Showing 126001 words to 129000 words out of 136985 words
bros yaushe zaka je da Ni Abuja wurin Khadija?"
Ya waigo Yana yi mata wani kallo ya ce "Ba ma maraba da gulma idan har itace zata kaiki don nasan Zee ce taki don haka ki tattara kayanki ki je ki tayata zama idan na koma, ko ko karatu na ki ya zaki yi da shi idan kin je cen?"
Ranta a ɓace ta ce "Ni dai yayanmu cen nike son zuwa don ALLAH ka je da Ni in zaka koma yanzu, sai ka sakani makarantar a cen don nafi son inyi karatuna a cen"
Ya miƙo mata ledar saƙon da Dijen ta aikowa Hajiyar yana faɗin "lalle baki da hankali kina year 2 ki nemi barin makaranta saboda daɗin da ya yi maki yawa ko? To ki jira idan kin fara aiki sai ki koma cen da karatun kina biyawa kanki, Ni matsa ki bani gu tun ban hanɓarar da ke ba"
Fiddo ta yi cikin gidan tana gunguni don ita zaman garin ne ya gundureta, saboda in suna chatt da Husnah tana turo mata pictures ɗinsu in suna shaguna ko wuraren shaƙatawar da suke yawan zuwa, abun yana burgeta sosai shiyasa tasawa ranta itama zata koma cen a fantama da ita, amman dai ga shi ya gwasaleta a tashin farko.
Ya fisgi Motarshi ya nufi gidanshi, haka kawai yake jin baya son shiga gidan don ya daɗe zaune a parking space yana firarshi da ma'aikatan gidan, don ko jakarshi tuni aka shige da ita ciki sannan ya fito ya nufi sashen Zee ɗin zuciyarshi a cunkushe, sai dai yanayin da ga Zee ɗin yasa ya yi saurin sakin fuskarshi saboda ba ƙaramin bugawa zuciyarshi ta yi ba, ganin yanda ta yi baƙi ta rame sosai amman a hakan har da fara'a kwance a fuskarta da ta rame sosai tana yi masa sannu da zuwa.
Ya zauna tare da bin falon da kallo kamar mai neman wani abu sannan ya dawo da kallonshi gareta ya ce
"Ke fa? me ya sameki kika rame irin haka??"
Ta duƙe hawaye suna zuba ta fara wasa da yan yatsunta, cike da tausayinta ya ce
"Zo zo inji me ke faruwa ne?"
Zee ta durƙushe ƙasa tare da riƙo ƙafafuwanshi tana wani irin kuka take faɗin
"Plss ka yafe mani don ALLAH nasan ban yiwa kaina adalci ba, don ALLAH ka ce ka yafe mani ko da zuciyata zata yi sanyi"
Safwan ya ɗagota ya zaunar da ita kan kujerar da yake yana share mata hawayen ya ce "komi ya wuce ki daina wannan kukan yanzu ba gamu tare ba?"
Zee ta sake fashewa da kuka tana faɗin "na cutar da kaina da hannuna don ALLAH ka yi haƙuri"
Dole Safwan ya ajiye komi ya fara lallashinta, sannan ta kaishi ya yi wanka ta rakoshi diny inda ta shirya masa abinci mai kyau, yana ci yana janta da fira saboda ganin har lokacin bata daina hawaye ba.
Cikin dauriya ya bata kulawa ba yabo ba fallasa haka suka kwana kowa da tunanin da ke cike cikin zuciyoyinsu, ita tana ganin kamar yana riƙe da ita shi kuma yana tunanin irin lalacewar da ta yi.
To mu dai sai dai muyi maku fatar ALLAH ya bada zaman lafiya da hkr😝
Akafta😊
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Aski ya zo gaban gashi Mutanena💃🏻*
*Lamba 70 *
Haka dai suka kwana ba natsuwar zuciyoyi, bayan SALLAHr Asuba Safwan ko da ya dawo masallaci ya taradda Zee tana ta karatun Qur'ani, abun ya buregeshi kuma haka ya ba shi mamaki sosai, saboda sanin da ya yi mata ada da ƙyar ma take tashi yin SALLAHr a lokacin, sannan idan ma ya matsa mata ta yi tana kammalawa take yin kwanciyarta ko addu'ar kirki bata tsayawa yi, amman yanzu ita ce har da su karatun Qur'ani, cike da jin daɗin sauyin da aka samu ne ya zauna kan gadon yana ƙarasa addu'o'inshi na azkar, har bacci ya fara janshi ya kwanta ba shiri saboda baccin da ya fiegeshi ba tare da ya shiryawa hakan ba.
Misalin ƙarfe takwas ya falka saboda ƙamshij abun break ɗin da take haɗa masu, mamaki ya sake kamashi ya fito ɗakin ya nufi kitchen yana kallon yanda take ta hadadarta, cikin shigar wata doguwar riga ƴar kanti, tana ganinshi ta diririce tana gayar da shi cikin ladabi, bayan ya amsa ne zuciyarshi cike da jin daɗin sauyin da ta samu, ya fice kitchen ɗin zuwa sashenshi saboda zuciyarshi da ke ta kwaɗayin son jin muryar Uwargidanshi, don tun yana kan hanyar shigowa garin da suka yi waya ta ji ya sauka lafiya ta kashe wayarta, saboda kishin da ke cin zuciyarta game da zuwanshi wurin Zee, da abun ya kwana a ranshi saboda ya yi ta kiran wayoyinta a kashe ta Husnah ma a kashe, cikin takaici ya kira Aunty Ummi ya ce ta haɗashi da ɗaya daga cikinsu yana son yin magana da Dijenshi, Aunty Ummi ta nuna masa dare ya yi sosai ya dai haƙura sai da safe, saboda a lokacin ƙarfe sha biyu da mintuna dole ba don ya so ba ya haƙura amman zuciyarshi cike fal da son jin dalilin da Dijen ta aikata hakan.
Shiyasa ko da ya shiga sashenshi ko wanka bai yi ba ya fara nemanta a waya, aka yi da ce ta shiga itama caraf ta ɗaga sai dai shirun da ya ji ta yi masa ne yasa shi saurin faɗin
"Me na yi maki kika horani da rashin jin muryarki?"
Sheshshekar kukan da ya ji ne a kunnenshi yasa ya yi saurin sake wata maganar a rikice ya ce
"Subhanllah me ke faruwa ne? Me aka yi maki? Wa ya taɓa man ke don ya ga bana nan?"
Dije ta sake fashewa da kukan gaba ɗaya cike da ruɗewa ya ce
"Plss babyluv don ALLAH ki daina kukan nan ki sanar da ni abunda ya faru idan har kina son ganin natsuwata"
Cikin kukan Dije ta ce
"Ka gaisheta"
Tana ƙare faɗar hakan ta datse kiran, cikin wani sabon tashin hankali ya sake bi da wani kiran amman har ta tsinke bata ɗauka ba, ganin hakan ya sa ya dinga kiran Husnah kira bayan kira, tana bacci dole ta miƙe ta ɗauka ya ce da ita ta kaiwa Dijen, ta miƙe cike da jin haushin katse mata bacci da aka yi, sai dai kukan da ta tarar tana yi ne yasa jikinta ya yi sanyi, ta miƙa mata wayar ta fito zuciyarta cike da jin zafin kukan da ta ga Auntynta tana yi, don tun jiya take lallashinta akan ta yi haƙuri ta daina kukan da ta ke yi na rashin Auncle ɗinsu, ta yi kamar ta haƙura ashe bata haƙura da kukan ba.
Dije ta kara wayar a kunne tana share hawayenta ta ce
"Ba wani abu fa kaina ne yake ciyo"
Daga cen ɓangaren ya sauke ajiyar zuciya yace, "haba haba My luv to meyasa ba zaki sanar da ni ba kike wahalar man da kanki da Babyna? Yanzu ki shirya Aunty Ummi zata zo ta kaiki Asibiti sannu kin ji? ALLAH ya baki lafiya"
Ta ce "Ameen" cen cikin maƙoshi sannan ya sake cewa "ya kwananki da na Babyna?"
Ta ce "ƙalau"
Cike da mamakin yanda take ta ba shi amsa a taƙaice ya ce "Babyluv ko na yi maki wani abun ne ban sani ba?"
Ta ce "A'a" yace 'to wacece kike cewa da ni in gayar?"
Ta murguɗa baki kamar yana gabanta ta ce "wadda ka je wajenta ko ba'a buƙatar gaisuwar tawa ne?"
Ba shiri ya rufe bakinshi saboda fahimtar inda ta dosa, cikin dariyar da ta so kufce masa ne ya ce
"Ana buƙata kuma an karɓa hannu bibbiyu ALLAH ya saka da aljannah, amman fushin na minene? ko kin manta Umurninki na bi? To yanzu kuma tunda an yi maki abunda kike buƙata kuma ta dawo kamar yanda kika roƙar mata alfarma Ni kuma mi ye laifina a ciki?"
Ta ce "ba ko ɗaya hasali ma ka yi abunda ya dace" zai sake yin magana ne Zee ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da nufin sanar da shi komi ya yi ready, ganin yana waya ya sa ta yi saurin juyawa da nufin komawa, ya yi gyaran murya ta waigo ya yafitota ta ƙaraso wurinshi, ya miƙa mata wayar cikin jarumta ya ce "kHadija ce ku gaisa"
ZEE ta karɓi wayar cikin sanyin jiki tana shirin yin magana ta ji Dijen tana faɗin
"Dawo da itan ai abu ne wanda ya dace, kuma kai kanka zaka gano alfanun yafiya ga wanda ya yi maka laifi, saboda ladarka tana wurin Allah Kuma insha ALLAHu za ka ga sakamakon abun alkhairin da ka yi, fatana kawai ALLAH ya baka ikon yi muna adalci, kada don an sami ta ƙarfen a juyawa ƴar ƙauye baya"
Zee ta yi saurin faɗin
"Insha ALLAHu in dai ta ɓangarena ne matsala ta ƙare, da ni da ke yanzu mun zama abu ɗaya babu wani gorin asali ko wani fifiko, a zahirance ma kin sha gabana don kin riga da kin yi man fintinkau tunda har kike da zuciyar imani, kika ɗora Mijinki akan hanyar dawo da ni cikinku duk da abunda na aikata maku a baya, don ALLAH ki yafe mani kinji insha ALLAHu zan yi ko yi da kyakkyawar zuciya irin taki, saboda yanzu na gano cewa ko wane mutum da kalar baiwar da Allah ya yi masa, sau da yawa wanda ka ke renawa sai ya zo ya fi ka ta hanyoyin da kai ko da kuɗi ba zaka iya binsu ba, matuƙar sheɗan yana buga ganganunshi saman kanka, na gode sosai da taimakon da kika yi mani aka dawo da ni, kuma ki sa a ranki cewa kina da ƴar'uwa saboda yanzu Zee ta ɗaukeki tamkar ƴar'uwarta ta ciki ɗaya tunda har na gano ke ɗin alkhairi ce garemu ni da shi"
Tana ƙare faɗar maganar ta miƙa masa wayar ta fice da sauri tana kuka, ya bita da kallo sannan ya sauke ajiyar zuciya yace
"Babyluv sannu da namijin ƙoƙarinki, lalle ke alkhairi ce ga rayuwata, ina ta ya ƴaƴana farin cikin samun uwa ta gari irinki, fatana kawai a yanzu ALLAH ya sauke man ke lafiya ki bani Babyna a hannu in ɗauka"
Dije ta goge ƙwallarta ta saita natsuwarta ta ce "Insha ALLAHu ƴaƴa har sai ka ce in tsaya haka nan in huta , don in na Fara watso maku su sai ka rasa da hannun da zaka riƙe sauran"
Safwan ya fashe da dariya cikin dariyar ya ce "au watsosu ma zaki yi don salon mugunta?, To bari ki ji ko da jefosu zaki yi ta yi duk bayan minti biyar Habibynki ba zai taɓa rasa hannun da zai karɓesu ba, ke dai kawai ki natsu ki sako man su sannu a hankali ina karɓewa cikin farin ciki ba tare da gajiyawa ba ko ƙosawa"
Haka suka yi ta firarsu mai cike da barkwanci da raha har dukansu suka daina jin damuwar rashin ganin juna, sannan Dije ta daƙile firar dolenta don bata son ta shiga haƙƙin Zee, ba don ya so ba suka yi sallama cikin kewar juna tare da kwaɗayin ganin junansu, saboda mugun sabon da suka yi wa juna da kawunansu.
Har ga ALLAH Safwan ya ji daɗin yanda Zee ta dawo macen kirki, shiyasa cikin dauriya da kai zuciya nesa ya mu'amalanceta har lokacin barin garin ya yi ya tattara kayanshi ya koma Abuja, wurin Matarshi da ya ke jin a duniya kaf ba ya da matar da zata kamo ƙafarta ma bale ta kamota, ko da ko akwai ɗiyan lu'ulu'u da murjani a cikin.
****
Haka rayuwa ta yi ta shurawa sannu a hankali har cikin Surayya ya isa haifuwa ta haifo ƴarta mace masha ALLAH da ita.
Cikin zumuɗi Dijen ta yi ta murnar zuwa Yolar sai dai idan ta tuna da zata ga Zee sai jikinta ya yi sanyi, dole dai haka ta daure ta matsa masa ya barta ta biyo su Aunty Ummi suka nufo Yola, saboda a lokacin shi ana tsaka da aiki don during working hours ne, cike da jin daɗin yarinyar Dije ta fara santi tamkar ta sace yarinyar take ji saboda sonta da take yi, Hajiya Mama da su Surayya sai dariya suke yi mata ganin yanda ta maƙake yarinyar bata son kowa ya ɗauketa, don har goyeta take yi sai Hajiya ta yi faɗa take sauketa, Zee ma kullum tana zuwa da ita ake komi shiyasa Dijen ta rage kishinta da take ji aranta, saboda ganin yanda ta ke ta haba haba da ita tamkar cewa babu abunda ya taɓa shiga a tsakaninsu, haka ma da yanda take ta janta a jiki tana nuna mata cewa ai an zama ɗaya babu zancen wata kishiya shiyasa itama ta ajiye komi suka fara ɗasawa, wanda hakan ba ƙaramin daɗi ya yi wa Hajiya Mama ba, ta ƙara godewa ALLAH da har ta jajirce Safwan ya dawo da aurenta, don tasan dole ne sai ya nemi wani auren tunda har ya saba da mace biyun, kuma da wacce ba'a san halinta ba gwara wadda daman cen an san halinta sai a ci maganin matsalar.
Aka yi taron suna lafiya cike da ƙayatarwa yarinya ta ci sunan uwar Mijin Surry ana yi mata laƙabi da ilham, bayan suna Safwan ɗin ya zo ya yi kwana biyu sannan ya kwashi Matarshi suka koma Abuja. kawosu ita da
Sannu a hankali itama Dijen cikinta yana ta miƙawa har ya kai watannin haifuwa, Hajiya Mama ta matsa masa akan dole ya dawo da ita wurinta ta haifu, amman ya nuna shi dai ya fi son idan ta haifu sai su dawo yolar, saboda cen ɗin tana samun kulawar manyan likitoci a Asibitin da take awo, sai da Hajiya Mama ta yi masa jan ido sannan ya kwasota da himilin uwar siyayarta da ta jaririn da za'a haifo masa, don daman cen shi rabuwa da ita ne ba ya so saboda ko da take da titsetsen cikinta idan jarabarshi ta motsa tasan ta yanda zata faranta masa har ta gamsar da Habibynta.
Shi yasa ko da suka zo Yolar ya kasa ya tsare gidan Hajiya Mamar ya ƙi barin garin har sai da korashi saboda yanda ake ta nemanshi a ma'aikatar ta su, saboda muhimmancin da yake da shi dole ne wani abun sai da shi.
Satinta ɗaya a Yola ta fara jin sign na naƙuda, Hajiya Mama tana bata kula sosai da sosai don itama ɗin har nurse's ta samo mata masu duba mata ita har gida ba sai anje Asibiti ba, Zee kanta kullum tana gidan ana renon cikin da dakon zuwan haifuwar, sai ko ga shi cikin ikon ALLAH wata ranar juma'a Asubar farin ta fara naƙuda, jikin Hajiya Mama yana rawa ta saka direba ya kwasheta da kayan da duk za'a buƙata suka nufi wata babbar Asibin da ke garin yolar, cikin nasara kwata kwata bata yi minti goma da shigarta labour room ba ta haifo santalelen yaronta Mai kama da Ubanshi sak, fari jajir har wani yalo yalo yake yi saboda tsabar farinshi, ga shi ƙatoto da shi masha ALLAH tamkar ba haifuwar Dijen Baffah ba.
Farin ciki wajensu Hajiya Mama da fiddo da ma Zee ɗin abun ba'a magana, saboda har rige rigen ɗauka ake yi tsakaninsu su biyu, Surayya ma rufe ido ta yi tace tunda da ita yaron yake kama itace zata riƙeshi, Hajiya Mama dai sai dariya take yi masu idonta akan ɗakin da Dijen take tana ta baccin sauke gajiyar naƙudar da ta sha.
Ango ƙarni kam daman yana kan hanyar zuwa Yolar sai ga kiran Fiddo ya shigo wayarshi cikin kuwwa da ihun murna take sanar da shi an samu Baby boy, ba shiri shi ma ya buga wata ƙatuwar kabbara ya ce
"ALLAHU Akbar? Alhmdllh! Shikenan na zama Baba, Little sis kina da tukuici mai tsoka a wurina, to ya ita Mamar boy ɗin lafiyarta ƙalau dai ko?"
Cikin murnar albishir ɗin da ya yi mata na tukuici ta ce "fine take big bros bacci ma ta ke yi yanzu haka"
Baki a washe ya ce
"Ok Ina Kan hanya daman ganin na kusa ƙarasowa garin ki shafa man kan babyna"
Cike da jin daɗi fiddo ta koma ɗakin tana dariya ta ce "Wayyo daɗi Ni ce na yiwa yayanmu albishir ya ce in tsumayi tukuicina"
Surayya da ke ta faman murnar ta sameshi a wayar da nufin ta riga kowa sanar da shi ba shiri ta kashe wayar tana harararta ta ce
"Ai WALLAHI kin ƙware da mugunta yanzu don salon yaudara shine kika fice waje kika rigani to ai dole mu raba koma minene"
Zee sai dariya take masu Hajiya Mama ta kira cen garinsu Dijen ta sanarwa da su Baffah, sannan ta dinga kiran mutane yan'uwa da abokan arziƙi tana ta sanarwar haifuwar, kafin ka ce me Asibitin ta cika da yan taya murna kowa baki har kunne.
Angon ƙarni ma ko da ya zo ya taradda mutane ciccike sai tayashi murna ake yi, sai washe baki yake yi amman idonshi suna cen wajen dubo ta ina zai hango kyautar da ALLAH ya yi masa?, Aiko sai ga shi ya hango babyn hannu wata dattijuwa tana tofeshi da addu'o'i.
Cikin sauri ya nufeta ba kunya ya saka hannu ya karɓe yaron tamkar ya yi ihu saboda daɗin ganin yaron a hannunshi, ba tare da tuna da inda yake ba ya kaiwa yaron kiss a goshi da baki, sannan ya hankalta da mutane bakinshi ya ki rufuwa saboda dariyar kanshi da jin daɗin ganin ɗan shi,sannan ya miƙa yaron yana tambayar Hajiya Mama Dijen ta yi masa nuni da ɗakin da take hutawar, ya nufi ɗakin zuciyarshi fess da farin cikin hangota kwance har a lokacin tana ta baccinta, ya tsaya jikin gadon ya shafo kanta tare da duƙowa ya yi mata kiss sannan ya riƙo hannunta, cikin sauri ta buɗe idonta ta saukesu a kanshi ba shiri ta washe baki da murmushi akan fuskarta ta ce
"Habiby"
Ya riƙe hannunta duka biyu ya ce "sannu da ƙoƙari kin ji? ALLAH ya biyaki da gidan Aljannah, naga yarona Masha ALLAH har ya fiki kyau"
Ta ɓata fuska tare da turo baki ta ce
"Saura ƙiris in fara kishi da shi yasin"
Yana dariya mai cewa cike da zallar ƙaunarta tare da shauƙin sonta da ke ɗibarshi, ya