi zuciyarshi tayi mishi nauyi tausayin kanshi yake ji, wani iri yake ji. Bakin yanayin da yake ji a jikinshi. Musamman mugun ganin da yayi ya kuma karya mishi zuciya.

Lumshe idanu yayi a sannu barci yayi gaba da shi, bamu farka ba sai karfe shida na safe da sauri muka shiga wanka a tare, muna fitowa sallar muka gabatar, sannan muka koma gado Dan barci bai ishenmu ba.
Ina manne cikin jikinshi, kaina yana kirjinshi, dan haka fitar numfashinsa yana sauka a kirjinsane, shafe kaina yayi cikin jin kunci irin na wanda yake jin zai rabu da abinda yafi so a rayuwar shi, damuwa ce ta ƙara mishi yawa. Mikewa yayi zai fita daga d'akin, yayi maza tare da riko hannunshi, nace.
"My Man! Ina zaka je i need you."
Haurowa gadon yayi cikin sanyin jiki. Ya janye bargon ya shiga min tausa, juyar dani yayi ya zuba min ido, ganin yadda nake mika yasashi shiga cikin bargo a sannu ya cigaba da min tausar tare da salon shine me taba zuciya, lumshe idanuna nake ina bud'e su, shigewa jikinshi nake sosai yasashi fahimtar ina bukace dashi........

Kuyi har maneje
[22/02 11:08 AM] My 2nd Mtn: Masoyana na Nijar ga number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah......

MJ
BOOK-2
19-2-2020

✋🖕
     Shafar fuskana yayi a hankali, lumshe idanuna nayi, tare da kwanciya sosai a jikinshi.
      "Baby baka hakura bane!?"
    Na tambaye shi, muryata na rawa.
        Sumbatar kumatu na yayi tare da gyara min kwanciyata a jikinshi yace.
      "A'ah ai ba zan iya fushi dake ba, kwanta ki huta."
      ........ Wannan halin ko ina kula da Dr yake min ya fara damun rayuwata, dan kuwa a cikin lokacin ƙalilan na zabge, na fita hayacina, babu shiri muka bar Oman, dan ha fahimci Dr so yake zuciyata ta buga haƙa muka dawo tattaro zuwa naija.
    Dr Shabhan ne yazo ya dauke mu,  muka nufi gidanmu. Tun daga nesa naga gidan ya koma kamar irin tsohon gidan nan. Duk wasu flower da aka saka a gidan ya mutu, kamar ba a mishi ban ruwa, haƙa Dr Shabhan ya shiga da motar shi ciki damu,
    Tunda na kalli gidan sai da zuciyata ta buga, tsabar tsoron da gidan ya bani, bakina dauke da addu'a na amshi key na nufi gidan. Wanda yayi yanar gizo gizo.
        " Gidan nan naku akwai matsala! Ina shigowa da motana na fahimci hakan."
     Dariya Dr yayi sannan yace.
"Babu komai Wallahi, kawai kana dai tunanin hakan ne."

    Duk yadda Dr Shabhan yaso fahimtar da DR yaki fahimta. Yana fita daga gidan, Me gadin ya bishi da mugun kallo tare da idanunshi da suka koma ta kare.
      ...... A sannu na shiga gidan na samu yayi kaca-kaca, ga hotunan mu a farfashe. Kome na gidan a juye fa. Safe goshina nayi sakamakon ganin wulgawar wani bakin kare, cikin yan second.
          Sunan Allah na shiga kira a hankali har na shiga d'akina. Shima an lalata min kome, Ni abin ma tsoro ya fara bani,

        Wasu irin abin mamaki nake gani dukda bakina dauke yake addu'o'i.
     Dafani aka yi aikuwa na fasa ihu, da sauri ya rungume Ni tabaya yana cewa.
"Beauty!!! Nine fa"
Da hanzarin na juya tare da shigewa jikinshi, ina rintsa idanuna.
       Ajiyar zuciya nake saukewa. Cikin damuwa nace.
"Nikam,"
       "Ke kam! Me?
    Cikin wani irin murya nace.
"Gidan tsoro yaƙe bani"
  "Kai nifa banga abin tsoro ba kawai idanun ku na nuna muku wani abu na daban ne."

   Duk yadda naso ya fahimta yaki dan haka na hakura muka fara gyaran gidan, sallah ce take tsayar damu, dake tasowarshi asuba ce sai muka iso karfe sha daya na safe.
Biyar na yamma muka gama aikin har da girki, tare muka ci sannan muka yi wanka gidan Ammah ya tafi yabarni a gidan, dake Ni ɗaya ce sai na kunna ta. Naga ana film din wani horror bai min  ba sai na mai dashi zuwa, Saudi one sun kuwa saka karatun Alkur'ani. Cikin suratul ma'edah. A sannu barci yayi gaba dani wajen biyar da kwata.

         Barcin ba wani nisa nayi ba, amma ba fara wani rudaɗɗaɗiyar mafarki na wanan karen da naga kamar gizo shi na bina da gudu, sai da yayi wuf zai kamani naga anyi sama dani, shi kuma yana kasa sai haushi yake.
       Cikin salati na farka, dai dai Lokacin da aka wucce wuf ta window na, mikewa nayi naga ashe ina kwanciyar aka dauke wuta. Fitowa nayi na hango mai gadi yana zaune, amma kanshi a sunkuye. Kiranshi nayi da cewa,
"Malam Ali!"
     Bai d'ago kai ba, na kuma kiranshi, amma yaki d'agowa sai da na isa inda yake na fara magana da cewar.
"Malam Ali ya ina magana kaki amsa min ko ba kaji ne?"
                "Bani ne bana ji ba! Kece baki ji! Sai da na gargadi akan kowani namiji Safinah baki ji ba."
     D'ago bakaken idanunshi yayi baya nayi tsoro ya kamani,
               Horn din Dr yasani manta abinda na gani, dan shima mikewa yayi yaje ya buɗe get din sam na manta abinda na gani har Dr ya shigo gidan, gabaki d'aya kaina ya kule, ina ƙoƙarin tuno abinda na gani amma nakasa,
      Jan kafaffuna nayi naje na bude mishi, fuskarshi ɗauke da murmushi ya fito yana cewa.
"Beauty! Ina can zuciyata tana gareki, gaya min keke faruwa?"

    Kallon Malam Ali nayi naga baya gun, rungume shi nayi tare da kwantar da kaina a kirjinshi nace.
"Babu!"
A takaice, janye Ni yayi ya dawo dani gabanshi, yace min.
"Muna da bakuwa fa"
         Juyawa nayi na hangonta tana zaune, a bayan mota sai wani d'aga hanci take.
   "Wacece ita!?
       "Yar gogg."
     "Goggo Aminah ko? Hmm kace ta fito."
     Magana ya mata ta fito tana yatsina fuska, tabe baƙi tayi sannan tace.
"Toh kayan fa? Waye zai dauka min!"
     Juyawa yayi zai je kamar zan rike shi sai na kyaleshi, ya sauke mata kayanta muka shigo gidan,
      D'akina na wucce bani takansu ba, dan matukar nayi haka tabbas bani da adalci, kuma kamata yayi na amshi ta, amma bazan iya ba kuma bazan wulakanta ta ba, nuna Mata dakin kusada nawa, ta saka kayanta.
           Sannan ya shigo d'akina ya dame Ni na fito daga ban daki, ina tsaye zuwa gabana yayi ciki  sanyin jiki yace min.
"Kiyi hakuri!"
  Murmushi nayi sannan nace..
"Name fa!?
       D'ago hannuna yayi ya daura a gefen fuskarsa, yace..
"Kiyi hakuri dai, na kawo miki wata gida."
  Murmushi nayi tare da kai ɗaya hannuna din na tallafe fuskarshi nace.
"Ko ɗaya idan nayi haka na zama mara imani tamkar butulcin zan kira Kai na tunda ta ko ina. Allah ya bani nasara yan uwansa nima yan uwana ne, don Allah karka saka komai a ranka ina tare da kai."
           Jan kumatu yayi sannan yace.
"Allah ya bar min ke!"
  "Tare da kai!"
      ....... Kitchen muka shiga tare muka fara girki abincin dare, muna cikin aiikn muka ji kiran sallah rage wutar muka yadda abincin zai nuna, a d'akina mukayi sallah sannan muka tare, bakuwarmu na gani dauke da abincin da ko d'and'ana shi ba muyi ba, ta shake har yayi soro.
   Ban kalle ba , nayi wucce wata kitchen na sauke sannan na juye na fito mana dashi, akan kafet na ajiye mana, dan jollop ɗin taliya ce,
     Gabanshi na shiga na zauna, tare da ɗaukan abincin na kawo gefenmu muka fara ci, tsaki yarinyar tayi dan bata wucce Sa'ar  Nanah ba,

        Ni yake bawa abincin a sannu ina ci muna hira, yana gamawa ya na juya na fara bashi. Kamar yadda ya bani, muna gamawa na tashi zan Kai kwanikan ya amsa ya dawo dani, ya sannan ya dawo tare da tissue, ya goge min hannuna,

   Nan muka cigaba da kallon labarai, har wajen tara sannan muka tashi zuwa cikin, wanka mukayi sannan ya sani nayi alola muka yi sallar Isha tare da shafa'i da wutir.
      Muna idarwa ya riko Ni tare da zare min hijabi na, rage wutar d'akin yayi sannan muka kwanta.
   
   "Kiyi hakuri da abinda Sa'ima tayi mana, bana son ace daga zuwanki har an fara samun matsala daga gareki, zata zauna na wata shida ne, yazo service idan tagama shikenan da."
        Murmushi nayi tare da janye jikina daga nashi nayi rubda ciki, ina Son jin zafin abinda yayi min amma ba halin haka dole na juya mishi baya, yana tabani nace.
"Please barci nake ji."
    Matsowa yayi ya kwantar da kanshi akan bayana, sannan ya zagaye hannunshi inda ya turani cikin jikinshi, lumshe idanuna nayi kwallar da nake b'oye suka fara sauka a kan matashin.
           Jin yadda nake jan hancina ya fahimci kuka nake, amma bai hanani ba, sai ma kara k'amk'ame ni da yake.

          A hankali barci yayi gaba damu.
      00:1am na tsakiyar dare, agogon d'akin ya buga "katttt"
Gyara kwanciya nayi ɗan har lokacin ina kwance ne Dr na sama na.
   Juyawa nayi a sannu, sai naji anan magana ƙasa-ƙasa, haɗe da kukan jarirai, abin mamaki Kuma a cikin d'akin nake jin maganar, sake ware idanuna nayi ina niman inda ake maganar, kuma abin damuwar sam baka fahimtar Abinda ake cewa. Jin digar abu a kumatuna yasani shafowa, wani bakin ruwa ne me mugun wari, d'aga Kaina saman nayi.
    Wani uban salati nayi gaskiya ban kuma sanin inda kaina yake ba, sai bayan kwanaki biyu, sannan na farka na ganni a kwance a d'akin Ummina,

     A hankali na bud'e idanunshi, tana zaune akan abin sallah, a hankali nake addu'an tashi barci... 

  Tasowa tayi tazo inda nake tace.
"Sannu SAFINAH, ya jikin naki."
   Gyada mata kai nayi "da sauki." Nace mata a sanyayye,
      Kallona tayi taga ina son ƙarin bayani, ruwan wanka ta fara haɗa min sannan ta dawo ta kama hannuna muka shiga ban daki nayi wanka da taimakonta dan zata fita na riƙe hannunta, shine ta dawo ta cude min bayana tare da kaina Ni kuma nayi sauran ina gamawa ta miƙa min towel.

         Muna fitowa  ta bani kaya nasaka sannan na zauna, tace.
"Naga kinyi alola a ciki ko Zaki yi sallar kafin na kawo abincin."

"Toh Ummina!"

........ Bayan naci abinci anan na zuba mata ido tace.
"Shekaran jiya! Abdulhameed, ya kiramu wai kumar suma da harbe harbe kamar me cutar jinmu, kuma daman kafin ya kira Ashraf ya fara mana maganar cewa zai dawo yana jin baki da lafiya dan yaji haka a jikinshi. Toh da muka ki nashi sai ya tattaro ya biyo jirgi, inda ko tsayawa ayi bikin shi bai yaƙi, a ranar da ya dawo. Yaje gidanki a daren. Mijinki ya kiramu. Toh a daren Abbanku ya gayawa Ashraf, shi Kuma dama yana unguwar ku, dan haƙa ya shiga gidan, dan yasamu Kofar gidan a buɗe. Shima yasha wuya sosai kafin ya shiga cikin gidan dan duk jikinshi ya ji ciwon. Koda ya samu ya shiga tare da mijinki suka fito dake kina fisge fisge, shi yaso a dawo dake gida amma mijinki yace scale kuje asibiti.
Tunda aka kai ki banda allurai, ganin. Har muka zo jiya, shine Wani mutum da Abdullahi ya taimaka, yazo ya ganki yace ba ciwon asibiti bane, na gidane, abin mamaki mutumin na fita mota tabi takanshi. Toh dai Abbanku yasa aka dawo dake gida dazun nan inda aka kira wani malami ya baƙi magunguna."

Lumshe idanuna nayi, sannan na gyara kwanciyata akan cinyarsa,
***
A sannu sai da nayi sati biyu a gida kafin aka mai dani gidana, sosai naji sauki,

Sati na biyu da dawowa, hmm wani sabon lamarin ya faru, kaina na bisa cinyar dr, yana wasa da gashina.
Haka kawai naga gidan yana juya min tare da ciwon ciki, buɗe idanuna nayi zan gaya mishi, sai ganin wannan abu ranar. Ihu nayi tare da yunkurin mikewa. Ji nayi abu mazuna daga kasana, aikuwa na kafe mishi a gurin.

Faɗan irin wahalar da nasha, tun Dr na nuna damuwarsa har ya fara ganin kamar da gayya nake kome, ƙarshe Sa'ima ta gayawa Uwarta, kuma dama ba wani shiri muke ba, gashi bana son zama Ni ɗaya amma haka zasu fita abinsu Ni ɗaya a gidan, haka zan dimauce. Na fita hankalina.

Watanni mu biyar, ina fama da wannan matsalar, hmm a sannu Kowa ya daina damuwa da halin da nake ciki, Ashraf ne yaƙe ƙoƙari a kaina. Shima kuma ba kaunar ganinshi nake ba, idan kuma ya kawo magani daukewa ake.
Nayi imani haka shine tawada kaddaran, dan kuwa nasha mugun wahala. Babu wani kulawa nake samu gurin Dr ba, ga rashin mutunci da yar uwanshi take min,

Ban tashi fahimtar abinda ke faruwa ba, sai da aka kawo min Kayan fadar kishiya, nan na fahimci mijina yayi min nisa, domin gefe ina fama da wahalar ciwo, suma kuma suna bunkasa masifa, sai gashi na zama marainiya da iyayena, na zama kamar mahaukaciya, ko me tambotsa, toh bana barci ido biyu nake ganin masifa, ba dole kai ya kunce ba. D'akina kaca kaca.
Ni kaina kana ganina zaka sanyani a class din mahaukata masu degree a cikin hauka,

Gidan kam zan iya cewa sun manta dani ma gabaki d'aya, a cikin zuri'arsu, dan babu me tunanin.
Abinda na iya ganewa shine Dr ba a gidan zai zauna ba, kuma a Cikin wannan lalura bai hanashi idan masifar ta Ciyo shi yazo yayi min wasa wai nan ya biya bukatarsa,bana hmm bana humm. Ina nan dai ido kawai nake bin kowa dashi, dan bakasan wata irin rayuwa nake ba, zan kwanta amma ba barci nake ba,

...... Haƙa aka yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login