Showing 366001 words to 369000 words out of 450388 words

Chapter 123 - Gudun Aure Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

4238

ciwo kuma suka haifar mana da zuria masu tarin yawa da ba su d'auke da wata lalura makamaciyar wannan don haka wannan magana da kuka zo mini da ita ba za ta dakatar da ni daga abinda na niyyata ba a yau idan har Alhaji Tajo ba kai zaka nuna mini cewa ba ni da alfarma a wajenka ba."
"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! abinda yake ta fad'i kenan a cikin ransa zuciyarsa na wani irin dokawa da tashin hankali da damuwa. Babu fa wani dalili da zai sanya shi yin rayuwar aure mai nisan zango da yarinyar nan dalili kuwa shine yana da burin kara samun haihuwa. Tabbas Allah ne mai yin yadda ya so idan ya so zai iya bashi lafiyayyun yara da yarinyar ba kamar yadda yake hasashe ba amma rashin nutsuwa da lamarin ya sanya masa fargaba yarinyar ba tsararsa ba ce gabad'aya koda an daura masa aure da ita ba ya tunanin zai iya had'a shimfida da ita balle har ta kai ga ta d'auki ciki suka shiga cikin zullumi akan abinda za a haifa mai lafiya ne ko mara lafiya. Amina ta riga ta zama k'addararsa shine dalilin da ya sanya yake ji a zuciyarsa wannan dalilin ba zai sanya ya rabu da ita ba kuma zai iya cigaba da zaman aure da ita. Amma dai a yanzu ba ya tunanin zai sake yarda ya auri wadda jininsa da nata bai daidaita ba.
Maganar Malam Nuhu ta katse tunanin da yake yi ya ji shi yana cewa..........
'?
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*152*
Suka juya gabad'aya suna kallonsa a lokacin da ya fara magana kamar haka. " Ya kamata a k'ara duba wannan uzurin da suka zo da shi Allah Ya gafarta Malam nasan da wahala Alhaji Tajo ya d'auki aniyyar tozartaka a irin wannan ranar da gabad'aya ta zame mana abar alfahari da farinciki mussaman da muka tabbatar da cewa wanzuwar lamarin shine abinda ka fi buk'ata a yanzu domin sake kulla zumunci mai karfi tsakaninka da abokinka Alhaji Ibrahimu Allah Ya yi masa rahama da gafara."
Suka amsa da "Amin gabad'ayansu kafin ya sake nutsuwa sosai ya cigaba da cewa zahiri wannan lalura da suke magana akanta akwaita kuma har yanzu tana k'ara yaduwa a wasu wuraran da ba su d'auki abinda ya zo a zamanance da muhimmanci ba. Malam ko dai ka manta shekarun baya ashirin da biyu da suka wuce muka dinga dawaniya da mai sunan Inno har Allah Ya d'auki ranta a asibitin Murtala na cikin garin kano wanda sai a lokacin ne gabad'aya muka san ga cutar da ta zama ajalinta."

ABINDA YA FARU.
Shekaru ashirin da bakwai can baya Malam Nuhu ya auri matarsa ta fari Lantana wadda a yanzu ba ta raye ta rasu dalilin farfadiya tunda tana da mutanan b'oye sa'i da lokaci sukan tashi. Auran soyayya suka yi a cikin kauyen nasu kamar yadda al'ada take duk da wannan lalurar tata ta farfadiya hakan ya zauna da ita tunda yana sonta shi kansa mahaifinsa ya bashi gudumuwa kwarai wajan yi mata magani idan ciwon ya tashi. Da ta samu ciki sai wahalar da take sha ta sake ru'banya tunda kowa ya san yadda masu wannan ciwon suke shan ba'kar wahala a duk lokacin da iskar ta buge su a kan titi ne ko a kasuwa ko a gida sun dinga katantanwa kenan da jikinsu suna malkwadewa tare da taune lebensu da kumfa dafara mai hade da jini.
Suka dinga bige ta a kai akai don babu wanda ya tsammaci za ta haife wannan ciki da yake jikinta lafiya saboda yadda take jigata.
Cikin ikon Allah da lokacin ya zo ta haihu kalau aka samu 'ya mace wadda ta ci sunan Inno Ramatu suke kiranta da Rahma. Tun tana yarinya jinjira ta fara nuna alamun rashin lafiya ido ya jirkice daga fari zuwa yellow cikinta ya yi kurcici sai siraran kafafu da hannu. Da masifar kukan tsiya da zafin jiki domin koyaushe idan aka ta'ba jikinta radau ake jikinsa. Da yake kauyene a wancan lokacin da babu wayewa sosai kamar wadda suke ciki a yanzu sai duka daga can b'angaran iyayenta dana shi Malam Nuhu suka alak'anta lalurar da yarinyar take yi akan shafar aljanu dalili uwarta tana da su kuma sun tashi sosai a lokacin da take d'auke da cikinta a jikinta..
Suka dukufa wajen yi mata jike-jike na maganin gargajiya daga can b'angaran malamin kuwa yana yi mata rubutu da tofi ana bata tun tana jaririya ta saba da shan sassaken magani mai d'auke da ruwan rubutun da kakanta yake yi mata. Har hayaki sukeyi wa yarinyar saboda duhun kai har rukiya sai da Malam D'aha ya yi mata da abin ya ci tura duk a tunaninsu aljanu ne suke tsotse ta kuma suke hana ta bacci da daddare suke firgitata tana kwanan kuka. Duk wannan wuyar da yarinyar take ci Allah bai amshi abarsa ba sai da ta yi shekaru hud'u tukkuna cikin halin rai da rayuwa domin a duk lokacin da ciwon nata ya tashi hayaki ake yi mata aka dingi bata sassake da saiwa wadda aka dafa da jar kanwa.
Wajan cirani can Katsina uban suke hira da abokinsa yana gaya masa halin da yake ciki da yarinyarsa wannan mutumin a irin bayanin da ya yi masa ya gane cewa babu maganar iska sai dai idan wata lalurar ce shine ya ba shi shawara kan cewa ya kaita asibitin cikin gari na kano general ne na kowa da kowa domin yawanci ma mutanan kauyen sun fi morarsa har ya ta'ba bashi labari shima daga nan k'atsina garinsu ya ta'ba kai mahaifiyarsa asibitin na Murtala aka dubata har ta kwanta na tsayin sati hud'u kuma ta samu kulawa kwarai ya ce masa su jarraba yin na asibiti ko za a dace.
Koda ya dawo gida ya sanar da Malam D'aha da kyar ya amince da a d'auki yarinyar a tafi da ita a ganinsa abinda yake damunta bai had'a hanya da asibiti ba domin duka sun d'auka cewa lalurar uwarta ce ta shafe ta.
Ba a tafi da uwar ba tunda tana halin ciwo Inno kakarta ita ta goyata suka tafi dawowar da yarinyar ba ta yi ba kenan domin kwanansu daya a asibitin ciwon ya tashi da masifar k'arfi likitoci suka dinga kai kawo a kanta inaaa babu jini ya kone ta rasu.
A wannan lokacin ne likitan da yake tsaye a kan yarinyar ya zauna ya dinga yi musu bayanin musabbabin abinda ya yi ajalinta babu iska sai tsananin ciwon da Allah ne kadai yasan maganinsa.
Duka ba su gazgata hakan ba a lokacin suka dawo gida da gawar yarinyar daga lokacin ne Malamin ya ce kada a sake daukar wani daga cikin zuria'arsa a kai asibiti duk cuta akwai maganinta cikin al'kur'ani mai girma.
Shekara biyu bayan rasuwar yarinyar uwar ma Allah Ya d'auki rayuwarta sakamakon wata fad'uwa da ta yi iskokai da suke tare da ita suka bugeta a bakin kofar bandaki daga lokacin jikin nata ya'ki dad'i har dai rai ya yi halinsa.
Wannan shine abinda ya shud'e a shakarun baya kuma a iya gwagwarmayar da yake da sauraran redio hurd'a da mutane bambamta tunda a can katsina wajan da yake gudanar da sana'arsa birni ne ba kauye ba ya tabbatar da cewa duk bayanin da ake yi akan wannan lalura gaskiya ne ya gazgata itace silar yarinyarsa ta fari Rahma wanda ada can suke d'auka shafar aljanune.

Malaman D'aha ya yi shiru jikinsa ya d'an shika kadan a lokacin da yaron nasa ya tariyo masa abinda ya shud'e a cikin wasu shekaru da suka gabata. To amma shi a ganinsa wannan kadai ba zai hana k'ulla aure ba domin a zamanin baya wanene ya san da yin wani gwajin kafin a yi auran kuma cutar ba ta yawaita ba."
Malam Rabi'u da jikinsa ya gama mutuwa saboda wannan lamari ya furta." Ya Malam a duba wannan lamari a kawo sasanci a cikinsa domin kada a zo a yi abu anan gaba a koka tun yanzu ya kamata a ce an magance matsalar nan domin ana yin aure ne domin samun zuri'a wadatattu kuma masu lafiya muna neman alfarma a duba a kuma yi adalci ta kowane bangare."
A dan sanyaye ya furta." Rabi'u ba na 'ki ba ne zuwa yanzu ni ma jikina ya yi sanyi tunda zamani aka ce, Annabi Muhammadu S.a.w shi kansa ya yi magana akan zamani duk yadda muka kai ga ta'kawa da gudun sa'bawa Ubangiji idan abu na zamani babu yadda muka iya amma abin lura anan shine mu yi yaya da jama'ar da muka tara domin taya mu murna wannan shine abinda ya fi damuna a yanzu."
Malam Nuhu ya furta." Abu ne mai sau'ki Ya Malam kana da almajira da suka 'yantu da yawa wasu sun shiga cikin gari neman arziki kamar yadda ka saba duba nagarta da cancanta a cikinsu ka bashi auran Hajara a daura da duk wanda ka zab'a mata in sha Allahu ba za a samu wata matsala ba daga kowane bangare."


na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba.

Daga can b'angaransa kuwa ya kira sunan Ubangiji babu adadi ya yi tahamidi tare da jaddada godiyarsa a gare shi ganin yadda aka samu kan malamin cikin k'ankanin lokaci ya magantu cikin kwarin gwiwa ya furta." Idan babu matsala an kuma ba ni wu'ka da nama ina nemawa wani aminttaccen yarona auran yarinyar zan kuma zame musu Uba gabad'aya."
Malam Nuhu ya washe bakinsa Yana fad'in." Ka ji wani iko Allah ko Malam ina ganin duk wanda zai fito daga wajen Alhaji Tajo za a samu nagarta da sasihancin abinda ake buk'ata an samu mafita cikin sau'ki sai a juya d'aurin auran zuwa gare shi.""
Malam D'aha ya dube shi cike da damuwa ya furta." Na so tabbatuwar auran nan da raina ya kwadaitu da shi Alhaji Tajuden amma ga yadda Allah Ya juya lamarin muna fatan hakan ya zama alheri da samun abinda ake buk'ata na kuma baka wu'ka da nama akan Hajara."
Ya dinga godiya kuwa kamar wanda ya yi masa gagarimar kyauta Malam Nuhu fadi yake yi mu ne za mu yi godiya fa Alhaji Tajo mune muke da godiya a wurinka.
Ya tashi ya fita tare da fad'in su jira shi lokacin rana ta yi sosai sha biyu da rabi ana ta haramar tafiya massalaci kai tsaye mota ya nufa Sukairaju ya hango shi ya fito da sauri ya bude masa ya shiga ya mayar da kofar ya rufe ya tsaya daga waje tare da harde hannunsa a k'irji.
Ya sauke ajiyar zuciyar da ba zata lissafu ba godiyar Allah kuwa a cikinta yake yi sai dai yana d'an zullumin saurin yanke hukuncin da ya yi bai kira ta ya ji ya ake ciki ba. Shin wane yaro ne take nemawa aure a yadda yanzu malamin ya karrama shi tare da bashi amana baya tsammanin zai yarda da kowane irin za'bi. Idan wanda take nemawa auran bai yi masa ba zai aurawa Sukairaju yarinyar duk tsiya ya fi shi kuruciya kuma ya tabbatar da cewa zai rike masa ita da amana amma hanzari ba gudu ba shine menene matakin jini tunda dai shi a kan haka ya bijire yana da kyau daga kowane bangare ya samu gamsashen bayani kafin a k'ulla auran.
Jikinsa ya sanyi sosai ya lalubi wayarsa dake cikin aljihu sai a lokacin ma ya lura da kiran da ta yi masa.
Ina zaune jikina duk ya yi la'asar ganin d'aya saura na rana zuciyata na tabbatar mini da cewa wannan auran fa sai an daura shi da mijinki Amina tunda ki ka ga har yanzu bai kira ki ya gaya miki wata matsala ba. Dama fa yana so yaudara ce kawai yake yi miki akwai wani namijin da zai ce baya sha'awar budurci mussaman na yar k'aramar yarinyar irin wannan wadda yanzu take tashi.
Na kwanta a hankali saman gado ina kallon Minal tana yi mini 'buruntu saman madubi yaran dake cikina sai wutsil-wutsil suke yi tabbacin suna buk'atar abinci ba ni kuma da niyyar shiga kicin din babu ma kuzari da karsashin da zan iya gudanar da wani abu.
Na tashi da sauri jin kiran waya na d'auka da sauri shine na sanya a kunnena har muryata na rawa na amsa sallamarsa kafin na ji shi a dake yana fad'in." Wane yaro ne ki ka ce za ki nemawa auran yarinyar nan.''
Jin wannan maganar daga bakinsa na ji sanyi ya cikin zuciyata na daidaita maganata ganin yadda yake furta tasa da isa na ce." 'Kanina ne Usaini dazu na kira shi na gaya masa kuma mu yi maganar genotype domin shine akan gaba kafin komai. (AA) genotype blood group (o)" Duka na zayyano masa wannan bayanin babu hadiyar yawu.
Ya furta.'' Ya kuke da shi Usainin kuma menene sana'arsa kin tabbatar dai da nagartarsa ko domin yanzu amanar yarinyar tana hannuna. Na ji maganar daidaituwar jini amma ina so kada ki rufe mini da son lallai aure ya tashi daga kaina ya koma kan waninki, ki gaya mini halinsa dalili mas'ala irin ta aure mussaman irin wannan da ta zo a jirkice ba a rufi ana fayyace gaskiya daga kowane bangare da ni da ke gabad'aya mun sheda nagarta da tarbiyar yarinyar nan shi wanda ki ke nemawa auran nata nake so na ji bayani na gaskiya a kansa kada ki rufe mini komai a kansa."
Na ji kaina ya wani sara saboda tsananin mamakin maganganun da yake furta mini. Wato da irin abinda zai saka mini kenan. Kwanaki uku da suka wuce ya zama kamar wani mahaukaci saboda tarin damuwa da tashin hankali. Na shiga cikin matsalarsa na bashi shawara domin samun mafita shine yanzu zai juya maganar ta wata siga daban neman mafitata ne ya sanya na ce zan nemawa dan'uwana auranta saboda shi kada ya aureta tunda Ina kishi akan yarinyar. Wannan shine karatun kawai domin duk yadda ya yi maganar a kudindine na fahimta tunda ni ba mahaukaciya ba ce.
Na daure sosai tare da danne tashin hankalin da yake yun'kuro mini na ce." Usaini kanina ne ubanmu daya ba zaka san shi ba gaskiya tunda shi namiji ne kwarai don samun kamarsa a cikin maza a yanzu dai sai an tona yaro ne mai zuciya kuma ba makwad'aici ba. Koyaushe cikin neman na kansa yake yi. Yana da shagon sayar da zannuwa a kasuwar kwari.
Sannan ya tsayar da sallah ya yi karatu daidai gwargwado na addini dana boko baya sata kuma baya shaye-shaye, wannan shine abinda na sani a kansa. Amma idan kana shakku za ka iya kiran waya idan kana da ido ko wanda kake mu'amula da shi cikin unguwarmu ta kabuga ka ce a yi maka binkice akan Usaini Salisu maihula na lungun itacce sunan layinmu ya yi suna haka zalika ma gidanmu ya yi suna babu wanda bai sani ba tun daga bakin titi zuwa cikin lungun Babanmu fitacce ne."
Ya yi jim daga daya bangaran ina sauraran amsarsa gabana na fad'uwa saboda tashin hankali mutumin nan mara mutunci ne tsantsa kuma mai mance alheri da ni yake magana."
Na ji yana fad'in." Ni da Sukairaju na yi wa sha'awarta shima ai kin sheda nagarta da cancantarsa ko na jima dashi Amina bai ta'ba cin amanata ba."
A takaice na ce." Da shi da Usainin duk daya ne ni a wajena idan ka yarda da cancantarsa a yi dashi kawai Allah Ya tabbatar da alheri."
Ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in." A a ayi dai da Usanin kawai tunda yanzu shine sakamakonsa ya bayyana kuma kin tabbatar mini da cewa babu matsala na aminta a yi da shi din.''
Na ce.'' Idan an biya sadakin zan biya ka idan ka dawo a basu dubu dari biyu. Duk abinda ya kamata na al'ada wanda suke yi za mu yi musu."
Ya yi shiru bai ce mini komai ba nasan haushin maganata ya ji. Na sake ce wa." Ka na jina ko idan kuma dari biyu ta yi kad'an daga dari uku zuwa abinda ya yi sama ka biya zan baka kudinka idan ka dawo."
Sai ya kashe wayar bai ce komai ba. Na ja tsaki tare da ajiye tawa wayar zuciyata na tsalle tsabar takaici da b'akinciki da ya guma mini. Wai mutumin da ya rasa mafita ya gigice tare da zama sullutu shine ya yanzu saboda ya samu kansa yake ko'karin juya alheri zuwa sharri. Duk yadda nake 'kin auran a cikin raina ban ta'ba fitowa fili na nuna masa ba saboda gudun irin haka da yake ya iya sharri da lauya zance yana fad'in saboda kada ya aureta na ce ina nemawa d'an uwana auranta. K'warai wannan magana ta tsaya mini a cikin raina ko da na shiga kicin domin d'ora abinci ina tunaninta da mamakin fitowarta daga bakinsa........
'?
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*153*
Haka na kammala aikin da takaici da kuma farincikin nasarar da Usaini ya samu wajan samun damar mallakar Hajara a matsayin matarsa uwar yaransa anan gaba. Akwai daidaito ta kowane bangare a tsakaninsu babu cuta babu kuma cutarwa yadda yake a nutse haka itama yarinyar take a nutse kuma babu rawar kai da iyayi na 'yan matan yanzu matsalar kawai babu zurfin boko a tare da ita wannan
kuma bai kai ace an damu dalilin rashin samuwarsa ba tunda da akwai na addinin zai kori duk wata tangard'a da za a samu a zamantakewar auran nasu wadda ba mu fatan hakan in sha Allahu rabbi.
Wajan uku saura na kintsa jikina sosai kwalliya na yi irin wadda na jima ban yi irinta ba na zuba lece brown a jikina wanda ya ji stones ta ko'ina ga kyau ga kudi na yi amfani da set din gold dina da ban jima da saye ba.
Tare muka ci abinci da yarinyar kamar koyaushe tana yi mini hirar 'yan uwanta da alama ta yi kewarsu nasan duk yadda aka yi sun iso yanzu suna gidan Hajja.
Ina idar da sallar la'asar ya kira ni dama dakon kiran nasa nake yi domin na ji a ina a akwana.
Ya ce

Chapters

Related Ebooks
03, August 2026
Aisha kabir iliyasu

Please book for gudun aure

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login