Showing 243001 words to 246000 words out of 450388 words

Chapter 82 - Gudun Aure Complete Hausa Novel

16 Jul 2026

4322

jikina na kama hanyar fita raina a masifar 'kuntacce.
Ban sauka ba tukkuna sai da na daidaita yanayina na sauka na same su suna nan a wurin suna hira Hauwa hannunta ri'ke da apple tana ci babu abinda ya dame ta sai addu'a da ko'karin rabuwa da cikin jikinta lafiya.

Ban zauna falon ba kai tsaye d'akina na nufa na yi zaune zugum a gefan gado zuciyata na ta yi mini sa'ke-sa'ke masu kyau da marasa kyau! Lallai cikin wannan duniya babu komai face rikici da tarin kalubale.
Babu yadda ban yi ba da Hauwa akan ta shirya bayan magriba mu shiga mu duba Momi amma fafur taki tace itama abar dubawa ce domin kuwa bata kaita jin jiki ba. Ganin taki fahimtata ya sanya na kyaleta kawai muka shirya da Baba Tabawa muka tafi dubanta.
A harabar gidan muka riski Salim da Adam a tsaye suna magana. Da sauri shi babban ya d'auke kansa yayin da karamin ya sassauta a nutse ya dube mu da ladabi yake fad'in." Mama ku ne."
Na ce." E, mune Adam mun shigo duba Momi ne. Sai ya yi yar dariya wadda babu annashuwa a cikinta ya furta." To shikkenan mu je na yi muku jagora."
Gaba ya yi muka bi bayan shi yayin da Salim din yake ta ciccin magani har da jan tsaki. Murmushi kawai na yi a zuciyata gabad'aya yaron ma ni tausayi yake ba ni, domin kuwa ya d'auki lamarin da zafin gaske.
Falo muka zauna ya nufi bedroom din ta yana fad'in ."Bari na sanar da ita." Ba mu kai minti biyar da zama ba daya daga cikin masu aikinta ta fito daga kicin da wata madaidaiciyar roba a hannunta Hassana da Minal suna biye da ita. Ganinmu a zaune ya sanya yaran suka tsaya. Ita kuma mai aikin ta karaso wurin da muke har sai da ta risina kafin ta gaishe mu gabad'aya.

Ina kallon yadda Baba Tabawa take jan yaran da wasa da tsokana amma suna can nesa da mu sun tsaya suna ta kallonmu kamar sun ga dodanni. Duk da akwai sabo a tsakaninmu dalilin shigowar da suke yi amma ganinmu a gidan sai ya zame musu wani banbarakwai
Raina ya 'baci nan take zuciyata ta dinga raya mini abubuwa marasa kyau to idan ba an zauna da yaran an fadi wata magana ba mai zai sanya k'ananun yara irin wad'annan su dinga yi mini wani irin kallo. Abin b'akinciki da takaici ma har da 'yar cikina 'kiri-'kiri saboda kin gaskiya.
Idona na zare musu sosai na ce." Tsayuwar ta mecece idan ba za ku gaishemu ba to ku daina kallonmu, ko mun yi kama da tibi ne.''
Matashiyar mai aikin da take jigila da su tana dariya ta furta." Ke Hassana ku zo ku gaisa Mama ce fa."
Na ce." A'a rabu da ita kada ta zo mu gaisa ta tsaya." Usaina ta fito daga kicin da shafceciyar wuk'a a hannunta tana fad'in." Mairo ga wukar ki yanka mana." Shiru ta yi tana kallonmu yayin da mai aikin ta je ta da sauri ta kar'bi wukar tana fad'in." A can sama fa na d'orata yanzu Usai sai da ki ka d'aukota."
Ba ta ce mata komai ba ta nufo wurin da muke zaune tana zuwa sai ta dora kanta a cinyata tare da zura yatsanta babba a baki tana tsotsa. Na yi shiru ina sauke ajiyar zuciya yayin da na d'ora hannuna a saman kanta.
Ganin haka ya sanya Hassana da sauri itama ta zo ta yi yadda Usainar ta yi dama tuntuni Kamalu ya gaya mini kishi ne da su, duk abinda daya tayi to babu shakka yar uwata ma sai ta yi. Da hannu na yi wa Minal alama ta zo wurina. Ta kuwa taho kataf-kataf domin yanzu itace take tashen ki'ba a cikinsu. Na ri'keta sosai Ina fad'in." Ina Khalil yake?" Cikin yanayin maganarta ta furta." yana can gidan anti Nusaiba."
Baba Tabawa sai murmushi take yi tana jan su da wasa. Hassana da Usaina iyayen miskilanci ne, Minal din ta fi su sakin fuska da son mutane. Tunda suka dora kawunansu saman cinyata babu wadda ta dago sai da suka ji muryar Babansu tukkuna.
Tare suka fito da Momin kallo daya na yi mata gabobin jikina suka shika wata irin rama ta yi mai ban tsoro kanta yana nema ya rinjayi gangar jikinta abinka dama da siririya idanuwanta sun yi kuru-kuru ta d'ashe k'warai da gaske ta yi fau, babu shakka babu k'arya a cikin lalurarta yadda mijinta ya dinga jadadda ciwon ya ci karfinta yanzu na sake gazgata kammaninta duka sun canza ta hadu da ciwuka masu hatsarin gaske sugar da hawan jini.
Ta zauna tare da taimakonsa suka zauna kujera d'aya yana dan gyara mata 'kafafunta ko daga inda nake zaune Ina kallon yadda jikinta yake rawa.
Ban ji haushinsa ba ko kad'an domin a yanzu dai babu maganar kishi ga matar da take cikin irin wannan yanayin na halin ciwo mai tsanani. Ta dinga fara'a a zahiri tana nuna jin dadinta. Muka gaisa cikin kulawa da mutunci. Na yi mata sannu da jiki haka zalika ma baba Tabawa ta dubata sosai. Ta dinga dariya ganin yadda twin's suka yi mini farincikinta ya kasa 'boyuwa ta ce." Ai maigidan yake gaya mini ba ku ji labarin na kwanta a asibiti ba, ku yi hakuri don Allah da yake ni kaina lokacin ba ni hayyacina sai da na kwana na yini tukkuna na fara gane wanda yake kaina. Ko da na tambayi Nusaiba da Nabila shin an sanar daku suka ce mini eh sun sanar daku halin da ake ciki, na gode sosai Amina Allah Ya bar zumunci."
Cikin nutsuwa da kulawa na ce." Allah Ya sawwa'ke yasa kaffara ne amma maganar gaskiya babu wanda ya gaya mana cewa baki da lafiya balle mu ji cewa kin kwanta a asibiti na tsayin wannan kwanakin." Na yi shiru Ina mayar da numfashi kafin na cigaba da cewa." Tabbas da mun sani me zai hana mu zuwa asibiti mu duba ki, babu niyyar wulakanci ko kuma nuna wariya a tsakaninmu dake kuma ciwo ake ce kin ga kuwa lalura ta kori komai, Ubangiji Allah Ya sawwa'ke, Hauwa ta ce a duba ki da kyau kuma tana yi miki sannu da jiki itama kwana biyu da yake ta yi nauyi sosai ba ta jin dad'i ne."
Yanayinta ya nuna alhini da damuwa a zahiri abinda ta nuna kenan. Sai ta gyad'a kanta a hankali ta ce." Babu komai Amina komai ya wuce kuma na ji sau'ki sosai wallahi sai dai rashin 'kwarin jikin da yake d'an damuna yanzu, a cewa da Hauwa ina amsawa Allah Ya raba lafiya."
Na ce." Za ta ji in sha Allahu rabbi."
Tun kafin mu yi sallama take yi mini godiya har sai da jikina ya mutu tsabar tausayin halin da take ciki. Mairo ita ta janye yaran ta tafi dasu tana yayyanka masu mangwaron da tun farkon shigowarmu suke he rigima a kansa....
'?
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *2k ON TALGRAM*
*VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK*
*07084653262*
*V-VIP AREWAPEN*
*Wsp Gruop 1k*
*103*
Duk abinda muke yi bai ce mana komai ba, mun dai gaisa amma tun bayan gaisuwar bai sake magana ba, sa'i da lokaci dai yakan amsa waya idan an kira shi.
Misalin takwas da wani abu muka fito daga gidan tun a hanya muke alhinin yanayin da muka risketa Baba Tabawa dai kasa daurewa ta yi a hanyarmu ta shiga gida ta fashe da kuka da sauri tasa gefan jihabinta ta rufe fuskarta . To ni ma dai kukan zucci nake yi domin na shiga rud'ani ba karami ba ganin yadda Allah Ya mayar da baiwarsa. Idan kudi na sayan lafiya nasan da ba wannan maganar ake yi ba. Wannan da duniya ta yi mata sheda cewa mutuniyar kirki ce wadda tun a duniya mijinta ya ce ya yafe mata itace cikin irin wannan yanayi to ina ga wanda ya shure umarnin Ubangiji kuma, Ubangiji Allah kasa mu dace Amin.
A haka muka shiga gidan Hauwa na kwance saman kujera 3str tana kallo abinta. Ganinmu sukuku ya sanya ta tashi zaune tana tambayar lafiya.
A takaice na ce." Lafiya lau." Na shige d'aki domin yadda kafafuna ke rawa ba zan iya tsayuwa a wurin ba. Na zauna gefan gado tare da rafka tagumi wani abu ne ya zo ya tsaya mini a wuya na tsananin fargaba da tashin hankali mace ta koma sai kace mai cutar kanjamau! ko mai farfadiya sai an rirriketa. Hawaye suka fara sauka a kumatuna. Haka kawai na ji duniyar ta fice mini daga raina gabad'aya.
Shigowarta ya sanya na daga kaina na dube ta. Ta zauna gefana babu babu fallasa ta ce." Ashe kema kukan ki ke yi Amina." Sai ta sa dariya kafin ta cigaba da cewa." ga Baba Tabawa can ma tana yin nata, ni kam matar nan ko dame take yawo wallahil-azim kurwata tafi tata d'aci, wallahi ni zan yi maganinta."
Na gyada kaina ina ko'karin ture kutittiran abinda ya tsaya mini a wuya na ce." Hauwa k'ullaci da tsananta gaba da k'iyayya wallahi babu inda zai kai ki sai tashar dana sani. Matar nan dai duk rashin Imanin mutum ya ga halin da take ciki sai ya tausayata mata don Allah mu dinga sassautawa kanmu Hauwa."
Ta ja tsaki tare da furta."lalura fa kowa yin ta yake yi, wallahi na fita jin jiki, ni mai yasa ban lanjare ba, saboda ba ni da hakkin kowa a kaina, ita kuwa bari na gaya miki abinda ta shuka ne take girba tun a duniya hakkin mutane ne wallahi."

Na jima ina kallonta tare da auna maganganunta. Yadda take tabbatar da abinda ba ta da tabbas akai shine abinda ya fi daga mini hankali da lamarinta. Wace irin kiyayyace wannan. A ganina wannan abin da take yi jahilci ne tsantsa da rashin sanin abinda ya dace. To ba ni da bakin magana domin kuwa yadda ta yi nisa irin haka babu wani kalami da zan yi mata ya sanya ta sassauto daga irin kiyayyar da take yi wa matar nan wadda alherenta suke dabaibaye damu bakidaya.
Ganin ban ce mata komai ba ya sanya ta tashi tana fad'in." Matsantawa kai ne kawai kowa ya kashe wutar gabansa. Shi kuma ai hakkin rai tun a duniya Ubangiji yake fitar da shi wallahi tallahi yanzu ta fara gani.

Sai kawai na saki bakina ina kallonta har ta fice daga d'akin ban d'auke idona ba.
Na jima a zaune Ina tufkewa da warwarewa kafin na tashi jiki a sabule na shiga bandaki domin watsa ruwa a jikina. Gabad'aya cikina ya cushe babu dandano a bakina ko kad'an yunwar ma sam ba na jin ta, daga zarar na tuna halin da muka riski matar nan a ciki sai hankalina ya tashi.
A haka na shirya cikin kayan bacci ina tsaye gaban madubi ina busar da gashin kaina. Ya turo kofar d'akin ya shigo. Ban yi zaton shigowarsa ba. Muka had'a Ido ya nufo wurin da nake tsaye daf da ni ya tsaya na gama abinda nake yi yana ta kallona ta madubi na juyo kirjinmu ya hadu waje daya. Kusan a tare muka sauke ajiyar zuciya. Ya riko hannuna muka zauna gefan gado. Yanayin fuskarsa kadai shi ya nuna mini cewar ya ji dadin abinda na yi. Ya furta." Kin kyauta sosai kuma na ji dadin abinda ki ka yi, idan haka kuke yi mini kara akan abinda nake so mai zai sanya ni ma na 'bata muku ai babu abinda ya fi zaman lafiya dadi ko."
Kanzil ban ce masa ba. amma maganarsa ta d'an dake ni wato shi baya jin nauyin gaya mana irin son da yake yi wa matar nan tasa.
Ya d'ora hannunsa a tudun kirjina wanda tun zaman da muke yi a wurin hankalinsa yake kai. Ya nisa kafin a kasalance ya furta." Momi ba ta da lafiya Amina cikinta da wajenta wallahi, tausayinta nake ji sosai domin lalurai sun gama dabaibayeta."
A nutse na furta." Allah Ya yaye mata, da sauran al'ummar musulmi."
Ya amsa da Amin kafin ya dora da cewar." Kin san yanzu wani result din ya sake fitowa bayan gwajin da aka yi mata satin da ya wuce cancer bakin mahaifa."
Da saurin gaske na dube shi. Ya gyada kansa "Wallahi ni kaina na kad'u Amina na tausaya mata k'warai da aniya yanzu haka za mu yi booking domin zuwa india akwai kwararrun likitoci a can da za su caje mini ita sosai."
Jiki a masifar sanyaye na furta." Tabbas Ubangiji shi yake saukar da ciwo ya kuma saukar da maganinsa, ina yi mata fatan alheri tare da addu'ar samun lafiya madawamiya, kai kuma Allah Ya baka ladan jinya."
Ya sake amsa da "Amin Ya Allah." D'akin ya d'auki shiru har yanzu hannunsa na saman kirjina yana dan tattabawa. Ban hana shi ba kawai dai ina mamakinsa ne a ganina yanayin alhinin da yake ciki da damuwa akan rashin lafiyar maid'akinsa bai kamata a ce wani abu na jin dad'in duniya yana bijiro masa ba, to mai ma zai fahimta bayan yana cikin tashin hankali a haukana fa kenan
Na dube shi yana lumshe idonsa kamar wanda ya samu audiga na dan ture hannun nasa muka kalli juna a sa'rke na ce." Dama ina son magana da kai."
Kai tsaye ya furta." Idan har akan zuwa maiduguri ne to kada ki bata bakinki babu inda zakije....

Na kudi ne littafin don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba.

Na ce." To saboda me, kafi kowa sanin matsayin anti Yagana a wurina ko?"
Ya gyad'a kansa a tsanake ya ce." Da dai ban rantse ba ne sai na bari ki je, amma wallahi na riga na rantse ki ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?yi hakuri bayan bikin sai ki je ki ga d'akin amarya."
Zuciyata ta dinga tiriri na dinga danne abinda yake yun'kuro mini domin ba ni son na nuna masa damuwata a kan haka a gaba ya samu abinda zai k'untata mini idan wata matsalar ta faru a tsakaninmu. Na gyada kaina tare da furta." Shikkenan mu ajiye wannan maganar ina so ka gaya mini matsayin zamanka da Hauwa a gidan nan, domin ni har yanzu na kasa gane abinda kuke nufi da kai da ita."
Ya dube ni sosai kafin ya ce." Ke ina ruwanki kuma?"
Na ce." Ni ce kuwa nake da ruwa tunda duk wata mas'ala da kuka samu da kai da ita a kaina ne, yanzu a matsayinka na babba mai hankali da jagoranci abinda kuke aikatawa daidai ne."
Ya ce." Ai taki ta amince da cewar ta yi lefi, sannan taki ta bi umarinina idan tana so magana ta shige mai yasa bata biyo ki zuwa duba Momi ba. Ta cigaba da zama a haka duk ranar da ta gaji sai ta nemawa kanta mafita."
"Gaskiya hakan ba daidai ba."
Ya 'bata rai yana fad'in." To nuna mini daidai Amina."
Shiru na yi ban sake magana ba. Ya ja tsaki yana fad'in." Na yabe ki sallah za ki kasa alwala, Hauwa ai ba yarinya ba ce idan tana son zama da ni ta ba ni ha'kuri ta kuma bi umarina."
Na ce." To ai kaine babba ha'kurinka shine zai fi rinjaye."
"Na yi iya wanda naga zan iya yi a kanta Amina, wannan ya zama na farko ya kuma zama na karshe, kada ki sake titsiyeni akan lamarin Hauwa ko ni din sa'anki ne?"
Shiru kawai na yi Ina kallonsa. Ya cigaba da ce wa." Dangane da maganar kwanan aure kin ga Momi bata da lafiya ya kike ganin za a yi?"
Na ce." Yadda muke yi mana."
Sai ya yi shiru yana tunani kafin daga bisani ya furta." Shikkenan sai a cigaba da tafiya a hakan, zan kwana biyu ban koma legos ba, domin idan na kai ta asibitin na dawo zan dan jinyaceta."
Uffan ban ce masa ba, ya tashi tsaye yana kallona cikin sigar kulawa ya furta." Ki same ni a sama zan shiga in yi wanka." Ban iya ce masa komai ba har ya fita daga d'akin Ina zaune zuciyata ta kasa tsayuwa wuri d'aya.
A daran na gurzu a hannunsa k'warai da gaske kamar wata sabuwar amarya sai da na yi ruwan d'umi domin kusan sau uku ya yi mu'amula da ni. Farkon dare da asuba bayan ya dawo daga sallah. Still Yana gama breakfast nan ma ya sake yin wani haka na sauko daga saman a galabaice. Na yini ciye ciyen kayan da zasu saukar mini da ni'ima domin na tabbatar da cewar a wannan daran ma ba zai daga mini kafa ba..

***
Bayan kwana biyu da misalin biyar na yammar ranar talata muka yi ba'kuwa a gidan. Hajiya Aziza sunanta matar abokinsu ce Alhaji Sulaiman duk dai abotar tafi karfi tsakaninsa da Alhaji Amadu mai rasuwa dalili shi da girmansu suka hadu ba abotar kuruciya ba ce. Sai bayan rasuwarsa tukkuna abotar ta maye gurbi akan shi da yake ba ni labari. Uwargidansa ce kuma tare suke da maigidan sun zo duba jikin Momi ne tunda ko bayan rasuwar Alhaji Amadun suna yin zumunci dalilin da ya sanya ma kenan Alhaji Sulaiman din yake binbinin abotartasu ta yi karko kamar yadda ta yi da Alhaji Amadun. Shigowarta kenan ya kira wayata ya yi mini wannan bayanin wai ta ce za ta shigo ta gaishe mu kafin su tafi yanzu shi suna tare da maigidan nata a can gidan Momin.
Na ce masa in sha Allahu babu matsala. Sosai na marabceta na sanya Baba Tabawa ta kawo mata abinci tana fad'in a 'koshe take ta ci abinci kafin ta fito nace ta daure ta sanya mini albarka.
Hauwa ta fito suka gaisa sama-sama cikin rashin sakewa ta koma dakinta. Na kira Baba Tabawa domin ta zo ta kwashe kayan abincin da ta jera wanda kad'an ta ci daga ciki. Duk da babu sabo a tsakaninmu amma na lura tana da kirki kuma ta girme mu gaskiya zata iya yin sa'a da Momin ina tambayarta yara ta ce suna nan lafiya biyu suna d'akin mazajensu kenan ta auran da yara biyu akwai hud'u a gida uku maza sai 'yar autarsu mace. Su uku ne a wurin maigidan ita ce Uwargida.
Ta ce." Ai na ga yaran a can gidan Hajiya Maryam twins sun yi wayo sosai sun zama 'yan mata, Ubangiji Allah Ya yi musu albarka."
Na amsa da amin Ya Allah, ai

Chapters

Related Ebooks
03, August 2026
Aisha kabir iliyasu

Please book for gudun aure

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login