Showing 18001 words to 21000 words out of 244256 words

Chapter 7 - GANIN IDO COMPLETE BOOK BY MAHMUGEE

MAHMUGEE   

08 Aug 2026

477

ba har iyayensa kuwa.

Da zatai tafiyar akace tabar Hakeem tinda ya isa yayewa kuma daman ba wani sosai yake shan nonon nata ba sbd yanayinta da kuma jinyar da zatai ga rasuwan Amminta.

Wani nauyi ne mai tsananin gaske ya sake danne kirjinta kaman zuciyarta zata kama da wuta haka take ji dan haka bazata iya hayaniya ba tinda ba lafiya a tattare da ita kwata kwata.

Fasa tafiya da fatima tayi tace ta zauna da Raheem a matsayin yar rainansa tukuna.

Fatima ta shiga tashin hankali sbd tsoron abinda take gani a zuciya da idanuwan fammah akan duka abinda yake faruwa amma batada zabi haka ta zauna aka tafi da fammah tabar mata 'danta RAHEEM wanda zatai zaman renansa a jeerah a matsayin Nanny.

A daren da zasu tafi sai a wannan daren ne fammah ta fasa wani irin kukan daya saka fatima sauke kai itama tana tayata kukan datake jin yana ratsa dakin da tsananin tsima.

Washe gari da asuba jirginsu ya daga da fammah da Hakeem dama su Daddy da ummah da zasuje gaisuwa dukansu.
#MAMUH
#FLEET RAHEEM JEERAH
#MUHAMMAD NASIR IBRAHIM
#S.A.N.A.H

GANIN IDO 2026
Mamuhgee
1k
Vip 5k
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

12
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
Bayan tafiyar Fammah daga Nigeria fatima jin tayi tana rasa nutsuwarta da kanta dan kuwa kadaici ne ya sakota gaba da kewa da damuwa,

Babu wanda aka bari a tareda ita a bangaren daga ita saisu Raheem da nasir sai kuma saratu,

Babu me zuwa bangaren kwata kwata sedai duk safiya idan tayiwa su Raheem din wanka suka sha nono ta hada musu da cereal da sukesha zata kai Raheem can gurin su Ummah sbd abinda akace mata kenan.
Acan zai dan wuni saiya gaji yayi bacci a dawo dashi sai kuma washe gari ta sake kaisa.
tin tafiyar batai nisa ba rayuwar ta sauya mata kwata kwata musamman da duka su biyun qyuya ne dasu basa wani yadda da mutane ko Raheem dinma daga baya yadda da kowa a cikin familyn bayan Mamma dinsu fatima da ita suka sani.

***Isar su Dr fammah qasar Morocco har lokacin babu wanda tacewa komai dan kuwa kwata kwata idanuwanta a rufe suke ma ruf babu alaman idonta biyu dan hakane kowa ya qyaleta ta samu dan rintsawar sbd tana buqata ko dan yanayinta dakuma damuwar rashin mahaifiya.

Hakeem dake zaune a kusa da ita ya san idanuwanta biyu dan kuwa yanada tabbacin babu baccin da zai dauketa a rayuwar dasuke kai yanzu,

Duk yanda yaso mata magana ganin suna tareda iyayensu yayi shiru shima dan kuwa ko jirgin dasuke cikinsa zai juye dasu yayi fata fata bazata taba tankasa a yanda yasan zuciyarta.

Kallanta yakeyi a kai akai harya hakura ya dena kallanta ya kama nasa girman sbd kada ya zamana kaman yana shakkarta ne.

Ita dai a nata bangaren batajin akwai wani a cikinsu dama danginsu dake gida da suka rage da kowace qima ko daya a idanuwanta jinsu takeyi tamkar wainda zama guri daya dasu yana danne numfashinta.

Motocin da familyn Jeerahs din suka tanada ne suka taho airport suka daukesu guda uku na alfarma kai tsaye gidan iyayenta suka nufa.

Suna isa koda fammah ta hada ido da mahaifinta wata irin rawa jikinta yafara ahankali kafafunta na kasa daukanta sbd sama da shekaru uku kenan bata sakasu a idanuwanta ba tin wani zuwan datai ganin gida ta koma,

Kasa iya daga kafafunta tayi ta sauke kanta ahankali wasu irin hawaye masu tsananin zafi suna gangaro mata abbun da kansa ya taso ya iso gareta daidai Hakeem ya miqa hannu zai kamata sbd har lokacin daman bata iya tafiya ita kadai da kanta sai an taimaka mata.

Abbunta ne shima ya miqo mata hannunsa ta kama a sanyaye batareda ma tako kalli inda Hakeem yake bare ta nuna tasan da mutum,

Kuka ne mai karfin gaske ya taho mata take mahaifinta ya rungumeta yana lumshe ido tareda sauke ajiyan zuciya.

Ciki sukai gabaki dayansu zuwa palon Abbun da babu mutane sbd basa zaman gaisuwa tinda akai janaizar ta aka kaita kowa yayi gaisuwansa ya watse dan haka koda aka kwana zuwa yau babu kowa duk anyi gaisuwan an watse sai iya qanwar Ammin data taho daga Cairo da babban 'danta.

Zama akai tsakanin Abbu da familyn jeerahs sukai gaisuwa tareda jajantawa da nuna kulawa kafin suka tafi masauki bayan sun dan jima sosai a gidan.

Tinda suka taho ciki akai da fammah dan haka har suka tafi basu sake ganinta ba Hakeem dake tsananin son ganinta da magana da ita haka yaga babu alaman ma zai iya maganarta dan haka suka tafi.

Kukan dukkanin baqin ciki da kunci da kadaicin dake cike zagaye da rayuwarta fammah ta sake tana jin rayuwa ta gama juya mata bangare mara dadi sbd a yanzu batasan tayaya zata fuskanci wannan masifar rayuwar ba babu Amminta,Amminta ta tafi tabarta a rayuwar da babu komai sai son zuciya da son kai tareda zalinci,

Irin kukan datakeyi da yanayinta da suka gani mai muni da tada dukkanin gashin jiki ya saka duk karfin halin mahaifinta da manyancinsa fasa wani irin kuka yana jin tsananin dacin mutuwar rayuwar yarsa daya tak hakama yana jin gwara da Allah bai nunawa Amminta ita ba a wannan mummunan yanayin data koma kamar wadda take dauke da qanjamau dan kuwa hatta haske da lafiyar farar fatarta duk sun tafi koina qashi ne a jikinta kawai yake gani.

Ita kanta qanwar Amminta Anne kuka ta fasa tana rerawa jikinta nawata irin rawar tashin hankalin ganin Fammah a hakan ma wai tana aure a familyn da suke billionaires a can qasar.

Ayau da suka ga yar Ammin a gabansu suke asalin kukan rashinta a cikin mummunan yanayi.

Kukan mahaifinta shine abinda ya qarawa yanayin muni da tashin hankali.

Kwana sukai a cikin damuwa me nauyi da qunci babu kowace irin farin ciki a gidan da mutanen gidan ga damuwar Raheem da aka baro data saka mahaifinta jin kaman ma zuciyarsa zata buga dan haka washe saida shima aka kawo masa likita ya dubasa.

Jeerahs washe gari ma sun sake zuwa suka wuni a gidan zaman gaisuwan da babu kowane sakewa a yanayin dan Abbu ba lafiya bai iya fitowa ba haka sukai zamansu suka tafi ko fammah bata fitoba sbd sunsan yanayinta.

Hakeem ne ya shiga har can ciki dakin Amminta ya dubota tana zaune ta dunqule guri daya idanuwata sunyi jajir sun kumbura ba kyan gani.

Duk yanda yayi magana da nuna mata kulawa ko kadan bata iya juyowa ta kallesa ba dan kuwa a duk lokacinda zai wanzu a guri zuciyarta da idanuwanta tareda jinta dauke mata sukeyi dan haka har yayi maganganunsa ya gaji ya miqe ya fice babu abinda taji bare juyawa ta kallesa.

Bayan tafiyarsu ranar saida suka kwana biyu basu sake zuwa ba gidan banda Hakeem da kullum yana gidan amma sam ko Abbun bai samun ganin fammah din kawai yake gani sai masu aikin gidan itama tin yana jin karfin gwiwa harya rasa abin fada mata sbd batama responding bare yasan akan matakin datake na ta fahimci abinda yakeson fada mata.

Sati biyu suka share a qasar suka tattara zasu koma suka tafi gidan sukai musu bankwana dan Abbun ya fito sun tattauna akan zasu tafi da Fammah daga nan zaa wuce da ita india ne asibiti.

Abbu bai musu ba ya amince musu da fatar allah yasa a dace dan bayason hayaniya a yanzu da rayuwarsa data yarsa suke cikin duhun damuwa da kadaici.

Bayan tafiyar su Alh babba masauki Hakeem ya shiga har ciki ya samu fammah ya sanar mata maganar tafiyarsu a jibi.

Dagowa tayi a karan farko ta kallesa da idanuwanta da suke jajir a bushe kaman yanda takejin ko zuciyarta ta bushe babu abinda takeji.

Kallansa datai ya sakasa sauke numfashi da ajiyan zuciya sbd yasan lokacin maganarta yayi.

Bude baki tayi a natse da sanyi tace

'Aure zakayi HAKEEM?

zuba mata ido yayi yana kasa bata amsa sbd bayason sakata a wani mummunan halin.

Bata dauke idanuwanta akansa ba ta maimaita tambayarta da cewa

'Hakeem wata macen zaka kuma aura bayan ni??
Hakeem sbd rayuwata ta lalace ne bazan iya sake haihuwaba zaka sake aure?
Hakeem bazaka iya hakurin na samu lafiyar dana rasa ba?
Hakeem menene saurin da kukeyi?
Hakeem menene amfanin rayuwata a cikin familynka????

Dakatar da ita yayi da cewa

'Karki saka a ranki cewan sbd kin rasa lafiyarki ko haihuwa ya saka zaayi wannan auren Fammah sbd kinsan kece soulmate dina,bazan taba son kowace mace ba a duniya bayan ke,
Kece ni fammah,wannan auren aurene kawai na umarnin da bazan iya kaucewaba....

Fammah bata girgiza ko jin kalamansa ko dayaba a jiki da zuciyarta saima wani dacinsu dataji yana ratsata dan haka kai tsaye ta sake kallansa da jajayen idanuwanta tace

'Ka fada musu bazaka iyaba,
Bazaka iya hada matarka da kowa,
Bazaka iya auren kowace macen ba,
Bakada raayin kara auren kowace mace har karshen rayuwarka,
Bazaka iya cika wannan umarninba ka fada musu sbd idan ka fada babu wanda zai maka dole tinda kai ba yaro bane shekarunka sunkai har sun wuce...

Da mamaki ya kalleta yanda take maganar kai tsaye cikin kaifin harshen daya hango matakin datake tsaye akai kenan.

'Iyayena ne ake magana anan kina tina hakan ko??

Wani numfashi me zafi ta fidda tana sake riqe nutsuwanta sbd kwakwalwanta dake neman bugawa da abinda take ji tace

'Hakeem jeerah ni fammah wallahi tallahi matikar zakai wannan auren nabarka na bar aurenka har abada bana fatar sake ci gaba da zaman aure da kai da familynka......

Da tsananin mamaki ya kalleta yana shiga shock da bugawan zuciya ya kafe idawanta dake bushe da kallo sunyi jajir shima nasa jan sukai ya bude baki yace

'Fammah,kinsan me kike fada kuwa?
Kin rasa hankalinki ne ko me?
Akan wani auren kike cewa kin gama naki auren?
Idan nayi auren zai raba mu ne kokuwa zai rage soyayyar dake tsakaninmu??

Lumshe idanuwanta tayi ahankali kalamansa na ratsata sbd auren dai yi zaiyi bazai fasa ba ko maganar dakatawa ta samu lafiya ba da futa quncin rashin mahaifiyarta data rasa ba.

Miqewa takeson yi a hankali tabar masa gurin amma ta kasa tashi hannuwanta na wata irin rawa ta boyesu a cikin jikinta tana jin zuciyarta kaman zata fashe.

Duk maganganun dayake yi cikin tashin hankali baiga alaman tana jinsa ba sbd idanuwanta da alamar sun bushe batareda yasan zuciyarta wani irin kuna da kuka takeyi ba me tsananin abinda yake shirin yi mata ba na zabar auren wata ba a cikin wannan halin datake ciki datake tsananin buqatarsa fiyeda koyaushe ba na rayuwar aurensu.

Miqewa yayi ya fice daga dakin ko gani sosai bayayi ya nufi gurin Abbu muryansa harta fara shaqewa ya zauna gabansa ido jajir yafara jero masa abinda yake faruwa wanda ya saka Abbun zuba masa ido bako kyaftawa sbd baimasan da maganar aurenba dan fammah bata fada musu ba.
#MAMUH
#JEERAHS
#DR MUM FAMMAH
#BROTHERS
#RAHEEM HAKEEM JEERAH
#MUHAMMAD NASIR IBRAHIM

GANIN IDO 2026
Mamuhgee
1k
Vip 5k
0022419171
AccessBank maryam sani gummiGANIN IDO 2026
Mamuhgee

13
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
Abbu har a cikin zuciyarsa wani irin zazzafan kishin yarsa da bacin rai ne ya rufesaai tsananin daya kasa dauke idanuwansa daga hakeem dayake kallansa yana fada sbd zai qara aure fammah na cewa zata rabu dashi.

Numfashi me sanyi da mutuwar jiki Abbu ya sake yana jin nauyin kirjinsa na qaruwa ciwonsa na son tasowa amma cikin karfin hali ya bude baki yana kallan hakeem din yace

'To kai Hakeem da gaske auren zaka kara a yanxu da iyalinka batada lafiya sosai ko tafiya fa kanaga bata iyayi sai an riqeta,
Batada cikakkiyar lafiyar komai da komai harma da kwakwalwa dan kuwa ayanzu datake cikin ciwon da fiyeda shekaru biyu tana jinya a kwance komai sai anmata ga mahaifiyarta ta rasa ga danta kun rabata dashi kuma zaka iya aure ka tafi gurin wata kai ka huta
Kasan da baqin cikin duka wannan lamarin da wanda zasu kara mata zai zama ajalinta??

Shi auren bazaa iya hakura dashi ba zuwa gaba ba kodan darajar dan dayake tsakaninku???

Shiru Hakeem yayi sbd yasan ba abune mai yiyuwaba tinda ko yanzu tafiyar nan zuwa Morocco da sukai ta saka aka qarawa auren sati uku yanzu sunyi biyu saura kwanaki kenan daurin auren dan kuwa su acan anacan an fara shagalin bikin tini amarya na cikin lalle an saka.

Rasa abin fada yayi sbd shima duk yanda suke tinanin a fasa auren yanayi yana kuma fada amma bazai taba iya bude baki ya cewa iyayensa aa ba sbd ita fammah ma ana auren daga india idan ya baro Nigeria so yayi ya dauketa su tafi America tare amma gashi lamarin na neman rikice masa.

Bude baki yayi ya bawa Abbun hakuri da tabbatar masa auren bazai saka fammah ta kasa samun kulawansa da kaunarsa ba har abada.

Ganin duk yanda ya fito fili ya roki alfarmar a daga auren daga hakeem bazai yiyuba sbd abinda ya nuna masa bazai taba iya bijirewa iyayensa ba akan komai dan haka Abbu daya rasa abin yi magana yayi da fammah wadda ta gama yanke hakeem daga zuciyarta har abada matiqar zaiyi auren nan da ko rasuwar mahaifiyarta bazai saka a daga mata kafa ba idan bazaa duba yanayinta ba da depression ma tini yake kokarin illata kwakwalwanta.

Abbu kai tsaye ya zabi bin bayan yarsa sbd tako ina yasan anci Amanarta an cutatar da ita an kashe rayuwarta an gama illatata tako ina dan haka babu amfanin zama a cikin mutanen dasukeda tsananin qabilancin da kansu kawai suka sani gwara ta dawo hannunsa kawai ya nema mata lafiyarta data rasa.

Tsayuwa akan raayin fammah da abbu yayi ya saka zancen zama babba har saida su Alh babba suka shigo akaita fama har lamarin ya fara zama babbar matsala me girma,

Sudai jeerahs basu taba hada sunansu da mutuncinsu da komaiba har abada dan haka maganar janye auren Hakeem sam bata taso ba suna dai bada hakurin ayi hkr fammah ta dawo ga mijinta tayi hakuri zasu kula da ita sosai zasu nema mata lafiya kuka bazasu bari hakeem ko kishiyarta su shiga haqqinta ba amma dai ba maganar fasa auren da anacan an fara biki.

Wannan maganar tasu ta sake ciresu daga zuciyar fammah sbd ji da tabbatarda ana can ana bikin ma kenan,
Babu sauran mutunci ko raayin cigaba da zama da hakeem da jeerahs a rayuwarta dan haka a gavan su Alh babba ta dago idanuwanta ta yanke dukkanin wata kauna a tsakaninsu ta maimaita ta gama zama da hakeem da familynsa bata buqatan sake rayuwa a cikinsu har abada.

Mamakinta sosai su Daddyn sukai hakama hakeem mamakinta kashesa yayi yanda iyayensa suka basu hakuri suka rokesu akan komawarta amma ita zuciyarta ta gama bushewan da taurin kai dana zuciya hakama Abbunta ya tsaya cak akan raayin yarsa dan baiga alaman zata samu kwanciyan hankali a tattare dasu ba.

Duk yanda hankalin hakeem ya tashi ya shiga mummunan tsoro da tashin hankali sbd yana tsananin son fammah kaman rayuwarsa bayajin ma zai taba iya rayuwar jin dadi idan bada itaba amma kasa barin girmansa da zafinsa yayi ya zube dan kuwa bayajin shima zai bari ta shimfida masa sharadi ya hau sbd shine yake aurenta ba itace take aurensa ba,

Idan har ta zabi ta rabu dashi sbd auren daya fada mata baso yake ba to shikenan zai bata abinda take son dan kuwa a matsayinsa na cikakken namijin dayake shugaba a dagar yaqi mace bazata juya sa ba ga iyayensa sun roketa da kansu amma ko gezau.

Dagowa yayi ya kafeta da ido daidai nan Ammin cairo ta shigo palon itada SHAKUR babban danta wanda yake balaraben asali ta uwa data uba kaman Fammah din.

Gefen Fammah ya zauna cikeda kulawa ya kalleta yana mata larabci da turanci akan duka abinda yake faruwan sbd lawyer ne babba kuma shine zai zama cikakken lawyer dinta a komai daga yanzu.

Dagowa fammah din tayi da idanuwanta da sukai jajir ta kalli Shakur din tai masa kalma daya tak da labari ya dan gyada kai natse suna maida kallansu kan Alh babba dake magana alama ransa ya fara baci da hukuncin da abbu ya tsaya akai.

Hakeem kuwa da idanuwansa sukai mummunan jajir hatta jijiyoyin kansa sun fito yanayinsa yayi munin gani idanuwansa ya tsayar akan Shakur dake kusa da fammah wadda ta riga ta kafe babu abinda duk duniya yanzu dazai sauya raayinta dan kuwa koda son captain hakeem jeerah zai kasheta ta zabi hakan tafison ta mutu amma ta gama dashi har gaban abada.

Jeerahs basu taba sheda karfi da taurin zuciyar larabawa ba sai a yanxu dan kuwa wata irin zafi da bushewan da suka gani a tattare dasu ya saka lamarin komawa bacin rai da zafin kishin daya rufe idon hakeem sukai fada mara dadin daya sakasa ajiye mata takardar rabuwa da ita kaman yanda ta buqata.

Tsananin zafin juna da wata irin tsanar juna da jin har abada sun gama da juna suka rabu akai wanda iyayensu suma suka rabu akai tareda fizgewa da cire juna a zuciya da rayuwa kwata kwata.

Sun barin qasar suna dawowa da kwana shida aka dauka aurensa da sabuwar matarsa Fadeela.

Aurensa da fadeelan ya karbesa ne a yanzu da hannu bibbiyu sbd zafi da radadin fammah dan haka yake kokarin yin rayuwarsa hankali kwance,

A bangare daya kuma ga fatima da tashin hankalin duniya tana cikinsa na wannan rabuwar data gama sanin ba abu bace me gyaruwa sbd sanin halin Fammah da kakkaifan raayin da babu wanda ya isa ya sauya mata shi.

***Acan fammah kuwa rayuwar tsaya mata tayi cak da zallar baqin ciki da radadin datake jin kaman zai kasheta,
Ta tsani hakeem ta tsani danginsa ta tsani duk wani ahalin jeerah da Nigeria tsana me girman gaske da ita zata mutu tabar duniya,
Tsanar da batajin harta mutu xata dena musu,
Mutum uku ne a duniya dake Nigeria da kawai take kauna da sune kadai suke hana ta tsinewa nigeria da wanda suke cikinta a kowane dare da rana wato Raheem dinta da fatima da nasir.

Mahaifintane yayi waya da fatima ya sanar da ita komai ya kuma qara bata amanar Raheem dan itace uwarsa itace dangin uwarsa kuma itace idonsu da zuciyarsu akansa suma dan fammah bazata nemesa a yanxu kusa ba saita samu lafiyarta da zaa nema mata.

Wannan shine sabon rudanin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login