Showing 39001 words to 42000 words out of 104042 words

Chapter 14 - MASARAUTAR JORDAN

CHN   

30 Oct 2025

3181

hannuna, nasa kai zan fita ya d'ago Ni tare da dawo dani d'akin.
"Baki da hankali ne!? Baki san jikinki da ciwo ba!?"

     "Toh ina ruwanka da ciwona ko a jikinka yake. Kaga bani hanya na fita ko na maka rashin mutunci."
      
           "Ki saurareni nace don Allah!?"
Ya daka min tsawa, b'oye fuskana nayi a kirjinshi, na fashe da kuka.
   Rungume Ni yayi jikinshi a mace.
    "Kiyi hakuri kinji bazan kuma ba, ki zauna zan je na jira Ghaniyu yazo ya biya kuɗin asibitin yanzun."

           Bakin gadon ya mai dani na dan zauna kaɗan, ya fita. Yana fita nima na fita a hankali.
    Ta kofar baya bani dan naga akwai Kofar zaka iya fita ta baya a asibitin.
     Kallon unguwar nayi sannan naga nasan unguwar sabida kawata Weedanh,  a hankali nake tafiya, dan bazan iya sauri ba.
     Ina zuwa gidan na samu tana nan,

    A sannu na shiga falonta duk yadda naso kuka haka na daure, ganin kayan Ashraf a jikina yasani kuma fita daga gidan dan kamar tonawa kaina asiri ne, mota na dauka har gidan Dudu, Allah da ikonsa na samu baya nan sai Sophia, Ina shiga na fashe mata da kuka, ai itama sai ta birkice. Tana shirin kiran mijinta nace.
"Bani kayaki nan wanda mukayi ankon Mukarramah."
 
   Safe goshinta tayi tana cewa.
"Wayyo Allah! Na bawa Safnah kanwata."
  
  Hannuna na daura akaina nace.
"Na shiga uku na lalace! Me zancewa Ummina."

"A'ah baƙi shiga uku ba, ina da super na irin shi bari na ciro miki"

"Nagode sosai Allah ya bar zumunci, Allah ya baki abinda kika so."

Tare muka shiga d'akinta nasakan sannan nace.
"Bani 3k zan turo miki in na koma."

Ba musu ta ciro ta bani, na mata godiya har zan tafi na tuna da ban ce karta gayawa mijinta ba, kunsan mace da zaran taki zandariya wallahi zata hau Yaren novel (🤫😂🤣)
Dan haka na na roketa da ta rufa min asiri, sannan na fito na same me taxi da ya kawo Ni, hakuri na shiga bashi sannan na mika mishi dubu biyu, ya kai Ni har kofar gida.

Gabana ne ya fadi sakamakon hango Ashraf a tsaye hannunshi hard'e a kirjinshi, ji nayi zuciyata tayi wani zillo.

A sannu na fito daga motar, cak na tsaya lokaci guda cikina ya shiga kad'awa. Wani mugun tsoron shi had'i da bakin cikin janyowa kaina masifar da nayi, tabbas na dibo ruwan dafa kaina.
Takowa yayi cikin tsukewar fuska yace.
" Wannan shine karo na farko, karki kuma na biyu! Ki nemi iznina kafin ki aikata wani abu, idan kuma kika yi gaban kanki."

Shafa beard dinsa yayi sannan ya gyara tsayuwar shi. Kauda kanshi yayi tare da juya idanunshi k'asa-k'asa yace.
"Wannan cin da na miki banyi kome ba! Dan na gaba sai an rike miki hannu dan ki taka, bana son rashin kunya bana son gardama, ki bani matsayina na Ubangidanki ke kuma baiwata."
Kai na a sunkuye ban ce mishi kome ba, sai hawayen dake zuba.
"Baki ji bane!?"

"Naji!"
Na fada da shakekken murya, ina toshe bakina.

"Kishiga! Amma ga maganinki nan, yaushe zaki zo kwana dan bawai na samu nutsuwa bane, akwai abu a cikin pouse dinki. Sannan jibi idan jikinki yayi kyau ki fito dasu Husnah park, Ina son shan madara."

D'agowa nayi idanuna cike da kwalla, yadda ya tsare Ni da mayatattun idanunshi yasani kasa da kaina, saka hannunshi yayi ya shiga goge min, yana faɗin.
"Good girl! Idan nayi magana da ido ya zama na an san menace bawai a zuba min ido ba, ina magana kina magana waye shugaban! Ki had'iye zuban hawayen nan dan zan iya mai daki gidana, daga yau karki kuma min abinda zai taba min zuciya kin fahimta."

Gyad'a kai nayi ina shanye kuka na.
"Bana son Body language. Bud'e baki Kiyi min magana."

"Toh."
Na fada a hankali.
"Ki kula min da kanki karki sake ko hannunki ya taɓa min waje, kuma ki ci abinci sosai. Karki kuskura ki kashe wayarki."

Gyad'a kaina nayi ina had'iye kuka na.
Bud'e motarshi yayi tare da ciro ledar magani, me tambarin NBC.
Karba nayi na shiga takawa a sannu har na shiga gidan,shafa kanshi yayi cike da samun nutsuwa da ya jima yana nima, sannan ya shiga motar shi ya kalli maigadin kiranshi yayi sannan ya mika mishi kuɗi masu mugun yawa yace.
"Wanda zai auri Safinah nake son sanin idan yazo."
Washe baki mutumin yayi,cike da farin ciki ya shiga godiya,
Shi kuma yaja motar shi tare da barin kofar gidan.

.......
Ummi bata falo tana cikin da yaran na shige ina jan kafata a hankali.
Ina shiga dakin na saka key zubewa nayi a kasa na sake kuka sosai, inayi ina karawa.

Sai da nayi ya ishe ni sannan na tashi na fada ban daki nayi Wanka, na fito nayi sallah Asr.

Ina idarwa zazzaɓi na rufa min, a cikin ledar har da pouse dina da wayata, sai wani farin takarda.
Dake ni ban cika son magani ba sai ya zama dole,, ɓalle maganin nayi nasha sannan na koma gado na kwanta, sosai nake jin jiki, gashi ba halin na haɗe kafana sai dai aware.

Sam Ummi bata san na dawo ba,sai dare lokacin zazzaɓi ya sauka min. Na lallaba dakyar na fito.
Kallona tayi cike da mamaki tace.
"Me yasame ki! Na kira wayar ki a kashe."
A hankali na taka kusada ita, na kwanta a jikinta, na sake kuka me cin rai. Jikin tane yayi bala'in sanyi, riko hannuna tayi ta zaunar dani, kamar na fasa ihu dan zafi. Tace,
"Meke damunki!? SAFINAH! kukanki Nan na meye? Wallahi ji nake zuciyata kamar zata buga."

Fuskana da dama sun jima da kumburi ta kalla, Bama kamar idanuna da suka koma sak na yan Chinese.

"Ummi kiyi hakuri!?"
Rungume Ni tayi a jikinta, tare da shafa bayana tana cewa.
" Ashraf ko!? Kiyi hakuri baya cikin kaddaranki ne shi yasa baku sami juna ba."

(Lallai Ummi ai kece bahuwa, dan yarki take gunshi ya durjeta son ranshi 😂🤣)

Kallon yarda da amincin da Ummi tayi min yau gashi naci amanar wannan yardan, zamewa nayi na kwanta akan cinyar ta. Ina sauke a jiyar zuciya. Sai nasiha take min, nan kuwa ina nan na gama zubda abinda take ce min.

Bayan ta gama min nasiha ta tashi ta kawo min abinci na tsakura kadan naci shima karya zarge Ni yasa nayi haƙa.

Ina kwance sai ga Dudu ya shigo gidan ido ya zuba min na kauda kaina daga gare shi, dan likita ne sai ya iya gano abinda na aikata.
Zama yayi kujeran shi na kallona, jinjina kanshi yayi sannan yace.
"Meye had'inki da gayen nan naji ance ya kawo yaranshi, wallahi ina baki matsayi ne na yayata, idan kika kuskura nayi fushi, SAFINAH zan miki mugun duka, Wallahi kinji na rantse miji."

"Koda wasa! Ko a mafarki kaga haka ya faru, kana tashi kayi sadaka. Ko bayan raina naji ka d'aga muryanka akan SAFINAH ban yafe maka ba! Babu wanda yafi karfin kuskure. Itama bata da yadda ta iya ne da zata dakatar da abinda ke faruwa da ita."

Jikinshi ne yayi sanyin, na tabbatar da Ummi zata san abinda na aikata, hmm da kanta zata bawa Dudu bulala ya zane Ni.
Kwanciya nayi ina jiyo fadar su Aanih da Aamih yara sun koma tankar kaji suna haɗuwa zasu hau rigima.
Tashi nayi ina cizon lips dina, a hankali na mike zuwa d'akina. wani irin kallo Ummi suke bina dashi. Me cike da Ayar tambaya(⁉️)

Har na wucce ta ta kirani.
Da sauri na dawo ina raba idanu nace.
"Gani Ummi!?"

"Hmm! Me yasa nemi!? Kike tafiya haka, SAFINAH ki rufa min asiri wallahi zuciyata bazata iya ɗaukar wata kasada ba wallahi, dan matukar kika sake lakato min magana tabbas gawata zaki samu sai hankalinki ya kwanta, Safinah me ya faru dake!?"

A rud'e na shiga shirya mata karya ina kuka nace.
"Wallahi, ina fita daga gida na samu me taxi shine muka hadu da sojojin, suna nasu hidimar kawai me motar ya shiga musulunci, shine suka masa duka mu kuma saka sakamu tsallen kwad'o, Ummi shine cinyoyina ke ciwo"

Na karshe mata da kuka, Ni kuka na na ƙaryata da nayiwa Mahaifiyata ce, ita kuma kukan tausayina take,

Kallona Dudu yayi sannan ya fita a gidan, d'akinta ta kaini. Ta haɗa min ruwan zafi ta kuma haɗa min da wani wanda zan fasa cinyoyina.
Sannan ya koma kitchen tayi min kunun tsamiya, wanda take da ajiyayyen tsamiyarta, sai farfesun kaza wanda take min na gyaran jiki.......


_Ku bani aron lokacin ku duk abinda zamu rubuta sai minyi bincike sosai akai muke rubutawa ban san sauran marubuta ya suke ba amma wannan labari nayi bincike da nazari na wata shida zuwa takwas. Na maida hankali sosai akan labarin sabida fidda wasu illolin da yake addaban rayuwar wasu, idan ban nuna wani abu akan SAFINAH ba, me karatu ba zai fahimci Illar dake tattare da wani abu ba, yau topic ɗin da ya ɗauki hankalin masu karantar labarin inda suka yi ta gwarani da tambaya wasu da kukansu kartayi zina!? Wannan kalmar tana min nauyi sosai ku biyo NI dukda na baku bouncing na labarin 😊☺️ karku yarda na kara kamaki a wani episode din San zan baku wahala kafin na duba korafanku ku bani goyan baya na kaiku har Jordan_
[27/02 5:17 PM] My 2nd Mtn: *number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah......

1️⃣9️⃣
    Komawa daki nayi na zauna a karkace ina kuka, sabida karya da na mata.

   Banko kofar yayi tare da saka key a Kofar gabana ne ya fad'i, tashi nayi na zauna ina bata rai.

   "Didih! Wallahi bazan zuba ido ki kashe mana Uwa ba, me yasa meki!?"

      Tab'e baki nayi cikin murya kasa ƙasa nace.
"Babu ruwanka dani."

      A fusace yayo kaina kamar zai rufe Ni da duka, duk sai na diririce, tare da kafe shi da ido.

   Kamar zai fashe da kuka yace.
"Don Allah ki rufa mana asiri karki kashe mana Uwa. Duk abinda zakiyi ya tsaya iya kanmu ban da mahaifiyar."

  Duk yadda yaso nayi magana fir naki cewa kome, ina kwance abuna. Fita tayi daga gidan ranshi na kara ɓaci.
       ★★★
  Tunda Ashu ya tab'ani ya nemi nutsuwarshi ya rasa, kamar ya biyo NI gidanmu yake ji, ga yaran shi da suke hannuna, kullum yana sintiri a cikin area dinmu.

          Yana addu'a na fito ya samu ya sunkume Ni yaje ya zungure Ni mai wato.
         ★★★
    Sati Daya kenan da fadar mu da Ashu, ina tsaka da gyara farcena suka shigo shida Abba sai fada yake akan me aka hana Ashraf shigowa. Sanye nake da atamfar Zahra riga da zani. Cas kayan yayi min.

            Zama yayi a kujeran dake kusadani yana cewa.
"Ai ina son mu gaisa ne sai a bani yaran nayi baki daga lebeno zasu ga yara."

  Ƙasa yayi da kai cikin kunyar karya, sanna ya cigaba da cewa.
"Inda Hali a bani aron Mamansu, na kaisu gurin bakin da suka zo su gaisa."

Shiru falon ya dauka ban dani wacce tsoron had'uwarmu.
Ke haifar min da faduwar gaba.

"Shi kenan Amma zaku tafi da Anas, yayi muku rakiya." Inji Ummi,

"Ummina nifa bani zuwa ko ina! Wallahi bana jin daɗin jikina." Na fada a sanyayye har kwalla na shirin zubo min,

Ita kuwa ta zata dan anki bani shi ne yasani k'in amincewa, sai ta b'ata rai har da fadar ta. Kuka ne ya kwace min, ina cewa.
"Don Allah karki ce min na bishi."

Abba akan dariya ya min cikin son ya zolaye Ni Yace.
"Toh Uwata! Ashraf ɗin kike kuka dan ya nemi tsakiyarsu"

Duk yadda naso musu bayani na kasa, haka suka sani a gaba na shirya muka fita, hmm mutumin da ya shirya taya yaro kamar Anas zai kawo mishi tsiko,

Gidan shin muka je ba wasu bane bakin, sai Ghaniyu da Fahad, sai me renon Yan biyu.
Suna ganin Anas suka shiga rena mishi hankali, tare da jera mishi kayan kwadayi, Yan biyun suna ganinsu suka haye jikinsu.

Takura kaina nayi gefe naki sanki jiki dashi, har suka fita a falon suka ja Anas zuwa can garden, suna fita ya dawo kaina.

Zama yayi kusadani bai ce kome ba, sai kallon tv yake. Ni kuwa tsabar tsoron shi, kamar yace kyas na zura da gudu.

Kallona yayi cikin son na sake dashi, yace.
"Ban dauko ki dan na kwanta dake ba, sai dai na nime shak'uwa dake! Idan yayi miki zaki ya sake jiki dani idan bai miki ba, zaki iya tafiya."

Ina zaune hannuna cukwaikwaye da hijab dina, sai raba ido nake.
Miqewa yayi tare da had'a Game, sannan ya miqo min pad din, shima ya rike d'aya ya fara Game ɗin, ganin har lokacin ban fara ba ya kalle ni, cikin nutsuwa yace.
"Kinga cire himar ɗin sai kifi sakewa, ki nutsu babu abinda zan miki kawai ina kewarki ne yasa na dauko ki, amma bawai na saki kuka ba."

Rike pad din nayi bayan ya zare min hijab dina.
"Masha Allah"
Ya furta, tare da cewa.
"Ki nutsu idan na cinyeki me zaki bani."

Kamar zan saka mishi kuka nace.
"Amma kace min ba abinda zaka min"

Dariya yayi yana kallon kallar dake bin idanuna alamun zasu sauko.
Saka yatsar hannunshi yayi ya lakuce kwallar da suka fara saukowa, yace.
"Kinsan me!? Karki min kuka idan kikayi bazan ji dad'i ba, zanga kamar na kuntatta miki ne Ni ba kukanki nake so ba, dan na san tunda abin nan ya faru baki walwala, hatta kariyar da kikawa. Da jinyar da Ummi ta miki SAFINAH ina sane da kome akanki kawai ki saki jiki muyi game dinmu."

Kallon mamaki da al'ajabi nake mishi tare da kasa da kaina nace.
"Eh nasan da haka amma taya kasan da haka!? Bayan ba gida daya muke ba."

Nuna min tv yayi tare da cigaba da kafta game ɗin shine, yana cewa.
"Labarin wata sarauniya da ta tafi da zuciyar Sarkinta! Tana dakyau a cikin jinsinta tana da jajjercewa akan abinda tasa kanta, bata da tsoro akan duk wani barazana, sai dai kash haɗuwa da Sarkinta yasa ta zama matsoraciya ta koma raguwa, me raina miyar zuciya."

Kallon shi nayi murmushi yayi tare da nuna min tv.
Sannan ya cigaba da cewa.
"So ya makantar da ita! So ya kashe mata zuciya. Bata da katabus sai yadda akayi da ita. Kin san wacece Sarauniyar."

Girgiza mishi kai nayi ina kallon shi.
Juyawa yayi ya kalle cikin idanuna yace..
"Kece!!! FINAH."
Kauda kaina nayi tare da maida hankalina kan tv. Sannan ban san me nake aikatawa ba, amma nasan ina hanya mara kyau.

"Muhammad! Bakayi karya ba! Amma kai kafini sanin abinda muke yi bai dace ba. Kayi hakuri dani kayi hakuri da abinda zan gaya maka ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login