Showing 123001 words to 126000 words out of 136985 words
tare da yi mata kashedi da gargadin cewa duk ta yarda Daddynta yasan halin da take ciki a gidan gwaggonta sai ta tsine mata, tana kuka take komawa yanzu har ta haƙura don kanta ta daina gudun, ganin hakan yasa Gwaggon ta fara sassafta mata daga matsin lambar da take yi mata, don kuwa ta ladaftu sosai kuma ta gano irin kuskuren da ta so aikatawa, ta yiwa ALLAH godiya da yasa Ruma bata bari ta aikata mugun abun da ta yi niyya ba, ga shi ta rasa Safwan ɗin kuma Aminun ma ta rasa shi don kuwa yanzu haka ƙawarta Sadiya yake aure, don Ruma ya so aura ta nuna masa amincinta da Zee bazata iya aurenshi ba, Sadiya kam hannu biyu ta karɓeshi yanzu haka da ƴarsu tana nan mai sunan Mahaifiyarshi.
Zee ta shiga damuwar rashin jin Safwan ɗin da kullum take tsumayin zuwanshi gareta ya ce ta dawo, amman shirun da ta jini yayi yawa ne ta fara tunanin binshi da kanta, don laifin da ta aikata masa ko ma wanene dole ne ya sallamata, kasancewar tasan numbarshi akanta yasa da Ruma ta zo ta ari wayarta ta kirashi, kasancewar baya da layin Rumar a lokacin shiyasa daga baya ya bi miss call ɗin da ya gani kusan goma sha bai ma san an kira ba, sai dai jin murya Ruma yasa ya yi saurin faɗin
"Wacece ??"
Jikinta yana rawa ta ce "Rumasa'u ce ƙawar Zee don ALLAH ka yi haƙuri da abunda ta aikata ita ce ta kiraka ɗazu da naje wurinta ta ari wayar ta kiraka baka ɗaga ba, saboda WALLAhi yanzu Zee ta canza sosai kuma ta yi nadamar abunda ta aikata"
Cike da mamaki ya ce
"Daga ke har ita kada ku sake nemana matuƙar kuna son kanku zaman lafiya"
Ƙittt! Ya kashe wayarshi gaba ɗaya cike da jin haushinsu duka, Dije da ke shigowa ɗakin da tiren coffee'nshi ta ajiye tiren akan stool ta ɗauki cup ɗin ta zauna tana kallonshi tare da nazarin yanayi shi, sannan ya zura hannu da nufin ya karɓi kofin ta riƙe gam idonta a kanshi ta ce
"Wa ya taɓo man Habibyna? Don haka na fita na barshi ba plss ka yi haƙuri ko ma mene saboda zama cikin mutane sai da kai zuciya nesa Mijina"
Cike da jin daɗin kalamanta ya duƙo ya kurɓi coffee'n sannan ya ce, "waɗannan ba irin mutanen da kike tunani bane, ki share da su kawai don na riga da na shafe babinsu a rayuwata"
Dije ta miƙa masa cup ɗin ya karɓa ya dinga sha a hankali har ya shanye, sannan ta karɓi cup ɗin ta ajiye ta kalle da kyau ta riƙo hannunshi ta haɗe da nata ta dunƙule waje ɗaya ta ce
"Wacece ta kiraka?"
Cikin diriricewa ya ce
"Ruma ce ƙawar Zee take rokona akan inyi haƙuri in yafe wa Zee wai ta yi nadamar abunda ta aikata"
Dije ta ji wani ɓacin rai ya ziyarci zuciyarta, amman ta yi dubarar ɓoye damuwarta ta ce
"To kai kuma me ka ce?"
Ya ɓata fuska tamkar a lokacin sannan ya sanar da ita abinda ya ce da ita, Dije ta ɗauko hannunshi ta ɗora a saman cikinta da ya fara turowa kaɗan, ya bita da kallon ƙarin ba'asi sannan ta kashe masa ido ɗaya ta ce
"Nasan kana sonshi ko?"
Ya maka mata wata harara, ta zunɓuro baki ta ce "Ni dai ka daina hararata amsa nake nema"
Ya yi saurin faɗin
"Yo idan ma ba don kina son kawo man reni ba ta ya zaki kalli tsabar idona ki tambayeni ina son abunda Ni da kaina sai da na zuba ƙarfi kafin in sameshi?, Kin fi kowa sani kaf duniya babu wanda zai fini son abunda ke cikinki ko da ko ke ɗin ce da zaki haifo man shi"
Dije ta ƙumshe dariyarta ta ce "au abun har ya kai cen?"
Yana dariya ya ce "ya ma wuce ai" tace "well yanzu idan na ce ka yi mani wata alfarma saboda son da kake masa zaka yi?"
Cikin sauri ya ce
",Me zai hana in dai har hakan zai faranta ranki da unborn ɗina"
Ta ce "to in ko haka ne bari in zube ƙasa in rok'i alfarmar don ina son ayi saurin amsa mani"
Ta sauko ƙasa zata durƙusa ya riƙo hannunta tare da dawo da ita kan gadon ta zauna ya ce
"Faɗi buƙatarki kawai ba sai kin cutar man da abun ciki ba"
Dije ta yi dariya cike da jin daɗi sannan ta riƙo hannunshi ta matse gam ido cikin ido ta ce
"Daga Ni har babynka Muna so ka dawo muna da Aunty Zee ko don mu sami abokiyar shawara tunda har an ce ta yi nadamar abunda ta aikata"
Cike da ƙunar zuciya ya ƙwace hannunshi tare da miƙewa tsaye ya kalleta ranshi a ɓace ya ce
"Wannan rana da wannan lokaci su zamo na ƙarshe da zaki sake tunkarata da wannan zance"
Yana ƙare faɗar hakan ya fice ɗakin fuuu ya barta zaune sake da baki, zuciyarta cike da tabbacin abunda Inna ta nusar da ita wanda ita ta kasa gano hakan sai yanzu da ta tabbatar da hangen nesan Innarta, cikin tsananin farin ciki tace
"ALLAH ya ƙara maki tsawon rai innata"
To Ameen Dijen Safwan tare da namu Innonin duka kuma ya ƙaro masu lafiya mai ɗorewa Amee🤲🏻.
Akafta🥰
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*
*Lamba 69*
Duk da take cikin farin ciki haka ta fito ɗakin haɗe da fuska ta zo ta zauna tana shan ƙamshi tare da mayar da hankalinta ga kallon tv'n da ke ta aiki shi kaɗai, don shi kwance yake tare da rufe fuskarshi da hannu alamun yana cikin damuwa a zahiri, jin motsin shigowarta yasa ya buɗe ido yana kallonta, ganin yanayinta kuma ta ƙi kulashi yasa ya ji ba daɗi, ya miƙe zaune yana kallon yanda ta haɗe fuska tamau ba alamun wasa, cikin danne dariya ya taso ya zo gabanta ya yi tsugunno tare da riƙo hannunta yace
"Wai ke wace irin mace ce ke? Ni dai nasan kowace mace tana kishin mijinta amman ke har ingizashi kike yi akan ya yo maki kishiya"
Dije ta zare hannunta a hankali zata miƙe tsaye ya yi saurin dafeta ya ta shi ya zauna kan kujerar ya rungumota jikinshi ya ce
"Ki ji tsoron Allah kar ki jefa Mijinki a damuwa saboda macen da bata san muhimmancin kanta ba ma bale tasan na wani, kina kallo gaban idonki ta so kashemu da ma bata sami sa'a ba wuƙa ta ɗauko da nufin ta soka man, yanzu irin wannan matar kike so in sake dawo da ita cikinmu?"
Dije ta riƙo hannunshi ta ce "ba laifi bane don an yi maka laifi ka yafewa wanda ya cutar da kai, don ALLAH da kanshi haƙuri yake yi da mu da halayenmu saboda darajar fiyayyen halitta Annabinmu Muhammadu s.a.w da muke cin albarkacin shi, kuma a shirye yake da ya yafe muna a duk lokacin da mu ka yi tuba zuwa gareshi, tunda haka ne mu me zai hana mu yafe mata akan abunda ta aikata muna a baya?, Don ALLAH ka yafe don ni tuni na yafe mata ka sake bata wata dama matuƙar ka tabbatar da ingancin nadamar da ta yi "
Safwan ya sauke ajiyar zuciya yace "zan dawo da ita kamar yanda kika nema in har na tabbatar da gaske ta yi nadamar, amman da sharaɗin bata zo nan Abujar ba sai dai idan har ta amince zata zauna Yola, don bazan haɗaku waje ɗaya ba ta je ta koya maki mugun hali"
Dije ta ji wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyarta cike da tsantsar farin ciki tace " ina sonka Mijina ALLAH ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu"
Ya lakuce mata hanci
"Ya ce Ameen Matata ke ma ina sonki son da Ni kaina ban san iya adadinshi ba, na godewa ALLAH da ya azurtani da samun mace irinki, wadda take da wankakkiyar zuciya mai sowa wata abunda ta sowa kanta, don ba kowa ce mace zata iya yin abunda kika yi ba, ALLAH Ubangiji ya yi maki albarka ya kuma saukeki man ke lafiya tare da Babyna"
Cike da jin daɗi take ta faɗin "Ameen Ameen Habibyna, tom kirata yanzu ka sanar da ita ta dawo ka yafe mata"
Ya maka mata wata uwar harara ya ce "su kenan ba sai an tantance ba? Ai WALLAHI sai na tabbatar da lalle ta gyaru sannan in ce ta dawo, don bazan taɓa yarda in siyowa kaina rariyar da zata yi man asarar ruwa ba"
Dije ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "uhummm har na tuna lokacin da ake yi man kashedi akanta, daɗin abun da dai komi yake wucewa don yanzu ga shi kai da kanka ka bayyana mata matsayina bayan ka gama yi mata ɓoyo, ai WALLAHI kai ma da naka laifi Malamina don da tun farko ka sanar da ita da abun bai yi tsananin irin wannan ba, don da ace ta kashemu da shikenan mun tafi bamu bar masu yi muna addu'a ba"
Ya sosa kanshi cike da jin nauyin maganar tata ya ce "Ni dai bana son tone tone idan abu ya wuce a dinga barinshi a matsayin ya wuce, ki ta so mu je dai ki ji wata magana dare ya fara tsalawa"
Ta bishi da wani kallo tana ƙumshe dariyarta tace
"Ni yau anan ma zan yi baccina na gaji da kwanciya akan gadon nan"
Ba shiri ya waigo ya ce "Ashe ko da ke ce zaki wahala don WALLAhi in Banda tausayin abun cikina da kinsha mamakina, amman tunda hakan kike so bari in zo daga baya na baiwa abun cikina haƙuri"
Sanin halinshi yasa ta yi saurin tashi tana dariya ta ce "mu je Ni dai yasin idan na koma haifuwa garinmu sai na yi kusan shekara ban dawo ba"
Ya riƙo hannunta yana dariya ya ce "ki ce kawai in rubuta takardar barin aiki don kin san ƙafata ƙafarki kuma idan sun gaji da halina sai su korani in koma Yola dolena"
Ta yi masa wani mintsina a gefen ciki tana dariya ta yi ɗakinta da sauri tana faɗin "banji bakinka ba WALLAhi, Ni da nake shirin zama student kake so ka yi man ciki baƙi?"
Ya bita yana dariya ya ce " to Alhudahuda ai dai kya bari ki haife man abun cikina ko?"
Haka suka dinga wasarsu cikin raha har suka kwanta bacci bayan sun gama farantawa juna cikin tsantsar ƙaunar juna.
****
Ruma kam jikinta yana rawa tun da sassafe ta je ta sanarwa Zee abunda ya faru bayan barinta wurinta, cikin sanyin jiki da zubowar hawayen tausayin kanta ta karɓi wayar ta sake kiranshi, sai dai ta yi rashin sa'a wayarshi a kashe lokacin suna gudanar da wani meeting, ganin ta ƙi samunshi ne yasa ta rubuta masa saƙo ta tura masa kamar haka
_Aslm_
_Plss my Man Ni ce Zee don girman ALLAH ka yafe mani abunda na yi maka WALLAhi na yi nadama kuma na yi godiya ga Allah da ban ci nasarar abunda na so aikatawa ba, don yanzu haka Daddyna yana kwance har yanzu bai koma dai dai ba, kuma Mummy ta tsaneni ko kusa da ita bata bari inje, gani gidan ƙasar Daddy sai azabtar da ni take yi da ayyuka kala kala don ALLAH ka taimaki rayuwata ka ce in dawo ɗakina, WALLAhi na yi alƙawarin ba zan sake_ yin abunda bai da ce ba, plss ka yafe mani mu cuddle bear wallahi sonka ne ya
rufe mani ido ya janyo
na so aikata duk abunda ka gani, don ALLAH ka ce ka yafe mani in dawo don ALLAH my Bobbie.
Tana kuka take rubuta text ɗin bayan ta tura kuma ta sake bi da kira amman kuma bata shiga ba, saboda bai buɗe wayarshi ba har sai ya dawo gida ne bayan ya gama komi sannan ya buɗe, aiko buɗewar ke da wuya sai ga saƙon Zee ya danno kai, ba ɓata lokaci ya duba duk da ya tausaya mata amman hakan bai sa ya mayar mata da amsa ko ɗaya ba, asali ma goge text ɗin ya yi gaba ɗaya a wayar, sannan ya mayar da hankalinshi akan sauran saƙonnin da suke ta shigowa.
Zee ta gaji da jira ta sake gwada kiran sai ko ta yi dace ta shiga cike da tsananin jin daɗi ta yi wani ihu saboda murna, yana ɗauka ta daburce tana ta kame kame ganin bata da abun faɗa ne ya sa ya katse kiran, cikin sauri ta sake binshi da wani kiran har sai da ta tsinke bai ɗauka ba, bata gaji ba ta sake kira ganin zata dameshi ne yasa ya ɗauka, cikin rikicewa ta fara rawar murya tana faɗin
"Don Allah ka yi haƙuri ka yafe mani my Bonnie plss"
Cikin ko in kula ya ce
"Ni fa yanzu matata ta isheni bana fatar haɗata da kowace mace a matsayin kishiya ballantana mai som ta kashe mu Ni da ita, don haka ki ƙara haƙuri sai na yi shawara in ta amince tukunna"
Yana kare faɗar maganar ya kashe wayar, Zee ta fashe da kuka cikin tsananin takaicin kanta da har ta yi abunda ya janyo mata faɗuwar daraja warwas, don daman cen ya lafiyar kura ballantana yanzu ta ci sarauta?, Dole sai haƙuri cikin kukan ta sake kiranshi caraf ya ɗauka cike da Muryar kuka ta ce
"Ko a ƴar aikinta ka ce in zo Zan zo idan har zaka yafe man abunda na yi maka"
Safwan ya ɓata fuska kamar yana ganinta ya ce "kina da labarin ina Abuja yanzu ko?"
Ta ce "a'a bani da labari" ya ce "Ok tom yanzu haka ina Abuja Ni da Matata nasami aiki ne a cen, idan kin shiryawa zaman Yola to ki tattaro kayanki ki koma, amman ki sani weekend kawai zai dawo da ni Yola idan kin amince shikenan fine, idan kuma kin ji ba zaji iyawa ba Tom sai mu sahalewa juna"
Cike da jin daɗi bakinta yana rawa ta ce
"Na amince My Man amman don ALLAH ka ce ka yafe man, itama ka nemar mani tafiyarta kafin ku haɗu"
To kawai ya ce ya kashe wayar, Zee ta yo sororo da waya a hannu tana kallon Ruma ta ce
"Ya ce in koma amman har yanzu bai ce ya yafe mani ba"
Ruma cike da tausayinta ta ce "kada ki damu a hankali yafiyar zata biyo baya in har ya fahimci kin canza ba Zee ɗin da ya sani ba ce a cen baya, fatana kawai ki san yanda zaki taushi zuciyarki saboda tsoron aikata abinda za'a azo ana da ansani daga baya"
Zee ta share hawayenta ta ce "Ai Ni tuni na gano cewa zafin nema baya kawo samu, don da banda ke da yanzu Ni kaina bana duniyar an riga da an kasheni, wanda ta sanadin haka ina da tabbacin Daddyna ma zai mutu itama kanta Mummy zata shiga muwuyacin hali, saboda gorin mutane ƙarshe itama ta bimu, Nagode sosai Ƙawata lalle ke ƙawar amana ce ALLAH ya bar zumunci kuma ya baki miji nagari ke ma ki je ki yi aurenki ki huta"
Ruma ta ce "Ameen"
Tare suka je suka samarwa Baabaah Asaben abunda ke faruwa cike da jin daɗi ta nufi gidamsu Zee ta sanarwa Mahaifin Zee saboda murna sai gashi da tashi zaune ba shiri zuciyarshi cike da jin daɗin jin wannan abun farin ciki, Mahaifiyarta ma ba ƙaramin daɗi ta ji ba da jin maganar, shiyasa ta nemi alfarmar ganinta ba ɓata lokaci Baabaah Asaben ta kira wani yaronta ta ce ya ɗauko Zee ya kawota.
Satinta ɗaya gidansu Mahaifiyarta tana nusar da ita tare da nasihohi kala kala da misalan abubuwa da yawa wadañda suka faru a duniya masu daɗi da akasinsu, sannan aka fara gyarata na tsawon kwana uku sannan Mahaifinta ya yi mata huɗuba sosai da kanshi ya ɗauketa ya kaita gidansu Safwan wurin Hajiya Mama ya bada haƙuri sosai sannan ya ɗauketa ya kaita gidan Safwan da hannunshi tare da yi masu addu'ar zaman lafiya.
Satinta biyu a gidanshi ba tare da ya waiwayota ba, har sai da Hajiya Mama ta nuna masa rashin kyautawarshi sannan ya baro Abuja ya nufo Yola ranshi ba daɗi, don in ta shi ake bi abarshi da Dijenshi ta isheshi rayuwa a duniya.
Ko da ya shigo garin sai da ya je wajen Hajiyarshi suka gaisa ya bata tsarabarsu sannan ya ɗan taɓa fira da fiddo da Surayya da aka dawo da ita haifuwa saboda Mijinta da baya nan, bayan sun gama tambayar juna bayan rabuwa ne ya miƙe zai tafi Hajiyarmu ta ce
"Ka kula da matarka don na hango shiriya a idanuwanta, kuma ka yi haƙuri da ni don nasan ba da son ranka ba biyayya ce kawai kake yi man, to ka sani duk lokacin da wani ya sami shiriya ta sanadinka ba ƙaramar lada zaka samu a wurin Ubangiji ba, shiyasa duk da nasan ta aikata mummunan laifi amman hakan bai sa na barka ka yi abunda ka so ba, don ina jin tsoron ka sake auro wadda zata aikata abinda yafi wanda ya yi muni, don gara ita da kishinta yake a fili yake kowa zai gani, saɓanin wasu da suke ɓoyewa a fili su nuna ba komi kuma su bi ta ƙarƙashin ƙasa su wargazaka daga kai har matar taka, to ko a hakan ma ka godewa ALLAH da baiwar da ya yi maka tunda bai haɗaka da mace mashurika ba mai biyar bokaye, wadda ba matarka ba har Ni da na haifeka da ƴan'uwanka duka zata iya rabaka gaba ɗaya"
Cikin sanyin jiki ya ce
"Na gode Hajiyarmu ai nasan daman ke baki ɗora wani ma a hanyar da bata dace ba bale ɗanki da kika haifa, Ubangiji ya ƙara bar muna ke ya karo lafiya da nisan kwana Hajiyarmu, na gode sosai kinga na manta da tsarabar da ɗiyarki ta bada in kawo maki"
Ya kalli fiddo ya ce "ke zo mu je ki karɓo na tafi Hajiyarmu sai na dawo"
Fiddo ta biyoshi zuciyarta cike shakkun abinda zata faɗa cen dai ta danne ta ce "big