Showing 54001 words to 57000 words out of 136985 words
firgigit ta miƙe kamar wata mahaukaciya sabon kamu tana waige waigen faɗin
"A ina nake? me ya kawoni nan? don Allah Aunty kiyi haƙuri WALLAHI ba da gangan na zubar da ruwan ba, don ALLAH ki yi haƙuri kar ki dakeni"
Wasu daga cikin Ɗaliban da ke tsaitsaye suna kallonta suka fara faɗin
"Ai na faɗa maku baƙaƙen aljanune da ita kuka ƙi yarda ai to yanzu dai gaskiya ta fito"
Hannatu tana kuka ta ratso students ɗin ta zo gaban Dijen ta tsaya tace
"Khadijah sannu"
Dije ta waiga ta kalli Hannatu tace,. "Me ya kawoni nan Hannatu??"
Malamin ya ƙura mata kallo yana nazarinta, sannan ya sa aka ta yiwa sauran masu aljanun addu'a suna tashi ɗaya bayan ɗaya, bayan komi ya lafa ya dawo wurin Dijen ya tambayeta minene asalin abunda ya haɗata da Ruƙayya, Dije ta zaro ido tace
"Wace Ruƙayya?? Ni fa banyi faɗa da kowa ba". Yace ba kiyi faɗa ba kika ji mata rauni har kika tsige mata tsoro ɗaya? Gashi a sanadin hakan kin janyo ta suma zaki faɗa ko sai na saitaki yanzu?"
Dije ta fashe da kuka tace,. "Ni fa WALLAHI Malam ba wanda nayi faɗa da shi ka tambayi Hannatu ka ji"
Malamin ya kalli Hannatu yace, "Au kenan da ke aka haɗu aka jiwa yarinyar mutane ciyo ko?"
Hannatu ta fara rantsuwar ita kam bada ita ba a tambayi kowa zai faɗa, daga nan ta yi bayanin yanda duk abun ya faru, Malamin yasa
wasu Prefects ɗin su rubuto masa sunan Dijen da duk wanda aka yi abun gabanshi tun farko, yace da su su kawo masa su gobe idan an tashi assembly, sannan aka kori kowa ya watse Dije ta miƙe da ƙyar suka nufi Hostel ɗinsu, don ranar kam gaba ɗaya labarin ake ta yi duk faɗin school ɗin inda wasu da yawa sunji daɗin abunda aka yiwa Rukayya saboda muguntarta, sai tsiraru ne suka ji tausayinta tare da jin haushin abunda Dijen ta yi mata cikin bainar nasi, yayin da wasu da yawa suka fara jin tsoron Dijen don gudun kada su ma ta yi masu abunda ta yiwa senior Ruƙayya.
Dije dai kam duk da ta yi mugunta amman hakan bai hanata jin tsoron makarantar ba, saboda tashe tashen aljanun da ta ga ana ta yi ranar ya firgitata sosai, musamman da dare ya yi ta kasa bacci har kowa yayi bacci ita ido ƙyamas zuciyarta cike da jin tsoro, aiko tana kwanarsu kwance kan gado ta ji takun tafiya ƙwass! Ƙwass! Ana tafiya da talkami ƴan'tsini ana karkaɗa awarwaro suna ƙara kuma direct wajen gadon da take kwance aka nufo, cikin tsananin firgici da tashin hankali ta sha jinin jikinta sai kawai ta ji an fisgi gadon da take an jijjigashi da ƙarfin tsiya, ana walili da gadon kamar fanka tare da ita anata zagaye ana faɗin
"Ba ke bace kike ƙarya da mu ba to gamu munzo me kike soooooo! me zamu yi makiiiiiii!"
Dije saboda tsabar tashin hankali sai addu'a take zubawa fili, sai dai kam in ta kamo wannan ta suɓuce ta saketa ta sake kamo wata haka ta dinga yi har ta ji anyi jifa da ita tun daga kan gadon har tsakiyar dogon ɗakin nasu, ba shiri ta ƙwallah wata arniyar ƙara tana faɗin
"Wallahi na daina bazan sake ba na tuba ku yafe mani wayyo Baffahna"
Tana cikin surutan ne ta ji an dafata ta zabura da sauri za ta zuba da gudu taji muryar Hannatu tana faɗin
"Ni ce Khadijah lafiya kike wannan uban ihun cikin daren nan?"
Dije ta tsurawa Hannatu kallo tuno abunda taji da kunnuwanta yasa ta ruƙunƙumeta tana faɗin
"WALLAHI mu bar makarantar nan aljanu ne da ita kasheni zasu yi Ni dai gida za'a kaini bazan zauna ba wayyo ALLAHna WALLAHI na daina bazan sake ba, an kashe kowa mu ne kawai muka yi saura"
Hannatu ta riƙo hannunta tace,. "Kalli ki ga? ga kowa nan lafiya ba abunda ya samemu kema tsoro ne kika ji tashi muje mu kwanta"
Wata senior ta zo ta riƙata ta tashi tsaye ta kaita kwanarta suka kwanta tare tana ta tofeta da addu'o'i saboda ba ƙaramin tausayi ta bata ba.
Aiko tun daga ranar Dije tasha jinin jikinta da lamarin duniya don ko malamin da ya tarasu don yiwa kowa hukunci bata ɓoye ba ta sanar da shi ba wasu aljanu ƙarya ce itace,. Amman kasancewar ganin irin ta'adin da ta yiwa Prefect ɗin yasa ba'a yarda da zancenta ba, an dai yi mata gargaɗi sosai akan kada ta sake in kuma ta sake za'a koreta makarantar bayan anyi mata horo mai tsanani, tsoron hakan yasa Dije ta sha jinin jikinta da kowa.
Ranar da aka yi visiting Hajiya Mama da Surry suka zo mata Visiting tare da uwar siyayya da abinci mai rai da lafiya da suka kawo mata, bayan zuƙa zuƙan namomin da aka soyo mata daban tare da wanda aka tsatstsago mata cikin miyar tumaturin da aka ciko mata wani ƙaton ƙaramin bokiti.
Sun sha fira sosai inda har ta gabatar masu da Hannatu Hajiya Mama ta yi ta murnar ganin Dijen ta fara rage ƙiriniyar da take yi, shiyasa ta yiwa Hannatu kyauta tare da ƙara nuna mata ta dinga fahimtar da Dijen abunda ya dace, da kuka suka rabu Dijen tana ta faɗin ita dai a kaita wurin Baffah'nta ta fasa karatun, da ƙyar Hajiya Mama ta zille mata suka tafi suka barta tana ta kukan ita garinsu take so ta koma ta fasa karatun bata son zama likitar.
Dije a hankali ta fara rage rashin jin nata saboda ita kullum dare da tsoro take kwana matuƙar ba tare da Prefect ɗin nan take ba, shiyasa kacokam ma ta koma kwanarta don tafi jin natsuwa idan tana tare da ita, saboda Senior Aysha ba dai addini ba sannan uwa uba tana da tausayin na ƙasa da ita sosai gata da natsuwa, don kuwa ita ko shirgin sauran ɗalibai bata shiga, iyakacinta karatu tare da zuwa masallaci da kullum jam'i baya wuceta saboda addini ya ratsa jikinta sosai.
Sannu a hankali shaƙuwa ta shiga tsakaninsu har itama Hannatun ta dawo wurinta suka yi zamansu hankali a kwance, idan zata je masallaci tare suke zuwa haka ma abinci bata jin ita senior ce da su take bajewa su ci abinsu, wanki ma itace take yi masu su iyakacinsu ɗaurayewa su shanya, ta kamasu ta kwance masu kansu ta tsantsara masu kitso mai kyau don tana jinsu tamkar ƙannenta na jini, musammam ma dai Dijen da yawan gashinta yasa take ƙara sonta saboda duk ta yi mata kitso sai an dinga zuwa kallonshi.
Gata iya gata Senior Aysha tana nuna masu hakan yasa Dije ta kwantar da hankalinta ta fara jin daɗin zaman makarantar, duk da wasu da yawa ma akan abinda ta yiwa Senior Ruƙayya Yusuf yasa suka daina shige mata da nufin cin zarafinta ko su sakata wani mugun aiki.
Don ko da aka yi hutu Dije ƙaguwa ta yi da ta dawo makaranta saboda mutuncin Senior Aysha da kuma ƙawarta Hannatu.
Watan Dije biyar a Yola da aka yi wani hutun second term Hajiya Mama ta shirya ta da uwayen tsaraba suka nufi ƘIRIU waton garinsu Dijen Baffah ɗiyar Inna Hasiya kanwar Usmanu mijin Hansai.
Ina yinku sosai mutanena😅🤝🏻
Akafta😛
D/AUTA Ce😊
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Ɗaukaka da baiwa ALLAH sai ya baka in ya so, babu Malami ba boka zaka zamo mafifici ko da maƙiyanka basa so, ilimi nagarta ke saka ɗan'adam sahun farko, babba ko ko yaro adalci ke saka ka yo ƙarko, daina hanzari magana jari salonta na ɗauko aha😉duniya rawar ƴanmata na gaba sai ya yo baya, inda lokaci zamani ba shi ɓoye baiwata🥴*
*Lamba ta 36*
Tun daga farkon shiga garin Dije ta fara hango mutanen da ta sani, aiko sai faman murna take yi tana ɗaga masu hannu, kafin kace me yara da abokan Dijen da ƴan makarantar allonsu duka sun biyo motar suna kuwwar faɗin
"Ga Dije, ga Dije, Dijen Baffah ta dawo ƘIRIU"
Direba da ƙyar ya samu wajen da ya raɓa ya yi parking saboda cincirindon yara da matasan ƴanmata har ma da wasu samarin duka, kowa fatanshi ya fara yin ido biyu da Dijen, saboda labarin da suka ji cewa Dijen ta yi aure gidan masu kuɗi.
Aikam itama Dijen cikin ƙaguwa ta ɓalle murfin motar ta fito bakinta a washe tana faɗin,. "Wayyo daɗi gani na dawo garinmu"
Aguje ta zanƙara da gudu ta yi cikin gidansu inda taci karo da Inna rik'e da zane tana ƙoƙarin yafawa yana zarmewa, saboda tsabar saurin taje ta ga Dijenta da taji anata ihun faɗin gata ta zo.
Suna cin karo Inna ta zaro ido cike da mamakin ganin Dijen tare da buɗe baki saboda tsabar farin ciki ta ma rasa me zata faɗa, Dije kam tsalle ta yi ta ruƙunƙumeta tana faɗin
"Wayyo ALLAHna daɗi kasheni gani ga Innata, yi huhu ina Baffahna ALLAH yasa yana gida"
Ta saki Inna ta yi cikin gidan aguje sai dai dole ta ci ƙaton birki saboda ganin ɗakin Baffahn a rufe, cike da jin haushi ta ɓata fuska ta nufo Inna da ke ƙoƙarin dawowa cikin gidan tana faɗin
"Bari inje in dubo Baffahna Inna idan mutanen sun shigo ki basu ruwa kafin ina dawo"
Inna ta yi saurin faɗin
"Au! Ki ce ba tare da mijin kaɗai kuka zo ba? To ki jira mana yana ƙofar gidan Maigari yanzu a je a kirashi ai tunda......"
Maganar ta maƙale ne saboda ganin yara sunata shigowa da buhuhunan shinkafa tare da sauran kwalaye, Inna ta bi yaran da kallo riƙe da baki zuciyarta cike da tsantsar farin ciki, sai ga sallamar su Hajiya Mama da su surry, da sauri Inna ta juya tare da washe baki cikin rawar jiki ta nufi ɗaki ta ɗauko sabuwar tabarmar ta shimfiɗa masu a kofar ɗakinta da yake share fess! Da shi, tana tambayarsu ya hanya tare da yi masu barka da zuwa, cikin sauri ta je ta ɗebo masu ruwa ga tulunta mai shegen sanyi cikin babban kwanon sha sabo dal, tayi masu farau faraun fura ta miƙa masu sannan ta dinga taimakawa yaran da har lokacin basu daina shigowa da kayan tsarabarba.
Dije kam tana samu ta fice ta nufi ƙofar gidan Maigarin ƙawayenta su Lanti da Hansai da Mune suka biyota kowa yana ƙoƙarin ya dai samu ya riƙa hannunta, ita ko sai wasar baki takeyi tana faɗin
"Hansai da Lanti kuna nan ku har yanzu baku yi auren ba ashe? Ina Jummala ko anyi mata auren?"
Mune tayi caraf tace,
"Ko sati biyu ba'ayi ba da aurenta ai, sai dai kam ko jiya da naje na isketa sai kuka take yi, ke baki ma sani ba tun ranar da aka kaita ta gudo cikin dare ta dawo gida, wai ita bazata kwana da Garbati ba tunda ɗan'iska ne"
Dije ta yi saurin faɗin
"To faɗi ba'a tambayeki ba, wai ke Mune har yanzu baki daina gulmar taki ba?, To ke yaushe za'ayi maki auren ne?, Amman dai Ni dai WALLAHI ina baki shawara ki daina yawan gulma nan kada watarana ki janyowa kanki a lakaɗa maki shegen dukan tsiya"
Mune ta yi shiru zuciyarta a cunkushe tace, "Ai gaskiya ce na faɗa WALLAHI ki ma tambayi su Hansai ki ji in nayi ƙarya"
Dije tace "Ni dai fa bance kinyi ƙarya ba amman na ce ki rage yawan surutunki na tsiya da baƙar gulmarki da kika saba, don Ni dai WALLAHI banga laifin Jummala ba haka kawai a kaika wajen Namiji ace ku kwana ɗaki ɗaya, don kawai salon ya lalataka azo daga baya ana faɗin ka zama ɗan'iska"
Hansai ta ƙyalƙyale da dariya tace,. "Cafɗi Ni ma fa wai an kusa aurena da Usmanu, amman Ni dai yasin har na matsu ayi a ƙare saboda nasan shi Usmanu ba ɗan'iska bane, Jummala dai kam sai haƙuri tunda Garbatin ya riga da ya tanbaɗe sai neman shiriya"
Lanti kam da tunda ake ta surutun bata ce komi ba, cikin sanyin jiki ta sauke ajiyar zuciya tace
"Ni WALLAHI har ma tsoro auren yake bani musamman yanda Jummala take ta kuka duk dare sai ta gudo Gidansu ana maidata, ni na rasa me ma Garbatin yake yi mata da har take jin tsoronshi"
Cikin tsananin tsusayin Jummalar Dije tace
"wai ina Ladiyo ita dai ai suna zaman lafiyarsu ko?"
Mune ta yi saurin faɗin "cabɗi ai billahillazi ko jiya sai da na taraddasu suna ta kokawa Duduwa tana rabasu suka ƙi bari, Bala sai zagin Ladiyo yake yi wai sai ta biyashi kuɗinshi da ta sata"
Dije da suke tafiyar a hankali suna firar ba shiri ta ja ta tsaya, cikin sabon ɓacin rai ta ce
"Wai kunsan wani abu kuwa??"
Dukansu suka ce "A'a"
Ta dafa kafaɗar mune tace,. "Na dafeki da alkhairi yau halinki zai yi man rana ko da ko ban biya kwandala ba, karkaɗe kunnenki da kyau kiji Mune Bala dai ashe kuɗi Malaminmu ya bashi shiyasa ya janye zancen aurenmu da shi aka ɗaura da Malam Safwan, ashe daman cen ba son ALLAh da Manzonsa ya ke yi man ba, don haka ki je ki yi ta yamaɗiɗi da wannan zance Mune na baki kyauta, kar ki yi sanya ina son kafatanin wannan garin kowa ma ya san da wannan sirrin da Balan Duduwa ya rufe lokacin aurena dashi, ki bankaɗe komi ƙawata kinji? Tunda har shi ya zama baƙin zalamammen banza kwaɗayayye"
Ba Mune da Dijen ta ke baiwa labarin ba har su Lanti sai da suka jinjina irin abunda Bala ya aikata, Dije zata sake yin magana kenan ta hango Baffah'nta da yake ta sauri tun daga nesa Bakinshi a washe, wanda ko tantama babu akan cewa labarin zuwan Dijen ne ya kai gareshi, aiko aguje ta zanƙara da gudu ta nufeshi tana faɗin
"Wayyo Baffahna Oyoyo Oyoyo wallahi nayi missing ɗinka"
Tana zuwa ta faɗa jikinshi, shi ma cike da tsananin jin daɗin ganinta yace
"Baƙin birni sannunku da zuwa yanzu nake ji ashe ko da gaske Dijengalata ce ta zo ganina"
Ya riƙo hannunta suka nufi gidan sai tsalle take yi tana wasar baki tana murna, su Lanti suka bi su a baya Hansai kam ta doje ta yi gida saboda kunyar surukuta da take yi da Inna Hasiya.
Ko da suka shiga sun taradda Hajiya Mama da su Surry cikin ɗakin Inna sun gama SALLAH, Inna ko sai haɗa wuta take yi tana jefa masu ɗanwaken da ta gama kwaɓashi a gaggauce, don kawai ta sami abun tarbar baƙinsu da shi saboda ita dambun gero ne ta yi tana ganin idan ta basu ƙila ba za su iya ci ba.
Baffah ya isa ƙofar ɗakin cikin farin ciki yayi masu sallama, sai da suka amsa sannan ya shiga yana yi masu sannu da zuwa tare da tambayarsu ya hanya?.
Cikin mutunta juna suka gaggaisa sannan ya fito Dije ta biyoshi a baya tana faɗin
"Baffah banga yaya Usmanu ba"
Ya waigo zuciyarshi fess yace
"Tun da safe ya je birni cin kasuwa kinsan yanzu a cen yake kasa kayan koli yana sai dawa tun lokacin da muka dawo garin Mijinki"
Dije ta washe baki tace,. "ALLAH sarki yaya Usman ashe an kara sanin ciyon kai"
Inna da take dakan toshshi ta goge fuskarta da jiɓin da feso mata tace,.
"Saura k'iris ma ya rage ayi aurenshi kinga shikenan kun zama ɗaya ba zancen wani gori bale har nan gaba ki ɗauka cewa ke ce yayarshi tunda kina ganin kin rigashi aure"
Baffah ya maka mata harara yace, "ko yau aka yi auren ai dai na Dije ne aka fara yi, don haka a daina yi muna wani feleƙe tunda har mu mun riga da mun yi ɗin ai kuma mun wuce wurin"
Dije ta washe baki tace,. "Shiyasa kullum sai nayi mafalkinka Baffahna saboda duk garin nan kafi kowa sona"
Mama Hajiya da ke ɗaki tana ji yo su ta yi murmushinsu na manya zuciyarta cike da sha'awar ahalin sabida barkwancinsu da kusan rabi duk Dijen garesu ta gado, uwa uba ma sun burgeta saboda ganin yanda suke nagartattun ma'aurata masu son farantawa junansu cikin barkwanci.
Fiddo kam sai yatsine yatsine take yi tana ƙarewa ɗakin Inna kallo, Hajiya Mama tana yi tana yi mata kashedi da ido amman duk da haka sai ta fakaici idonta ta yi guntun tsaki.
Baffah ya koma waje inda aka shimfiɗawa Direban tabarma gindin wani iccen dake ƙofar gidan, yana shan iska, ya zauna suka sake gaisawa a tsanake.
Dije ta nufi wurin Inna ta karɓi taɓaryar tana daka toshshin su Lanti suka karɓe suna daka mata, suna ci gaba firarsu ta yaushe gamo.
Bayan Inna ta kammala ɗan'waken ta zubawa Hajiya Mama ga sabon kwanon Samira, su Surry ma kowace da sabon kwanonta haka ma Direban da suka zo da shi, Dije kam dambun geron ta ɗauko ta fara ci Surry ta ce ta zo su ci ta ji don k'amshin dambun sai kai mata yakeyi a hanci, duk da ko shi kanshi ɗan'waken ba ƙaramin daɗi ya yi mata ba, aiko tana guma lomar dambun ta yi saurin faɗin
"Uh! uh! uhm!"
Sai data haɗye sannan ta ce "cabɗi ashe Khadijah da wayo kika so ki yi man wannan abu da daɗin gaske yake yasin"
Sai ci take yi abunta babu ƙyama cikinsu Dijen da Lanti da Mune da suka fara ci tare, Inna da su ko sai faman dariya suke yi mata da ma suka cenye Inna ta ƙaro masu sannan Baffah ya shigo da ledar ruwan sanyi har suraci suke yi, tare da lemuka irin na ƴan'birni da ya bada aka siyo masu babban garin da ke kusa da su.
Fiddo kam zurum ta yi tana kallon kwanon abincin ta kasa ci, Hajiya Mama da ke ɗakin Inna tana cin abincinta hankalin kwance, ta kalleta tace
"Ke ba zaki ci abincin ba ne??
Fiddo ta turo baki ta ce
"Gaskiya Ni bazan iya cinshi ba ku dai ku ci idan mun fita wannan ƙauyen sai a siyo man wani abu sai in ci"
Hajiya Mama ta wulla mata wata ƙatuwar harara ta ce
"WALLAHI muddin baki ci ba to har mu koma gida bazaki ci komi ba"
Fiddo cikin tsananin ɓacin rai ta ɗauki cokali ta ɗauko ɗan'waken cikin ƙyama ta kai bakinta, sai gashi yayi mata bazata don kuwa wani