Showing 6001 words to 9000 words out of 104042 words
haka naso ba😼😿_
****
Barci Ashraf yake tare da mugun mafarki, a firgice ya tashi.
*"SAFINAH!!!"*
Ya furta kenan duba agogon dake kan wayarshi yayi, yaga biyu da rabi. Safe goshin yayi jikinshi na bashi wani yanayi akanta, lumshe idanu yayi yana tuno abinda ya faru sati biyu da suka wucce.
......
Bayan koran Feener da yayi yana kofar shi ya rufe, jikinshi ne yayi mugun sanyi shi kaɗai ya shiga cewa.
"Indai sabida Wancan zata bada kanta a karo na biyu toh babu amfanin na amshi aurenta zan hakura da ita take ta zauna da wanda take so"
Kusan ranar raba dare yayi yana sakawa. Har barci yayi gaba dashi.
Da asuba bayan sun dawo masalaci yasami Abba da Maganar cewa.
"Hmm! Dama akan maganar mu da Binti ce, ina ganin tun da baka baka fadawa Hameed ba, kawai kabarsu, suyi zamansu Ni na hakura."
"Scale Sultan! Nasan zai fahimce Ni Indai Dr ne."
Murmushi Yayi dan wani lokaci idan yana abu sai ya fito maka da nagartanshi da kuma nutsuwa irinta saraki, idan yan mutuncin na kusa, koda yake wa SAFINAH yake wa rashin mutuncin ba dukka mutane ba.
Cikin son jaddada adalci, ya fara magana a nutse yace.
"A wannan zamanin anyi auren soyayya ya aka kare zama bai dadi ba, balle kuma auren biyayya, zata muku biyayya dan ta zauna dani amma har abada zuciyarta bazata taba yafe muku ba, sabida tana da wanda take so kuka hanata, kuka bata zabin ranaku. Akan Wani dalili na daban, tabbas hakkin ku ne zaba mata miji. Idan kun sami na gari, amma bana gizo ke sakar ba, shin kune zaku zauna mata? Shin kusan irin hatsari da kuka wurgata? Idan aka samu me karamin tunani. Abinda zai zo mata ta kashe mijin kawai sabida bata so aka bata dole, me dogon tunani kuwa bazata taɓa kyautatawa mijin ba, wanda sanadin haka zata faɗa hallaka, Ni a nawa tunanin a barta da wanda take so, indan tanine, ina nan ba inda zabi zan fara kasuwanci a ƙasar nan, dan na dawo nan kenan. Sabida Yaranmu matukar na tafi dasu bazai zauna ba, shi yasa zan zauna a nan suna jin dumi mahaifiyar su."
Abba tsintar kanshi yayi da gyada mishi kai dan ganinshi yake kamar Sultan Abdullahi, wato mahaifinsa.
...... Wannan ne abinda ya faru......
🙈🙈🙈🙈🙈🙉🙊🙊🙊
[22/02 11:08 AM] My 2nd Mtn: *Masoyana na Nijar ga number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
*Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*
Oum Muwaddah......
MJ
BOOK-2
17-2-2020
Page.✌️✌️
..... Jikinshi rawa yaƙe haka kawai yake jin duk yadda aka yi Abdulhmeed yana tarayya da SAFINAH, wani Irin abu yaji ya tsaya mishi a wuya, tashi yayi ya ɗauki goran ruwa ya buɗe tare da kafawa a bakinshi sai da yaga goran ba kome sannan yayi wuri da ita, kirjinshi na masa zafi ji yaƙe kamar yaje ya kamasu yayi ta jibgarsu.
Banɗaki yashiga tare da da budewa kanshi ruwa, dan ko kayan jikinshi bai cire ba. Mai da gashinsa baya yayi, take yalwantaccen gashinsa ya sauka a dokin wuyarsa. ya jima a cikin ban dakin sannan ya fito alola yayi dan yaga lokacin sallah ta gota mishi.
Doguwar jallaɓiya yasaka, sannan ya shimfida abin Sallah.
Tunda ya idar yake addu'o'i tare da niman sassauci halin da yake ciki.
Yana cikin addu'a suka shigo da gudu har suka fad'uwa kasancewar har yanzu tafiyar su bata nuna ba, suna zuwa suka zube a jikinshi.
"Ankul! Didi"
Tausayi suka bashi rungume sun yayi cike da kaunarsu.
Cikin harshen larabci yake ce musu.
"Kuyi shiru zan kaiku gurinta, amma sai ku daina guje-gujen."
Kwantar da kansu suka a jikinshi, Aanih tasa yardar ta ɗaya a baki, ta fara rero mishi baitukar kuka tare da kiran Didi, ga hawaye ga yawu Manyan idanunta masu kama da na Ubanta sunyi ja, ba can ba rarrashin ya fara, yana gamawa da ita Aamih itama ta fara nata, wasa wasa yaran nan suka manna mishi ƙaramin hauka, yana gama rarrashin wannan wancan zata fara.
Wayarshi ya dauko tare da danna kira, yayi ringing amma ba a d'aga ba, haka yayita gwadawa, karshe da ranshi ya ɓaci doka wayar yayi da bangon, jikinshi na wani Irin tsuma, yayi imanin da a jordan yake da yau sai yasa an ware mishi kan Binti da na Dr.
Tashi yayi ya ɗauki yaran, suka fita daga gidan.
A waje suka haɗu da Ghaniyu yasa hannu ya ɗauki Aanih Aamih tana kafadar Ashraf.
Kallon Ashraf yayi cikin sanyin jiki yace.
"Sultan!"
D'aga mishi hannu Ashraf yayi, cikin wata Irin Muryar wacce rabon shi da ya juya muryan ya shekara kusan biyu har da watanin.
"Gidanka zaka kai mu."
Shan jinin jikinshi Ghaniyu yayi, yasan yau an tabo ubangidanshi, tunda yaji an bada umarni kamar ana jordan, tabbas an kai shi makura kuma yasan da a Jordan da hukuncin gintsewa ko ladbatawa ya danne kan wanda ya tabo shi.
Cikin motar ghani ya ajiye Aamih, Shi kuma ya zauna a gaba, rike da Aanih wacce take kukana. Ganinsu da Aamih tayi a gaba ta tsalla ihu, tana kiran didi.
Dawo da ita gaba yayi ya haɗata da yar uwanta.
Gidan Ghani suka wacce....
***
🙈🙊
Sosai Dr ya jiyar dani kalar tashi soyayyar, domin kuwa na Ciyo(🤣😜) ko tuwo albarka. Kifa kanshi yayi a goshina yana jero min yabo da sanyawa albarka. Banda kuka babu abinda nake sabida bakin ciki da takaici fanko nazo gidan mijina, a haka yake kuma nuna min Farin cikin shi.
"Nagode sosai Beauty! Allah yayi miki albarka, bar kukan nan don Allah."
Janyen wa yayi zuwa gefe, yasanya hannunshi ya jawo Ni jikinshi, kuka nake har da shasheka.
"Idan baki yi shiru ba zan kuma."
Buɗe idanu nayi dagaske kuma karawa zai yi dan na fahimci hakan ne ta cikin kwayart idanunshi. Tura mishi bakina nayi aikuwa ya chafko. Kamar zan cinye Ni haka ya koma..
Sai da ya kuma dulmiyar dani ruwa, sannan ya jani muka shige ban daki. Nan ma bawani wanka mukayi ba sabida bata lokaci mukayi muna wasa a cikin ruwa, sannan muka fito zama yayi a stool. Dake gaban mirror kura mishi ido nayi haka kawai sai naga ya tuna min zaman da nayi a jordan, amsar towel ɗin hannunshi nayi na shiga goge mishi kai. Ina cikin goge mishi kai ya riko hannuna ya dawo dani gabanshi, zaunar da Ni yayi akan cinyarsa. Sumbatar gefen hannuna yayi tare da daura kanshi a kafadana.
"Beauty! An jima zamu tafi Poland, da fatan ban takuraki ba. Zaki rakani ne daga can Kum..."
Yadda yaƙe sumbatar jikina na fahimci sauran Zance a raina nace.
*Wannan shima dangin Babansu Aamih ne da jarabawar*
Koda yake zan iya cewa yau ɗaya na fahimci Dr bai kai Babansu Aamih fitina ba, domin shi nasa me sauƙin ne kuma baya min kallon d'anye nama, Baban su Aamih kuwa kamar ya cinye i d'anye yake ji.
Kauda tunaninshi nayi a raina, dan banga dalilin yin haka ba, tunda ba zamanshi nake ba.
....... Sai da na tabbatar da ya shirya tsaf sannan muka fito zuwa d'akina, nima nashiyar sannan yajamu Sallah azhar da muka rasa muna idarwa ana kiran la'asar.
Dan haka muka daura muna idarwa, ya tashi kitchen ya nufa, tare da sako mana abincin bayan ya sake maida su wuta, yana gamawa ya kawo har cikin dakin ya ajiye. Cikin lokacin ƙalilan Dr made me like Queen, kome yi min yake. Karewa da na kurbi ruwan tea na riƙe bakina, duk sai ya diririce, kamar ya amsa a bakina.
"Sannu Muhammad bakin, bud'e min sannu."
Had'iye tea nayi sannan na buɗe mishi, hura min iskar bakin shi ya fara sai da yaga ina lumshe idanuna yace.
"Zaki iya ci ko na baki."
Zuciyata kamar na cirota dan farin ciki kasami namijin da zai maida ka tamkar sarauniya wannan abin da burgewa yake, gyada mishi kai nayi cikin jin dadi nace.
"Baby! Zan iya ci da."
"A'a beauty bari na baƙi a baki dan nasan ba wani ci zakiyi ba, ai Dr Kyari ya gaya min kina gaba da abinci, baki so sai ki wuni baki nemi abinci ba. Dan haka matso nayi na baki da hannuna"
Kamar na fasa ihu haka nake ji,babu yadda na iya matsawa nayi jikinshi, ya fara bani haka nake amsa ina ci ina jin wani irin karo na farko a rayuwata bayan Nannah yau ga Dr na ciyar dani cike da so da kaunarshi, sai da yaga ina kauda kai yace.
"Beauty! Kin koshi ko?"
Gyada mishi kai nayi sannan ya fara cin nashi.
Yana gamawa na mike tare da tattara kayan zuwa kitchen, shi kuma ya gyara inda muka bata,
Muna gamawa muka yada zango a falon, riko hannuna yayi na, Ni kuma na zube a jikinshi.
"Wai! Gaskiya beauty kina da nauyi kutt, kin karya Ni."
Duka na kai mishi tare da kwantar da kaina a kirjinshi ina murmushi, sannu hiranmu yaƙe sauya salon, a hankali Dr yake niman wani magananka zare idona nayi akan fuskarsa nace.
"DON Allah kabar Ni haka har yanzun."
Kwantar da kaina yayi A kirjinshi, ya cigaba da shafa bayana, har barci yayi nasaran daukar mu.
***
Karfe biyar saura muka tashi shima sabida ana buga Kofar gidan ne, salati yayi tare da kallona ya zare Ni a jikinshi, a hankali rike shi nayi cikin barin da bai gama sake Ni ba nace.
"Please."
"Lokacin Sallah ya gota."
Tashi mukayi , shi ya fita waje Ni kuma na shige daki. Nayo alolar Sannan na fito shima shigowar shi kenan nace.
"Ya kadawo."
"Eh wallahi na tambaye bana megadi waye yace ba kowa shima haka yaji ana buga Kofar ciki da ya leko yaga babu kowa.".
Sam bamu dauki abin da wani muhimmanci, kasancewar bawai munyi nazari wani abu zai iya kawo mana matsala ba.
Bayan mun idar, da sallah yasani a gaba na sauya kaya na diba min kala hudu tare da nyt gown, muka fita bayan ya kwashe kome da zai ɓaci a gidan muka fits,.
Gidansu muka nufa, can ya barni Ammah tashiga hidima dani, me kike so me zaki ci, karbi wannan sha wannan. Wallahi dattijo nan lokacin kankanin ta kashe Ni da kaunarta, bai dawo ba sai karfe shida da rabi. Inda yazo muka ci abincin dare, daga nan gidan. Ya kai Ni gidan mu, a can ma Ummi da Umma sai wani haba haba suke dani. Karfe gomaw muka bar gidan ina son tambayan yarana na kasa dole nayi shiru.
Daga nan Airport muka wucce.
***
Kwance yaƙe shi ɗaya sai juyi yaƙe, kallon yaranshi yayi yaga yadda suka kwanta sai yaji ba dad'i, dan ya fahimci suna cikin maraicin Uwa. Tun da aka daura auren SAFINAH, ya daina fahimtar kome gashi azahiri mutum amma zuciyarshi ta gama cutuwa, lumshe idanunshi yayi yana tuna wasu abubuwan da ya shiga tsakaninsu. Daurawa pillown da kanshi yake nauyin yayi. Iska yaja tare da bud'e idanunsa da suka yi fiki-fiki yayi da idanunshi tare da jin sabon yanayi na musamman, ji yaƙe kamar yayi rashin babba. Itace yasashi kuka, ita ce ta tunatar dashi abinda yake aikatawa, bata barshi a haka ba sai da ta farka dashi barci da yake, sai da tabbatar ya mutu da kaunarta, ta kuma lugwaigwaita masa zuciyarsa da sonta amma tayi masa yankar kauna bayan tace amanar Ruhinsa.
Yayi imanin babu Macen da zata iya dashi sai ita amma haka ya tsallaka tabar mishi yaransu masu kananun shekaru.
Gyara kwanciya yayi zuciyarshi na bashi shawaran ya amshi Auren Natashah, dafe goshinsa yayi da hannunsa na dama, sam baya son auren Natashah. Bawai dan bata haɗu bane a'a sai dan ya gama tsara rayuwar shi da Uwar yaransa zai yi, kuma yasan halin matan su larabawa suna da kishin gado, musamman aka zandariya.
Murmushi yayi sabida tuno wasu abubuwan da suka faru ba ƙaramin masa dad'i yake ba. Can kuma ya tsuke fuska kamar bai taba dariya ba, wani fitinanen kishin tane yake damun zuciyarshi anya bazai sanya a sace mishi Dr ba??
*Idan kayi haka har abada bazata yafe maka ba, dan ka cutar da abinda take so.*
Juyar da kanshi yayi ya kalli yaranshi suke barci. Cikin kwanciyar hankali sauke ajiyar zuciya yayi tare da lalubabar karamar wayar da ya amsa a hannun Ghaniyu ya shiga duba number Amminshi ya lalluba, tana ɗauka ya sauke ajiyar zuciya, tare da gyara kwanciyarsa kafin yace.
"Na Amince da Natashah."
Murna tashiga yi tare da sanya mishi albarka, sannan tace.
"Zaka zone! Ayi bikin da kai."
Kamar bazai ce Wani Abu ba. Ya gyara riƙon wayar, sannan yace.
"Nufa na dawo nan innalillah! Ku kawo ta nan, kuma bana son Jordan su san inda nake don Allah."
Muryanta na rawa kamar zatayi kuka tace.
"Habibi! Ka dawo gareni"
Cike da tausayi ta yace.
"Kiyi hakuri bawai naki bane, yaran ne bana son suyi kewar Mahaifiyar su, amma zan zo."
Lallashin Nannah yayin sosai da ya fahimci tana cike da kewarshi, tabbas da ciwo a rayuwar shi, amma bayi da zaɓen da ya wucce.
Kashe wayar yayi a sannu ya tashi zaune, a tsakiyar gadon zuciyarshi ba dad'i taya zai zauna a Oman Bayan shi yanzun baya kaunar dukkan wata alaƙa da mulki, sam ji yaƙe ina ma bai haɗa Nasaba da mulkin ba, da yafi mishi alkhairi. Zai iya cewa tun tasowarshi bai taɓa niman abu ya rasa ba sai ita, sabida ya taso inda ko kallon abu yayi za a kawo mishi. Da ace ya taso ne a gidan da basu kai haka ba, da bazai tashi a murdadden hali ba,
Wannan murd'add'en halin ya kai shi ya baro shi dan da bai nunawa Safinah ikon bala'i ba da yana nan tare da ita amma ina ya zauna sai juyata yake son ranshi,
Toh taya mazata amince min, ya jima yana saka da warwara, kafin kuma ya shiga ban daki yayi alola ya fito ya yadda sallah inda zai kai kukanshi gurin me dukkan, dan ya fahimci ba inda yake samun nutsuwa sai ya kai kukanshi ga rabbi.
Koda ya gabatar da Sallah ya jima yana kai kukanshi, tare da niman biyan buƙatar shi na rayuwa...
Ya jima a gurin sannan ya miqe, zuwa, dan ya fara jin barci.
***
Shakeni wuyar Mamie yayi cikin ɓacin rai yana kara matarsa yana cewa.
"Me yasa! Akan me zaku tashe ni, ina barci na, kusa min muradin wani bani Adam a cikin zuciyata, dole na ɗauki fansa kafin na koma makwancina, dole na cika mishi burinsa, ki tafi gidan ki kai wannan tukunya a matsayin kyautar da ita, Ni kuma zan bata kyautar da na shirya mata, sai na shayar da ita madaran bakin ciki wanda babu irinsu duk fadin duniya, kamar yadda suka sashi ya rasa rayuwarsa sai na sadaukar da ita na zubda jininta ga doran kasa, wucce ki fita kuma ki kawo min kawarki Salmah dan jininta zan sadaukar ga abin da nake bautawa."
Da sauri ta fita tana rike wuyarta tare da shiga ruɗani ganin abinda zata aika ta, jinin Salmah zata bada Innalillah.
"Na shiga uku! Yau na yadda abin da ya dame ni. Ina zan kai hakkin Salmah."
Haka ta dauki tukunyar tare da barin gidan, jikinta a mace.
Dole haka ta faru da su tunda sun nace sai sun jefa rayuwar wasu a matsala gashi Tun basu je ko ina ba tasu ce a matsala, garin k'iyayyar SAFINAH ta wulla kanta cikin cikin damuwa, taya zata kawo karshen bala'in da ta jefa mata rayuwarta, bazata kira haka da zanen kaddarta bane, sabida shi zanen ƙaddara Allah ne ke zana maka, ita kuma wannan ita ta zamawa kanta katon layi me girman gaske, ita kuma wannan ita ce ta zamawa kanta, bata jin badaru da Maryam zasu yafe mata, idan suka ji abinda ta aikatawa yarinyar da sukafi SO duk cikin yaransu, Domin son da suke wa SAFINAH daban ne a cikin yaransu, suna matuƙa mata wani irin sone na musamman.
Wannan dalili ya jefa mata k'iyayyar SAFINAH, dan gani take duk cikin Yaran badaru yafi fiffita SAFINAH akan sauran yaransa.
***
Tun da ta iso gidan dare yayi sosai, dan haka dakinta ta wuce, tare da kwanciya, ko sallah batayi ba,
Washi gari tana tashi. Ko sallah batayi ba ta fito daga