Showing 99001 words to 102000 words out of 244256 words

Chapter 34 - GANIN IDO COMPLETE BOOK BY MAHMUGEE

MAHMUGEE   

08 Aug 2026

431

din kai tsaye fammah daki ta koma gurin SANAAH ta kwanta itama Mum kuwa mijinta tabi zuwa palonsa sika koma.

Bayan kusan awa daya sai ga Imran na knocking kofar palon farko maana main sitting room din tareda budewa ya shigo da wata sabuwar qwararriyar likita itama halfcast ce ya nuna mata guri ta zauna ya daga wayarsa bai kira Fleet ba sbd sanin abinda yakeyi kai tsaye Fammah ya kira.

Tana dauka ya mata ya jiki ta amsa a dan natse kafin yace

"Ga Dr zata duba ku tana sittin room zaune"

Dan shiru tayi tareda kasa fahimtar kalmar "ku" daya ambata sai ta juya a natse ta kalli SANAAH takai hannunta ta tabata taji jikinta yayi wani irin zafi sosai ta kalleta da dan sauri tana mamakin da gaske dai batada lafiyar itama.

Batada kowace irin doguwan nazari da hada lissafin tinanin komai na rayuwa wanda hali ne da Mum dinta data gado dakyau dan haka batai tinanin komai ba na yanda Imran ya saniba ta kalli wayarta tana gyara zamanta a kunnenta tace

"Gamunan fitowa SANAAH dince ba lafiyan yanzu sosai"

Kashe wayarta tayi tareda son tada SANAAH din amma kuma sai ta fasa ta sauk gadon ta fita zuwa sitting room din.

Tana isa gaisawa da Dr din sukai cikin yar kokarin riqe kuzarinta dayake dawowa tace su tafi can daki ta duba SANAAH din.

A bakin gado ta zauna tareda dan miqa hannu ta yaye rufar SANAAH din tana sake taba jikinta zafin sosai yana nan dan har wani hucin zafi ne ya fito daga rufarta data yaye.

Sake shafata tayi tana ambatar sunanta da sanyi.

Ahankali ta bude idanuwanta bayan ta farka daga baccin datakeyi din.

Bata motsaba idanuwanta kawai ta sauke akan fammah din tana jin karfin zazzabinta na qaruwa.

Sanar da ita Dr zata dubata fammah tayi da kulawa tana taimaka mata ta tashi zaune.

Kallan dr din tayi tareda bude baki cikin dauriya ta gaidata tana kallanta.

Dr tasowa tayi ta iso gurin SANAAH din fammah ta bata guri ta zauna gefen gadon tana fara dubata da tsananin kulawa da yan tambayoyi.

Yanda SANAAH din takeda sanyi da rashin sauri ko hayaniya a komai bare yanxu datake cikin tsananin zazzabin ya saka suka dauki time kafin suka gama tukuna ta duba Fammah itama wadda ta sake jinta ta warware sosai batajin komai.

Bayan lokacinda Dr ta bata mai tsayi ta wuce SANAAH ta samu ta sauko gadon ta isa bathroom ta shige tayi brush da sauran abubuwanta kafin tayi wanka da ruwan zafi sbd taji ko zata samu karfinta da abinda takeji na zazzabin ya sauka.

Tana fitowa sama sama ta iya dan shafa body mist na oud mai sanyi da tsada ta saka silk riga da wando marasa nauyi ko kadan ko bra bata iya sakawa ba tasha tea kadan akan tirsasawan Fammah tukuna tasha magani ta koma ta kwanta sbd kanta tsananin ciwon gaske yakeyi.

Tana kwantawa bacci ya dan sake daukanta fammah ta kashe mata wayarta sbd kada a bata kowace irin hayaniyar da zata hana ciwon kanta sauka.

Mum kuwa jinsu shiru ta fito tana waya ta nufa dakin ko data shiga taga halinda SANAAH take ciki dan haka ta nuna damuwanta da kulawanta itama dubata tace su bawa SANAAH din isashen hutunda har sai ciwon kanta ya sauka kada a bata kowace hayaniya.

Fitowa sukai suka barta bayan ta sake samun bacci,
Fammah bangaren Mommy ma takeson tafiya dan tabar SANAAH ta samu hutun itama taje can ta kwanta tayi hutunta acan.

Mum ma gurin Rabin ranta ta wuce acan take sanar masa SANAAH din ba lafiya sosai kaman Dad ne ya aiko Likita ta dubata sedai sai ahankali jikin nata kila zuwa yamma ta warware.

Baice mata komaiba wayarsa dake hannunsa yake ci gaba da dubawa batareda bawa zancenta hankalinsa ba kokuma alaman yamasan abinda take fada.

Safiya ce ta shirya musu dining da rana sukai lunch guraren karfe uku da mintina kafin suna gamawa Mum ta sake zuwa ta duba SANAAH dake bacci har lokacin bayan tayi sallan azahar daqyar ta koma ta sake kwanciya da rufe jikinta duka.

Ganin bacci take ya saka Mum itama barin bangaren bayan Safiya ta sake tattara komai fes ta bar bangaren itama.

Gurin Mommy ta tafi suka baje suna firarsu bayan ta sanar da mommyn SANAAH insha Allah taji sauki tana tashi lafiya kalau zata tashi.

Mommy ma sbd kara bata damuba firar su sukeyi hankali kwance da shagala gashi daman duk taxo bangaren sai dare ko magrib take komawa.

Sunacan sunata firarsu fammah ma bacci me nauyi ne ya dauketa bayan azahar dan baka babu wanda ya sake zuwa dubota.

Bayan sallan laasar wata kishirwa da yunwa mai tsananin gaske ta tada ita daga baccin bayan dan zazzabin ya dan saukar mata dan haka ta farka tayi shiru tana jiran zuwan wani dan tana tsananin buqatan ruwa tasha amma me dumi takeso sbd yanda takejin kaman zatai amai.

Shiru babu wanda ya shigo dakin dan haka ta tashi zaune ahankali da tsananin rashin karfi da da jiri sosai sbd rashin komai a cikinta.

Idanuwanta da sukai wani irin laushi da bayyanarda wata irin kasala da lumshewa akai akai ta juya ahankali ta kalli dakin dayake da rashin haske sosai da aka rage mata taga ba alaman fammah bata ciki dan haka ta hadiye wani numfashi mai tsananin kasala tareda yunkurawa ta yaye duvet din jikinta ta ziro kafafunta qasa tareda dan rufe ido ta bude ahankali tanajin kaman bazata iyaba amma yanda takeji kaman zata mutu ne idan bata sha ruwaba.

Miqewa tayi tana dan dafa bango ta zira soft slippers a kafafunta tukuna tafara takawa ahankali tana rufe idanuwanta da dan dauriya tana budewa jiri takeji sosai da amai na neman yunkuro mata amma haka ta isa kofar bedroom din ta fice.

Palo ta nufa tana tafiya ahankali tana dan dafe cikinta kadan da hannu daya tana barin dayan dan bawa kanta kariyar daga duk inda zata fadi sbd jirin dayake dibanta.

Kai tsaye hanyar kitchen ta nufa bayan bayan ta isa palon,

Tana isa kitchen bata rufe kofar ba ta dakata ahankali tareda dafa kitchen island tana rufe idanuwanta tana fidda numfashi ahankali da ajiyan zuciyan abinda takeji.

Dakatawa tayi tsawon mintina saida ta dan samu sassauci tukuna ta iya daga idanuwanta da suka sake laushi sosai ta janyo electric kettle takai bakin fanfo ta kunna ruwa ya shiga ta kashe ruwan ta jona kettle din tana yin baya tareda da dakatawa ta dan huta kadan daga muguwan mutuwan jiki da kasala da rashin karfi ko kadan.

Numfashi ta dan sake saukewa tukuna ta daga kafafunta har lokacin tana jin jiri ta isa inda fridge yake takai hannu ta bude daqyar tukuna ta saka hannunta daya ta dauko yoghurt dayake ciki ta zuba a cup hannunta na dan neman gazawa ta mayar tareda kai glass din bakinta tasha da wani irin sanyi dayayi sosai.

Bata gama shanyewa ba wani irin amai ya yunkuro mata gabaki daya dan haka cup din ya subuce daga hannunta tayi sink din kitchen da sauri tafara fesa wani irin amai mai sautin yunkurin gaske sbd babu komai a cikinta sai yoghurt din daya shiga cikinta yanzu din.

Wani azababben yunkuri da kakarin amai takeyi mai sauti sosai da tana neman jin kaman zata mutu idanuwanta sun gama bayyanarda azaba take cikinta.

Tsit babu kowa a bangaren dazai jita bare bata taimakon datake tsananin buqata dan ta fita hayyacinta take.

Dawowansa kenan tin bayan daya fita sallan laasar sbd ya dan tsaya ya gaisa da mutane da har ya dan jima kafin ya dawo din.

Yana shigowa palon kafin ya doshi hanyar wucewa nasa palon sautin yunkurin aman ne mai karfin gaske ya fara shiga kunnensa daya sanyasa dakatawa cak daga inda ya dosa sbd a tinaninsa da saninsa babu kowa a bangaren dukan su suna can kuma yanda yaga Meenah din na yi sai dare ko yamma sosai dan haka a natse ya juya zuwa kitchen din cikin takun tsanaki.
#MAMUH
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

60
*ZUZEAM VENTURES*
08144015291
https://wa.link/l1gcz8
ASSALAMU ALAIKUM
Mata masu abun duniya🔥🔥🔥
*Zuzeam ventures* takawo muku babbar gara basa Duka akan 7k ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki Garabasa gara basa, Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 7k na
1. Sashen kaza
2. Ciccibi
3. Gumba madara da chocolate
4. Gari 7in1
5. Tsimi mallaka 5. Tsimin matar minister
6. Women coffee 3in1 sunada kyauta abubuwa kamar haka:Matsin ba a Fira da wando 1k,Matsin maganin infection 1k,Dripping pills 1k,Turaren mallaka 2k
Total total gift 5k
Kiyi kokari ki kasance aciki Garabasa kan garabasa Da 7k dinki ki mallaki kayan da ko 16k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah 08144015291 Maman yasmeen takuce For more information say hi
Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam ventures tashirya tsaff dominku muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu
*DAHUWAR KAZA*
Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt Akwai kyauta mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya
MASU JEGO DA AMARE
Karku bari wannan dama ta wuceku
Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 2000 kacal.
Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd
Infection set
Sabon budurci set
Niima set
Basir set
Matsi mallaka
Amarya set
Uwar gıda set
Mai jego set.

*******
Wani yunkurin ne mai karfin gaske ya sake zuwan mata ta saka kanta tana yi take dan karfinta ya qare jirin datake cikinsa yayi tsananin gaske ta rufe idanuwanta tana yin baya daidai nan ya iso ba tsammani ya tare bayan nata da kirjinsa ahankali tareda saka hannunsa daya ya tarota gabaki daya yana hana jiri yadda ta take wani yunkurin ya taho mata dan haka da kansa ya rankwafar da da ita tana aman wanda baya wani fita,

Yawa azabar tayi mata batasan ma lokacinda hannunta dayake dafe da kirjinta gurin amanba ya sake zai sauka a inda kettle din ruwan ke tafasa ba cikin nutsuwa hannunsa ya riga nata isa ya tare hannun da tafin hannunsa wanda nata tafin hannun ya saukar masa daidai da sake zuwan wani wahalallen yunkurin da batasan lokacinda ta manne tafin hannun nasuba tana qanqamesa zafin dumin dayake jikinta ya ratsa tafin hannunsa daya mannu da nata ya saka hannunsa daya a hankali yana shafa bayanta tana samu aman yana fara fitowa kansa shima a rankwafe sbd irin yanda bayansa shine ya zama kariyar daya baya ta hanata faduwa tinda hannunsu daya yana manne da juna dayan kuma yana shafa bayan dan haka fuskansa take kusa da tata sosai.

Muryansa ce ta fito daga bakinsa ta ratsi kunnenta na dama da bakinsa yake kusan saiti dasu daidai ya furta

"Sannu,Sannu ko" a wata irin tsanakin data bude idanuwanta cikin wani irin slow ahankali sbd aman ya fada mata a take tareda tashin tsigar jikinta ahankali....

Hannunsa da kansa yakai ya zuba mata ruwa nata dayan hannun ta wanke bakinta ya birkito da ita ba tsammani a hankali dan haka ta kasa dago idanuwanta da sukai tsananin laushi ta zame hannunta dayake hade da nasa tana kasa motsawa kuma jiri takeji har lokacin.

Kallo daya yayi mata ya lura da hakan dan haka ya dan juya ya kalli kitchen din dabai san ina zaiga cup ba sai ya dawo da kallansa akan fuskanta ya bude baki yace

"Ina cups??

Dagowa tayi da wata slow na rashin kuzari bata kallesaba ta dan daga kafafunta batareda kallan gabanta ba zata nufi inda cups din suka.

Bata sauke kafarta data dagaba hannunsa daya ya zagayota hannunsa na sauka akan shafaffen cikinta da babu komai na abinci a cikinsa tareda dauketa sama yana dawowa baya da ita sbd glasses din da sauran kiris ta dora kafa akansu na cup din data saki kafin fara amanta.

Jin tayi jirinta na qaruwa sbd wata irin faduwan gaba data shigeta da kuma jin hannunsa zagaye da ita dan haka ta rufe idanuwanta tana jin ya saukar da ita ahankali gefe jikin fridge tareda miqa hannu ya zaro robar ruwa bara sanyi ya bude ya miqa mata a natse da sai a lokacin ya sauke mata idanuwansa gabaki daya yana kallan fuskarta dake kamanninta ke azabtar da wani bangaren na kirjinsa.

Ahankali ta iya dago hannunta dayake cike da kasala sbd tana tsananin buqatan ruwan ta dora akan roban zata amsa hannunsu ya gadu cikin sanyin daya sakasa maida nasa idanuwan akan hannuwan nasu a tsanake kafin ya sake dagowa cikin wata slow ya sake sauke mata idanuwansa yana kallan yanda takesan ruwan suna bin maqoshinta ahankali suna wucewa ba sauti ko daya.

Idanuwansa suka saka ruwan isarta da kuma qara kasalarta dan haka ta zare ruwan ahankali daga bakinta tareda dagowa cikin wata kasalan da bata taba shigaba ta idanuwanta suka sauka akan fuskansa da idanuwansa masu wani irin sakar da kasala da kwarjini tareda haiba mai nauyi suke akanta.

Yanda idanuwanta suka dago tattare da kasalan datake cikinsu ta saukesu akansa ya sakasa kallan cikinsu ahankali take kafafunta jiri ya koma cikinsu suka sake zasu zube qasa ya sake mata wani riqo dakyau cikin sanyi sbd daman tana jikinsa har lokacin tinda ya dauketa bai zare hannuwansa daga zagayewan da yayi mata ba.

Jin tayi numfashinta yana neman yankewa sbd yanayin dasuke ciki da kuma kasa iya daukan kallansa da idanuwanta da gangar jikinta sukeyi ta motsa ahankali tana son zarewa daga jikinsa a lokacin ne ya dauke idanuwansa masu kaifi daga gareta yana kai hannunsa wuyanta ahankali ya dora bisa fatarta datake bayyane take taji tsigar jikinta ta sake tashi sbd batai tsammani ba dan haka ta qarasa zamewa daga jikin nasa gabaki daya tana qin sake kallansa ta juya baya tareda bude baki da sauti mara karfi tace

"Thank you Da.."

Kasa qarasawa tayi tana dakatawa cak shima idanuwansa ya kalleta dasu wanda taji saukansu a kanta dan haka babu wanda ya ce komai a cikinsu suka fice kusan a tare daga kitchen din.

Shine ya fara bacewa daga palon kafin itama tai kokarin xuwa daki ta nema wayarta ta kunna ta saka kiran Safiya cikin rashin kuzari.

Safiya ba bata lokaci taxo ta hada mata tea ta gyara kitchen din ta kawo mata da banana bread tasha daidai cikinta ta sake shan magani sai a lokacin ta dan samu kuzari.

Duk wani motsinta kamshinsa ne yake tashi a jikinta dan haka ta lallaba ta shiga bathroom.

Wanka tayi ta sake samun karfin jikinta sosai tana fitowa ta tadda Fammah ta dawo tana dakin itama wankan tayi jikinta ya sake samun karfi a tare sukai sallan laasar.

Suna idarwa Safiya ta kawo musu simple abinci ta jere musu a dakin.

Fammah dake jin yunwa sosai gurin abincin tazo ta zauna tana kallan SANAAH datai shiru ta zuba mata ido tana kallanta a tsanake da mutuwan jiki.

Hannu ta daga mata alaman "akwai wata damuwan ne??

Numfashi SANAAH din ta sauke tana kasa dauke idanuwanta daga kanta idanuwanta masu kyau na sake saka fammah jin kaman zata dawo mata da zazzabinta ta bude baki zatai magana SANAAH ta girgiza mata kai ahankali tana dan bude bakinta tace

"Kici zanzo nima naci"

"Kin tabbata?" Fammah tace mata da sautin kulawa.

Gyada kai tayi tana dan lumshe idanuwanta tana barinsu a rufe tsawon mintina kafin ta budesu ahankali tareda tasowa ta taho ta zauna gefen fammah din tana daukan spoon ta saka a plate din famman tafara cin abincin.

Kadan taci ta koshi sbd tariga tasha tea ta miqe ta koma kan sofa ta dan zaune tareda miqar da qafafunta akai.

Safiya ce ta shigo tana tattara gurin tana kokarin jansu da zance kaman yanda suka saba har suka dan daure suna bata amsa musamman fammah data warware.

Safiya bata fito dakinba sai da akai magrib ta fice tana dariya suma suna dan yi sbd sai data sakasu firar dole sbd akwaita da kulawa da son fira.

Safiya na ficewa Mum na dawowa bangaren dan haka sallah ta fara yi kafin ta fito taxo dakinsu ta dubasu dukansu tana kallan SANAAH wadda ta kasa dagowa ta kalleta dakyau ita kuma sai sake lallabata takeyi da kulawa da sake tambayar ko zaa kira likita ya dubata.

Girgiza kai tayi a tsanake tareda bude baki tana dagowa ta dan kalli Mum din tace

"No naji sauki Mum,kawai dai rashin karfin jiki ne shima zuwa safe insha Allah zan koma normal.

Dining safiya ta dawo ta shirya da abincin daren dazaa ci a bangaren na lafiyayyan abincin da Mommy ta dafa musu sbd Raheem kaman kullum.

Kafin lokacin ishai suka hau table dinner wanda daqyar SANAAH ta iya fitowa sbd takurawan Mum dan haka doguwan riga mai fadi da gabanta a bude ta doro akan riga da wandon dake jikinta da suka dan lafe mata sai silk scarf data dauro akai dan rife gashinta.

Itace tayi karshen shigowa bayan har sun fara kokarin fara cin abincin sbd Fleet daya qaraso ya zauna qamshinsa na gauraye gurin gabaki daya.

Tana sako kai kokarin hana kanta kowace damuwa tayi ta qaraso a natse tareda zaunawa kujeran gefen Fammah a natse

Tana kokarin dagowa Mum ta katseta da cewa

"Baby SANAAH ki daure kici abinci sosai"

Kallan Fleet tayi wanda ya miqa hannu a natse ya dauki glass din ruwa da lemon a ciki da sanyi kadan yakai bakinsa tace

"Fleet Baby SANAAH ba lafiya fa tin asuba ma, a kwance ta wuni yau"

Dagowa yayi da idanuwansa da hatta ita kanta Ms Meenah din saida zuciyarta tayi wani skipping beat ya saukesu akan SANAAH din wadda itama takai hannu a natse ta dauki glass na ruwa takai bakinta tasha kadan sbd jin spoon din farko na white couscous din data saka bakinta ya tsaya cak a maqoshinta.

Taji saukan idanuwansa akanta dan haka taqi dagowan sai saukan muryansa taji ta ratsi kunnuwanta da cewa

"Allah ya bata lafiya,zuwa gobe Dr zataxo ta dubasu su duka"

Yana fadan hakan Mum ta washe baki tana maida kallanta akan SANAAH da fammah tana cewa

"Allah ya bawa yan matana lafiya"

"Amin" SANAAH ta bude baki ta furta a hankali ita kuma fammah dad din ta kalla tace

"Thank you Dad"

Kallanta yayi da miqa hannunsa daya ya shafi gefen fuskanta yace

"Just get well soonest Mamanah"

Murmushi tayi daya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login