Showing 117001 words to 120000 words out of 136985 words

Chapter 40 - DIJE ƘARANGIYA

09 Apr 2026

2087

kuka za ta fice Daddyn ya ɗaga hannu ya yafitota alamun ta zo wurinshi, da sauri ta dawo jikin gadon ta tsaya tare da riƙe kan gadon tana toshe kukan da ke ta fitowa a bakinta ta ce

"Don Allah Daddy ka yafe mani nasan na yi kuskure ka yafe man......."

Ya riƙo hannunta hawaye suna zuba akan fuskarshi ya ce, "me yasa kika aikata abinda zai janyo muna surutu a bakin mutane?"

Zee ta riƙe hannunshi gam ta durƙushe ƙasa ta ce "plss Daddy ka yafe mani abun kunyar da na janyo maku don ALLAH"

Baabaah Asabe ta fisgota da ƙarfi ta fiddata ɗakin sai da ta yi nesa da ɗakin Daddyn sannan ta wurgar da ita cikin fushi ta ce

"Na ƙara ganinki a ɗakin nan sai na baki mamaki WALLAHI, abun kunya kuma da kike so ayi haƙuri kanshi ke me ya hana ki yi haƙurin a lokacin da kika ji ɓacin ran da ya janyo kika yi wannan rashin hankalin?, Yanzu in Banda ALLAH ya taƙaita wahala kinsan iya adadin rayuka nawa zaki saka cikin ƙunci?? Bayan waɗanda zaki yi sanadin barinsu duniya? Ko ko an faɗa maki cewa idan kin kashesu ke ƙyaleki za'a yi?, To buɗe kunnuwanki da kyau ki ji gidana zaki dawo da zama daga yau har zuwa lokacin da Mijin naki ya ga dama ya nemeki, tunda don kinga Yaya Mani ya sake maki da yawa ne shiyasa kike ganin dai dai kike da kowa, to har abada na gaba yana gaban kuma ba zai taɓa dawowa baya ba, don gashi cen yanzu kin baro mata gidan tana jin daɗinta da mijinta ke kuma ga ki nan kunci zai kasheki tare da Iyayenki, to Ni dai WALLAHI wannan karon bazan zuba mako ido kina yin abunda kika ga dama ba, dole ne a nuna maki cewa ƴa ce ke kuma haifarki aka yi akwai na gaba da ke har gobe"

Tana ƙare faɗar maganar ta koma ɗakin Daddyn inda ta taraddashi sai shar ƙwallah yake yi, da ban baki da lallami ta samu ta shawo kanshi da ƙyar ya yi shiru, cikin nadamar irin damar da ya baiwa Zee a farko yake ta baiwa yar uwarshi haƙuri akan abunda ya aika akan Aminu, don itama tana cikin mutanen da suka yi fushi da shi akan auren sai dai don ance hannunka baya ruɓewa ka yanke ka cire inji hausawa fa, don kam a wannan zamani da muke ciki sau nawa aka yanke hannun aka jefar? ALLAH dai yasa mu fi ƙarfin zuciyarmu.

Zee ta daɗe durƙushe anan tana kuka har sai da Ruma ta zo ta ɗagata suka shiga ciki, inda suka taradda mahaifiyarta itama sai kukan take cisga gwanin ban tausayi, saboda takaicin abinda Zee ta aikata wanda tuntuni take nusar da Daddynta akan sangarcin da ya yi mata don ko kaɗan baya so a kyareta bale a nuna mata laifin da ta aikata ta gyara, to ga irinta nan yanzu ta janyo masu abun gori wurin mutane, Zee ta je ta rungume Mahaifiyarta tana wani irin kuka mai cike da ban tausayi, Mahaifiyar ta tureta har sai da ta faɗi ƙasa, sannan ta miƙe tsaye tare da nunata da yatsa ta ce

"Babban kuskuren da zaki aikata shine ki sake zuwa kusa da ni, don haka ki je tunda kin isa da kanki ki aikata duk abunda kike so, duniya ce wanda bai zo ba ma jiranshi take yi, kuma ta ishi kowa riga da wando har da zanen ɗaurawa"

Tana ƙare faɗar haka ta shige ɗaki abunta har da su dantse ƙofa, Zee ta sake fashewa da wani sabon kuka Ruma ta dinga bata haƙuri, amman ina yanayin da take ciki yafi ƙarfin ban haƙurinta, dole ta zura mata ido tana kallo zuciyarta cike da jimamin abun a ranta, tare da godewa ALLAH akan ƙoƙarin da ta yi wajen hana Zee cika burinta akansu Safwan da abunda zai faru ALLAH kaɗai yasan iyakacinshi akan matsalar.

****

Dijen Baffah kam ita da Malaminta sai cin amarcinsu suke yi hankali kwance, don ma masu zuwa jaje suna takurasu amman duk da hakan bai hanasu baiwa juna kulawa ba, cikin ɗan lokacin daga shi har ita sun sauya saboda natsuwar da suke samu da junansu, don shi Safwan ko tuno Zee baya son yi a ranshi, saboda ya riga da ya shafe babinta a rayuwarshi duka kuma yasa a ranshi duk runtsi ba zai sake zaman aure da ita ba, igiyar auren ce dai ta yi ta sha zamanta lafiya ko ita don ba ya iya saɓa umurnin Hajiyarshi ne da tuni ya cikasa mata ukunta ta huta.

Safwan kwance a falon Dije yana mayar da reply ga masu yi masa jaje ne ta fito ɗakinta cikin sanɗa ta zo bayanshi ta tsaya, sannan ta yi saurin duƙowa saitin kunnenshi cikin ɗaga murya ta ce

"Habiby!!!!!!"

Ba shiri ya zabura tare da jefar da wayar cikin firgicin da ta sakashi, Dije ta dafe ciki tana ƙyalƙyala dariya tana nunashi da hannu, cikin dariyar shi ma ya miƙe da nufin kamota ganin haka yasa ta fara gudu tana dariya, shi ma ya biyota yana faɗin

"Babyluv ki tsaya tun baki janyowa kanki aiki ba"

Dije ta dinga gudu sunata zagayen falon har ya ci nasarar cafketa suka faɗa kan kujera tare suna mayar da numfashi, Dije tana kyalƙyala dariya tace

"Don Allah Malam ka yi haƙuri ba zan sake ba"

Safwan ya cusa kanshi cikin wuyanta yana shinshino ƙamshinta idonshi a rufe ya ce

"Tunda baki tausayin kanki ai nima bana gajiya"

Dije ta yi sauri zaro ido tare da marairece fuska ta riƙe kunnuwanta duka biyu ta ce

"Am sorry my luv"

Idonshi a lumshe ya fara yamutsata tana zillewa tare da bashi haƙuri amman duk da hakan bai hanashi yin abunda yake so ba, bayan ya kammala ne ya koma faɗin

"Ke kika janyoni don haka dole ne ki yi haƙuri da halin Mijinki, faɗa man me kike so in yu maki ni ma wanda zan faranta maki tukuicin farin cikin da kike sakani?"

Dije ta zumɓuro baki wa je ta ce

"Baffah'na nike son in je in gano kwanan nan sai mafalkinshi nike yi"

Safwan ya zaro ido waje ya ce "canza wani don bazan lamunci doguwar tafiya da ke ba a yanzu, don ban sani ba ko na yi ajiya a jikinki ki zo ki jaza man jinya ba"

Dije ta ɓata fuska tace

"To Ni dai shi kaɗai nike so tunda na riga da na zana jarabawata da sai in ce ita, sai kuma in zaka kaini in fara karatun nursing ɗin tun yanzu"

Ya miƙe ya nufi ɗakinshi yana faɗin "in dai karatu ne har sai kin ce kin gaji amman tafiyar da kike so ce nake tantama, amman idan na yi shawara zan sanar da ke abunda na yanke"

Dije ta yi saurin miƙewa ta biyoshi tana faɗin "Don Allah ka barni inje WALLAhi na yi kewarsu Inna raboda da cen tun lokacin da Hansai ta haifu fa"

Ya yi saurin juyowa ya ce "to ke ma idan kin haifun ai sai ki je ba wani abu bane ba"

Dije ta fara kumbura fuska tare da rufe ido ta ce ",to Ni ina na isa yin cikin ma?"

Ba shiri ya fashe da dariya tare da dawowa inda take tsaye ya rungumota yana kallonta ya ce

"Baki isa ba ko?"

Ta ɗaga masa kai tana rufe ido, ya sake yin wani murmushi ya ce "Ok tom ya yi mu je in aunaki in gani in har da gsk baki isan ba"

Dije ta zare jikinta ta ce "A kaini Asibiti dai likita ya aunoni ai shi zai gano ban isa ba"

Ya ƙara janyota jikinshi ya sakar mata wani kiss a wuya ta zabura tare da kai masa wata kalar harara, ya yi dariya sannan ya ɗago fuskarta ido cikin ido ya ce

"A ganinki akwai wani likitanki bayan Ni Malaminki? To buɗe kunnuwanki ki ji, kinga waɗannan abubuwan sun ƙara cikowa"

Ya ƙare maganar tare da damƙo dukiyar fulaninta ta yi saurin lumshe ido, ya bita da kallo cike zallar ƙaunarta da sha'awarta da kullum take ɗibarsa, ya sake matso hips ɗinta ya ce

"Shi ma wannan ya ƙara buɗewa alamu sun nuna ni ɗin ba ƙaramin jarumi bane, don haka daga yanzu ki ɗauki kanki dai dai da matsayin mace mai ciki, saboda haka ba inda zaki je amman in har su ɗin kike son gani zasu zo har gidan nan ki gansu insha ALLAHu"

Dije ta yi saurin buɗe idonta tare da yin wani tsalle ta maƙalƙaleshi cike da tsantsar farin ciki ta ce

"Wayyo Habibyna shiyasa nike bala'in sonka"

Baki sake ya ce

"To bi a hankali kafin ki sanar da ni irin bala'in sona da kike yi don bazan lamunci a yi man asara ba"

Dije ta rufe idonta tace

"Wai da gaske cikin ne da Ni?"

Yana dariya ya ce "idan kina tantama ki bani nan da sati biyu zaki gasgatani"

Ta yi saurin barin wurin ta shige ɗakinta tana dariya wai ita kunya, ya bita da kallon ƙauna sannan ya shafo kanshi ya shige nashi shima saboda magriba ta kawo jiki kuma yana so ya sami jam'in SALLAH a Masallacin da ke manne da gidanshi, wanda bai wuce sati ɗaya da buɗashi ana sallah a ciki ba.









Tsuntsayen soyayya ayi a hankali kar ƙone wajen cinta da zafinta😝








Akafta👩🏻‍🦯







D/AUTA Ce ✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*



*Lamba 67*


Zancen Safwan ya tabbata don kuwa sati biyu bai cika ba Dije ta fara laulayi mai ɗan karen zafi, don kuwa ruwa ma idan ta sha sai ta amayesu, ga shi a lokacin Safwan ya fara zirga zirgar neman aikinshi, inda aka yi dace aka nemeshi Abuja interview, shiyasa ya mayar da ita wurin Hajiya amman ko da yaushe suna maƙale a waya har ALLAH ya dawo da shi, sannan ya kwashi Matarshi suka koma gida yana ci gaba da renon abarshi, don kuwa duk abunda take so baya jin nauyin dattijuwar da ke taya Dijen aiki yake zagewa kitchen ya yi mata, ko ba daɗi ta cinye tana santi daga baya kuma ta amaye tass!, Haka suke abu ƙaɗan ya ce sai sun je Asibiti an dubata don baya son ta zauna cikin gida da wata matsala a tattare jikinta, shiyasa duk wani abu sai ya nemi sani tare da shawarwarin ƴan Asibitin, duk da wani zubin yana biyewa son zuciyarta ya yi mata duk abunda ta ke so saboda kawai ta yi farin ciki, don ba ƙaramin jin jiki take yi ba, cikin haka ne Safwan ya tura direba ba tare da ta sani ba ya ɗauko su Baffah da Inna da Hansai da Usmanu don Gambo ta ce ita ta yi tsufa ba zata iya yin wannan doguwar tafiyar ba, duk da har a ranta ta so ace ta je ta dubo jikallenta, amman yanayin jikinta na tsufa yau lafiya gobe ciyo yasa ta haƙura ba don tana so ba.

Dije cike da mamakin ganin gidan wasu ƴan'uwansu Safwan da su Surayya a kitchen sai hidimar dafe dafe da soye soye suke yi, in sun sauke wannan su ɗora wancen gida ya runtume sai zuba ƙamshin garar da ake ta haɗawa su Inna ake yi, duk abunda aka yi sai an kawo mata ace ta ɗanɗana ta ji in ya yi, cike da mamaki take tambayarshi wai halan wasu baƙi ne zai yi masu muhimmanci shiyasa ake ta wannan hadahadar?, Yana dariya ya ce

"Ke dai ki ci ki ƙoshi ki sha maganin amanki ki je ki yi wanka ki tsalo kwalliyarki cikin sababbin ɗinkunanki"

Cike da jin daɗi ta fara cin wani dambun nama tana ci tana kaɗa kai alamun ya yi daɗi sosai, hannunshi riƙe da plate ɗin tana ci yana yi mata dariya, bayan ta ci abunda zata iya ci ne ya bata magani ta sha sannan ya je ya taimaka mata ta yi wanka, wanda ko shi ɗin sai da suka ɓata lokaci sosai sunata wasarsu ta ma'aurata, tare suka yi wankan suka fito sannan suka shirya cikin taimakekeniyar juna, kafin ka ce me sai ga su dukansu sun fito shar! Abunsu kowane sai tashin ƙamshi yake yi, duk da ta yi rama amman hakan bai hana kwalliyar ta yi kyau ba, don kuwa fatarta ta washe sosai ta yi haske dai dai jikinta, haka ma ta ƙara yin kyau masha ALLAH dukiyar fulaninta sun ƙara cikowa sosai a ƙirjinta, waɗanda a kullum baya gajiya da lalacewa akansu yana santin yanda suke ta ƙara hawa tamkar an hura masu iska ga taushi tamkar balombalom, dole ba don ta so ba take sakin jiki ta barshi ya yi abunda yake so don duk da ciyon ta wannan ɓangaren baya ɗaga ƙafa, a cewarshi wai duk wani maganin da zata sha bai kai wannan tasiri a jikinta ba, da wayo da lallami yake samun abunnda yake ƙulafuci, don idan ma ta ce zata yi tirjiya ma ba haƙura zai yi ba shiyasa take ta danne zuciyarta tana faranta masa, amman ita sam bata son damuwa a wannan lokacin da zai barta na tsawon watanni da tafi sha'awar hakan fiye da yanda yake manne mata akan biyan buƙatarshi.

Bayan sun gama kimtsa komi da ko'ina ne Safwan ya kawo falo ya ce ta zauna ta jirashi minti biyar kacal zai je ya tarbo baƙinshi ya dawo, aikuwa cike da mamakin da son ganin waɗanni baƙi ne haka?, Ta zauna tare da su Surayya suna kallo a falo suna fira jefi jefi, don ko ita ya ja kunnenta sosai akan kada ta sanarwa da Dijen zuwansu Baffahn ya fi so ta gansu unexpected, ai kuwa suna nan suka ji saukar motoci, Surayya ta yi tsalle ta kalleta ta ce

"Yau fa manyan baƙi ne da mu a garin namu"

Dije ta yi wata dariya tare da cewa "ai kam ga shi na ga alama don ko mu mun sheda da waɗannan manyan baƙi"

Surayya ta nufi hanyar fitq falon da sauri tana murna duk da itama cikin ne a jikinta, Dije ta bi ta da kallo ta ce

"Aunty Surayya dai ba'a girma ba har yanzu, da cikinki kike wannan uban rawar jikin ki je ki janyo muna jidali muna zaman zamanmu"

Surayya ta ɗaga murya kafin ta ƙarasa ficewa ta ce "ai sawun Giwa ya take na raƙumi wannan abun murnar dole ne mu nuna farin cikinmu"

Dije haka kawai ta ji ta kasa ɗauke idonta a ƙofar da ake shigowa falon, saboda jinta da take yi cikin ɗokin ganin su wanene waɗannan baƙin, ai kuwa sai ga Surayya riƙe da Abba yaron Usmanu wanda aka yiwa Baffah takwara da shi, cike da mamaki ta zaro ido cen sai ga Hansai bayan Surry, a zabure ta miƙe Baki a sake zata yi magana kenan ta hango Inna a bayan Hansai, aiko ba shiri ta fasa wata uwar kuwwa ta nufosu aguje tana kururuwa sai ga Baffah ta hango da Usmanu tare da Habibynta, cike da tsantsar mamaki ta dinga rufe ido tana budewa tare da murzasu tana faɗin

"Wayyo ALLAHna shin mafalki nike yi ko gaske?"

Hansai ta riƙo hannunta cike da jin daɗin ganinta ta ce

"Ido buɗe ne mune muka kawo maku ziyara"

Dije ta ruƙunƙumeta tana murna ta saketa ta nufi Inna ta faɗa jikinta tana ihun jin daɗi, ta saki Inna ta zo gaban Baffahnta ta riƙo hannunshi tana faɗin

"Ashe ko da gaske kai ne Baffahnah wayyo daɗi kasheni Ni Dije"

Usmanu ya hararota ya ce "ashe dai har yanzu da sauran hankalin?"

Tana dariya ta saki Baffah ta ce

"Yaya Usmanu ya zu fa na girma kai ma ka sani ai"

Surayya ta kai su Inna har falon sannan ta dawo ta ce da su Baffahn su shigo a gaisa kafin a kaisu muhallin da aka tanadar masu, Safwan dai tsaye kawai yake hannunshi a aljihu yana kallon Matarshi wadda ita har kullum bata gajiya da abun dariya, haka ma shagwaɓarta da wautarta suke ƙara dulmiyashi cikin ƙaunarta, waɗanda a cen inda aka fito yake ganin shirmenta amman sai ga shi yanzu sun yi masa rana, don kuwa salon ba ƙaramin burgeshi yake yi ba.

Bayan sun zazzauna ne aka sake sabuwar gaisuwa Dije baki yaƙi rufuwa saboda murna, Hansai kam sai yi take yi tana satar kallon falon saboda ganin tamkar ba a duniya take ba, don ko ita kanta Inna ta jinjina irin wannan daula da Dijenta ta ke ciki, shi kam Baffah ba ma maganarshi ake yi ba don sai hamdala yake yi cikin zucinshi akan wannan ni'ima da Allah ya wadata Dijenshi da ita.

Bayan an ƙare gaiigasawa ne Dukansu aka kaishi masaukinshi, Inna da Hansai aka kaisu wani ɗakin baki da ke cikin sashen Dijen, Baffah da Usmanu kam takanas Safwan ya yi masu jagora zuwa ɓangarenshi, inda aka kaisu wani ɗakin alfarma da aka haɗashi tamkar ɗakin wasu sarakuna don kuwa ya sha ado ta ko'ina sai ƙamari ke ta shi.

Sannan aka kawo masu abincinsu da aka tanadar masu kala kala, bayan sunyi Sallah ne suka fara lodawa cikinsu suna jinjina irin wannan uwar gara da aka tanada donsu kawai, Usmanu ya buɗe ƙafafuwa sai jan girki yake yi yana faɗin

"Ashe Baffah shiyasa kake ta farin ciki saboda kasan inda ka kawo ƴarka?, To Wallahi a ja kunnenta duk tsanani ta ci gaba da yi masa biyayya, don ko watarana ta yi masa shirme ya kaita ƙofar gida ya ce ya ce ta fi gida, to ta ce masa ita ba inda zata je don taga wurin zama, yana kaita tana dawowa har sai ya gaji don kanshi ya haƙura ya ƙyaleta"

Baffah nama cike da bakinshi ya ce "ba ma zata aika shirmen ba bale har akaita ƙofar gidan, don haka ka godewa ALLAH ka godewa Dijengalata don sanadinta ne kake cin wannan naman"

Haka suka dinga firarsu da suka saba cikin raha da tsantsar farin ciki da jin daɗin ganin Dijensu ta yi dacen aure.

Inna Kam da Hansai su ma suna inda aka saukesu Hansai tare da yaronta sai jan gara suke yi Inna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login