Showing 81001 words to 84000 words out of 136985 words
cen, haka ya yi ta zagayen wuri wuri amman ko mai kama da ita bai gani ba, dole ya yi parking ya fito dafe da kanshi da ke yi masa mugun sara gashi dare ya fara yi da ke yi, saboda tsabar tashin hankalin da yake ciki sai waige waige yake yi a tunaninshi ko zai hangota, yana cikin hakan ne ya ji wayarshi ta yi Virbration cikin sauri ya ɗaukota tsammanin Hajiya ce zata sanar da shi cewa ya dawo an ganta, sai kawai ya ji Muryar Zee tana kuka tana faɗin
"Munafukin banza baƙin mayaudari ashe daman kai maƙaryaci ne ban sani ba? To asirinka ya tonu yau gaskiya ta fito labarin aurenka ya zo kunnuwana, ashe daman cen kana da Mata shine ka ɓoye man, to ka sani na tsaneka na tsaneka tsana mafi muni a rayuwata"
Ƙitttt ta kashe wayar, cikin wani sabon tashin hankalin da ya ƙara ziyartoshi ba shiri ya kai zaune daɓas ƙasa dafe da kai yace
"Kai wannan bala'in da me ya yi kama wayyo ALLAHna khadija ina zan ganki WALLAHi ina sonki don ALLAH ki dawo gareni plss!"
Ni ma dai tashin hankalin yasa alkalamina ya faɗi ba shiri🙀
Akafta🤪
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Kar kuji komai allurar ƙarfi aka yi man😂😂😂😂😂shiyasa na zauce hannuna ya HAUKACE yana ta suburbuɗo maku typing, ku sha sha'aninku kawai kafin Nima in sha nawa idan allurar ta sakeni yasin😝*
*Lamba ta 49*
Dijen Baffah kam tunda ta fito ɗakinshi ta nufi ɗakinsu cikin dubarar rufe fuskarta da ɗankwalin doguwar rigar da ke jikinta, ta ɗauko jakarta da kuɗin liƙinta suke ciki ta rataya, ta fito kamar wacce zata shiga wurin walimar ta fice gidan cikin sauri ta tare Napep ta haye sai babbar tasha, ta ce motar garinsu take nema aka ce da ita sai dai ta Gombe idan taje sai ta shiga motar Kano, daga cen sai ta shiga motar da zata kaita babban birnin garinsu, cikin rashin tsoro ta faɗa motar jikinta yana rawa ta tambayi kuɗin motar aka faɗa mata ta biya, da aka zo wajen rubuta suna da numbar waya kamar tasan za'a nemeta ta rubuta sunan ƙarya da numbobin banza, tunda ita ko wayar ma bata da bale ta yi number, zuwanta bai wuce minti goma ba motar ta cika suka tafi don ko da tara na dare ta buga tana garin Gombe, sai da aka je cen ne wani tsoro ya shigeta saboda batasan inda zata je ta kwana ba, ta rakuɓe gefen wata mota tana ta sharar ƙwallah saboda motar da taga za'a hau a lokacin kuma a ce wai tafiya za'a yi cikin daren, tana nan tsaye sai ga wani ɗan union ya zo yana faɗin
"Ina zaki je ne Kano ko Kaduna ko Bauchi Sokoto ko Zamfara?"
Dije ta yi saurin goge ƙwallarta tace "kano"
Yace "to zo mu je ga motocin Kano cen ina kayanki?"
Tace "babu"
Ya yi saurin waigowa yace, "bangane babu ba an sace kayan ne ko yaya?"
Ta ce "bani da kaya"
Ya ce ",to ai sai ki yi bayani yanda zan gane zo mu je kar motar ta tashi don ta kusa cika"
Dije ta bi bayanshi har inda motar take aka yi mata mazauni ta yi tsalle ta shige saboda ƙatuwar mota ce, ta sami wuri ta rakuɓe tana muzurai saboda tsoron yanda za'a bi hanyar zuwa wani gari cikin daren, zamanta ba wuya aka tada motar suka kama hanya, tafe take tana addu'ar ALLAH ya kaisu lafiya har bacci ya yi awon gaba da ita, ga masifar yunwar da ta addabeta don rabonta da abinci tun Yola.
Cikin ikon Allah Asubar farin suna isa Kano, bayan an saukesu mutane da yawa suka fara arwallah domin su yi SALLAH, itama ta bi sahun mutanen ta siyi ruwan ta yi arwallah ta yi SALLAH duk da masifar ciyon da kanta take ji, sannan ta tambayi wani ina ake shiga motar Katsina, ya yi mata jagora har zuwa inda motocin suke ta ƙara ce da shi "don ALLAH Malam ina zan samu abinci inci WALLAHi yunwa nike ji sosai" ya ce ta zo su je ya nuna mata wani shagon sayar da abinci, aiko ta bishi har zuwa wani ƙaramin shagon, yace da ita ta shiga ta zauna ta jirashi ya kawo mata abincin, ba wani tunani ta shige shagon ta zauna tana kallon mutanen da ke wulgawa ta Kofar shagon, ƴan mintuna a sai gashi ya dawo yana wata dariyar rashin gaskiya, yana zuwa ba wani jinkiri ya rufe shagon, cikin tsoro Dije ta ce
"Ina abincin ?"
Ya sosa kanshi yace
"Ki fara bani naki abincin sannan sai in je in kawo maki nawa kafin lokacin ma mai abincin ta kammala"
Dije cikin mamaki tace
"Ni ina naga abincin da zan baka?da ina da shi ai bazan tambayeka ba"
Ya yi sake yin wata dariyar shakiyanci yace
"Ke ko kike da abincin ci ki natsu kawai mu gama komi cikin lokaci kafin mutane su fara cika tashar"
Dije ta zaro ido cikin tsoro tace, "WALLAHi ko ka bani hanya in fita ko yanzun nan in yi maka sanadin barin duniya"
Cikin dariya ya nufota zai cafkota ta zille ya sake yunkurin kamota ta ɗaga jakarta ta buga masa ita iya ƙarfinta, aiko cike da jin haushi ya damƙota ta fasa wata uwar ƙara, shi ko ba kunya sai ƙoƙarin mannata da jikinshi yake yi, ganin da gaske keta mata haddi yake so ya yi ta fasa wata uwar kuwwa bakinta a sake sai ihu take yi, suna cikin kokawar ne aka banko Ƙofar shagon da ƙarfi ta buɗe ya yi saurin kallon ƙofar yana muzurai, Dije ta yi waje da gudu a firgice ko ɗankwali babu bale takalmi, jikinta sai rawa yake yi tana faɗin
"WALLAHi sai na kasheka azzalumi shegen banza ɗan'iska"
Mutane suka taru a kanta saboda ganin yanda take ta kuka tana tsine masa, sai tambayarta ake ba ɓata lokaci ta yi bayanin duk abunda ya haɗa su, aiko nan take mutane suka yi ta tsine masa suna aibatashi, wani ya shiga ya ɗauko mata jakarta da talkami da ɗankwalinta ya bata ta saka, sannan wasu matasa suka rufeshi da duka, cikin tausayinta wani bawan ALLAH ya je ya siyo mata tea da biredi ya kaita wani waje ta raɓa ta sha, sai dai tana gama sha amai ya biyo baya ba shiri ta fara rawar sanyi, mutumin ya siyo mata magani ta sha sannan ya sakata motar katsina sai da motar ta tashi sannan ya tafi yana jinjina halin wasu iyaye masu yiwa ƴaƴa riƙon sakainar kashi, su yi ta sakin ƴaƴansu duk inda suka ga dama.
A galabaice Dije ta isa babban birnin garinsu ta shiga motar da zata kaita ƙauyensu, har ƙofar gida Direban ya kaita saboda babu ko sisi a hannunta duk mota ta cenye kuɗin, asalima ko kuɗin zuwa katsinar ma sai da wata mata ta cika mata da nata basu kai ba, cikin tsananin galabaita ta faɗa gidansu yaran da suka biyo motar suka bita suna ihun ga Dije ga Dije amman ko ta kansu bata bi ba.
Tana shiga kai tsaye ɗakin Inna ta faɗa ta haye gado ta dunƙule cikin zane tana rawar sanyi, Inna daga bayi ta jiyo muryar yara suna ta kuwwar zuwan Dijen, jikinta yana rawa ta nufi ƙofar gidan inda suka ci karo da Hansai da itama ta fito daga sashenta aguje cikin murna da ɗokin ganin Dijen.
Amman basu ganta ba sai Direban da ya kawota kawai da ke ƙofar gidan yana bada saƙon a karɓo masa kuɗinshi tafiya zai yi, Inna ta tambayi yaran ina Dijen suka ce tana cikin gidan ta shige ɗaki, gaban Inna ya ƙire ya faɗi saboda jikinta ya bata cewa ba zuwan lafiya ne Dijen ta yo ba, cikin sauri ta kwance ƙullin da ke haɓar zanenta ta re da tambayar nawa ne kuɗin?
Direban ya faɗa ta bashi ta yi masa godiya cike da rawar jiki ta koma cikin gidan gabanta sai faɗuwa yake yi, sai dai tun kafin ta isa gadon ta jiyo sautin nishin Dijen, da ke ta rawar sanyi haƙoranta suna haɗuwa suna karkarwa, cikin sauri Inna ta zauna ta re da yaye rufar da ta yi ta taɓa wuyanta ta ji zafi zau!, Cikin faɗuwar gaba tace
"Dije lafiyarki ku wa?ina Hajiyar? Ya aka yi kika zo ke kaɗai bayan kuma nasan buki kuke yi?"
Dije cikin rawar baki hawaye suna zuba gefen idonta tace,. "Ni kaɗai nake ai"
Hansai ta shigo jiki a sanyaye ta zauna gefen Dijen tace, "Sannu Dije baki da lafiya ne?"
Dije ta ɗaya Kai Inna ta miƙe ta je ta ɗauko mata magunguna ta matsa mata sai da ta sha sannan ta koma ta dunƙule, Inna ta kalli Hansai tace
"A sami yaro a aikashi gidan Maigari ki ce ya zo gida ana nemanshi"
Hansai ta fita Inna ta dawo ta sassafta murya tace, "Dije faɗa man gaskiya kafin malam ya zo shin Mijinki rabuwa ya yi dake ne ko yaya?"
Dije ta yi saurin girgiza kai tace,
"A'ah Inna ba ma wanda yasan na tafo"
Inna ta sake jin wani sabon fargaba, ta tada ita zaune tace "Kallanni da kyau Dije bana son Baffahnki ya shigo baki sanar da Ni gaskiyar abunda yake faruwa ba"
Dije ta ja jikinta ta jingina da bango tace,
"Ba rabuwa ya yi dani ba Inna amman WALLAHi ni na gaji da aurenshi tunda yake son ya lalace mani rayuwa"
Inna ta zaro ido waje tace "bangane ya lalace maki rayuwa ba? ki yi man bayani dalla dalla yanda zan gane"
Dije ta share hawayenta tace
"Inna jikina yake taɓawa WALLAHi har kayana ya tuɓe yanata yi man wani iskanci a jiki........"
Ba shiri Inna ta kai mata wani bahagon mari a baki cikin fushi ta nunata da hannu tace, "au Wai daman akan wannan dalilin ne kika gudo tun daga Yola har zuwa garin nan? To buɗe kunnuwanki da kyau kiji WALLAHI matuƙar kika ce bazaki iya yiwa Mijinki biyayya akan duk abunda ya zo maki da shi ba, to Ni Ko ko kaɗan ba zamu shirya da ke ba"
Dije dafe da gefen da ta sha marin cike da mamaki tace, "Inna WALLAHi har ƙirjina yake taɓawa yana ƙoƙarin cire mani ɗan kamfai, kuma ma har dukana yake yi fa"
Inna ta wurga mata wata ƙatuwar harara tace, "abunda ya fi duka ma idan ya yi maki kin cancanta ai, to bari kiji duk abunda kika ga ya yi maki ko yana ƙoƙarin yi dake to tuni Baffahnki yayi hakan dani, kuma gani daram har yanzu kin ganni ba abunda ya sameni, don haka tun wuri WALLAHi ki shiga taitayinki miye amfanin karatun da kike yi?, Saboda haka tun kafin ki janyo wa kanki abun gori cikin mutane, sannan ki tsallake Hajiya ki nufo gidan nan ke kaɗai ko tsoron abunda zai sameki a hanyar baki ji ba, yanzu da wane ido kike so mu kalleta ace kin tsallaketa akan wannan guntuwar matsala kin nufo gida?. "
Dije ta zumɓuro Baki tace, "kedai Inna don baki san me yake yi mani bane shiyasa"
Inna ta buge mata baki tace "ina ko zan sani tunda ban taɓa yin auren ba, to bari kiji in baki sani ba ki sani shekarun baya akan wannan dalilin ne aka ɗaure Jummala, ke ma idan kina son ayi maki haka to WALLAHi ko a cikin ɗakin nan zamu iya ɗaure masa ke, ya yi duk abunda yake so da ke tunda ba zunubi ne zai aikata ba"
Dije ta zaro ido tace
"Inna yanzu daman akan haka ne aka ɗaure Jummalar? Cabɗi to WALLAHi gaskiya kam ba'a kyautawa rayuwarta ba, to ni dai WALLAHI bazan taɓa bari wani ƙaton banza ya yi iskanci da Ni ba ina kallo in ƙyaleshi ba"
Inna ta sake Kai mata wani marin wanda ya yi dai dai da shigowar Baffah tana faɗin
"Mu zaki tonawa asiri Dije?"
"Wane asiri zata tona bayan yanzun nan muka gama waya da Uwar mijinta an sanar da ita Dijen tana nan saboda ta ɗaga hankalinta sosai akan rashin ganinta, don haka ki bar yarinya ta huta da wahalar motar da ta kwaso sannan ki fara dukan nata tunda ke hannunki bai girma da bugunta"
Ya ƙaraso wajen Dijen ya shafo kanta yace, "Dijengalata me yasa kika baro cen ba tare da sanin Mijinki ba"
Dije ta fashe da wani sabon kuka, Inna ta ce da Baffahn ya zo ya ji suka fita tare har zuwa ɗakinshi, cikin ɓacin rai ta sanar da shi dalilin da ya dawo da Dijen, Baffah ya yi shiru yana nazari saboda shi tsammaninshi ma tuni an wuce wannan babin, ashe yanzu ake matsalar ya sauke ƙatuwar ajiyar zuciya yace
"A gaskiya yaron nan ya yi haƙuri da yawa WALLAHi, amman ita kuma a hankali zaki fahimtar da ita ba da duka ko faɗa ba, saboda yanzu haka mijinta yana kan hanyar zuwa garin nan, kuma da ya zo nike son ta bishi su koma don banga amfanin zaman da zata yi muna anan ba"
Inna ta sauke ajiyar zuciya tace, "ALLAH ya kawoshi lafiya amman kasan dai ko kaɗan bata kyautawa Hajiya ba ko?, Ace duk dawainiyar da take yi da ita amman ta tsallaketa ta zo wurinmu akan wannan guntuwar matsala"
Baffah yace
"Haƙuri za'a yi kuma yanzu tunda dai mai afkuwa ta riga da ta afku, sai a kira ita Hajiyar a bata haƙuri shi kuma idan yazo mu bashi haƙuri ya tafi da matarshi"
Inna sauke wata ajiyar zuciya tace "ALLAH ya kawoshi lafiya sai dai ni naso ace a barta ta yi kwana biyu anan, saboda in fahimtar da ita abubuwan da suka shige mata duhu"
Baffah ya ce "aganinki ba za'a ga munyi ƙaranta ba?"
Inna tace "izininshi zamu nema ai saboda duk abunda zai sa ta kamo hanya tun daga cen har nan to abun ba ƙarami bane, saboda haka don ALLAH idan ya zo ka nuna masa kana son a bar Dijen nan ta ɗan kwana biyu"
Baffah cike da mamakinta yace, "ke fa kika ce da ni ga dalilin da yasa ta gudo to kuma yanzu sai ya zo tafiya da ita kuma muce a barta ta yi kwana biyu?, Ni fa bana son abunda zai sa mutanen nan su ga rashin kyautawarmu, ko dai akwai wani abu bayan wannan ne?"
Cikin damuwa Inna tace, "babu wani abu amman kasani ko yanzu tsugunne bata ƙare ba, matuƙar ta koma ba tare da an fahimtar da ita minene auren ba da abunda ya ƙumsa, saboda ina jin tsoron tace zata sake biyo doguwar hanyar nan ita kaɗai ko don gudun wani abu mara kyau ya sameta"
Baffah ya yi shiru yana nazari sannan yace, "to kuma Hasiya kin yi nazari anan, to ALLAH yasa shi ma idan ya zo ya amince ya bar muna ita ɗin"
Inna tace "ai nuna masa ɓacin ranka zaka yi akan sakacin da ya yi har ta biyo wannan uwar hanyar ita kaɗai"
Baffah ya yi saurin faɗin, "kar fa ki janyo inji kunya wajen surukina?"
Inna tace "ba wani jin kunya hakan da zaka yi shine zai ƙwatowa Dije ƴancinta, saboda gobe ya ji tsoron ƙara yin sakaci da ita har ta biyo hanya ba tare da sananinshi ba"
Tofa Inna uhum da kinsan halin da mijin Dijen yake ciki da ba ki ce haka ba😔
Akafta😉
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*DOMIN JIN DAƊINKU MASOYANA ku natsu tsaf ku ci gaba da kwasar ganima😂😝*
*Lamba ta 50*
Safwan kam firgicin da yake ciki ne yasa ya baje ƙasa cikin kiɗimewa yana ta sambatun kiran sunan Dijen, tare da faɗin
"Ina kika shiga ne don ALLAH ki dawo wallahi ina sonki ke ma kinsani ai"
Har dare ya raba yana ta abu ɗaya zuwa lokacin mutane sun fara taruwa kanshi ana tambayarshi mafari, da dai ya fahimci ya tarawa kanshi ƴan kallo ne ya tashi ya faɗa Motarshi ya nufi gidansu wani ɗan uwansu kuma abokinshi, cike da tsantsar tashin hankali yake yi masa bayanin duk abunda yake faruwa, Abokin nashi ya jinjina abun a ranshi sannan ya ce
"A gaskiya Abokina ka yi kuskure babba yanzu mafita ɗaya ce ka je ka baiwa Hajiyar Haƙuri kafin ka kama hanyar zuwa garinsu yarinyar, saboda jikina yana bani ta yi gida don ta gaji da abunda kake yi mata ne shiyasa ta gudu"
Sannan Safwan ya tuno da wayarshi ya ɗaukota da nufin kiran Hajiyar sai ga kiran Lawi da Kamal ya fi ashirin a wayar, cikin sauri ya kira Lawin da rawar baki yake faɗin
"An ganta?"
Lawi murya mai cike da damuwa yace "WALLAHi ba'a ganta ba ni na fara zargin ko ta yi garinsu"
Safwan ya dafe kanshi cikin wani sabon firgici yace,. "Don Allah Abokina ka roƙar mani Hajiya in dawo gidan in bata haƙuri WALLAHi gobe tun da sassafe zan kama hanyar garinsu Khadija in dawo da ita"
Lawi yace "kayi haƙuri Abokina WALLAHi Hajiya ta shiga damuwa sosai akan ɓatan khadija yanzu haka ma da ƙyar na lallasheta ta daina kuka, ga gidan gaba ɗaya hankalinsu ya tashi madadin farin ciki gida ya koma na jimami"
Safwan a kiɗime ya kashe wayar tare da furta "Innalilahi wa'Inna ilairraji'un Allahumma la sahla illa maja'altahu sahla, ALLAH ka tsare yarinyar nan a duk inda take, Ubangiji ka bani ƙarfin gwiwar tunkarar wannan mummunar ƙaddara da ta faɗowa rayuwata"
Ya kalli Abokin nashi da jajayen idanuwanshi yace, "bari inje Mubarak banga ta zama ba tunda har nine na janyo komi"
Mubarak cike da tausayinshi yace, "ba dai yanzu kake nufin zaka bi bayanta ba?"
A zafafe ya faɗa motarshi yana faɗin "banga ta zama ba ai kuma matuƙar ba ganin yarinyar nan nayi ba....."
Kiran wayarshi ne ya katse maganar da yake yi cikin sauri ya ɗaga saboda ganin numbar Hajiyarshi ce, kafin ma yayi magana yaji muryarta cikin muryar kuka tace
"WALLAHi matuƙar baka dawo man da yarinyata ba to kada ka kuskura ka tako ƙafarka cikin gidan nan"
Cikin rawar murya yace, "ki bini da addu'ar tsari kawai Hajiyata, nayi maki alkƙawali bazaki ganni ba sai tare da Khadija insha ALLAHu"
Kittt! Hajiyar ta kashe wayar saboda wani kukan tausayin kansu da ya kamata, Surayya dake ta bata haƙuri ta yi saurin faɗin
"Don girman ALLAH Hajiyarmu ki yi haƙuri Insha ALLAHu ba abunda zai sami Khadijah ALLAH zai kareta a duk