Showing 135001 words to 136985 words out of 136985 words
kowa sai nan nan ake yi da ita da kuma yaronta, don ma Gambo bata son ana yawan fita da shi don ƙa'ida ne kullum sai ta tofeshi da addu'o'in tsari, sannan ta ce dole itama Dijen sai ta tosheshi da addu'o'in saboda kariya daga sharrin mutum ko aljan da wasu masu kambun baki, saboda farin yaron da yanda yake kyakkyawa ga shi ɓul ɓul dole ne mutane su yi shaawarshi, sannan uwa uba ga shi fes fes kullum cikin shiga ta alfarma kuma irinta wayayyun ƴan birni.
****
Wasa wasa Dijen Baffah sai da ta yi wata biyu a garinsu sannan Angonta ya garzayo ya kwashi Matarshi da yaronshi suka koma Yola, suka bar su Inna da Baffah da mutanen garin da kewar Dijen da ɗan baturen yaronta mai kama da indiyawa samfurin larabawa kalar yan Ethiopia.
Hajiya Mama ba ƙaramin daɗi ta ji ba da ta ga yanda yaron da mamarshi suka yi sharr abunsu, cike da tsananin farin ciki ta karɓe shi tana ta yi masa wasa yana wasar baki, Fiddo ta karɓeshi tana faɗin
"Coming to your mama my beautiful boy"
Hajiya Mama ta kalleta tana dariya ta ce "in dai ɗanku ne ga shi nan don ma na yi maku kara na ɗauka?"
Fiddo tana dariya ta ce "WALLAhi Hajiyarmu son yaron nan Nike yi, don ALLAH ki ce da Yayanmu su tafi da Ni Abuja don bana son a rabani da shi ALLAH"
Hajiyar tana dariya ta ce "ki jira idan kunyi jarabawar ƙarshe sai ki tattara inaki inaki ki koma cen duka tunda ke baki fatar ki je naki gidan mijin sai taya wasu zaman aure"
Dije dai dariya kawai ta ke yi cikin dariyar ta ce "ai Insha ALLAHu acen ma zamu yi mata aure don bama fatar a raba uwa da ɗanta"
Safwan da ke shigowa ɗakin ya ce "ba inda zata je don tana kammala karatunta zamu auradda ita"
Fiddo ta zumɓuro baki ta ce "to ai Ni bani da miji"
Dije ta dafe baki ta ce "Mukhtar ɗin fa? Ko an ɓata?"
Ta miƙe tana dariya ta ce "yarona zo mu je tunda yau haɗe man kai ake yi a gidan"
Ta fice suka bita da kallo Safwan ya ƙaraso ya zauna suna ci gaba da firarsu kafin lokacin tafiyarsu ya yi suka tafi duka har Fiddon cen gidan nashi, inda Surayya da wasu yan'uwa suke acen suna tsumayin zuwansu.
Aiko shigarsu gidan mutane suka zo tarbarsu cikin farin ciki ana yi mata Barka da dawowa, Zee ta karɓe yaron tana ta juyi da shi Safwan ya riƙo hannunta ya yi mata raɗa ta yi saurin rufe ido, Dije ta bisu da kallo cikin gefen ido sannan ta shige sashenta tare da mutane tana dariyar yaƙe, Zee tayi sashenta da Sayyid tana ta murnar dawowarshi.
Dije kam tana shiga ta faɗa toilet tana share ƙwallar kishin da ya turnuƙota, sannan ta watsa ruwa ta ɗauro arwallah, bayan ta fito ne Surry ta ce "haba Hajiya daga zuwa ba wani jira sai shige abunki ki barmu a falo muna jiranki?"
Dije ta washe baki cikin ƙarfin hali ta ce "Tom bari in shirya in zo inji me da me aka tanadarwa baƙuwar?"
Surry ta riƙo hannunta ta ce "ki daina ɓoyo nasan me ke damunki to Aunty zee dai ciki. E da ita shiyasa kika ga yayanmu ya hanata wannan tsallen da take yi don kada ta janyo muna aiki, saboda haka plss a yafewa yayanmu don ALLAH, kada a lalace masa wannan dare da yake ta tsimayin zuwanshi"
Dije ta rufe baki cike da jin kunyar ganotan da surry ta yi ta ce
"Bafa wani abu Ni daman cen ban ji komi ba Aunty Surrynmu"
Surry ta fice tana dariya tace "ki dai zo ga delicious cen mun haɗa ma ku yana jiranku ke da Big bros"
Dije ta bita da kallo tana dariya sannan ta fara shiryawa tana jin daɗin cikin da aka ce ZEE tana da itama, don ƙaunar Sayyid da take yi yasa ko kaɗan bata kishin abunda zata haifo itama, Shiyasa ta yi mata fatan alkhairi a zucinta.
Bayan ta yi sallah ne tashirya cikin wani voil da yaji aiki tun daga sama har ƙasa sannan fara fesa turare sai ga Safwan ɗin ya shigo ɗakin, yana hangota ya ƙaraso ta bayanta ya rungumota a jikinshi, sannan ya sunsuno dogon wuyanta tare da sauke masa wani wawan kiss, ba shiri ta zabura tare da ɗauke wuta na wuccin gadi, sannan ta kai kallonta jikin madubin tana ƙare masa kallo cikin wani sihirtaccen kallon da shi kanshi baisan ta iya shi ba, ba shiri ya ji yar ya jikinshi tsikarshi ta miƙe, ya yi saurin kwantowa bayanta yana sauke hannunshi akan dukiyar fulaninta da suke cike fam, ta yi saurin runtse ido tace
"Da zafi fa"
Ya juyota a zafafe ya dinga tsotse mata baki tamkar zai cire mata shi, da kyar ta samu ya ta ƙwaci leɓenta sannan ta ɗago tana kallonshi ido cikin ido da wasu jajayen idanuwanshi da suka rine a lokaci daya, sannan ta ce
"Mu je mu ci abinci yana jiranmu"
Tana gama faɗar hakan ta zille ta fice ta bar masa ɗakin ya bi bayanta da kallo tare da dafe jarumarshi da ta miƙe tana kallon gabanta, ya nufi toilet minti biyar a tsakani sannan ya fito ya fice cikin wata kasala da ta diro masa.
Har suka ci abincin suka ƙare ba wata walwala a fuskarshi, yana ƙarewa ya shige ɗakinshi na sashen Zee sai dare sosai ya dawo sashen Dijen, inda ko da ya taradda ita har ta yi bacci ita da yaronta, cikin dabara ya ɗauke yaron ya kaishi cikin gadonshi ya ajiye sannan ya dawo kan gadon ya janyota jikinshi sai rawa yake yi,
Cikin bacci ta jiyo saƙonshi yana sauka ta ko'ina cikin jikinta, dole ta wartsake ta karɓi mijinta hannu bibbiyu suka dinga farantawa juna cikin farin ciki da ɗokin juna, ALLAH ya taimakesu yaron ya basu haɗin kai domin shi ma kanshi a gajiya yake shiyasa yake ta baccinshi su kuma suna ta shan soyayyarsu kan kari, don Safwan ya susuce akanta sosai sai zuba santin daɗi yake yi yana nishi saboda irin bala'in daɗin da yake ji yana ratsa koina na jikinshi, sun daɗe suna abu ɗaya har sai da Sayyid ya falka sannan suka haƙura ba don sun so ba.
Da safe ma ba ƙaramin rawar jiki ya yi akanta ba don ma yana kawaici baya don Zee ta ganoshi, gudun janyo wata sabuwar fitinar yasa kwanansu biyu a Yola ya tattara Matarshi da ɗan shi suka koma Abuja, inda suka ci gaba da jiyar da junansu daɗi tare da tarairayar juna kamar yanzu ne suka yi sabon auren, a gefe ɗaya kuma suna renon yaronsu da ko kaɗan basu son ganin kukanshi don inda hali ma ƙuda basa son ya hau kanshi.
Watan Sayyid huɗu Dije ta fara zuwa school saboda ƙulafucinta akan makarantar, dole aka nemo mata wadda zata dinga kula da Sayyid saboda hidimar karatun ba wasa ba.
*****
Bayan shekara biyar Dijen Baffah ta yi karatunta ta ƙare har ta sami aiki a wata babbar Asibitin da ke Abuja, sannan ALLAH ya sake bata wata haifuwar inda ta sami ƴa mace aka saka mata sunan Hajiya Mama ta ci sunan Sayyada, Zee ma ta yarinyarta ɗaya mai suna Ummusalmah itama tana aikinta acen Yolar cikin amincin ALLAH, Fiddo ma anyi mata aure har ya haifi ɗanta masha ALLAH, Surayya ma yaranta uku Husnah ma ta yi aure da ƴarta mai sunan Nasiba.
Zamansu lafiya har lokacin saboda akwai fahimtar juna sosai a tsakaninsu, shi ma kanshi Uban gayyar ya zama ƙaton Alhaji don kuwa daga shi har Matanshi duka sun sauke farali, Inna da Baffah ma da Gambo da Maigari duka sun je, a gefe ɗaya kuma Dije daga lokacin da ta fara karbar salary ne ta fara asusun gina makarantar boko da islamiya garin na su, ga alkhairin da take yi wa yan garin da guminta bayan na Maigidanta, izuwa lokacin su Ladiyo kansu sun zama wata tsiya a sanadin Ƙawarsu Dijen Baffah, sai dai kwatsam ALLAH ya aikowa Gambo rasuwa bayan gajeruwar jinyar da ta sha, Dije ta yi kukan rashin Gambo saboda wani jigo ce ta rayuwarta, akan hakane ta yi ƙudurin gina masallaci a ƙauyen hadiyya zuwa gareta, ALLAH ya taimaketa Alhaji Safwan ya dafa mata ta cika gurinta, mutanen garin sai sambarka suke yi tare da godiya ga Ubangiji da ya sanya Dijen da suke aibatawa a baya itace yanzu ta zamo silar jin daɗinsu, Usmanu ma ya zama babban ɗan kasuwa yana samu daidai gwargwado don ya riki kanshi da Iyayenshi har ma wasu suna jin dadi ta sanadinshi.
Dije ma Cikin ƙashin kanta da shekaru suka ja ta biyawa Usmanu da Hansai Hajji, bayan sun dawo ne wata shekara suka yi haɗaka da Malaminta suka biyawa ƙawayen Dijen, Ladiyo Jummala Lanti da Mune tare suka je da su ma ɗin kansu suka sake komawa tare da su.
Wata shekara ma da kanta ta biyawa uwargidan Maigarin hajjin ta je don har abada bata mance karayar da ta janyo mata ta yi a lokacin gudun kura da suka yi.
Hajiya Dije da ALHAJI Safwan a ƙauyensu Dijen mutane sai turuwar zuwa gayar da su ake yi a ƙofar gidan Maigarin da suka fara zuwa domin su gayar da shi, sai ga wasu yan bautar ƙasa an turo tare da doguwar takardar da aka ce akawowa Maigarin, Maigarin ya karɓa yana kallon Dijen da ke dariya cikin ƙasaita saboda tuno abunda ya faru a baya, Dije ta karɓa ta dinga karantawa cikin harshen turancinta irin na ƴan America, bayan ta kare ta fassara masu duk abunda takardar ta ƙunsa, gaba ɗaya wurin manya da yara samari da ƴanmata aka dinga yi mata tafi ana yi mata kirari irin na mutuntawa da zayyano irin halayen kirkinta ita da Mijinta, zuciyarta cike fess da farin ciki ta tashi ta fara nuna jin daɗinta a fili sannan ta yi kira sosai ga mutanen garin akan su jajirce su dinga saka ƴaƴansu a makarantar boko da islamiya, saboda su ma su waye su zamo dai dai da kowa adaina yi masu kallon ƙauyawa, ta yi masu nuni da kanta da irin nasarar da ta samu duk a sanadin bokon wanda su kansu shaida ne ba sai an sanar da su ba, sannan ta yi kira ga iyaye sosai akan su dinga haƙuri da halayen ƴaƴansu musamman marasa ji, Baffah'nta ma ya tashi ya yi dogon jawabi akan alfanun yi wa ya'ya addu'a kuma kada a gaji da yi madu addu'a aduk wani rashin ji ko wani abu mara kyau da suka aikata, don ALLAH maji roƙon bawanshi ne kuma aduk lokacin da aka roƙa zai amsa sai dai jinkirin sakamakon a wani lokaci, mutane da dama sunyi alwashin jajircewa sosai akan karatun ƴaƴansu, kuma sunyi godiya da abun alkhairin Dije da Mijinta garesu, nan suka fito da kuɗi suka rarraba wa mutane duk wanda Allah ya sa da rabonshi ya samu, don ko yan bautar ƙasar ma sai da Suka wankesu da alkharinsu da suka saba.
Tammat bi hamdullah anan na kawo karshen littafin na *Dije ƙarangiya* masu comments masu masu yiman addu'a da masu yiman sharing book din a groups Kuma na gode sosai sai mun hadu a littafin na kuɗi mai suna *GIDAN AURE* littafi ne wanda ya kunshi rigingumun gidajen aurenmu a yau da kuma ma wasu abubuwa da baki bazai iya faɗa ba, masoyana masu son bin books ɗina a Koda yaushe idan kuna buƙata zaku sameni ta wannan numbar sai mu yi magana 09032685442 sai kuma na Free da zanyi don ku masoyana shi ma mai suna *SHAGALLIYA* wanda shi ma ɗin cike yake da barkwanci da nishaɗi ba kaɗan ba kusan ince fiye ma da Dijen Ƙarangiya, don haka ku ci gaba da bibiyata Ni *HADIZA IBRAHIM D/AUTA wadda wasu suka fi sani da PRINCESS DIJA* zaku iya nemana ta wattpad kamar haka *Princessdija246*
INA SONKU SOSAI MASOYANA ADUK INDA KUKE KUMA A DUK INDA KUKA KASANCE🤝🏻