Showing 87001 words to 90000 words out of 136985 words
auren baki canza wannan halin naki ba to idan ya je mantawa ma zai yi dake ya yi ta Amaryarshi, ya barki sake da baki anan kina lissafin lokacin dawowarshi, wataƙila ma idan ya ji daɗi sai dai kiji ya ƙara wasu shekaru yace ba yanzu zai dawo ba"
Dije ta yi shiru sannan ta ce "to yanzu idan nayi masa duk abunda yake son zai fasa auren ko kuwa??? "
Inna ta yi saurin faɗin
"Ina ruwanki da aurenshi ya auri matan duniya ma idan zai iya kedai ki bi hanyoyin da duk na sanar da ke ki samu ki samo kanshi, da kinyi haka shikenan kin gama da matsalar wasu mata cen, don shi da kanshi zai bayyanawa matan matsayin da kike da shi a wurinshi, kuma dole ma suma su shiga taitayinsu idan har suna son zaman lafiya tare da shi"
Dije tace "aiko inna sai na ba ki mamaki don kuwa bazan taɓa bari wani ya sake jin tsakanina da shi ba, in dai har hakan shi zai kankaro mani darajata a wurin ƴanmatanshi"
Inna tace "yawwa Dijeta ki gwada hakan da na sanar da ke ke da kanki zaki gano irin nasarar da za'a yi"
Haka Inna ta yi ta ɗorata a hanya har taga Dijen ta fara gyangyaɗi sannan tace su kwanta sai da safe a ci gaba, Dije ta baje tana ta sharar baccinta mai cike da mafalkai iri iri na Safwan da budurwarshi Zee.
Ko da safiya ta waye tun asuba Inna ta ci gaba da bata wasu darussan, Dije kam ta naɗe komi cikin ƙwaƙwalwarta har ALLAH Allah take yi ta fara aiwatar da su idan sun koma cen, fatanta kawai Safwan ɗin ya nunawa Zee irin yanda take da matsayi a wurinshi.
Hhhhhh wasar zata fara kenan😅
Akafta🤪
D/AUTA CE
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*ALHMDLLH MUTANEN ƘARANGIYA BA ABUN DA ZAN CE DA KU SAI GODIYA, SABODA KUN NUNAWA LITTAFIN ƘAUNA FIYE DA YANDA NAYI TUNANI, TSAKANINA DA KU SAI SAMBARKA DA SON SO IRIN NA FISABILILLAH😍 ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU*
*Lamba ta 52*
Ko kafin Safwan ɗin ya zo tuni Dije ta yi wankanta tsaf ta shirya, cikin zuciyarta cike take da ɗokin zuwan na shi saboda ta bashi haƙuri akan abunda ta yi masa, duk da kuma wani sashen na zuciyarta cike yake da jin nauyin haɗuwarta da Hajiya Mama, saboda yanda ta kamo hanya abinta ba tare da ta yi sallama da ita ba, bayan ta gama kammala duk abunda zata yi ne tace da Inna tana so ta je ta yi sallama da Inna Gambo, Inna tace ba inda zata je har sai Mijinta ya zo, ta ɓata fuska tace
"Inna fa sauri zan yi inje in dawo don kada ya zo yace sauri yake yi ba zai bari inje ba"
Inna tace "sai ki lallasheshi ai tunda kina son ya barkin"
Suna cikin wannan diramar ne suka jiyo ihun yara da saukar mota a ƙofar gidan, Dije ta diririce tace
"Kinji ko Inna gashi nan ma har ya zo ban tafi ba"
Inna ta maka mata wata uwar harara ta ce, "da kin je ai da zai ɗaukemu mutanen banza in ya zo bai taradda ke ba.."
Sallamar Usmanu da shi Safwan ɗin ne ya katse maganar Inna ta yi saurin faɗawa ɗaki ta sako hijabi ta fito suna gaisawa, Dije Usmanu yana baza masa tabarma da nufin ya zauna yace
"Ai da ka barta tafiya zamu yi saboda kada mu yi dare sosai kafin mu isa Gombe"
Usmanu ya kalli Inna yace "Ina Baffah su yi sallama to don naga baya gidan??"
Inna tace "yanzu nan zaka ganshi don bai daɗe da fita ba"
Usmanu ya baza tabarmar Safwan ya zauna yana kallon Dije dake zaune saman turmi tana yankan akaifa, don tun da ta gayar da shi ta sha jinin jikinta.
Baffah ya shigo cikin sauri yana yi wa Safwan Barka da zuwa bayan sun gaisa ne Baffah ya yafito Dijen ta taso jiki a sanyaye saboda yanda take jin gabanta yana faɗuwa tun lokacin da ta yi ido biyu da Safwan ɗin, saboda wani sihirtaccen kallon da ya jefeta da shi, ba shiri ta yi saurin kawar da idonta, shiyasa ko da ta zo wurin Baffan bata bari sun haɗa ido ba ta zauna gefen Baffan, Baffah ya kalli Safwan yace
"Bakina ba zai gaji ba wajen baka haƙuri akan ƙurciyar Dije, don ALLAH ka ƙara lurar da ita akan duk abunda ka ga ta yi na rashin kyautawa, kai kuma ka ji tsoron Allah ka riƙe matarka Amana, sannan ka yi mata uzuri akan abunda ta aikata a bisa kuskure"
Safwan ya sunkuyar da kanshi yace, "ba komi Baffah insha ALLAHu komi ya wuce kuma ma hakan bazata sake faruwa ba, adai ci gaba da yi muna addu'a kawai saboda addu'arku tana da tasiri sosai garemu"
Cike da jin daɗin zancenshi Baffah ya kalli Dijen yace "ke kuma ki yiwa Mijinki biyayya duk abunda ya ce dake ki yi kar kiyi masa musu ki amince, saboda in yasan abun nan ba mai kyau bane kema kinsan ba zai ce ki aikata ba, don haka yi nayi bari na bari shine halin matayen kirki, saboda haka kiyi ƙoƙari kiyi koyi da halin mahaifiyarki don kin fi kowa sanin yanda take zama dani, saboda haka kema ki koya ki zauna da Mijinki cikin girmamawa, ALLAH ya yi maku albarka ya baku zaman lafiya a cikin zaman aureku"
Daga Dijen har Inna har shi Safwan ɗin da Usmanu da ke tsaye sai "Ameen Ameen" suke faɗi, Inna tace ta je ta ɗauko Hijabinta sabo da ta bar mata, Safwan ya ciro kuɗi a masu dama ya ajiye gaban Baffah sannan ya miƙe, cike da jin daɗi Baffah yace
"Haba haba ai kuma hidimar tayi yawa gaskiya, ka barshi kawai ALLAH ya sa albarka"
Safwan ya nuna sam bazai karɓa ba dole Baffah ya dawo godiya tare da sanya alkhairi, Dije ta shiga ɗaki ta ɗauko Hijabin Innar da ta bata sabo fil,, Usmanu ya ɗauki manshanun da Baffah ya shigo da shi cike da galam ya je ya saka masu a mota tare da taimakon Safwan ɗin da ya bi bayanshi ya buɗe masa Boot ɗin, Dije ta sako hijabin tana ɓata fuska ta nufi sashen Hansai suka yi sallama, sannan ta fito ta kalli Inna tana matsar ƙwallah tace
"Inna yanzu shikenan bazan je inyiwa Gambo sallama ba? Ga shi ma gidan kowa ma baki barni na je ba"
Inna ta ce "ki tambayeshi idan ya amince ku je tare da shi ma sai ya gaisheta"
Dije ta fito Inna da Hansai da Baffah suka biyo bayanta suna yi mata ALLAH ya kiyaye hanya, sai da Baffah da kanshi yace da shi don ALLAH ya biya da ita ta yi sallama da Inna Gambon, cike da jin daɗi ta shige motar tana yi masu bye bye suna yi mata har suka bar ƙofar gidan, kai tsaye Safwan ya nufi gidan Maigari bayan sun gaisa sama sama ya yi masu alkhairi suka nufi gidan Duduwa tana nuna masa hanya, yara suka biyosu buuuu! A baya suna yi masu Allah ya tsare.
Bayan sun gaggaisa da Gambon ne itama ya yi mata alkhairi sannan ya fita, cikin barkwanci ta dinga tsokanar Dijen, sannan ta shiga ɗaki ta ɗauko wani abu a gorar lacasera tace ta sha rabi ta ajiye rabi daga baya ta shanye, Dije tana dariya ta kwankwaɗe abun duka ta yasar da gorar tana goge baki tace
"Haka kawai ki saka man wata doka cen marar tushe?, To yanzu dai na shanye sai inga kuma wani fi'ilin da za'a yi man"
Ta ƙare maganar tana dariya, Gambo riƙe da baki tace
"Ni ai tausayinki nake ji shiyasa kika ji nace ki raba biyu, saboda takanas na dafa maki shi da hannuna dalilin da yasa na yi ta aiken ki zo mu yi sallama, amman tunda ke jaruma ce ALLAH ya baki ikon jurewa"
Dije tana dariya tace
"Na shiga uku Gambo me yake sakawa ne???"
Gambo ta ce "idan kun zo kwanciyar auren zaki gane da kanki"
Dije ta ƙyalƙyale da dariya tace "Oh Ni Dije ai ke Gambo ni ba wata kwanciyar aure da nike tsoro, tunda asali ma Ni ba a ɗaki ɗaya muke kwana ba balle har ayi kwanciyar"
Gambo ta maka mata wata uwar harara ta ce, "to wannan karon WALLAHi kika gudo sai munyi maki bankaɗa a garin nan"
Dije zata yi magana taji horn ɗin motar da ƙarfi, ta fito tana dariya Gambo ta biyota a baya har wurin motar, in da suka taradda Balan Duduwa tsaye da Safwan suna magana, sai zuba fadanci yake yi yana godiya, wanda ba'a raba ɗaya biyu akan kamar ma kyauta ce Safwan ɗin ya yi masa yake godiya, Gambo tace da Dijen
"Kada dai ki mance ki tambayeshi abunda kika taɓa tambayata ko kin mance in tuna maki?"
Dije ta bud'e motar ta shiga ta zauna tana dariya tace,, "ai kuma yanzu wannan ya wuce Gambo tunda wadda ma aka yi abun kanta yanzu har ta mance da ma an taɓa yimata laifin, to ni kuma miye nawa na bin diddigi yanzu? ALLAH dai ya bamu haƙuri dukanmu"
Gambo tace "Ameen amman ya kamata kema ki tambayeshi saboda akwai ƙaruwa a ciki idan kin sani"
Dije tace "Tom naji Ni dai matsa kada mu tureki ki yi kuka"
Gambo ta dungure mata kai tace "kece dai wadda zaki yi kukan amman nikam me zai haɗani da kuka yanzu?? Sai dai kuma in na farin ciki idan ina da rabon ganin yaran da zaki haifowa"
Haka suka rabu Dije tana ta ƙyalƙyala dariya suka baro ƙofar gidan suka kama hanyar fitowa garin, Safwan yana kallonta sai dariya take yi ita kaɗai, sai cen kuma ta fara matsar ƙwallah cike da mamaki yace
"Kukan fa?"
Tace "WALLAHi kamar kada in baro garinmu gashi ma kowa banje gidanshi ba tunda na zo"
Safwan ya yi murmushi yace, "to ai gara da baki je ba saboda kada zunubin ya yi maki yawa, kin zo ba izinin miji kuma ki kwashi ƙafafuwa ki fara bin gidaje, ai sai ki janyo Mala'iku su yi ta aikin rubuta yawan zunubinki"
Dije ta share hawayenta tace, "ai dai yanzu ka yafe man ko?"
Ya yi yar dariya yace, "na yafe amman Ni ma zan fanshe wahalar da aka sakani, sannan Ni ma in nemi yafiyarki idan na fahimci abun zai janyo man aljanun tekun banbaradusa"
Dije ta yi saurin kallonshi tare da rufe bakinta tana dariya tace, "WALLAHi ba ruwana in har su mulƙutus baraƙus suka jiyoka, don tsaf zasu iya yin langaɓu da kanka a bakin tekun bangon duniya"
Ba shiri Safwan ya yi dariya saboda ba ƙaramar dariya ta bashi ba, amman ya waske yana yi a hankali don maganar da ta yi ce tasa ya tuno da labarin da wani ɗan Maigarin ya bashi nata, lokacin da ta yi ƙaryar aljanu a ƙofar gidan Maigari, musamman abunda ta yi wa Bafade ba ƙaramar dariya yake bashi ba idan ya tuna.
Ganin kamar dariyar taƙi ƙarewa ne saboda murmushin kawai yake yi yana dariyar a hankali, shi yasa ta ɓata fuska tace
"Wai yau kai ne kake dariya haka? Daman kana da fara'a shine kullum kake faman haɗe fuska??"
Safwan ya ci gaba da dariyarshi ba tare da yace da ita komi ba, itama ta yi shiru tana kallon gefen titi har suka shiga babban birnin garinsu Dijen, har sun wuce wani wuri ya dawo baya yana kallon bakin titin yace
"Ga mutuniyarki cen ta fito ko yau bazaki ci ƙosan ba? Ga wani abu cen ma tana suya da alamu shima zai yi daɗi"
Dije ta kai kallonta ga mai soya ƙosan dake bakin titi tace, "me ye abun da take soyawar? ba doya da ƙwai ba ce nake hangowa?? "
Safwan ya gimtse dariyarshi yace, "itace jirani bari in zo"
Ya fice Dije ta bishi da kallo tace, "Ni da ma ka barsu don ko ka saya ba ci zanyi ba ma"
Tana kallonshi har ya dawo da ledodin ya buɗe gefen da take ya ɗora a saman cinyarta, ta yi saurin zabura saboda ruwan team ɗin da suka zubar mata a jiki, sannan ya rufe ya zagayo ya shiga ya tada motar, ta bishi da kallo tare da ɓata fuska tace
"Me nayi maka da zaka ƙonani da tea??"
Yana kallon gabashi yace, "ke fa na siyowa duka ko baki so?"
Dije ta ɗauki kayan ta ajiye a bayan seat tace , "Ni bana sha'awar cin komi a ƙoshe nake"
Yace "ok to tunda kin ƙoshi Ni ki bani zan ci ai"
Ta yi saurin kallonshi tace, "da gaske kake yi zaka iya ci?"
Ya waigo ya kalleta yace, "to me zai hana yana da wani abun ne?"
Ta yi saurin faɗin "a'a"
Yace "to oya a fara bani ga bakin nawa yana jira"
Dije cike da mamakinshi ta ce "me zaka fara ci a ciki"
Ya ce "abunda kika san kin fara ci farkon lokacin da muka fara siyen irinsu"
Dije ta yi saurin kallonshi tace "ƙosai shi za'a baka?"
Ya ce "Yes! In jira ko rowa za'a yimani ne in haƙura?"
Ta sauke tagumin da ta yi tace, "ALLAH ya baka haƙuri ai abun bai kai cen ba, don kare da kuɗinshi ba za'a hana shi shan rubutun malam ba"
Ya yi saurin kallonta yace "au haka ne?"
Tace "eh kam yanda kowa ya siya ya sha haka shima za'a bashi tunda har da kuɗinshi a aljihu"
Ya yi shiru sannan yace, "nyc! Kice haka abun yake? to in fa shi malamin yaki siyar masa fa kuma bayan ya karɓe masa kuɗin?"
Ta yi saurin faɗin
"Bama zai ƙi siyarwa ba tunda dai ba kyauta aka ce ya bayar ba, sai da aka bashi kuɗi ya karɓa aiko ya zama dole ya bada ko yana so ko baya so"
Ya yi saurin faɗin "woww! Ki ce Ni nawa shan rubutun zai zo man cikin ruwan sanyi"
Tace "tabbas amman ka gwada ka ga in har kana shakku a maganata"
Ya yi saurin kallonta tare da yin wata siririyar dariya yace, "hmmm! ALLAH ya bani sa'a to"
Tace "Ameen"
Hmmmm nima dai nace Ameen ɗin don tsuntsun da ya ja ruwa ..............😝ku ƙarasa mata ni dai na yi nan🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️
Not edited
Akafta😹
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Sai kun yi haƙuri dani kwana biyun nan saboda uzurora da suka sha kaina, amman insha ALLAHu zan ƙoƙarta in yi maku ko ba yawa, sai dai ina son ku yi man uzuri idan kuka jini shiru ba ba daga gareni bane kamawa ta yi*
*Lamba ta 53*
Haka ya buɗe baki tana ta bashi ƙosan yana ci yana tuƙinshi hankali kwance yana jin kanshi cikin wani sabon nishaɗi, don ko tea ɗin ba ƙyama ba wata damuwa ya karɓa ya dinga shan abunshi, ƙarshe ma itama sai da ya tilasta mata ta ci kaɗan sannan ta buge tana ta bacci abunta, don kuwa tun tana kallon gefen titin tana ta wassfa kunya zata ji idan ta je wurin Hajiya Mama, don sai yanzu take hango rashin dacewar abunda ta aikata, saboda ƙiri ƙiri ta haramtawa kanta tsayawa ayi bikin Surayya da ita, tana cikin tunanin ne taji wata muguwar kasala ta sauko mata a jiki, sai gata da jera hamma kala kala Safwan dai sai tuƙinshi yake yi yana kallonta ta gefen ido har baccin ya yi awon gaba da ita.
Tun daga babban birnin garinsu take ta sharara bacci mai shegen nauyi har ta kwashi kusan awa biyar bata falka ba, shima tun yana ganin baccin gajiya ne take yi har ya fara tsarguwa da baccin nata, dole da suka je wani gari ya sauka ya tada ita cikin mayen baccin suka ci abinci suka yi salloli sannan suka sake ɗibar hanya.
Tafiya tana miƙawa ta ci gaba da baccinta har suka kai Gombe bata san sun kai ba, saboda misalin sha biyun dare ne har da wasu mintuna sama suka shiga garin, daman yasa anyi masu booking ɗin wani hotel suka sauka da nufin da safe su kama hanyarsu ta zuwa Yola.
Shigarsu masaukin ke da wuya ya faɗa toilet ya yo wanka ya fito daga shi sai trouser yana goge ruwan da ke jikinshi da towel, ya kalleta a rakuɓe bakin gadon tana ta baccinta, cike da mamakin wannan bacci da take yawan yi ya duƙo ya sumbaci ƙwayar idonta da karan hancinta, amman ko motsi bata yi ba bale tasan me yake yi, ya saka hannu biyu ya tallafota jikinshi ta faɗo masa yaraf kuma still har lokacin baccin take yi, cikin fargaba ya ɗago fuskarta yana ƙare mata kallo sannan ya kai bakinshi cikin nata tare da jarumtar tsotso halshenta, sai gata da saurin buɗe idonta da suka yi jawur saboda baccin da ta sha ta saukesu duka a kanshi, ba shiri ta ƙwace daga gareshi tana ƙarewa ɗakin kallon sannan ta dawo da kallonta gareshi tace
"Safiya ta waye ne?"
Ya yi ƴar dariya ya ce
"Zata waye dai yanzu insha ALLAH, ki je kiyi wanka kiyo arwallah ga toilet cen ki zo mu yi sallah mu ci abinci"
Dije ta dafe goshinta saboda juyawar da taji kanta yana yi sannan ta nufi inda ya nuna mata ɗin, tsawon minti sha biyar tana toilet ɗin har sai da ya gaji da jiranta ya leƙo sai gata cikin bahon wanka tana bacci, da alama ma ko wankan ma bata fara yi ba, ya tako a hankali zuciyarshi sai nazarin dalilin wannan baccin nata yake yi amman ya kasa gano mafarinshi, ya ɗauki tsawon minti biyar tsaye a kanta yana ƙarewa cikar ƙirjinta kallo, ya lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya ya ranƙwafo ya saka hannu ya shafosu duka biyu ta zabura ba shiri, tare da saurin buɗe idonta cikin firgici da tsoron ganinshi a kanta, ta yi saurin ƙanƙame jikinta tana ɓata fuska, da wata murya mai cike da kasala tace
"Don Allah ka je ni dai yanzu zan yi wankan in fito?"
Ba shiri ya yi guntun murmushi ya yi kamar bai jita ba ya fara ƙoƙarin yi mata wankan tana zillewa, saboda inda yake son ya taɓo ta rufe da hannunta ta dunƙulewa waje ɗaya, ganin zata ɓata masa lokaci ne ya sake yin wata arwallah ya fice yana faɗin, idan bata yi sauri ta fito ba har ya dawo to shi zai yi mata wankan da kanshi, ai kuwa jin haka yasa a gurguje ta