Showing 99001 words to 102000 words out of 136985 words
shi ko waya babu a hannunta ba le ta kirashi ta ji daɗi, kuma kunyar idon Auntyn da kashedin Hajiyar yake sa ta ƙi tambayar a wane hali yake.
Ganin halin da take ciki ne yasa Aunty Ummi ta fara shiga damuwa duk da tana iya ƙoƙarinta wajen sakata nishaɗi saboda gurinta na son cire mata damuwa, shiyasa ko auren da ta ji ƙin nuna mata wani abu da zata gano ta yi, saboda jan kunnen da Hajiyar ta yi mata akan kada ta bari ta san da zancen, da ma lokacin auren ya matso ne ta yi mata ƙaryar wani biki ne daban zata je, da ma Dijen ta nuna tana son zuwan itama sai ta ce da ita ta yi haƙuri ba zata daɗe ba, don ma ta kwantar mata da hankali ta bar yaranta mata manya ta tafi da ƙananun saboda Maigidanta daman cen ba mazauni bane ba.
****
Biki bidiri bireɗe amfanin soyayya aure Zee ta angwance da masoyinta Safwan, zuciyarta cike da tsantsar farin ciki saɓaninshi da yake cikin ƙunci don duk wasu events ma ba da shi aka yi ba, an ɗauki Amarya daga Gombe zuwa Yola mahaifar Mijinta, inda aka wuce da ita gidan Hajiya Mama kai tsaye saboda ta kwashi tubarrakin uwar mijinta ta sawa aurensu albarka kafin akaita gidan angonta.
Sorry team Dije 🙇🏻♀️ku sani babu ruwana nidai 🙌🏻🏃🏻♀️
Akafta🙌🏻
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Mutanen Dije ina baku haƙuri🙏🏻dangane da auren Zee da Safwan ya yi, amman ina son ku sani ana yin book ne don faɗakarwa tare da wa'azantarwa sannan da kwatanta abunda ke faruwa a cikin al'ummarmu, saboda haka ku natsu tsaf ku bini sannu a hankali zan warware maku komi cikin tsarinshi😉*
*Lamba ta 58*
Har ƙuryar ɗakin Hajiya Mama aka kai Zee da ke ta rufe fuska tana ta wasar baki saboda daɗin da ya kasa ɓoyuwa a kan fuskarta, gaban kowa da mutanen da suka yi mata rakiya Hajiya Mama ta ce da Zee
"ALLAH ya baku haƙurin zama,
kuma albarkaci aurenku tare da zuri'a ɗayyaba gaba ɗaya, sannan da fatar zaman lafiya ke da abokiyar zamanki"
Dirim! dum! Shine bugun da zuciyar da Zee ta yi amman ta wayance tare da noƙe fuskarta tace "Ameen" Hajiya Mama ta ƙara da cewa
"Ki yi haƙuri nasan zaki ga abokiyar zamanki bata sami halarta bikin ba, to hakan ya faru ne a sanadin hidimar karatun da ya sha kanta, amman ina fatar a duk lokacin da zama ya haɗaku ki yi ƙoƙari ki baiwa Mijinki haɗin kai wajen yi maku adalci a tsakaninku, ALLAH ya baku zaman lafiya a tsakaninku duka ya kawar da sheɗan cikin gidanku gaba ɗaya"
Kowa sai "Ameen Ameen" yake faɗa sannan ta kawo dunƙulalliyar kyauta ta bata, aka fito da Zee mutane da yawa sai yaba kirkin Hajiyar yake yi, inda kai tsaye aka wuce da Zee katafaren gidan Safwan wanda ya laƙume maƙudan kuɗi wajen haɗashi ta ko'ina, inda itama kanta Zee iyayenta suka zuba ta su bajintar wajen ƙawatashi da kayan ƙarau lungu da saƙo, abun dai masha ALLAH sai wanda ya gani don tsayawa misalta haɗuwarshi ma ɓata baki ne, saboda haka masu karatu na baku wannan aikin wajen misalta gidan da kanku.
Har ɗakinta aka kaita iyaye da ƴan uwa da ƙawayenta sai addu'ar zaman lafiya su ke yi mata, saboda ganin yanda ta haye wajen samun kyakkyawan Miji da kyakkyawan muhallinta gwani burgewa, uwa uba itama gata kyakkyawar farar mace kuma ga su da hannu da shuni ta ko'ina suka motsa nera kukan wahala ta ke yi, saboda akwai kuma an tara babu abunda zai gagaresu nema matuƙar da kuɗi ake sakawa a nemi abun.
Abokan Safwan sun shirya dinner wadda za'a yi a wani katafaren hall, sai dai shi ango ya ce sam shi kam ba wata dinner da zai je, shagugulan da aka yi ma sun wadatar ALLAH ya sawa aure albarka, ba magiyar da Zee ba ta yi masa ba akan ya yi haƙuri su je ko da rage lokacin da aka ɗiba ne za'a yi sai ayi komi cikin lokuta ƙalilan, amman ya buga kanshi a ƙasa ya ce shi bai san da wannan zance ba, cike da jin haushi Zee ta fashe masa da kuka dole ya koma aikin lallashinta, ganin yanda ta dami kanta akan son zuwan ne ya shirya suka je, amman har cikin zuciyarshi ba ya wani murna da duk wani shagali, aure dai ne anyi to tsirfin na mi ne kuma?.
Har aka yi dinner aka watse Safwan fuskarshi ba yabo ba fallasa sai dariyar yaƙe da yake yi wa mutane, Amarya da ango sun fito sun yi rawa sun sha liƙi ta ko'ina kuɗi ne ake zuba masu, bayan sun ƙare ne suka yanka cake tare da ciyar da junansu mutane sai ɗaukarsu photuna da videos ake yi, saboda shagalin ya ƙayatar da rai sosai ba tare da jan lokaci ba aka watse koma ya kama gabanshi, inda Ango ya ɗauko Amaryarshi zuwa gida tare da rakiyar abokai da ƙawayen Zee ɗin da za su kwana da safe su kama gabansu.
Kasancewar part ɗinshi daban shiyasa kai tsaye ya nufi sashenshi ya barta tare da zugar ƙawayenta suka nufi sashenta, cike da tsananin gajiya ya faɗa kan gadonshi tare da dafe kanshi idonshi a sama yana kallon seilling yana hasko Dijen Baffah cikin idanuwanshi, musamman lokacin da ya sami sa'ar rabata da abunda har lokacin idan ya tuna sai ya ji shi cikin wani yanayin buƙatuwa da son komawa cikin tafkinta mai ɓulɓulo da ruwan kogin ni'ima, waɗanda ko a misali ba zai taɓa kwatanta irin abunda ya ji a jikinta ba, don duk abunda zai faɗa ganin yake yi kamar ya fi hakan, saboda shi kanshi ya yi matuƙar mamakin yarinya kamarta ace itace da wannan tarin albarkatun ni'imar a jikinta, sai dai idan ya yi nazarin cewa ance ko wace mace da kalar ni'imarta sai ya ajiye mamakin don yasan ALLAHn da ya raba ya baiwa kowa ce mace haka itama ya raba ya bata tata, don ikon ALLAH ya fi gaban a yi mamakinshi illah kawai mu ce Alhmdllh a kowane hali a kuma kowane yanayi.
ZEE kam kasancewar abokan nata su ma kansu a fashe yake, shiyasa suka sakata ta sheƙo wanka tare da tsara mata dress cikin wata arniyar night gown fara ta yi kyau iya kyau sai dai komi na jikinta babu wanda ya ɓuya don har pant ɗin da ke jikinta ana hangowa, bra ma cewa suka yi kada ta saka kasancewarta daman cen breasts ɗin nata ba wani yawa ne da su ba, don bafulatana ce ta usuli mai ƙananan nonuwa, amman a hakan ma ba laifi sun ɗan fito a cikin rigar kuma shigar ta karɓe ta sosai, sannan suka fesheta da tsadaddun turaruka masu ɗan karen ƙamshi, suka zaunar da ita suna yi mata bitar abubuwan da ta yi, tana daɗe tana zaman jiran shigowar angon domin ya tafi da ita, sai dai shiru shirun da suka ji ya yi yawa ne suka bata shawarar kawai ta je ta sameshi da kanta, cikin zumuɗi ta miƙe don daman cen kawaici ne kawai take yi saboda kar aga zalamarta, aikuwa ta zumbula dogon hijabi wata ƙawarta ta rakata har sashenshi sannan ta dawo, Zee ta daɗe a ƙofar tana wassafa irin kallon da zata yi masa wanda zai sa ta sace zuciyarshi a lokaci ɗaya ya faɗa tarkonta.
Da guntuwar sallama ta shiga inda sallamar ta katse ba shiri saboda ganinshi da ta yi kwance takalman da ke ƙafarshi ma bai samu cirewa ba, suna nan sanye a ƙafar ta shi har lokacin, hular kanshi kawai ya cire saboda damuwar rashin sanin takamaiman inda Dijen take, damuwar hakan ne ta cika masa ziciya, Zee ta tako a hankali cikin faɗuwar gaba ta zauna gefen gadon tare da ɗora hannunta akan jikinshi ta ce
"My Man wai meke damunka ne? Na fahimci akwai damuwa a tattare da kai musamman yau ɗin nan, me yasa zaka taryi wannan daren na mu mai tarihi a garemu da wannan sabon yanayin??"
Safwan ya yi saurin riƙo hannunta daga kwancen tare da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya ya ce
"Sorry ni ma ban san me ke damuna ba, haka kawai na tsinci kaina cikin wannan yanayin, ki yi haƙuri kinji?"
Zee ta sauko ƙasa ta fara cire masa takalmin da Safar duka sannan ta haɗasu ta kai muhallinsu ta ajiye, ta dawo ta kwanta gefenshi ta shafo fuskarshi tana yi masa wani kallo ta ce
"Plss Honeybee ka daina wannan damuwar ka tattara sabon yanayin nan ka a jiyeshi a gefe ka kalli sabuwar Amaryarka gata a kusa da kai tana buƙatar kulawarka"
Safwan ya saka hannunshi ya janyota kusa da shi sosai ido cikin ido suke kallon juna, yana yi mata wani kallon tausayi saboda yasan ba ƙaramin so take yi masa ba, cikin mairairece fuska da alamun son yin kuka ta ce
"Plsss! my man!"
Safwan ya janyota jikinshi all kasancewar ba wani kumari ne da ita ba ya sakar mata kiss a goshi sannan ya miƙe zaune ya ce
"Bari in je in yi wanka ko da zan ɗan ji ƙarfin jikina, sannan mu zo mu yi sallahr godiyar ALLAH ga Ubangijinmu"
Cike da jin daɗin maganarshi ta lumshe ido daga kwancen ba tare da ta ce ƙanzil ba, ya miƙe yana cire kayanshi ta bishi da kallon ƙauna har ya shige toilet sannan ta sauke ajiyar zuciya a ranta ta ce
_"ALLAH ka bani ƴa ko ɗa mai kama da kai sak! my Bunny"_
Har ya fito bata san ya fito ba saboda ta lula sosai wajen tunanin zazzafar soyayyar da take yi masa, sai da ya saka ƙafa ya soso sililin ƙafarta sannan ta yi saurin ta shi zaune tana murmushi, ya ce ta je ta yi arwallah ta zo su yi sallar, ta miƙe tsaye ta yi wata miƙa ta cire hijabin da ke jikinta ta nufi toilet ɗin cikin wani takun jan hankali, ya bi bayanta da kallo ya yi wani gajeren murmushi sannan ya saka doguwar jallabiya fara ya shimfiɗa ƙatuwar carpet yana jiran fitowarta.
Bayan sun ƙare sallahr ne ya yi ta jera masu addu'o'in neman zaman lafiya sannan ya fara latsa amaryarshi tun a nan, don ko kazar amarcin da ake ci su ba su sami damar ci ba, saboda angon ba wani sukunin zuciya ne da shi ba shiyasa komi ma ya fita a ranshi, ita kuma murnar ganin yanda ya fara nuna mata zallar ƙaunarshi ne yasa ta ƙi cin komi, a hakan suka baje suna ta farantawa junansu ta hanyar musayar abubuwa da yawa, saɓanin Dije da shi ya yi kiɗan kuma ya yi rawar har ma ya sami guzurin kukan da ta rufeshi da shi wanda ya zama tamkar taki wajen haukace mata, Zee kam jiki ta saki itama ta nuna masa ba fa shi kaɗai ya iya tarairayar ba, cikin salon ƙaunar da ta baibayeshi da ita ne ta ci galabar samunshi yanda take buƙata, don kuwa ya baje sosai ya karɓi budurcin Amaryarshi, ba tare da ya sha wata wahala ba, duk ko da yanda take jin azaba amman hakan bai sa ta nuna masa gajiyarta ba, sai dai sunan Khadija da bakinshi ya ƙi daina ambata ya sa ta shiga tunanin wace khadija ce yake faɗa a yayin kwanciyar aurensu na farko?, amman ta bar abun aranta don bata son ta ɓata masa rai cikin wannan yanayin da suke ciki, sai da ya tabbatar da ya jigatar da ita sannan ya saurara mata don kanshi, ya koma saka mata albarka tare da jinjina mata akan budurcinta da ta adana masa.
Haka suka kwana cikin damuwa dukansu kowa da tunanin da yake yi cikin zuciyarshi, inda shi ya kwana yana tunanin ƙira da cikar ƙirjin Dijen Baffah, yayin da ita kuma ta kwana tana tambayar kanta wacece khadijar da ya yi ta kira lokacin da suke faranta junansu?.
Bayan sun yi SALLAHr asuba ne Zee ta kasa haƙuri ta ce da shi
"My man Ina son inyi maka wata tambaya da fatar baza ka ga laifina ba?"
Ya shafo fuskarta tare da riƙo hannunta ya sakar mata kiss a bayan hannun sannan ya ce
"Idan har kin san tambayar ba mai laifin ba ce ki yi kawai a shirye nike da in baki amsarta"
Zee ta yi saurin riƙo hannunshi ta saka nata sama da ƙasa ta riƙe gam gam wasu hawaye suka fara zarya cikin idonta ta ce
"Wacece khadijar da na ji kana ta kira a jiya? Don Allah ka sanar da ni saboda ina jin tsoron ace sunan Uwargidanka ne ka ke ta ambata"
Safwan ya yi saurin kawar da kanshi gefe tare da jin nauyin abunda ya aikata mata cikin rashin sani, sannan ya ce
"Ki yafeni Matata nasan ban kyauta ba amman Insha ALLAHu hakan ba zata sake faruwa ba in dai har daga gareni ne matsalar ta fito "
ZEE ta share hawayenta da suke ta sauka akan fuskarta ta ce
"Ina jin tsoron ace akwai wadda ta fini samun muhalli a cikin zuciyarka, don WALLAhi matuƙar hakan ta faru to bazan taɓa yafe wa kaina ba"
Safwan ya rungumota jikinshi tare da ɗora kanshi saman kanta yana wassafo Dijen Baffah a ranshi da ruhinshi sannan ya sauke ajiyar zuciya yace
"So shu'umi ne my unique ki yafewa Man ɗinki albarkacin son da kike yi masa kin ji?"
Ta riƙo hannunshi sannan ta shafo fuskarshi ido cikin ido ta ce
"Ina sonka sosai My Man don ALLAH ka riƙeni amana ka ji?"
Ya lumshe idanuwanshi ya sake rufewa sai ga fuskar Dijen Baffah ta zo masa a cikin gilashin idonshi, cikin sauri ya yi saurin buɗe idanuwan yana kallonta fuskarta ƙur sai ga fuskar Dijen Baffah ta bayyana cikin ta ta, ya yi saurin duƙowa cike da zalama ya cafki leɓenta yana wata irin tsotsa tamkar zai rabata da bakin duka, cikin fitar hayyaci tare da rasa tunaninshi na wuccin gadi ya ɗago fuskarta idonshi a rufe ya ce
"Me yasa kika bari aka rabani da ke ne? Me yasa kika tafi kika barni? Kinsan iya adadin damuwar da kika sanyani kuwa? Plss ki dawo gareni khadija, plss ki dawo wurina na ce!!!!"
Ya ƙare maganar cikin zubowar wasu hawaye masu zafi waɗanda tunda ya shiga cikin damuwar bai sami damar yin ƙwallah ko ɗaya ba bayan kukan da ya yi wa Hajiya sai wannan, shiyasa hawayen suka kasa tsayawa sai sauka suke yi a fuskar Zee, saboda ta kasa ɗauke idanuwanta akanshi sabida mamakin da ya game jikinta da zuciyarta.
Zee cikin wani fushi mai cike da zallar tsagwaron kishinshi ta yunƙura cikin zafin nama ta yi saurin tureshi ta miƙe tsaye, idonta akanshi hawaye suna zuba masu zafi ta nunashi da hannu ta ce
"Ka yi gaggawar sanar da ni wacece khadija tun kafin ka janyo zuciyata ta buga"
To fa🙀Ke ko amarya kar ki yi fatar bugawar zuciya a ranar farko gidan aurenki😢
Akafta😝
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*special thanks to you all my FANS😉*
*Lamba 59*
Cikin sanyin jiki ya miƙe tare da janyo ƙafafuwanshi zuwa inda take sannan ya yi ƙarfin halin riƙo hannunta, cikin fushi ta ƙwace hannun tare da matsawa baya tana yi masa wani kallon mai cike da fushi tace
"Wacece wannan baƙar yarinyar da kake ambata a gabana?? Don na ce ina sonka laifi na yi da har kake ƙoƙarin baƙanta man cikin lokutana da Allah ya bani daga gareka??, Sakayyar da zaka yi man.. ke....nan?"
Ta ƙare maganar cikin sarƙewar murya tare da zuwan wani masifaffen kuka, cikin tsananin damuwa Safwan ya isa wurinta ya rungumota jikinshi, ba shiri ta faɗa ta narke masa tana wani irin kuka gwanin ban tausayi, cikin dakusasshiyar muryarshi da ta sha kuka ya shafo gashinta ya ce
"Don ALLAH ki yi haƙuri kinji? Insha ALLAHu hakan ba zata sake faruwa ba"
Zee ta share hawayenta sannan ta ɗago tana kallonshi tace
"Matuƙar kana son mu yi zama na jin daɗi da farantawa juna ni da kai, to ya zama dole ka nisanci duk wani abunda zai janyo muna matsala, saboda akanka wallahil'azim zan iya aikata koma menene saboda haka ka kiyayi faɗin sunan kowace shegiya a gabana, that's the first and last idan har kana son farin ciki a gidanka"
Safwan ya yi shiru yana nazarin rashin dacewar abunda ya aikata, amman duk da haka wani sashe na zuciyarshi cike yake da jin zafin baƙar da ta kira Khadijarshi, sai dai saboda sanin shine mai laifin yasa ya zare jikinshi daga nata ya nufi kan gadon ya kwanta, tare da dafe kanshi yana nazarin mafita akan matsalolin da suke son ruftowa rayuwarshi.
Cikin damuwa Zee ta bishi da kallo sannan ta ƙaraso ta zauna gefen gadon tare da riƙo hannunshi ta ce
"Baka sanar da ni matsayin wannan suna da naji kake ta ambata ba tun jiya har yau, wacece ita? Saboda jikina yana bani cewa tabbas itace silar shigarka cikin wannan sabon yanayin da ka ke ciki"
Safwan ya janyo hannunta saman ƙirjinshi sannan ya ce, "ki yi haƙuri khadija matata ce asali ma itace matar da kika ji an ce da ke ina da, kuma ita ce Uwargidana a yanzu haka, amman duk da haka nan ina baki haƙuri akan laifin da na aikata kuma insha ALLAHu bazan sake ba"
A hankali ta zare hannunta cikin na shi saboda wani kuka da ya zo mata, sannan ta miƙe cikin jarumta ta ce "bari in je wajen su Ruma kada su ga na barsu"
Ƙanzil bai ce da ita ba har ta fice zuciyarta cike da tsantsar baƙin ciki, tafiya take yi idonta a rufe saboda zallar tsagwaron kishin Dijen da ya rufe mata idanuwa, har ta isa sashenta bata san ma ta kai ba har sai da ta jiyo shewarsu Ruma sannan ta yi saurin share hawayenta tare da saita kanta ta shiga tana wasar baki, aiko suka yo mata caa da tsokana ko wa da abinda ya ke faɗa akanta, da kyar ta sulle ta faɗa toilet inda ta ɗauki lokaci tana ta kukanta sannan ta baiwa kanta haƙuri ta yi wankan ta fito.
Da taimakon ƙawayenta ta fesa wata arniyar kwalliya ta ci wani danƙareren less black colour tare da